SADAUKI ☆☆☆
N@ B ALEEYU
77...
Oyoyo my baby girl muahh, Ajlal ce ke cira yarta sama tana dawowa da ita a farfamiyar gidan, cak ta tsaya ganin sadauki a gabanta duk ya rame yatara suma dayawa akanshi, se alokacin yasamu ganin Ajlal tsawon wata biyu kenan an hanashi shigowa gidan, yar shi yake kallo Mai kama dashi, dasauri tasa ikram a keken yara ta tura ta zuwa cikin gidan.
Sadauki yaci gaban ta yarike keken, kallon shi take cike da tsana bata samu damar furta kalma ko daya ba, yayi karfin halin cewa koda bazaki bari mugaisa ba kindai bani 'yata in ganta, sakar masa keken tayi ta juya Zata wuce
Yariko mata hannu ta baya, seda yagama kallon 'yarshi yamata addua Sannan ya kalli Ajlal yace ya sunan ta? Tsaki ta buga ta kwace hannunta tawuce tabar masa ikram, murmushi yayi Koba komai yau zai samu bacci yaga kyakkywar fuskar ta yadade rike da ikram yana mata wasa Sannan wata hadimar tazo ta bukaci da abata ikram Zata mata wanka.
Ba musu yabada ta wayarshi tasoma ring yaduba yaga Dan tanin ne kamar bazai daga ba Sekuma yadaga.
Yeh oga yaushe zaka dawo ne? Sadauki yayi guntun tsaki yace har yanzu Ba abunda yacanza wlh sunki bani matata Amma fah na ganta yfan, Dan tanin yace ga shawara mezai hana ka gayawa yayanta Aakil, Sadauki yace wow haka ne fah Zan kirasa inji kafunnan ka Kara rokar mun Mai martaba yazo Dan Allah, dan tanin yace Ina iya kar kokarina fah mai martaba yace idan nakara zancen zaisa a bulaleni.
Sundade suna tattaunawa da Aakil sunyi kan Gobe zaizo yola, ranar kam cike da farin ciki Sadauki yayi baccinshi yarshi kawai yake gani yar fara sol da ita,
Da yamma ya iso garin baibi takan kowa ya yawuce đakin ummynsa yadade tsaye a gurin yana tuna wasu abubuwan da suka shude fuskarshi tabb da kwallah yamata addua Sannan yashige bathroom.
Bayan sallan magrib ne yacanza kaya ya nufi fadar sarki yaci saa bakowa se liman kadai, sarki Abdul Azeez yayi matukar mamakin ganin Aakil a wannan lokacin yace wannan tafiya ba sanarwa Ina iyalin naka? Aakil yazauna tareda gaida Abban nasa Sannan yace Ni kadai nazo abba,
Sarki yace Toh lfy dai koh? Aakil yace eh Toh lfy ba lfy ba, jin haka yasa liman tashi yace seda safe, Aakil yace a'a zauna zaka taimaka akan abun,
Kan zancen Ajlal ne da mijinta Sam baidace kayi haka ba,
abba Karka manta sadaukarwa da yayi da rayuwarshi akanka dani kaina shine ya farfado da rayuwar masarautar nan Sannan duk ta sana dinmu ne hakan yafaru dashi bayan doguwar jin yar da yayi, liman ya karbe zancen da cewa Nima Abunda nagani kenan yaron bai cancanci hakan ba kodan rikon da uban Shi yayi muku, sarki Abdul Azeez yace naji banki takuba Amma Sam bazai yu inaji Ina gani a wulakanta mun ya ba insa kafa in shure, nan dai sukayi ta bashi baki har ya sauka daga fushinsa ya yarda kan cewa Ajlal tabi mijinta,
Kwana biyu Ana fama da Ajlal amma taki tabi mijinta ita kawai takardar saki take nema, a gaban Sadauki tace tafi son ta mutu ba Aure akan ta koma gidan Shi, Aakil yajata suka shiga bedroom Sun dau 30 mns daga baya suka fito tana sharar kwallah, Aakil ne yatayata hada kayanta tsab tayiwa mutanen gidan sallama, Sadauki kam yaki bari su hadu da sarki wani tsoron haduwa dashi yake.
A mota se janta da fira yake taki kula Shi daga karshe ma baccinta ma tayi har suka kusa isowa gari Sannan yatada ta, ikram ma baccinta take, wata yar karamar market yatsaya yamusu siyayya mai yawa, Ajlal dai sai kallon shi take, har suka so gidan Shi tafito bata Kula Shiba ya Karbi ikram suka shige ciki. Bayan sun yi wanka ta shirya ikram yadauko musu take away, ko kallon Shi batayiba ta haye gado tayi light off tabarshi a gurin Zaune.
Dasafe ma haka tamasa tin da asubah ta gyara ko ina tahada musu breakfast tashige dakinta tarufe kofa, ba yanda baiyiba yaganta Amma taki Bari suhadu har yagaji yafita, direct gurin mama ya nufa ya mata albishir cewa yadawo da Ajlal gidanshi......
Tic-Tac-Toe | ||
+ | + | + |
+ | + | + |
+ | + | + |
New Game |
Ya dau dadi aci gaba thank's