Hausa novels sokoto Whatsapp 07068808039 FULANIN DAJIN@ B aleeyu page 1Joda! Joda! Joda! Wai kina ina neh haka Iye (anani) kinajinagwaggo ina zuwa , Bankara she kwalliyar ba kinsan yau ance Yan bunni sunzo gwara muyi kwalliya da kyau,gwaggo tace ke bana San shirme kizo kose dawon yayi karfi, tindazu kina abu guda , seda takare ranbade2 denta sannan tafito, kungan joda kuwa yarinya har yarinya amma ta bata fuskarta da Jan baki da bakin kwalli ko ina digagga ne afuskarta rigarta da zaninta iri daya Dan kwalinta kuwa na irin tsofaffin nan neRike da qugu tafito tana daga gira sama, gwaggo dubeni nayi kyau, gwaggo tace wlh da kina jin zancena dakin koma kingoge wannan haukar, buga kafarta tayi kasa ni wlh baxan goge ba, so kike Su hansai Su cemun bakauya, Gashi Yan bunni zasuzoGwaggo tayi murmushi shikenan zoki wuce, gyalenta tadauko tasha damara sosai, Yan kirgan Dan ginta suka Dan fito, gwaggo ta dora mata kwaryar dawo da nono akai, tana kara jamata kunne, banda shiririta fah,har takai kofa sekuma naga Tajuyo tanakallan gwaggo duk tabata fuska , sanin abunda take nufi yasa gwaggo yin murmushi to allah ya kiyaye hanya yakare mun ke yamaidoki lfy, murmushin itama tayi ko kefa gwaggo daso kike inje can infada kogin kada, Hava autare ya daya tamkar da dubu gudaliya, yar fillo yarinya se mai rakumi koh, bushewa tayi da dariya aikodai gwaggo inyita hawa abuna koh, gwaggotace sosaima kuwa kedai jeki maraice nayi,Tana fita gwaggo tasa dariya inbahaka nayi mata ba, bazata sa yadda dawon ba gurin wasa zataje, sallama akayi, dasauri tamike tana sannu dazuwa sannu da zuwa mai gida, hakin tasaukemasa akansa, takarbi karan dake hannunsa ta ajiye,Shimfida tamasa takawo masa fura mai sanyi taji nono, yasha ya koshi Alhamdulillah shine abunda naji yafada,(a kullum kada mu manta da hamdala ga ubangiji a duk lokacin da muka samu wata biyan bukata)Kallanta Yayi allah Yayi miki albarka , dukadda kanta tayi kasa tana cewa ameen kaima allah yasaka maka da gidan aljanna mafificiya, ameenIna joda taje, gwaggo tace ta tafi gurin talla, Yace Ince dai ko kin jamata kunnekada taje gurin Jan fada asace dawon tinda kullum seta batareda kudi, gwaggo tace to yazanyi da ita se addua,baffa yace to allah yashirya mana ita ameenFULANIN DAJIN@ B aleeyu page 2Tafe suke itada hansai se rangwada suke, wai Su Yan mata ne, Duk wadda suka hadu da ita se sunbushe mata da dariya, Su aganinsu sunfi kowa haduwaHansai kawar joda ce atare aka haifesukwana biyu ne tsakanin joda da hansai, an haifi joda jumu'a aka haifi hansai lahadi, Atare suka taso dayake makwabtane sedai mahaifin hansai yarasu daga baya yayansa ya auri uwar hansai din kasancewar sun rabu da tashi matar"Wannan kenan "Dai dai kasuwa suka tsaya suna waige2kozasuga wanda yazauna musu guri, babu kuwa hakan yabasu damar zarcewa gurin Su, arunfar mai shayi kenan, koshi mai runfar bai isa yahanasu gurin baHansai ta fidda shinkafa da wake , joda kuwa tasauke, kwaryar akasa tafara damawa habu mai shayi, coz tasan wajibine kullum seya sha furar ta, hansai kuwa harta zuba masa shinkafarkamun yagama Ci, joda tagama dama masa fura da nonoAsslamu alaikum sukaji ance da bakuwar, murya habu mai shayi shine ya amsa, hansai da joda kuwa sun mutu gurin kallan sa, wannan Dan bunnin kamar aljani,Am not aljan am also man, haka sukaji anfada se a lokacin tagane ashe afili take zancen, kunya ta lullubeta dasauri tarufe fuskarta da mayafinta , murmushi Yayi ahhh ashe kinsan kunya,adamamun fura da nono asaka sikari amma, kasa amsawa tayi se hansai ce tanawa,Zare ido Yayi yace bansan kota nawa zance ba, adamamun kawai wadda zata isheni, se a lokacin tayi magana to ay bamusan cikinka ba, murmushi Yayi tokidama mun dai2 cikinki,Dago idonta tayi tadora masa to kuma kasan ciki nane, ayku Yan bunni bakwa cin abinci dayawa, dariya yadiga yi harda hawaye yana rike ciki, injiwa ayko wa da nasa personality din , nidai kawai kidama mun dai2 cikinki dts oll,Dawo biyar naga tadakko ta zuba cup din, tafara damawa, kallanta yake yadda take aiki komai atsabtace, take yinsa, seda tagama sannan tazuba sugar ta naira goma tasaka masa ludayiaciki bayan ta sake dauraye shi,Sha yake se zuba santi yake, yana fadan duk sokoto babu mai irin wannanfurar, joda kuwa se dariya take zubawa ita da hansai, kadan2 yake shan furar wai bayaso takare, kafun nan har sun sayadda kayansuMikewa yayi yana karkade wandonsa dabadan karkice nayi santi ba danace, waiko da tsaba kuke wannan furar, aikuwa yade bowa kansa dariya haka Suka Dunkule Su biyu suna ta dariyaTin yana biye musu har yafara tsorata Anya kuwa wadannan yaran lafiyarsu, habu mai shayi yace dena mamaki indai Su hansai ne wlh se sufi awa sunadariya bakomai bane agaresuIdo yazaro yace toh , ungo kudinki nikam tafiya zanyi dari biyar yamiko mata, ta ware ido, yo ay ko duka dawonna dari ukku ne balanta wanda kasha kaga kudinka hamsin da biyar ne fah, dariya yayi hava dai ace duk wannan dadin gashi cikina yayi dam ace 55 naira kawai kinga naji dadin furar kije kawai nabaki canjin yajuya abun saSaurin shan gabansa tayi, tana rufamun asiri wlh gwaggo tahanani yin juye ma balantana wannan kudin ni kabada naira hamsin nayafe biyar din FULANIN DAJIN@ B aleeyu page 3Yace to kinga tsaya ni banda canji ko dari biyu banida , joda tace to ka tsaya habu yamana canji, batajira cewarsaba, taje tabawa habu kudin yayo musu chanji, seda takirqa Su cib sun cika sannan tacire kudinsa takaimasa ragowar,Kudin yake bi da kallo duk Yan biyar biyar ne se goma goma can yahango hamsin guda, cike da kyama yace miyewannan haka, joda tabude baki Au idonka baya gani ne kudinka ne mana , murmushi Yayi kinga kirabawa almajiraini baxan iya taba wadannan kudin ba, kema idan kinje gida kiwanke hannunki da sabulu yana kai nan yajuya yawuce yabar joda rike da kudinHansai takaraso tana tanbayar ta lfy nan take gayamata yadda sukayi dashi, hansai ta washe baki Iye daga allah yabamu allah kizo muci kashin bature (chocolate )Joda tace ke Dallah je can mai shegen kwadayi muka sani ko mubace idan muka Ci kudin , hansai ta ware ido hakane fah, Kinga muyi Gina muzuba kudin kawai, joda tace haka za'ayi ni har wadannan ma zubarwa zanyi,Haka kuwa akayi sukayi gina dai2 wani dutse suka binne kudin, kowannensu tsoro yakamata, addua kawai suke har Suka kai gida,Mahmud kuwa yana isa titi yatare Dan achaba se masaukinsu , yana isa yatarda dakinsu abude hakan yatabbar masa da cewa Ahmed na dakin, sallama yayi tareda cire talkaminsaAhmed ko kallansa baiyiba, yafada kan gadon yace man waya tabamun kai, Ahmed yaballa masa harara, zaiyi wata magana Ahmed yadaga masa hannu don't tell me anything,Mahmud yaji haushin abun amma kumaseya basar , tashi yayi yabude fridge yadauko masa eviron drink , ya zuba a cup yabasa, Ahmed baiyi wata2 ba yakarba yadinga sha gani nai kawai ya ajiye cup din, Mahmud yakallesa are you Okey?Yeah am ok, nikam mamaki ya cikani ace duk fushin dayayi yanxu babu shi, ko miye dalili oho, Mahmud yayi gyaran murya yace my man kaci abunci kuwa ?Ahmed yabisa da harara naci wanda ka kawo mun , dariya Mahmud yayi kaifa kace inje bazaka iya cin abuncin Yan kauye ba, so ni nasha furata mai dadi allah baka ganiba taji no.........shiru Yayi ganin yadda Ahmed yadafe bakinsa da hannushi , dasauri ya tashi yashiga toilet ya zubadda yawu,Mahmud kuwa laptop dinsa yajanyo yashiga danne2 abunsa, bayan kamar minti ashirin, Ahmed yace Kainifa yunwa nakeji wlh, Mahmud ya hararesa mezan maka yanxu ? Ahmed yace bansaniba afusace, Mahmud yayi tsaki allah ya gyara maka zuciyarka Dan wlh kana cikin uquba, yakarashe zancen cikin fushiAhmed kuwa yajanyo bag dinsa yafiddochocolate cornflakes yahada da madara yasha a karamun cup, yazo yayialwala yatada sallah abunsa, Mahmud yagirgiza kai cike da takaici aransa yace zanga randa Ahmed zai gyara behaviours dinsa, yanxu yana nufin masallacin ma bazai jeba sedai yayi sallah gidaBara muleka joda"Tana shiga gida da sallamar ta, baffanta ya amsa, Dagudu taje tafada jikinsa tana (inballi jam baffa ) ina wuni baffa " ya amsa mata lfy lau yar baffa, ya kasuwa, lfy lau baffana, baffa zanyi sallah, Yace to joda kiyi sallar kwarai, ana bukatar natsuwa da ikhlasi azuciyarki, ki qudurta aranki kamar kinaganin allah ne gaki gashi kitsarkake zuciyarki kinji yata, murmushi tayi nagode baffa, zanyi yanda kaceTagama sallah taje kitchen dinsu tadakko abuncin ta taci tasha sabon nono madara kenan, kayan jikinta taciretasaka nazaman gida, lekawa tayi taga bakowa awaje, tasaka talkaminta a hammata takwashe wandonta Sadaf2 take tafiya har takai kofa, anan taballa da guduCarab sukayi kabra da hansai itama ta tsero, rike hannunta tayi suka balbala da gudu se dandali, Koda sukaje har anfara kida, dama su barawa suke ba, Sedai suyi kallo sudinga tsegumin wasuMai fura taji anfada, dasauri Tajuyo dazummar fada domin ta tsani acemata mai fura, wazata gani Dan bunni ne nadazu lah kaine tafada tana murmushi mekazo yi nan? ke mekika zoyi nan?Wata yar Dariya tayi kallo mukazo yi mana, Yace kodai rawa kika zoyi, tace a'a wlh tadukadda kanta kasa, yayi dariya yayi fulanin usuli ansanku da kunya koh, hansai ta matso, Lah Dan bunni ne, Yace ke badan bunni sunana ba, sunana Mahmud, Mey? Joda ta tanbaya, yes it's my name , joda tarufe baki tab, Mahmud yace lfy kuwa, hansaitace sunan baffanta ne, hhhh ya aza dariya daga yau baba kohJoda tace waima baba, Mahmud yace Au ban haifekiba, ta gwaguda baki kaima kasani ai, yayi dariya yace to yaya, tace da dai yafi kam........Muje zuwaASEEYAH BASHEER ALEEYU9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫:FULANIN DAJIN@ B aleeyu page 4Yau alhamis ba'a zuwa makaranta, yaukuma Ranar da baffa yake zuwa dajise dare yake dawowa saboda kiyo shanun sa dayake dakuma gonakinsaJoda ta shirya cikin kayan Su na fillo tasaka riga iya cibiyarta takawo zani ta daura tarufe cikinta sedan wani abu akan ta fuskarta cike da kwalliyar haukaanyo mata kitson nan na fulani manya2 tazuboshi ko ina baya da gabaGwaggo awalijam ( ina kwana kenan ) ta amsa lfy lau auta kintashi lfy, joda tace lfy lau, gwaggo natafi, daji, gwaggotace to yata allah ya kiyaye mun ke daga kowane mugun kwaro, joda Dan allah banda shiga ruwa kinajina,Ta gyada kai to gwaggo insha allah lfy lau zan dawo baxan shiga ruwa ba in tsoron kogin kada, za gayawa tayi baya takoro shanunta biyar tika2 dasu gwanin sha'awa,Kofar gidansu hansai ta tsaya ta tada mabusarta ta fulani tana busawa, hansai dake saka talkaminta tace ina zuwa joda Bara nasha nono, joda tayi tsaki kya sameni ahanyaHansai tamaza tasha nonon taka do shanun ta, ukku suka biyo hanya kowacce da bulalarta suna dukan shanun Su idan sunbi hanyar da badai dai ba, hansai tace allah yasa muga Dan bunni joda, joda tace mezai kai shidaji, tinda ba ma kiyayi neba , ahaka suke tafe suna fira har Suka kai daji,Kowacce tabi tata hanya inuwar mangwaro joda tasamu tazauna, tafiddo furar ta tafara sha ' can kuma taajiye, tadauko mabusar ta tafara busawa,Zaune yake bakin rafi yana sha kar iskan dake kadawa, yazanyo jacket dinshi yasaka busa yakeji natashi irin tafulani, idonsa ya lumshe rabensa dayaji wannan busar tin mahaifiyarsa nada rai idan sunje kauyensu wato ba'are,Haka yacigaba da sauraren busar can kuma yadaina jin busar, ba afi minti goma ba yasake jin wata daban tamkar irin busar meminsa dasauri yamike tsaye yana bin gurin da yakejin busar har yakai wani guri!Ba yanata kawai yake hangowa cikin kayan fulani yana kallan yadda take juya kanta ahankali tana busar, ko shakka babu wannan cikakkiyar fulani ce yajuya kenan yaji muryar ta nacewa hansai kizo mu zaga, hansai tace to bara nasha nono, Duk wannan zancen cikin harshen fulatanci suke yinsa,Ganin suna kokarin juyowa yasa yamaza yalabe jikin wani iccen tsamiya,suna wucewa Yakoma mazunin sa, yadauko wayarsa yana daukar guraren da photoFULANIN DAJIN@ B aleeyu page 5Se guraren la'asar suka koma gida, jodatacire kayanta tashiga aykinta wato bacci, gwaggo tashigo kawomata abunci ta ganta aleme tana bacci tace oh ni ma'u ko sai yaushe yarinyar nan zatayi hankali oho, Mahmud yacewa Ahmed, ni man banganeba se yaushe zamu fara training din nan yaufa kawanan mu 3 , Ahmed yakallesa se randa kasaka tym, Mahmud yace oh dama ni kake jira ne, Ahmed yace of course, batareda yadago kansa ba Mahmud yace shikenan kobe za'a fara fita aiki, Ahmedyace okYauma kamar kullum Mahmud yazo shan fura zuwa yanzu har sun Dan sabasedai sun kasa sakin jikinsu dashi,sosai, shima dai yafahimci hakan saboda haka yashiga yin wasa dasu yana basu labarin sa,tagama dama masa furar sa, setaga yadauko wani Farin dutse a leda tace lah miye wannan zaka saka yace kankara ce sanyi zatayi, hava ta wangale baki tana kallo, ba afi minti ukku ba kan karar ta narke, Yace ungo shakiji yadda tayi tuni tasadda kai kasa, murmushi Yayi to sarkin kunya, bani roba sena zuba miki,Da sauri tace a'a kabarshi, Yace kinga koh wlh zanmiki kuka idan baki shaba, joda tace kuka kuma Dan allah kayi hakuri wlh bazan iya shan wani abu a kasuwa ba, murmushi Yayi to shikenan na fahimcekiKullum haka yake bata dari biyar yace tarabawa almajirai ragowar, ita kuma bata fasa zubasu aramen ba, sanin halin hansai yasa ta canza gurin zuba kudin, setabar nafarkon acan, hansai zata iya dauko Su tace zata Ci biscuit kowani abuGwaggo tasaka joda agaba tana fada seta gayamata inda take saka mata kudi kullum se ta batarda 55 naira , joda kuwa se kuka take domin idan da abunda ta tsana bai wuce fada ba, gwaggo abun yakara fusata ta tadauko murfin kwano ta kwadawa, joda zaki yimun shiru kose na karyeki, atake ta hadiye kukan sanin halin gwaggo, Gwaggo tayi Kiran hansai ta ginarsu dasuke magana da uwar hansai, tace larai Dan allah kituromin hansai, larai tace gata tana jinki, hansai duk ta tsoro ta bcoz taji duk fadan da ake yiwa jodaTa shigo gidan se makale take da ganinta kaga marar gaskiya, gwaggo tace zonan munafukan banza , hansai tazo tazauna kusaga joda, Gwaggo tace kigayamun gaskiya me joda keci da kudina kullum setace ba hamsin da biyar?Joda ta kwance hansai tuni hansai tagane nufina tace wlh in....In...da..dama.....gwaggo takwa damata murfin itama akanta, tuni itamatasaka kuka in in me kike fada dagani bakuda gaskiyaSeda Suka gama kukansu sannan kowacce takama gabanta, joda cike da tsoro tafita talla yau kam ba fira har Suka kai bakin kasuwa, suka zauna, anan gurin suka taradda Mahmud zaune yana jiransuMurmushi Yayi musu sannunku da zuwa kanwata, yasauke musu kayan, oya kiyi sauri kanwata yunwa nakeji, joda takalli hansai, hansai ta kalli joda, joda tafara in in kayi hakuri yau tin gida wani yasaye furar, yanxu babu ta sayarwaWhat? Yafada yanzu kina nufin baxan sha furar nan ba, ehh kayi hakuri, Mahmud yace bazai yuba kota waye kice yayanki yasha ay nima kudi zan biya , bai jira amsartaba yabude ledar yaciro dawo biyar yazuba a roba yace oya zuba mun nono ni bansan yakike ba......Shiru Yayi ganin tana kuka, oh shiit yafada, yanzu kanwata dan na dauka shine abun kuka ungo na maida yabudeledar yazuba mata dawon yakalleta yaciro handkerchief yabata, rikewa tayi Dan batasan abunda zatayi dashiba,Kishare hawayen ki mana, Nibansan abun zai bata miki rai ba ayda bazan dauka ba, se anjimaFULANIN DAJIN@ B aleeyu page 6Joda ta tashi dasauri tariko wandonsa, yaya Dan allah kayi hakuri wlh banso ranka yabaci ba, dagota yayi yasa hannunsa yagoge mata hawaye don't worry my 6 bana fushi kingane, daga kaitayi alamar ehhHaka yawuce aranta bataji dadiba, har Suka bar kasuwar yau babu wanda sukayiwa dariya, habu nata mamakin yauko lfy gashi yaga ko Dan bunni bata damawa fura ba yaso ya tambaya amma sanin halinsu yasa yaja bakinsa yayi shirucike da zumudi takai gida tadire kwaryar ajikin gwaggo, Gwaggo tace daganin kina saurin bani kudin kinsan kinyi abun kirki wato dama dagan gan kike batarwa, joda dai ba tace komai base yar dariyar da takeJoda! Joda! Joda! gwaggo tace wai lafiyar joda kuwa Bara naduba, Koda tasameta adaki, Dunkule cikin bargo tana rawar dari, subhanallah joda bakida lfy ne? Tana kai hannunta ajikin joda tamaza ta dauke saboda zafin data jiyaDagota tayi tana joda meke damunki sneezing dinda tafara yi da Tari yasa gwaggo yin shiru har tagama gwaggo tace sannu koh dkyar ta iya daga kanta,gwaggo tace inazuwa tashimfidar da ita tayiDakin baffa tashiga tadauko danyar citta da yaji da kaninfari se lipton irin nasu na fulanin daji, dama akwai wuta tadora tukunya ta aza mata, suna yin boiling tasauke suka Dan sha iska sannan ta juye a karamin cup takai mataUngo joda shanye kibani cup, joda cike da haushi ta shanye ganyen, gwaggo tace yauwa, sora alhini kiyi tadauko wani abu kamar tiger tazuba acikin boket da ruwan zafi, ta kwabe wa joda kayanta daga ita se pantBlanket tasaka tarufeta dashi hayakin dayajin suka dinga ratsa ta har ruwan yahuce sannan gwggaggo tadauko mata wasu kayan tasaka mata tarufe ta da bargo, taje tadauko kasko da garwashi aciki ta ajiye mata gefe inda tasan bazata shure ba,Hansai tazo biyawa joda suje talla , gwggaggo ta sanadda ita joda ba lfy, tace gwaggo meke damunta, gwaggo tace yo hansai ai ta tsuniyar gizo bata wuce ta koki, hansai tace oh ni husainatu ko se yaushe wannan shegiyar murar zata sakemun yar uwa,Gwaggo tace mura kam ai sedai ta mutu da ita Dan tagado ce tin kaka da kakani ansan fulani da mura balantana ma mu damuke fulanin daji, hansai taceto kenan yau bazuwa talla koh?Gwaggo tace aikodai babu, hansai tacea'a gwaggo yanzu yadda za'ayi ki kawo dawon se nasamu yaro basa nera goma yakai mun kasuwa, gwaggo tace ba ayi haka ba ya zakiyi da sana'a biyu wazai dama miki furar wazai sayadda shinkafar, hansai tace to ai zuba shinkafa ba wuya , kawai ki kawo gwaggo bazan bari kiyi asara ba, Duk yadda gwaggo taso tabar shi amma firrr hansai tace zancen ba , dole gwaggo tabata dawonA runfar mai shayi tayada zango, habu yace hansai lfy yau ina yar fillo, hansai tace wlh batajin dadi ne, habu yace ayya ki gaida ita Dan allah ba komai zatajiMahmud yazo yazauna tareda sallamarshi, hansai takarba seda yayi Jim kadansannan ya tambaya , cewa ko ina joda yau, hansai tace batajin dadi ne , meke damunta Mahmud ya tanbaya? Hansai tace mura ce , ayya kozaki kaini gidanku in dubata, Mey? Hansai ta tanbaya, Mahmud yace cewa nayi ki kaini gidanku in dubata,Hansai tace kayi hakuri wlh za'a mun fada, Mahmud yace fadan me kuma? Hansai tace kaga mufa ko makwabcin mu ba abari muyi fira dashi, Mahmud yace to nifira nace zanyi dake gidanku nace ki kaini induba yar uwarkiHansai tace naji babana zaice a ina nasanka kuma ya hanani kula maza sena girma, dafe kansa Yayi ganin yayi gabas tayi yamma, Duk yadda yaso ta fahimta takasa hakan yasa yakyaleta, badan yasoba yau ko furar bai sha ba yayi wucewarsa......... FULANIN DAJIN@ B aleeyu page 7Kwanan joda 3 tana famada zazzbin mura, hansai kuwa tacigaba da fita da fura, haka Mahmud yake zuwa gurin kullum Yayi mita har yagaji akan hansaitakaishi gidansu joda amma taki dole yahakuraJoda an warware yau tafito tallah duk tarame se laudi take kamar taliya, dama can haka take kamar zata karye, tafe suke suna firar yadda hansai ke gudanarda sana'arta biyu lokaci guda fura da shinkafa kenan,Hansai tace ke bafa wani wahala , jodatace nagode hansai allah yasaka miki, hansai tace kinyi fa haramun, joda tace menayi kuma na haram? Hansai tace godiyarki mana, joda tace to Dan nayi miki godiya shine haram, hansai tace sosaima kuwa yaushe zaki godemun akan abunda yake wajibi akaina , idan banmiki wazai miki, Miye amfanin abotar mu idan ban taimaka miki ba musamman wannan lokacin dakikafi bukatar taimakon,Joda tace hakika ke qawa ta gari ce, bakowace kawa zata gane hakan ba , allah yarbamu tare ameen yarabbi,Mahmud yayi tagumi yana kallan joda, kanwata kinrame dayawa fa, murmushitayi tasadda kai kasa, to sarkin kunya zaki fara koh, hansai tace aifa inaga wannan kunyar tata ita zata bata wahala nan gaba, dariya Mahmud yadinga yi, yana mamakin irin yadda suke zance kamar wasu manya, yaran dabasu wuce 13 years ba,Yau kam yasha fura kusan ta dari, sannan aka dama masa wata yatafi da ita, hansai tacewa joda, joda inagafa Mutumin nan bashida aibu , saboda haka mukaima gwaggo kudin nan inba hakaba wlh zata kidemu tamkar ganga, joda tace so kike gwaggon tawa ta bace ai wlh gwara tadakeni data bace kinaga Yan bunni da akace basa cin abuncin irin namu, amma shi wannan kullum seyasha furata, kofa shi babuHansai tace to wlh baruwana idan gwaggo ta dakeki ni zance bansaniba kona gayamata gaskiya, joda tace kadakimun haka hansai, hansai bata saurareta ba tayi wucewartaJoda kuwa nazuwa gida ta ajiye kwaryar bakin kofar dakin gwaggo tasaka kudin aciki, tashige dakinta tanakuka sanin hukuncin ta, gwaggo nafitowa dakinta taci karo da kwarya bismillahi shine abunda tafada, joda! joda! Tashiga kwala mata kira, lfy kika ajiye mun kwarya a kofa kadan takadani, mtsss yanzu haka fitsari yakorota shine tayadda kwaryar ananAdakinta tasameta ke bani ragowar kudin in baki ki auno mana dawa yau tuwo zamuyi dumm dumm taji gabanta yafadi , a rude tace gwaggo wlh muna gudu suka zube ahanya, gwaggo tace Mey? Wlh karya kike kwanan hansai ukku tana fita da furar nan amma bata taba batarda ko sisi ba seke koh, wlh yau kasheki zanyi, jin zancen gwaggo kuma tasan halinta zata iya zaneta tsab, yasa tafara kuka da karfi, gwaggokuwa tafita neman bulalaJin kukan joda yasa hansai fita aguje har tana tuntube , tana isa tafara Kiran gwaggo gwaggo tsaya nafada miki gaskiya, gwaggo tace oh dama kunsan abunda kukeyi dasu kenan, Hansai tacewlh gwaggo bakashewa muke, gwaggo tace to uwarme kuke Ci dasu, Nan hansai ta warware wa gwaggo komaiGwaggo kam ta tsorata ainun tace aiko in haka ne kin dena tallar gabadai, bazan yarda kije ya salwantar mun dakeba, joda tafito daga daki tarungume gwaggo tana kuka, gwaggo tace kiyi hakuri yata ai dakin gayamun bazan dakeki tun farko ba, kiyi hakuri kinji bamazaki sake zuwa ba kinji koh, tagyada kai, hansai tace dajin ja a dakeki abanza se tsoron duka amma ba.....bata karasaba joda ta jefamata Dan kwalinta, to kinfada kinji dadiFULANIN DAJIN@ B aleeyu page 8Sanin tanbaya da Mahmud zai mata yasa tacanza gurin zama dukda cike take da kewar joda,Mahmud kuwa yazo gurin yayi taji ra yaji shiru gashi yau habu mai shayi bai fito ba, dole yahakura Yakoma gida cikeda takaici ga yunwar dake da munsaJoda sundawo daga makarantar allo tana rike da allonta da sauran littattafan ta, hansai tace joda Dan allahmubiya kogin kada muga wasar alkuku, joda Ta ware ido Mey? Wlh kyaje ke kadai nikam ba inda zanje kada yacinyeni, hansai tabata fuska kefa shegen tsoro ne dake daga kallo mezai kaimu aciki ne, Kinga tafiyata inbaki zuwa,Joda ganin ran kawarta yabaci yasa tace to muje nidai amma wlh bazamu dadeba kinsan yau baffa na gida, hansai tawa she baki ai bazamu dade ba yanzu zamu dawoSuna isa bakin kogin suka samu gefe guda saman dutse suka rakube suna kallan wasa, joda se juye juye take, ita duk tsoro takeji ga gurin da shegen sanyi , ita bawani kayan kirki tasaka ba, kayan fulani ne ajikinta ko mayafi babu tini tafara rawar dari, Nan danan tafara sneez, takalli hansai taga ita ko ajikinta,tace hansai mubar nan gurin allah gabana kefaduwa kuma kinga munyi nesa da masu wasar nan kada majici yazo, hansai tace aike illata dake shegen tsoron tsiya ne dake wlh, joda tace nidai natafi sanyi nakeji,Dole hansai ta tashi tabita suka bi hanya koda suka zaga maza suncika gurin, dole suka koma bin hanyar baya inda babu taron mutane tafe suke joda na rawar dari hakoranta se bugun juna suke,Hansai ce gaba joda baya, Wata hanya suka bullah mai shegen duwatsu manya2 dasu, hansai tace lah kinga joda daga munbi can se dajin damuke kiyo, aiko ma wannan tafi sauri wlh, joda dai ba tace komai ba se biyar ta take, can taji ta taka tasaya tace hansaina taka kaya fa zoki cire mun, hansai tazo tace kai yabakiyi kuka ba kayar babba cefa kuma ta shugeki , joda tayi tsaki dallah kici remun in zaki iyaHansai taja dakarfi , Wata guguwa ta taso gurin kura tacika musu ido iska yadauki hansai sekan dutse kanta yabugu, joda kuwa mulmula tadinga yi hartakai gab da wani icce tarike shi gam tana, wayyo allah na kutaimakeni, hansai kuwa tana tasaki tasaka kuka dab bataga joda ba, can tadinga jin ihunta, dasauri taleka taga joda gab da ruwa ga kada can a gefe se bude baki take, tuni itama tasaka ihuAhmed dake gefen ruwan yana kallan Su duk haushi yacika shi, to inba iskanci ba meyakawo mata a kogin gurin da maza ke zuwa, abun haushi mayadda suka cika gurin da ihu , karar da aka saki sakice yadawo dashi daga tunanin dayake dubawa da zaiyi ne yaga har tafada ruwan itakuma waccan mahaukaciyar se hauka take, acewarsa itakuma hansai ganin kada tayo kan joda babu ko tantama cinyeta zatayiDogon Tsaki yaja ganin irin ihun dasuke domin idan da abunda ya tsana baiwuce hayaniya ba musamman ma na mace ,kai mata jakai ne wlh mtssss ,, , , nikuma asea nace harda uwarkaGun naga yajanyo a aljihun rigarsa , yasaita dai2 kadar yahalba toni gurin yadau wani irin ruri nikaina seda na tsorata irin yadda kadar ke fitar da iska tareda wani ruri kamar ana kidan gangasekuma ta tarwatse lokaci gudaJacket dinshi yacire, yafada ruwan kai lallai Ahmed ya iya ruwa nibanma gansa ba yanutse a ruwan se can nahangosa yadauko joda tamkar gawa, sekuma yasake nutsewa, nemansa nake wai sai gashi agabana har yafito rungume da ita fuskarta acikin kirjinsa duk ta dungule da alama tasuma dakyar ya ban bareta ajikinsa duk ta San kare tsaki yasaki ganin duk tabata masa farar riga da shegen Jan bakin ta jacket dinshi yadauko yasaka matayajuya zai wuce kenan yaji kamar anrikemasa hannu juyowar da zaiyi yaga ashesarkar dake kan kunkurunta ce tasarkeshi janta yayi dakarki base gata tawatse ba , haushi duk yakama shi yawuce yadauko wayarsa da glass dinsa yawuce abunsaHansai taleka taga yabace tafito dagudu tazaga ya gurin da ya ajiye joda,ta aza kunneta kan cikinta taji tana Dan sheda kadan2, Alhamdulillah tace, sekuma ta tashi dagudu bata tsaya ko inaba se bakin kasuwa ta taro mai jaki , suka aza joda saman jakin suka yi gida da ita,Suna isa kofar gidan tace ma jakin yashiga, gwaggo na surfen dawa taji kamar takun dabba dagowar dazatayi ne taga joda ajikin jaki, ai batasan randa tasaki tabarya ba tana subhanallah lfy hansai meya sameta, hansai tace gwaggo sauketa ,gwaggo tasauketa takai ta daki hansai tace gwaggo bani nera ashirin in bashi , gwaggo ta kwance zaninta tabata, hansai tamika masa yayi godiya yawuce.......FULANIN DAJIN@ B aleeyu 9 pageGwaggo tace hansai nifa banganeba meya sameta ne dubi yanda naganta duk gashin jikinta atashe gashi gabantase faduwa yake kamar ma a some take,meyasameta naga jikinta duk ruwa ne kasan kafarta jini ??????Hansai tafashe da kuka gwaggo tajanyota har tayi shiru sannan tagaya ma gwaggo abunda yafaru, takara dacewa ni dama ina tsoron wannan yaron Mahmud daganinsa bayahude ne,gwaggo kinga yadda yabidda bunduga (bindina) ya kashe kadar nan kwarankwatsa idan kikaji yanda tayi wani gurnani, gwaggo tace aikuwa duk dajin nan ba inda ba'aji ba,Hansai tace kinsanme gwaggo wlh yanda yayi tsallen kwado yafada ruwa shike bani mamaki nutsewa fa yake a cikin ruwan tamkar kifi , gwaggo tasa dariya, tace nidai allah Yayi muku tsari da wannan bayahuden yaron ameenGwaggo tacanza ma joda tufafi ta hada mata ruwan wanka tareda ganyayyaki aciki tagasata sosai sannan kuma ta saka garwashi adakin, hansai taki komawa gida gefen kadon karan joda tazauna tana ta addua allah yasa kar murar joda ta tashi,Joda ta warware sedai yar mura dake damunta gakuma yawan firgita datake yi data kwanta seta tuno wannan Ahmed din bakomai take tunawa ba irinyadda Yayi tsalle kamar aljani yanzu ko zata rufe idonta idan taga hakanHansai kam tadena fita tallah acewarta tsoron take tahadu da makashin nan, Mahmud yayi sintiri har yagaji baigansu ba, dole yahakura, Gashi sunkusa komawa tinda dama 2weeks ne zasuyi yanzu sunyi kwana gomaAhmed kuwa yana zuwa gida yacire kayan jikinsa ya shanya Su wanka yasake yi yafi awa yana darzar jikinsa acewarsa yatabi najasa, domin kauyawa nazajasa ne agurinsa musamman ma wadannan na daji gwanda kauyawa da Su,Mahmud dai yagaji da sintirin gurin yatanbayi mai shayi koya San gidan Su joda, mai shayi yayo masa kwtancen dukda baiganeba yace yagode, yabi hanyar gidan yana tanbaya abun mamaki duk Wanda ya hadu dashi se yaga suna guduwa, shi azatonsa duk kauyancinneNanko baisan kayan dake jikinsa suke tsoro ba, wato soldiers uniform dinshi, dayake ma farar riga yasaka wandon nekadai na soldiers se hula, hansai yahango, wani farinciki yaji ya lullubesa yakarasa kanta yana cemata to gani a gidanku ay gidanku ba zaiyi wuyar ganewa ba tinda duka dajin nan ba kuyi 5 hundred ba,Hansai tace Dan allah kada ka kasheni wlh banmaka komai ba, Shiru Yayi yana kallanta da mamaki in kasheki mekika yimun ko ance muki ni makashi ne,Hansai tace nidai Dan allah kada harbeni kamar yanda ka harbi kadar nanajiya, Mahmud yace wai mafarki kike kome kinga inane gidansu joda , tace wlh baxan nuna maba ka kasheta ay nasan ji yama ita kaso kashewa seka harbi kada wato kaga munki cin kudinka mubace koh mugu kawaiAna haka Sega baffa yadawo dauke da kara yace hansai lfy naga kinyi narai2 da ido, ta nuna masa Mahmud, atake yace innalillahi wa inna ilaihir rajiun, yaro lfy meya kawo mana makashi ananMahmud ya mai mata makashi kuma? Se alokacin yatuna kayan dake jikinsa, Yace I'm so sorry dady, baffa yace ce maka akayi munajin wannan yaren nakuna ya hudu da nasara,Mahmud yasosa kai yi hakuri baba, yanzu duk ba wannan ba naxo duba joda ne inji ko lfy kwana biyu nadena ganinta kasuwa, baffa yace ai kafi kowasanin halinda take ciki kazo kuma yanzu kana tanbayar mu,Kaga mungode da taimakon da kayi mata Dan girman allah kayi tafi yarka, muba muyi yi muku komai ba kinzo kinawani zanse can nadaban, se a lokacin Mahmud yalura da yadda suke duminsu, abun ma seya bashi dariyaGanin yadda Mahmud ke dariya yasa baba yin maza yasaka hansai cikin gidan yarufe ganbun........Muje zuwaASEEYAH BASHEER ALEEYU9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫:馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�Ahmed mura yakama shi sosai har ba'a jin zancen sa, sneez yake tamkar bunsuru 馃槀 , ga zazzabi yarufesa sosai, aransa kuwa allah ya isa ya keyiwa joda shegiyar bafulatana, natabbatarda sneez dinda take ne lokacin dana daukota aruwa shine ya shafeni ta likamun ciyon Su shaggun fulani, kuji Ahmed to waya saka dole ne馃槒Mahmud yashigo dakin da sallama bai amsaba dama kuma haka halinsa yake, tsaye yayi ganinsa acikin blanket, kafada yadaga , mutun kullum a kwance tamkar ruwa tsaki yaja yayi ficewarsa,Tea yahada mai kauri yasha tareda cake , yagama sha yadauko system dinshi yana dubawa, wani video yaga ana forward na wasu terro a garin bauchi , yafara Kiran Ahmed! Ahmed! Zokaga Dan allah jin shirun Yayi yawa ko motsi baiga yanayi ba, yasa shi ajiye system din, yaje ya yaye masa bargon da yayi rufa dashi, gwale idonsa yayi ganin yadda Ahmed ke rawar dari gakuma hakoransa se haduwa suke da juna bai kara rudewa ba seda yakai hannun sa kan Ahmed yaji zafi radau gakuma jijiyoyin kansa se bugawa suke,Subhanallah meyasameka man, Ahmedyakasa amsawa se kansa dayake nuna masa, ga atishawar data damesa dakuma Tari , Mahmud dafe kansa Yayi , mezanyi yanzu naji yafada, kome yatuna, naga yazubura da karfi, yadaukobag dinsu duk ya watse kayan amma baiga abunda yake ne maba,Yanzu idan nakira gida zan tada hankalin Dadyn Ahmed da kuma kanwarsa Hafsa, to yazanyi wannan serious sick ne abunda yakai man kawance aiba karamun abu bane,Fita yayi yabi hanyar kasuwa, har yakai cikin kasuwar ya tsaya yana tambayar ko akwai inda ake sayadda magani duk Wanda ya tanbaya dariyar sa suke, domin Su kowa shi yake yiwa kansa magani dakansa, dkyar yasamu wani tsoho yayi musa kwatancen wani gida yace nan ne a kullum baza arasa magani ba kowanne iri, Yace Dan allah baba kataimaka muje tare, bazan gane ba gidajen kamar iri daya ne,Haka kuwa akayi tsoho yarakashi har bakin gidan, zai wuce ne Mahmud yace baba nagode amma kozaka iya mun sallama da mai gidan, tsoho yace mushiga bakomai gidan aminina ne, suka shiga da sallamar Su, gwaggo ta karba tace musu ai baffa yatafi daji , tsoho yace aidama gurinki mukazo, gurina kuma inji gwaggo? Tsoho yace ehh wannan yaron bakin dajin nan ne inaga daga bunni suke, magani yake tambaya nace bari na kawo shi nan kozai samu,Gwaggo tadubesa da kyau tace wannanai bayahude ne koh? Mahmud yayi murmushi yace inna nifa musulmi ne kesan mu Yan birni munada banbanci daku, amma kudena kiranmu yahudu, yahudawa fa, ba musulmai bane, gwaggo tasosa kai, tace to wane magani kake nema, Mahmud yace na mura da zazzabi da ciyon kai, gwaggo tayi dariya tace to ay duka ciyon guda ne murar Itake haifar da zazzabi da ciyon kai kafahimta , Mahmud yace ehh,Gwaggo ta hura wuta dayake wutar karace nan da nan wutar ta ruru, ganyenshayi ta aza tareda citta da yaji da kaninfari , suka tafasa tajuye acikin wani kwano, inazuwa tace, wani mai tabasa tamkar RUBB tace wannan kashafa ajikin ka sannan a zuba acikin boketi a rufe jiki dashi hayakin da yaji nashiga jikinka insha allahu zazzbin zai karye murar kuma zata yi dama,Mahmud yayi godiya yace to inna nawane kudin, gwaggo ta ware ido, idan akayi taimako biya ake? So kake insiyadda ladata a'a kam sam bazata sabuba, lokaci guda yaji gwaggo tashiga ranshi dama ace haka sauran jama'a suke da an rage zafin wani abunSunafita yadauko dari biyar yaba tsoho, tsoho yaki karba yayi2 yaki karba dole Yakoma da abunsa yaba dada godiya, yana isa gida, yazube shayin a cup Yadago Mahmud yabasa abaki, Mahmud baiyi gardamaba ya shanye tass sema dadin shayin yaji saboda yanda yake da zafi gakuma yaji, boket yadauko yazuba man, yazo yacewa Ahmed kazo ga sauran maganin kayi tiraren ruwan zafi, Ahmed yace a'a kabarshi bana iya tashi jiri nake ganiDagosa yayi yacire masa riga da wandoyabarsa daga shi se base da wando karami, Ahmed yadago ido yana kallan Mahmud yace wannan iskancin fah yazaka tubeni bayan kasan sanyi nakeji,Mahmud yayi masa banza yacigaba da abunda yake, yazuba man da ruwan zafin, sannan yakawo Su agaban Ahmed ya ajiye yazanyo bargo ya lullubesa, kusan minti goma sannan ya bude shi, idonsa alumshe, zufa se karyemasa yake,馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 1鈨�1鈨�Saman gadon yamaidasa yasaka masawasu kayan, ya rufe sa, nana da nan bacci, ya kwashe shi, Ajiyar zuciya Mahmud yayi yace allah yasa yatashi garau, mu Ida wannan mission din lfy,Karfe 8 dai2 Ahmed yafarka , jikinsa garau se wani karfi daya keji, aransa yace wannan coffee din yayi energy coffee ne kenan dubi yadda nakejin karfi kamar zan iya fasa gina, lolMahmud yashigo dakin rike da kwanon fura ya ajiye gefe guda, Yace D boy yajikin, Ahmed yace normal wlh, coffee din yayi fah, ayki dari da dari yake, magani karfi, ga dadi again etc,Mahmud ya kyalkyale da dariya, waya cemaka coffee ne, coffee nada yaji ne? Ahmed yace oho to shayi ne koh? Mahmud yace koma dai Menene yanxu dai your normal so baruwanka, kafada yadaga, itso k"Mahmud yadauko furarsa yazuba kankara yafara sha , Ahmed yace wai Dan allah meyasa kai kake bala'in kazami, yanzu Dan allah furar Yan dajin nan kake sha , kofa fanfo basuda sedai ruwan rijiya, kai bakasan wanda wa yayidawon ba komai tsabta ne koya, kilamaan gurin dakansa ansaka da gwuda andake da sauro.....Mahmud yace ya isa haka, idan bazaka shaba ka kyaleni yazaka dinga kiramun kwari acikin abunci na, sokake inyi amai, Ahmed yace allah sauwake insha wannan abun, Mahmud yace okay better keep mouthAhmed yace base kace ba, ni inzaka sha wannan kazantar karika shan sha acan waje Dan wlh zubadda ita zanyi kasan bana son ganin irin wannan useless din, Mahmud yace shege kafasa koyanxu zaka iya zubadda ita , Ahmed yaza tsaki yafita daga dakin, yana fita Mahmud yace kai bakasan dajin daka raina shine yayi maka maganin ciyonka ba Dan iska kawaiJoda tace Dan allah gwaggo kibari nacigaba da tallana kinga anata zuwa nema , gwaggo tace nidai hankalina baya kwanciya akan hakan wlh kinga kohansai tadena zuwa, tace Mutumin nan makashi ne, da bundugar shi a aljihun saJoda tace wlh aa gwaggo bashi bane wannan mafa ya iya ruwa Mahmud kuwa yace tsoron ruwa yake , gwaggo tace kajiki da shirmen banza komai zai iya cemiki Dan yaci galaba akanki, joda tace wlh gwaggo bashi bane kamshinsuma badaya ba,Gwaggo tace shikenan tunda ke bakya jin magana dole joda taja bakinta tayi shiru, can kuma tace gwaggo yanxu a ina zamu sami kudin.....gwaggo tace wlh joda zan saba miki wato ni ban isa dake bakoh, joda tace gwaggo kiyi hakuri nadena zancen wlh, gwaggo tayi hanyar bayi batako bi takan joda baBaffa yashigo gidan jayeda saniyar sa, yaje gurin dasuke ajiye Su, yaturke ta, yazo yazauna yana Kiran ina auta joda, joda tafito da gudu baffa na, sannu da zuwa, baffa yace ina gwaggonki, joda tace tasiga bayan gida, baffa yace to zoki bude mun wannan ledar nakiya ce na siyo muku, cike da zumudi take bude ledar gurin sauri har rawa hannun ta keyi takasa bude ledar, baffa yace kawo nabude muki mai kwadayi,Gwaggo tafito daga wanka, ta yiwa baffa sannu da zuwa takawo masa fura da ruwa, sannan taje ta shirya tazo tazauna sunata fira, sallama sukaji anyidaga waje, baffa yace joda jeki dubo wake sallama awaje, takalminta tasaka tafita, wazata gani lah yaya Mahmud waya nuna maka gidanmu shima dai mamaki yacika shi, yo dama nan gidanku ne, joda tace ehh mana bagasi kinganni asiki ba, Mahmud danne dariyar sa yayi domin in suna wannan zancen dariya suke bashi, tace bismillah sigo siki, Mahmud yasaki yin sallama yashiga ciki.......馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 1鈨�2鈨�Baffa yamike tsaye da sauri yana nuna Mahmud da yatsa ke meyakawoki gidana sanake ziya nakoraki daga hanyata , saboda allah me mukayi miki kike bibiyarmu, mufa baruwanmu daku yahudu da nasara,Gwaggo tace dama shine kake gayaminziya, baffa yace sine mana, ziya da kayan yahudu yake yaukuma kinga yasaka na narasa, gwaggo tace zo zauna yaro, baffa yace kuttt bilahilazim bazata zauna gidana ba, canake angayamiki makashi ne,Gwaggo tace insha allah shine Wanda nabawa magani jiya, yaro zoka zauna , Mahmud se murmushi yake yajanyo kujera yazauna, baffa ma Yakoma yazauna, gwaggo ta dubi joda tace jodawannan shine yafidda ki ruwa, joda tace a'a bashi bane ba wannan kamshinbane, Mahmud ya zaro ido kamshi kuma sekace dai mai wanka da tirare, gwaggo tacewa Mahmud bawan allah kagayamuna tsakanin ka da allah meyasa kake bibiyarmuMahmud yace bakomai atareda ni se alkhairi inna ni musulmi ne, kuma mai tsoron allah ne, wani aiki mukazo yi nandajin jibi zamu koma gida, gwaggo taceto ai ba'anan gizo ke saka ba, kowa yasan Yan bunni da kyama musamman garemu amma kai babu wannan kome yasa? Mahmud yayi murmushi yace to inna miye abun kyama ga talaka ko ba kauyebayan allah dayayi mu shi yayi ku kuma badan baisonku yayi ku ahaka ba sedanyajaraba imanin , haka muma badan munbiyasa dako sisi ba yayi mu wayayyi masu kudi, badan kuma yafi kaunarmuba akan ku sedan yajaraba imanin mu yagani shin zamuyi amfani da dukiyar mu dayabamu da ilimin mu mu aiwatarda alkhairi, mukuma siye aljanna da ni'imar da allah yabamuBaffa yanisa yace hakika wannan yarinyar tasan allah tasan abunda take zucitarta cike take da zuhudu, yaro ka gafarceni, Mahmud yayi dariya yace bakomai baba nidama burina ku yarda dani ku kuma yafemun akan sakaku danayi acikin Dar Dar nakasancewata mutum nagari,Gwaggo tace wlh bkomaie ay muma rashin sani ne, murigada mun dauki Yanbunni abun gudu da kyama , Mahmud yace ay turawa sune ake kira da yahududa narasa ko acikinsu akwai musulmai dayawa,Baffa yace wani yare ne ake kira turawakuma, Mahmud yace a'a wani jinsi ne na Dan Adam a wani yanki ne cikin duniyar nan, baffa yace bayan kano damuke ji sekuma birnin shehu se gombe da sauran kauyuka kamar Su binji da sauransu akwai wasu kasashe ne,Mahmud yace ai duk wadannan garuruwa ne kano da sokoto, Duk acikinkasa dayane Nigeria, baffa yace me cece Nigeria kuma, Mahmud yace kasace duk acikinta muke sauran kasashen duniya a jirgi ake zuwa, gwaggo tace ni wlh nakasa ganewa, Mahmud yace bazaku ganeba inna saboda da ace kuna cikin gari ba dajiba duk zaku San wannan kauyawa ma sunfiku civilizations ,Yace ina zuwa wayarshi yafidda musu ya kunna musu baffa zai tsoro yakeji yadda yake ganin al-amurran wayar, joda kuwa se ihu take, Yace joda zonankigani tadawo kusansa hannunsa yasa yarungomota yadau kesu photo . yanuna mata tsoro yakamata sosai, Kiran gwaggo take, gwaggo zokiga mune fah muka fito acikin wannan abun,Haka yacigaba da daukarsu photo harda Su gwaggo da baffa yanata nuna musu suna jin dadi, Se kusan magrib yabar gidan cikinsa cike da fura,Koda ya isa gida yatarda Ahmed rike dajarida yana karantawa, baimai sallama ba sanin halinsa, shikuwa Ahmed hakanyasosa ransa nanko yakara kimtse fuska, Mahmud Baiko kula da halin dayake cikiba, wanka yayi yatada sallahabun shi koda yagama Ahmed yafita, saman gado yafada ya kunna wayarshi yana kallan pics dinsu, tsurawa joda idoYayi yau batayi kwalliyar hauka ba, kamar ma ba dade da wanka baFuskarta tayi haske sosai sedan kufan Jan bakin dake bakin ta ba inda take daDan kwali ya tsurawa gashinta ido lallai wannan gashin idan yaji retouch zaiyi kyau, haka yacigaba da sake2 sa aransahar bacci yakwashe shi,Joda takoma ma fita da farar ta, hansaima dole takoma ga tallanta na shinkafa, Mahmud kuwa yamaida gidansu joda gurin firar sa, yayi ta shan fura baruwansa da wani kyankyami, joda kuwa tana makale dashi ya kunna mata wayarshi tagani haka zai dinga kunna mata pics tana kallo tana ihu,Yau tin safe yatashi yahada musu kayansu tsaf Dan yasan wancan Dan iskan Ahmed ba hadasu zaiyi ba, yagama yacewa Ahmed inazuwa bai amsaba Shikuma yayi ficewarsa sai gidansu joda,Joda kuka take sosai tarike Mahmud, yace mata kiyi hakuri joda zandawo nanda sati guda , tashare hawaye da gaske yaya kayi alkawari? Yace nayi joda , Gwaggo takawo galan din fura danono tabashi Mahmud yaji dadi sosai yadinga godiya,Kudi yaciro yabasu amma suka ki karbaseda yayi kamar zaiyi kuka sannan baffa yace dari biyar ta isa badan yaso ba yamaida sauran, har bakin kasuwa suka rakashi...... HAUSA NOVELS SOKOTO wayarsa yace look.....sekuma yafasa , Mahmud yace mezan gani, manta kawai inji Ahmed, haka Suka cigaba daargument har 4 tayi Ahmed yace nifa nagaji dazama nan gidan, kawai mutun yadawo dan iskanci baza'a barshi yaje gida ba , Mahmud yace kana iya tafiya ai,Ahmed yajanyo wayarshi yakira driver dinshi yayi masa kwatancen gidan yaceyazo maza2 yadaukeshi nan da nan kuwa Segashi, amma me mai gadin gidan yaha nashi shigowa yakira Ahmed yagaya masa Ahmed yace whatnonsense gidan ubansa ne koya, Mahmud yace lfy sarkin masifaffu, Ahmed yace wancan banzar mai gadi ne wai driver bazai shigo ba, sekace gidan ubansa neMahmud yadafasa calm down man, order aka basa nasan commissioner ne, kasan yanaji damu soyake muhuta sosai sannan akaimu gida, duk Wanda yafito daga wancan dajin ai dole yana bukatar dogon hutu, Ahmed yace to cemasa akayi muna bukatar hutun nibana son haka wlh, Mahmud tashi yayi yadauko masa eviron drink, ya zuba a cup yabasa, Ahmed yakarba yafara sha seda ya shanye ta tass sannan yabasa cup huhhhhhh naji yahuro iska tareda ajiyar zuciya, are youOkey Mahmud ya tambaya, Ahmed dakansa yake kasa yace yeah.......馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 1鈨�4鈨�Bayan magrib commissioner yaturo musu da mota biyu kowacce akwai 2 soldiers aciki dayan tadauki Ahmed dayan kuma Mahmud kowannensu akayi dashi gidansu,Wani katon gida naga an faka da Ahmed kamar wani gari, tsarinsa kadai yakoda ni , carpet ce ja mai matukar laushi ashinfide mai tsawon gaske har zuwa wata karuwar kofa kamar dai get ,flowers ce shimfide ako ina, kamshi kadai ketashi narasa ta inda yake fitowaWata chocolate din yarinya naga tafito dagudu sanye cikin doguwar riga ta wani mayen less white & black tayi daurin dan kwali oll back simple make up tayi amma tahadu, hannunta rike da flower murmushi kawai take hakorantatass dayan haurenta sanye da hauren makkaFlower tamika masa tareda rungumesa tana wlcm bros, dariya yake nikam nayi mamakin ganin wannan hero yana dariya , hw ar u 6ter? Yarinyar tace am ok bros yagajiya, Yace bagajiya, 6ter gajiya tabi jiki shin ma wai kintaba ganin soja yagaji, yarinyar tace Au haka nefa, rugumeta yayi suka shiga daga ciki ,Katuwar kofar aka bude zokuga wani hadadden parlour tsayawa nuna irin haduwar gurin kauyancine, ku kissima aranku kawai, Wata kyakkyawar mata naga tafito tareda wata beauty se murmushi suke, matar takarso tace wlcm son, kansa kawai yadaga mata, yarinyar tasauko daga downstairs tana wani yauki tamkar miyar kubewa , ahankali ta furta big bros wlcm, tancuu shine abunda yafadaYarinyar dake makale ajikinsa tace brosmuje inrakaka dakinka nasan kana bukatar hutu, Ahmed yace 6ter jeki hutamana, tace no bros 2dy its ur dy, murmushi Yayi to naji muje , hannunsa tasaka ahamatanta tajashi suka bi watahanya, wani hadadden daki naga sun shiga, aiko nace baza'a barni abaya ba atare muka shiga, daki ne kato yafi halldin Dan fodio set din kujeru biyu ne aciki sannan wani wakeken gado mai runfa gadon tamkar na cikin joder akbar, kamshi ketashi kota ina , shkar kamshin yayi tareda Jan hancinsa yace 6tor I lyk it, yarinyar tace to ay gashinan sekayita shakaHannunta yajanyo suka zauna kan gadoyace Hafsa gayamun dame2 yafaru bayan tafiyata me akayi miki waya bata miki rai bayan tafiyata ???? Dariya ta aza kai yaya koma me akayi ai yawuce balantana ma ba abunda yafaru, Ahmed yace u ar lie, nasan dole Anyi wani bazaki gayamun bane, tace yaya believe me i swear, kafada yadaga any where zanduba camera ta, ido tagwale kai yaya allah bayasan tada fitina,Ahmed Yace zan mareki wlh get out b4 I show you my anger , kafadarshi tadafa tace relax bros, tarike kafadunsalok at me, lok into my eyes, jajayen idonsa yadago yakalleta sekuma yamaza yajanye murmushi tayi, ta tashitabude fridge tadauko masa eviron drink tabasa, amsawa yayi yasha, tace ar u okay, yeah ya amsa mata, tace gud nyt ta fice daga dakin,Tana fita tasame wannan yarinyar da matar adakin wato hajiya da amina, hjy takalli amina tace kalleta wai ita mai yaya, amina tace barta black gul kawai yarinya kamar yar tsintuwa babu inda tadauko abbanmu, hjy tace wayasani toko yarsa tinda kowa yasan halin gyatumarsu, tuni hawaye suka wanke fuskar Hafsa, kofar dasukaji anbude dakarfi ce yasasu juyowa azatonsu Ahmed ne har hantar cikin Su takada, abdallah ne yashigo se tangadi yake alamar yabugu,Hafsa tadubesa ta karkada kai cike da takaici, tawuce dakinta tabarsu atsaye, mamma zoki kaini dakina shine abundayake fada, tace wato ba sallama kawai in kaika dakinka, amina tace hava mama baki ganin yanayinsa neYace mamma yanaga anyiwa gidannan decoration ne baki mukayi, amina tace big bros ne yadawo, Yace wht nonsense big bros dady ne, ni lokacin da zandawo daga india ba shegen dayayi mun wannan decoration din se shi mai sati biyu kacal, in possible" yadauki cup shuri yatashi sama carab se hannun Ahmed yacabe cup din dukansu suka juyo suna kallansaGurinsa yadum faro kamar wani zaki tafiya yake tamkar ruhit acikin doom sumar kansa nata tashi sama dukansu sun tsorata daganin yanayinsa, wuyan abdallah yacabko ya wazga masa mari, ar u mad? Hjy tace kai mezaka masa ne haka, Ahmed yajuyo dakarfi yana cizon lebensa, Yace dukansa zanyi zaki rama masa ne ? Amina tace bros tomeyamaka ne?Ahmed yasaki wuyan abdallah yacakumi wuyan amina yace mekika ce, ta marmasa ido, tuni yawan ke ta damari yadago fuskarta yasake marinta yahankadata kasa hannunsa yadago zai sake kaimata duka, abdallah yarikesa tabaya, yajuyo yana yinayiwa hannun sakallan wulakanci yace ina tausayin wannan kucakin hannun naka alokacin dazan cire shi anawa , hhhhh馃槀 abdallah yace wai mekake takama dashi indan Dan wannan Dan iskan cos naka wlh bazai tsorata niba............馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page1鈨�5鈨�Ahmed yayi murmushi tareda kimtse fuska yasa hannunsa yadinga janye hannun abdallah se kat2 kakeji tuni abdallah ya kwarma ihu, Ahmed yace no no tin yanxu ya ciyo kwalarshi har sunajin bugawar zuciyoyinsu, Yace wato baka dena shaye2 ba koh? Abdallah yace meye matsalarka acikiHjy tace shi nagani inaruwanka da rayuwar shi, Ahmed yatura abdallah dakarfi yakaraso gurin hjy kamar zai hau kanta yace bakida hurumin hanani hukunta Dan uwana, hjy da tsoro tayi shiru gudun yamata wani abuTin safe Hafsa ta tashi tahada masa special break nuggets da tea se aresh da kwai , takai masa dakinsa danshi baya cin abunci a dining se in dady yana gari , ita ke basa tea din da nuggets har yagama tasaka tissue tagoge masa baki sannan itama taci nata , tagyara masa daki dukda bakomai yayi ba, tawanke toilet, sannanta kunna bona tarufe dakin,Ahmed yashirya cikin kananan kaya rigada wando black n Wight yaja motarshi se gidan commissioner yasanarda shi dalilin zuwansa gidan, wato yanaso acanza zancen tada fulanin daji, commissioner yace sedai kayi hakuri son amma har nacika file din , Ahmed yace shiit yanzu miye abun yi sir gsky Anci hakkinsu akwai wani gida danagani ance wai 1 million za'a basu alhalin gidan yakai 4 sannan duk sauranmutanen dajin wai dubu dari ukku za'a basu da hamsin,Commissioner yace karya ne masu gidan 10 million mukayi za'a basu sauran jama'ar dajin kuwa 1 million ne, Ahmed yace bahaka yafada ba a news jiya, commissioner yadauko wayarshi yakira minister, minister yace bincike yanuna babu komai agidan ansamu mistake ne afarko, girman gidan yasakaza'a basu 1 millionCommissioner ya ajiye wayar yace wannan shine fist work da zan baka kaje kabinciko mun, gaskiyar al amari, Ahmed yace ok sir gobe zakaji komai, commissioner yayi murmushi yace am proud of you son, I sure will do it, Ahmed yace yeah sir I shall do it with my heart, murmushi Yayi yace I know son, all d best.Haka yabaro gidan commissioner yanata nazarin yadda zai bullowa lamarin , Mahmud kuwa yanacan yana nasa tsarin, duk arude yake damuwarshi daya baisan inda zai sake haduwa da joda ba idan sukabar dajinA DAJI KUWA,,,""Mutanen dajin labari yazomusu cewa za'a zo atada Su saboda haka Suka farakoke2 gabaki daya dajin yazama tsit kowa da bukin zuciyarshi, gwaggo tacewa baffa tun ba azo aka wulakantasuba Su tattara inasu2 subar dajin kunsan fulani da shegiyar zuciya ,Haka Suka tattare duk wani abun amfaninsu, gwaggo tace sokoto zasuje sunemi Yan uwansu akwai kanwar babarta dake aure sokoto amma asaninta a masina suke, dajin kowa yafito yanata kukan rabuwa dasu hansai tarike joda sunata kuka kamar wadanda sakon mutuwa yariska har sunkai bakin kasuwa joda tace gwaggo ina zuwa, ta falfala da gudu , gwaggo na Kiran ina zaki amma ina har tabace musu dole suka tsaya jirantaJoda kuwa ramenta datakesa kudin da Mahmud kebata taje tabude tagansu kuwa suna nan, tayi hamdala tadauko har zata duba nafarko tace kai nama San hansai zata iya budewa, Dunkule Su tayi a zaninta takoma gun Su baffagwaggo tace mekika tusa azanin nakine haka, tace gwaggo kudin da yaya Mahmud kebani ne dik yasha fura nikuma se in sakasu arame gwaggo tace mugani, Koda aka kirga dubu ukku cib duk Yan dari biyar ne, gwaggo tace hamdan khasiran, wadannan sun ishemu rayuwar mu ko jirgi mukeso zamu samu, lol kuji gwaggo fah馃槄Dan achaba biyu suka tara daya da kayansu tareda baffa daya kuma gwaggo da joda, har Suka kai wajaki kauyen sokoto, Nan Suka dinga tanbayar gidan margayi alpha nuhu, dakyar suka sami wanda yasan shi yacemusu ay yadade da rasuwa sedai yayanshi suma kuma ukku daga cikinsu suka rasu sora biyu mujittaba se muktar mujittaba yana cikin garin sokoto muktar na masina shida iyalanshi,Mutimin yayi musu jagora suka shiga motar sokoto dari hudu da hamsin aka kaisu wato dari da hamsin2 abakin tasha aka ajiyesu, suka tan bayi gidan mujittaba aka nuna musu kusaga masallacin shehu inda makarantar almajiran fulani,gwaggo cike da murna tashiga gidan kasancewar gidan da tasha titi ne kadaiyaraba Su, rike take da hannun joda baffa na janye da kayansu.......WAYE JODA?MENENE ASALINTA?kubiyoni Dan jin wadannan amsoshinMuje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫:馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 1鈨�6鈨�Asalin joda =Alpha nuhu shine kakan gwaggo wandayahaifi mahaifinta wato muktar , mujittaba, ayuba, suwaiba se kasim ayuba da kasim da suwaiba duk sun rasu, dukansu yayan halimatu sadiya ne, wato matar alpha nuhuSadiya asalinta yar sudan ce, wato Arabagurin karatu alpha yahadu da ita anan ya aurota, yazo da ita kasar masina takusaga, kasar saudiyya, alpha fulani ne na usuli tin kaka da kakanni, kuma makoho ne sedai akwai dinbin ilimin addini agaresa hakama yayansa sunsami karatu sosai,Alpha yarasu yabar yayansa biyar tareda matarshi, maimuna itace mahaifiyar gwaggo wadda takasance ya tafari ga malam muktar, se kanwarta saratu sukadai ne ga malam muktar gwaggo ta taso cikin gata da soyy sutura babu wadda bata daurawa mujiGanin haka yasa A'i da yayanta ukku kishi wato luba, hadiza da abdul hadi, ganin uwayensu maza sundora ma gwaggo son duniya, hakan yasa A'i biyar bokaye tana karbar magani tanayiwa uwar gwaggo da itadin, tin ta nayi yana karyewa har allah yabata sa'aWatarana gwaggo tafito daga makarantar allo, tana shigowa gidan A'i tace mata tashiga bayi tadauko mata buta tana tafiya A'i najanta da fira har tamanta da addua daganan aljannun daaka tura suka figeta se dajin wajaki, suka yada ita sannan suka mantar da ita gidaAgida kuwa Anyi ne manta har an gaji babu haukar da uwayenta ba suyi ba daga karshe suka sangana dalilin dayasa mahifinta komawa kasarsu kenan wato masinaAi kuwa bokanta yatabbar mata cewa gwaggo bazata dawoba se har jikinta ko jikin danta yagamu dana dai daga cikin danginsu sannan zata dawo a hayyacinta, gwaggo kuwa abakin kogin kada aka yada ita, anan ne baffa yaganta , yadauko ta saman jakinsa yakaita gidan SuMahaifinsa barau shine yacigaba da kula da ita har taji sauki daga nan tazama yar gida, zuwa wani Dan lokaci barau yahadata aure da dansa wato baffa, shekararsu kusan biyar sannan gwaggo ta haifi danta wato sani baifi wata uku ba yarasu tasake haihuwar wani shima aka saka masa sani watansa bakwai yarasu seda tayi yaya kusan biyar suna rasuwa mata da mazadukansu bada shekara suke mutuwaJoda ce tashida itace kuma auta dalilindayasa ake sonta kenanWannan kenan "gwaggo tayi sallama tashiga gidan, Wani dattijo tagani rike sa alkalami da allo yana rubutu ahankali abubuwa sukafara tariyo mata, dasauri tace malam!Kansa yadago yana kallanta muryar wa nakeji kamar innata, tace nice malam, malam yace dama kina raye,Zama tayi tadinga basa labarin rayuwar ta har zuwa yanzu malam yakalli baffa yace angode Dan uwa allah yasaka muku da alkhairi ameen, tace malam inna baba da innata, malam yace suna masina tun bayan rashinki da mukayi, yakasa zama kasar nan, tace saratu fa? Seda yayi Jim sannan yace allah Yayi mata cikawa, yanzu shekara goma kenan, hawaye suka dinga zuba afuskartaMalam yace hakuri zakiyi yanxu ina zakimasina zakije ko nan zaki zauna domin nima kwanan nan nake shirin komawa can nagaji da nanan kudina kawai nakeso Su cika, gwaggo tace nawa akezuwa ai munada kudi, malam yace dubu goma ne duk mutun dayaBaffa hai bahause bata iya San kudi ba, mezatayi da dubu goma hanake ko makka zasu kaini, malam yace hmm nan fa ba irin dajinku bane. ....馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 1鈨�7鈨�Ahmed yayi duk wani bincike da zaiyi an tabbatar masa dacewa, babu komai acikin gidan, amma kuma seda yasamuganin governor da minister yayi korafi akan gidansu, haka yadinga shige da fice seda yaga anbiyasu yadda yakamata, sannan hankalinsa ya kwanta, yakira commissioner yashaida masa yayi murna kwarai yace Ahmed kwazonka da jajircewa na burgeni,Mahmud labari yazomasa, amma baisan wanda ya gyara al amarin ba, yadaiji dadi sosai , Yace insha allah zanje next week in kai musu ziyara kamar yadda nayiwa kanwata al qawari wato joda"Malam yakira gwaggo yagaya mata cewa tafiyarsu jibi ne dama bagabadai zasuba abdul hadi da matarshi nanan, gwaggo badan ranta yasoba tazauna suka wuce akabata dakin, hasiya tazauna aciki, haka suke zaman gidan a wahalce domin kuwa hadi bashida imani ko kadan, seda tagwammacezaman daji da gida, amma koba komai taji dadin ganin danginta, joda tazama boya agidan , duk jumu'a setafita da tallana ruwa bakin masallaci, dayake nan bakowa keson fura ba akwai ta ko ina ,Ahmed yatabbar da gaskiya ya kauda rashin",, ta ma'ana yatsaya tsayin daka aka gina ma kowanne mutun gida dai2 danasa tsarinsa dai2 talaka, gidan baffa ne kadai ba'a ginaba saboda ba asamu ganinsa ba andai killace gidan, Nan cikin kauyen sokoto wamakko kudin gidan dakomai suna hannun shamsudden wanda suke cewa deeni wato PA na minister,Ahmed yagama komai yaje yasamu commissioner yayi masa bayanin yadda komai yakasance commissioner yayita sakawa Ahmed albarka, yana fita yace aransa allah nuna mun ranarda zan aurawa Ahmed yata sarina, murmushi Yayi allah yanuna mun wannan Ranar ameen zanyi alfahari dashi cikin zuriata idan har yakasance surikina Ahmed yadawo daga barrack dinsu yashigohannunsa rike da hularsa, yana takon girma karar rawar gidan yadanna mai nuna ana bukatar ganin kowa dakowa, cikin minti biyar kowa yahallara harda abdallah da masu aikin gidan hjy da yar gold din yarta amina,Ahmed yace kunsan cewa taraku nan gurin agabadai yana nufin akwai important issue dazakuji, so ba wani abu bane, dad zai dawo gobe at 4 to 6 pm ana bukatar gyara agidan nan da cook, yakalli husaina wadda itace shugaban masu aykin abinci yace zanbaki list din abunda ake bukatar kidafa, hjy tace amma ai....Ahmed yada mata hannu 鉁嬸煆� amma me bannemi kowa Yayi mgn ba kona bada order ne, Iye?Yamaida kallansa ga mai gyaran gidan yacetsohuwa baki bukatar gyara ko bayani you know how to make diz house special nd cute veuryfull, ar u hear me? Tsohuwar tace Yes sir, Ahmed yace gud, se kai mai gadi kafi kowa rawar kan tsiya idan bakayi hankali ba kana kusaga rasa aikinka,Ali driver katabbatar anwanke duk motors din dasuke gidannan, remain you Hafsa yanuna ta, kibiyoni ki karbi keys din dakin dad kitabbatar kin gyara shi nasan zaki iya, abdallah ka kiyaye kanka daga shaye2 nan kasan abunda yakai baba Egypt natsawon wata shidda duk matsalarku ce kaida uwarka da wannan fantimotin yanuna amina, ta haifar masa da hawan jini,So all of you b care full idan akayi something bad or rubbish, har nagani white my ayes wlh, rankowa a gidannan zai baci, har yajuya zai wuce hjy tace inada magana, Tsayawa Yayi batareda yajuyo ba, Yace bayanzu ba banda enough tym dinda zan karbi korafin ku, dts oll yayi shigewarshiTo mekuke jira muna fukan banza kunwani tsayawa kuna kallona , tadaka musu tsawa tuni kowa yasani inda zashi , Hafsa ta kunshi dariya tabi yayanta da gudu.........馃巹 FULANIN DAJI 馃巹 N@ B aleeyu 馃挄 1鈨�8鈨�Dakinsa tabisa yabata keys din yakara jaddadamata cewa tana shiga tarufe kofa domin baya bukatar kowane Dan iska yashiga dakin , atake zasu sace wani abu tunda dukansu sunzama gwaska , Hafsa ta kyalkyale da dariya, hava yaya yadai sata, Yace oh to karya namusu ko sharri, Hafsa tace a'a bance ba, Yace dallah kije aykinki ko sekin gama min iyayin tsiya, har zata wuce yace look Tajuyo idan akayi sallar la'asar kizo nabaki list din girki dazamu bukata, toh kawai tace masa tafitaA parlour tasame Su hjy se zagin Ahmed suke, Hafsa tace dubi wai iskanci mutun da gidan ubansa a hanashi shiga dakinsa, hjy tace inbanda iskanci ma wai alhj zai dawo amma se abakin dansa zanji, sannan kuma shi zai tsara mana yadda komai yakasance banida ikon shiga dakin mijina se in yana ciki bani zan tsara girkin danakeso ba wai se shashan dansaHafsa tayi kamar batajiba tayi hanyar dakinta, amina tace ke zonan Hafsa tayi mata banza, abdallah yace ke Dan uwarki ba mgn ake miki ba seda tajuya sannan tace ai ba ke ne sunana ba, duk Wanda bazai kirani da sunan da ubana yarada mun ba ai seya bariAbdallah ya taso da karfi ya zare belt zai zaneta hjy tace a'a Dan mama kada ka tabata yayanta nagida,Da kibarshi yatabata wlh in nuna masa banbancin kashi da masa, gabadansu suka juya suna kallan Ahmed yace wato dama dukanta ake agidan nan idan bana nan, kekuma yanuna Hafsa shegiya wawiyar banza ni uwata ba haka takeba ba wanda zai takata bata rama ba bansan ko zuciyar wa kika gado ba, dad dina bahaka yakeba,Zuciyata ce tadauko, daga kofa sukaji wannan sautin, Ahmed yace woww abba kaine, nine ahmadu muhammadul mahi "!Hafsa ta aza dariya kai abba duk wannan sunansa ne, Yace sosai kuwa, kema in kina so injero miki naki dasauri tace Yes inaso, yafara hafsatu manga hafsi Hafsa, Hafsa tabata fuska wlh abba banason manga dinnan, Ahmed yace kedalla kiyi mana shiruko gaisawa bamuyi ba kin hausa da shegen surutu,Abba yace kabarta mana, aytafi wadanda sukayi halin ko in kula dani, Ahmed yadaka musu tsawa ku sha2 shan ina ne dazakuga ubanku ku tsaya kuna kallansa amina tace ina yini, abba afusace yace da ban yini ba zaki ganni shakiyiya kawai, yagalla wa uwarsa harara, abdallah yarusuna yace abba barka da zuwa , ya amsa ba yabo ba fallasa , hjy ta tabe baki tace yaya barka da wuni, abba yace barka DeMahmud yashirya tsab tun da asuba yabi jirgi se sokoto, daga nan yashiga mota zuwa wajaki, yana kai bai tsaya wata2 ba yatare Dan achaba se dajin fulani, amma me yaga ya badai anrushe dajin ko tsuntsu babu balantana Dan Adam, oh gush yadafe kai bin dajin yake da ido yadda akafara foundation agurin da alama gidan mai za ayi babba , ina zan ganta wazan tanbaya?Haka yabaro dajin rayuwar shi ajagule , kusan 4 ya isa gida wayarshi yajanyo yakira Ahmed yagaya masa cewa akwai matsala Ahmed yace Tamefa ? Mahmud yace yanzudaga dajin fulani nake na riske har antadasu, kai intakai cemaka har ankassafagurinAhmed yace hava dai, yanzun miye abunyi, Ahmed yace shine dalilin kiranka nima bansan abunyi ba yace ni yadda naji ance za'a gina musu gidaje amma banyi zaton har antada suba kodai karya ce, Ahmed yace wannan kuma seka binciki newscasterkaga inada abunyi yanzu yakatse wayar, Mahmud baidamu da halin koinkula da Ahmed yamasa ba burinsa yaga halin dasu joda sukeWAYE AHMED?Muje zuwa 馃巹 Dan jin wannan amsarASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 1鈨�9鈨�alhj usman shine mahaifin Ahmed da uwarsu margayiya Sarah wadda suke kira da ummah, alhj usman dane ga alhj zubairu wanda yayi tashen kudi azamaninsa yarasu yabarmusu dinbin dukiya lokacin dad na jamia inda yake karatun government, musa shine babbansu wanda suke kira da abba sedad alhj usman kenan se kanwarsu zainab wadda ke aure a kt yayanta ukku rufaida yasir se muniba, rufaida tagirma tana ss2 ayanzu,Abba musa yanada yaya ukku anty aisha se anty nana se karaminsu jalal, dukansu sunyiaure acikin kd, jalal kuwa yana turkey gurin karatu inda yake karanta businessAwani bincike da Su dad sukace sudan anan yahadu da ummah, suka kulla soyy kafin yadawo yanemi izinin aurenta aikuwa atake akabashi saboda kirkinsa, yana zuwa gida yasanadda yayanshi musa aikuwa cikeda murna, yasaka musu ranar zuwa ba adauki dogon lokaci ba akaje neman auren akasa auren wata shidda dai2 kare karatunshi kenanYana kammalawa koda yadawo har abba musa yahada lefe yagyra masa gidansa, alhjusman yayi matukar murna da hakan cikin sati ukku aka saka biki Anyi komai lfy amarya ta tare gidan mijinta dake unguwar maitama ,Zamansu suke lami lfy ko gardama bata hadasu da mijinta, haka take bin abba musatamkar mahaifinta da matarsa, batayi shekara daya ba tasami ciki, gidan kowa murna yake dasamun cikinta bayan shekaratajuye danta kyakkyawa tamkar Dan indiaAka sha biki sosai akasa masa muhammad shine suka maidashi Ahmed,ummah batasake haihuwa ba , alhj imaran wato mahaifin hjy ya umurci dad daya aure yarsa tunda haihuwa ta tsayawa matarshi haka yadaure ya aure ta badan yasoba sedan kawai baya iya jayayya da shi amatsayin shi na aminin ubansa, Koda dad yazoma ummah da wannan zancen seyaga tayi murna sosai hakan yasa hankalinsa ya kwantaHjy ta shigo gidan cike da isa da gadara, Sam bata ganin girman ummah, haka zata yi ta yima ummah habaici dayake ummah bamai son fitina bace setayi banza da ita, amma sam ummah batadaukar raini, ga zuciya kamar me irinta fulanin usuliHjy tasamu ciki se murna take tana kananan zancen ummah kuwa batako bi takanta ba, ahaka har ta haifi danta na miji wato abdallah alokacin Ahmed nada 6yrs, seda abdallah yayi shekara hudu sannan tasake haihuwar amina daga nan itama haihuwar ta tsayaShekara daya da haihuwar amina ummah tahaifi Hafsa, har an cire ran samun haihuwar, Hafsa ta taso cikin so da kaunar yayanta Ahmed skull kadai kerabata dashi,Ummah tarasu tabar Hafsa nada shekara biyar aduniya, baqaramun tabuwa dad yayi rashin ummah ba sedai yabarwa mai duka komaiAhmed yataso tun yana yaro da shegen girman kan tsiya, ga miskilanci har na tsiya, uwa uba bamai hanashi kudurinsa abunda kedamun mahaifiyarsa kenan, yana kare skull yaje Pakistan karatu acan yakare duk karatunsa, haka Suka taso da Mahmud tamkar tagwaye sedai hali ba guda ba, Mahmud kadai ke iyawa da Ahmed se kuwakanwarsa HafsaMahmud yayi karatunshi a Mumbai acikin kasar india saboda haka lokacin2 suka ziyarci juna kasancewar babu nisa tsakanin Pakistan sa india kusan ma kasa yanki dayane, sunyi sa'ar fito da kwali mai kyau tareda aykinsu ahannu.......馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�0鈨�Koda Ahmed yadawo daga kara2 har Hafsa tafara college, hjy na matukar tsoron Ahmed tun ranarda mahaifiyarsa nada rai tagayamata magana Ahmed yadauko cup din glass ya watsa mata shi aka kuma yadinga dukanta da kujera, dkyar uwarshi tarabashi da ita,Uwa uba karatun dayayi na soldiers shine karin bakin ransa kullum fuskarsa a tamke idan dai kinga dariyar shi to yana tareda kanwar shi Hafsa, wadda a duk lokacin daya kalli kwayar idonta yakan tuna mahaifiyarsa, Ahmed nada shegiyar zuciya amma me daya sha eviron drink zai dawo normal ,Yatsani ka masa laifi kabasa hakuri, yafi bukatar kabarshi da bacin ransa domin basa hakuri tamkar kada da laifi ne agurinshi , abdallah kuwa babu abunda yakoyo a indiaa illah shasahanci da shaye2 se biyar mata, hakama amina tana Dan tabawa ma'ana tafaye soyy zamani wato romantic loveHafsa kuwa baruwanta daga islamiyya se skull dinsu bata saurareni, kowani saurayi, Dukda ana ne manta, Sedai ta mutu son Mahmud amma batabari yagane ba, Sedai batasan tuni Ahmed yakamo tashar taba yadai samata ido ne kawaiMahmud yanada kama da Ahmed farinsu daya sedai Mahmud yafi haske, Ahmed kuwa yasurka da ja, karatun da sukayi a india, sundauki al adunsu da dama examplebarin suma, Sedai yayi retouching dinta amma baya cirewa sekuma ta dace da fuskar sa, dogo ne mai faffadan kirji, yanada dogon hanci da karamun lips wadanda suke pink sosai kamar ansaka musu lipstick,Sam Ahmed baya saka manyan kaya zai iya shekara bai saka manyan kayaba , ko ranar Friday sedai yasaka jallabiya fara, akwai shi da son kamshi ka tsantsainin tsiya, akwai shi da kyama mutane, bai dauki mace abakin komai ba, baruwansa da sha anin mata,Shi aduniya baida wanda ya tsana irin Wanda yace yana sonsa, ko agurin aykin suka je kowani mission. Tokuwa ko commissioner na tsoron Ahmed saboda saurin zuciyarsa, akwai lokacin da gardamata hadasu da wani captain abun yafara yabawa Ahmed haushi yaki sakar masa, binidiga kawai yafidda ya halbesa a kafa, indai agurin ayki ne suke to kowa kafa2 yake dashi, in kuwa agida ne belt ke ayki amina tasha dukanshi har ta gode allahYau tin safe baffa yatashi da ciyon kafa, Gashi yana son fita kiyo amma ba hali tin yana daurewa har yafara nishi, gwaggo tacebaffan joda lfyrka kuwa yau senaganka kamar ba kajin dadi ne , dakyar ya iya furta kafarshi, gwaggo duk ta gigice arude taje tasame hadi tagaya masa, Yace mata shi bashida kudin kai shi asibity, Gashi nan garin babu itace se daji balantana gwaggo tahada masa maganiHaka tacigaba da zama dashi har yafara kasawa domin kuwa baya iya tashi komai Itake yimasa, ga kafar har tafara doyi dominkuwa ruwa take fitarwa abun bakyan gani, gwaggo tayi fita a titi tana neman taimako amma dkyar tasamu wanda yabata dari biyu itama kuwa gurin cin abinci gari da sugar yakareJoda kuwa duk tabi tarame bata cin komai sedai tasaka mahsifinta agaba tayi ta kuka, haka zata rungume gwaggo suyita kuka, joda da bakar zuciya, ta fita daga gidan ganin yanda aka wulakanta ubanta da zummar zatayi aiki kona Menene tasamu kudi, shago2 take bi tana lekawa , tana neman taimako amma babu wanda yataimaka mata sedai akorataHar tajuya daga wani katon shago naka Yancosmetic , Sega wani babban mutun ya Parker da katuwar mota, tana daga gefe labe tana share kwalla, seda yagama siyayyar sa, sannan yace yarinya meke damunki kike kuka, kara fashewa tayi dawani kukan , tace wai ku cikin gari bakuda imani ne bakuda tausayi zuciyarku bushash shiyace, Mutumin yace to wai me aka miki ne haka, toba baffana bane bashida lfy kafarshi naruwa tayi karuwa kamar hularka amma narasa mai taimakamun mukaihi gurin bokayen turaiMutimin ya aza a dariya bokaye kuma, mai shagon yace alhj wannan fa, yar daji ce dubikayanta ma da kwalliyar ta , joda tafusata shibai taimaka mataba amma yazo yana zaginta dukawa tayi akasa tadauko katon dutse tajefa masa aikuwa Sega glass din gurin yafashe ,mai shagon yace babbar bura uba, wlh se an biyani kona kaiki station, mahaukaciyar banza, joda tace uwarka ce mahaukaciya馃槒 alhj kam yatsaya sororo yana kallanta, Yace yi hakuri manir zan biya kasan fulani da zuciya......... 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�1鈨�Alhj yabiya shi kudinsa kudin 30thnd yace wa joda kibiyoni amota na zamuje gidana inshirya semuzo adauki baffan naki amota, akashi asibity koh! Joda tayi shiru tana kallan motar tace ni zanjiraka anan yace a'anibazan dawo nan ba, zan iya mantawa, takalli mai shago tace Dan allah bawon allah bakomai idan nabisa, munir yayi murmushi lallai wannan yarinyar akwai wautar fulani acikinta inba hakaba seda tagama masa rashin kunya sannan yanxu tazo tana tanbayar shi, Yace bakomai ay halinshi ne taimakoCike da tsoro joda tabisa amotar, Shikuma se murmushin mugunta yake, seda Suka hau titin by pass sannan yadauko wata powder ya shaka mata, bata sake sanin inda kanta yakeba se bayan wasu awanni sannan ta farka ta ganta acikin wata motar tadaban bakowa aciki awani katon fili gurin mai kyau, ahankali ta buda inda taga ana budewa a shiga taji shi gam aikuwa tadingabubbuga motar da karfin allah amma ina bamai jintaAhmed yashirya yadauki Hafsa sukaje dauko dad , Karfe hudu tabuga yakalli Hafsayace dad ya iso, aikuwa Sega jirginsu ya sabka, aka gama duk wani shirye2 daza ayi, Ahmed yace 6ter sefa sunkai 30 mnt kafin Su fito, Hafsa tace abun haushi wlh bari indan sha ice cream, tafita ta siyo ice cream ta tsaya jikin wata mota tana sha gaf2 taji ana dukan motar jiyowar dazatayi taga joda kamar tayi hauka fuskarta duk tajijaIce cream din dake hannunta tayada ta sheka da gudu se gurin Ahmed tace bros c diz motor wata yarinya acike da alama satota akayi saboda daga ninta irin fulanin nan ne na daji fuskarta duk kwalliyar hauka ce, Ahmed yace a ina muje , Atare suka fito daga motar Tanuna masa, Ahmed yayi dannar ganbun har yagaji amma yaki budewa dole yayimata nuni da hannunsa datajanye yafasa glass din amma taki sunkai kusan minti goma amma taki janyewa Ahmed kuwa yafusataHafsa tace bros mezai hana kaballa kanbunyagalla mata harara , kafata karfece dazata bude wannan ganvun, Hafsa tace zaka iya bros ka gwada, mtsss yaja tsaki, hannunsa yasaka a aljihun wandonsa ya ciro bindina yasaita dai2 gurin key yaharba tuni ganbun ya bude yana fitar da hayaki , Hafsa ta karsacikin motar taga yarinyar akwance tace bros tafa suma, Yace tomezan mata kuma ayanzu, Hafsa tace mutaimaka mata mana, Yace wannan kuma se inke zakiyi babu wani dalili dazaisa intava wannan najasar, Hafsa ta gyada kai, tace to kabani key din motar zan kaita hospitalAhmed yace ar u mad, acikin mota na zaki saka mun wannan kazantar, Hafsa batasakecewa komai ba taciro wayarta takira driver tace masa maza2 yakawo mata motar a airport tana jira, Nan da nan kuwa Segashi yakawo mata, tasaka joda acikin motar tayima Ahmed sallama tawuce da ita hospitalAcan asibity kuwa joda seda tadau long time sannan ta farka tanata kankame jikinta, tana fadan daga zaka taimamun seka kawoni garin cire kai, Hafsa ta riketa tana fadan bashi bane kalleni, suna hada ido Hafsa taji wani shock itama kuwa joda dasauri kowannensu yajanye idonsa, joda tace Dan allah waye ke? Hafsa tace idan kinci abinci zan gayamiki joda tace ina wannan makashin yake?Hafsa tace waye makashi kuma ? Joda tace wanda yake yawo da bunduga, Hafsa ta kyalkyale da dariya tace kintaba ganinsa ne, joda tace wlh kuwa Hafsa tace a ina, joda tace adajin mu anan tabata labarin fadawarta kogi ita kanta Hafsa ta tsorata amma tasan Ahmed zai iya wannan Hafsa tace yayana ne, kuwa soja ne shi isa yake yawo da bingida saboda tsaro da ceton jama'a yanzu ba gashi ya cece kiba, joda tace ehh kamHafsa tace meya kawoki cikin wannan motar kuma meyasa kike kuka satoki akayi ne, joda ta fashe da kuka mai ban tausayi, Hafsa tadafata tace kigayamun mana ahankali tagaya mata, Hafsa tace inbanda jahilci yadebeki yazakiga mutum yabiya miki dubu talatin lokacin guda batareda kinsan shiba kuma ki yarda dashi ai nakwarai sun karamta aduniya, kuma har in zai taimaka miki ai seya baki kudin alokacintunda yana dasu amma seya jaki ke bakiyi wannan tunanin ba, joda tace kokadan cikinmuryar kuka, hafasa tace yanzu inane unguwar ku inmaidaki, joda tace masallacinshehu ne, Hafsa tace ina ne masallacin shehu kuma?Joda tace ai ance duk shine babba acikin garin nan, Hafsa tace wane gari kuma mukam nan bamuda masallacin shehu, joda tace asokoton nan akwai wanda baisan masallacin shehu ba, hafsa tazare ido sokoto kuma ke asokoton kike ne joda tace ehh mana hafasa tace tabdi waynzu kina abuja ne, joda tace inane abujan, Hafsatace tsakanin ta da sokoto tafiyar awa tara ne amma inaga ajirgi kukazo, tuni joda takurma ihu tazube kan gado. ........Muje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�2鈨�Hafsa tadago joda tace karki damu yar uwaba abunda zai faru dake se alkhairi yanzu kibari zuwa gobe , se a maida ki garinku, joda tace wayyo allah nah wlh gwaggo zata dakeni kuma inason ganin baffana, Hafsa tace to zaki iya biyar jirgi muje, joda tace Menene jirgi, oh tsuntsu mai tashi zama, Hafsa tadanne dariya tace ehh shi, joda tabata rai kwarankwatsa bazan shiga wannan mugun abun ba na yahudawa, Hafsa dai da taga abun bana karewa bane taje tasamu doctor daya duba joda tace masa Dan allah Yayi mata allurar bacciHaka kuwa akayi bayan Anyi mata allurar, Hafsa takira Ahmed takoro masa bayani haushin yarinyar yaci kashi yace yanzu akanwannan kucakar zakiyi missing din dad kije kaita gida why not da bazaki barta ba ay wannan ma dakikayi taimako ne,Hafsa tace hava Bro yanzun fa idan babartawlh zata iya Fadawa wani mugun hannun daban "plss give me one chance " Ahmed yace shikenan kiyi hankali dakanki kuma zanturo abbas yayimuku komai kina kaita gun iyayenta kijiyo kada kisa ba mun kinfi kowa sanin halina, Hafsa tace tnkuu bros insha allah bazanyi abunda badai dai ba,Haka kuwa akayi abbas yayi musu komai cikin minti ashirin suka bar abuja se skt har suka isa joda bacci take mota Ahmed yatura a airport din skt, tadaukesu se unguwar masallacin shehu, jin atsaya kiyyy da mota ne yasa joda farkawa , tagwale ido tana kallan unguwar juyowar dazatayi ne taga Hafsa na mata murmushi, tace to yanzu gamu a unguwar ku seki nuna mana gidan, joda tace yanxu kwananmu nawa muna tafiya, Hafsa tace kodaya ko awaya biyu bamuyi ba yanzu dai kinuna mana gidan ahankali tanuna gunda almajirai ke daukar karatu, Hafsa tace tnk god muje kohGanin taron jama'a yasaka joda kaduwa , tace lfy kuwa dasauri tashiga cikin gidan carab idonta yafada kan gwaggo tana rungume da hannayenta hawaye nabin fuskar ta Fadawa tayi kanta tana gwaggo bari kuka mana jikin baffan ne koh insha allah zaiji sauki, gwaggo takara fashewa dakuka tareda kankame joda ajikinta, tace joda ina kika je tin safe baffanki yayita Kiransunanki kafin yacika, joda batareda ta fahimci yacika ba, tace gwaggo yana ina in gaidasa, gwaggo tace joda zoki zauna wanda yafimu sonsa yakarbi abunshi, joda tace wai mekike son fadane haka, gwaggo tace wannan waye kuma Tanuna HafsaHafsa takaraso tazauna, joda tace gwaggo itace wadda ta taimakamun dana fada hannun wani azzalumi nan tabawa gwaggo labarin komai, gwaggo tace hava joda muda muke baki agari yaushe zakije nemantaimako bayan Bakisan kowa ba, hafsa taceayi hakuri dai allah yaji kan shi da rahma, joda tafashe da kuka gwaggo baffana yarasu ne, gwaggo tace ya muka iya joda baffanki yatafi gidan gsky sedai muyi masa fatan dacewaHafsa ta tausaya musu sosai, gwaggo tace joda ki shirya mana kayanmu zamu bar garin nan, yau baffanki yace mufita daga gidannan kada Su hadi Su salwantar da rayuwar mu, Hafsa tace yanzu to idan kuka bar nan garin ina zakuje, gwaggo tace neman aiki ba ance kunan cikin gari kuna daukar mata aiki ba, hafsa tace haka ne amma kuyi hankali mutanen duniyar nan se a slow tadauko kudi sunkai 20k tabasu tacegasu kurage zafi nizan koma gwaggo akan murna kuka takara fashewa dashi, joda taraka Hafsa har mota tanata daga mata hannu sannan takoma cikiHafsa kuwa bata koma gida ba se kusan isha'i cike da gajiya ta isa gida, tana ta zumudin ganin dad dinta, Ahmed taci karo dashi a kofa yana fitowa yace mata sannu da wahala, dariya tayi hava bros yade wahala, nidai ina dad, Ahmed yace kinyi late yashiga bacci sedai gobe, ta tabe baki kai bros, Ahmed yayi wucewarshi yabarta atsayeTin 6 Ahmed yaje yatada Hafsata ta tashi tashiga kitchen tareda mai girkinsu akafara hada abinci kala2 zuwa 8 komai ready har gidan angyara takoma dakinta tayi wanka tashirya , sannan tashiga dakin Ahmed tace bros zan gyara dakin, bai amsaba kuma batasa ran zai amsaba, toilet yashige itakuma tashiga gyaran dakin har tagama baifo ba seta dauko wani jarida tana dubawa kusan 15 mnt se gashi yafito daure da towel babba ya yaba wani sama Hafsa tashige toilet din ta wanke tass ta kunna turare ko ina sannan tafitaAhmed yakira dad awaya yace dad kaimu ke jira a dining fah, dad yace ina zuwa, kowa ya hallara a parlour dad kadai ake jira,yafito cikin shigar alfarma, yajanyo kujera yazauna, Hafsa tace mrng dad ya hanya, lfy lau hafsatu , ina kika je jiya? tace dad idan mungama break zan gayama yanzu lokacin karyawa ne, dad yace wato kema kindauki akidar yayanki komai yanada lkcn shi kenan"Murmushi tayi to dad ya kake son inyi ba kyau zance alokacin da ake cin abinci, Ahmed yace to yanzun ma mekike yi ne ? Hafsa ta dukadda kanta tacigaba da cin abunci,Gwaggo sungama hada kayansu kaf sukayi wa hadi sallama , se tasha inda ake shiga mota, tsaye sukayi Dan basu San motar dazasu shiga ba, sudai sunji anata dadan kano2 katsina, kaduna, gwaggo taduba tagamotar da ake cewa kaduna tafi mata dayawa Dan haka itama tashiga ciki , tarungume joda seda motar tacika kaf sannan suka dagaAnkai inda ake tsayawa saboda adan Ci abinci amma ina gwaggo tace bata cin komai joda kuwa najin yunwa amma tadaure tasha, ruwa kadai, matar dake gefensu na lure da yanayinsu aranta tace Tabbas akwai damuwa atattare dasu kamarma basu yarda da kowa ba,馃巹FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�3鈨�Matar tayago masa da malt tamikawa gwaggo tace yar uwa ungo bismillah, gwaggo cike da fargaba tace a'a mungode, matar tace hava keko ba a maida hannun alkhairi baya, dole gwaggo ta karba tabawa joda cikin sauri kuwa joda tacinye Su tass,Matar tace boyar allah meyasa baki siyama yarki abinci ba bayan kinsan tanajin yunwa, gwaggo tace toya zamuyi tunda yn kudin mu ba yawa ne dasu ba, matar tace to yanzu ina zaku, gwaggo tace munfito neman na kanmu neMatar tace idan na fahimta aiki kike nema ko muhallin zama, gwaggo tace ehh, matar tace bakida matsala da wannan ni dinnan yara da manya nake daukowa a kauye na kaisu gurin aiki garuruwa za abaki muhalli mai kyau iyakacinki kiyi goge2 ko kuma wanke2 da sauransu inkuma kin iya girkin zamani shikenan, amma da alama se an gyara ku akwai dinbin kauyanci acikinku,Gwaggo tace indai zamu Ci musha da muhalli to wlh komi nene zamuyi bama bukatar ko sisi indai muna da wadannan ababen, matar tace inafa dole in wata yayi abiyaku naku salary din, gwaggo tace ina ruwan riba gomaHaka dai suka cigaba da fira har Suka isa kaduna, matar takirga kudin gwaggo tacika mata tabiya ta tajata tace zo muje gidana,haka kuwa akayi suka tare taxi se gidan matar gidane babba mai kyau, Filin gidan kadai yana wani gida ga mota kusan ukku acikin gidan , har parlour Suka je, matar tace kuzauna ina zuwa , wanka tayi tacanzasutura sannan tafito takawo musu ruwa da abinci dakyar suke cin abuncin saboda basusababa , seda ta tabbatar sun koshi sannan tace subiyota ta nuna musu masaukinsu,Katon daki takaisu ciki mai katuwar katifa tashiga nuna musu abubuwan yadda suke toilet tashiga dasu tana nuna musu yadda ake amfani da komai Gwaggo kam imani yakamata joda kuwa ta matso safiya tawaye taje toilet din wani dadi yakamata jin ta bisa kaifa mai shegen laushi, ga bargosuyi rufa, salloli sukayi sannan suka kira safiyaKarfe bakwai matar tashigo tasamesu har sun tashi sukayi mata ina kwana gwaggo nata dada godiya, matar tace bakomai ay yiwa kaine ni sunana hjy binta inada miji yana abuja gurin wani aiki dana guda salim yana America gurin karatu, gwaggo tace allah yabarku da mai gidanki yakara zaman lfy ameen, hjy binta tace joda kinyi brush kuwa, joda tayi shiru Menene brush kuma hjy binta tace zo kiga tajata se toilet tazuba mata colgate a brush sannan tabata tace kinga yadda zakiyi tanata nuna mata kafin tafito kam rigarta sharkaf da ruwaJoda tace gwaggo kinsan abunnan danayiwa hakorana allah dadi ne dashi kamar minti yake, nikuma se tsotsewa nake, gwaggo tace to uwar kwadayi, hjy binta takawo musu tufafi joda kuwa nata duk kananan kaya ne, se dadi takeji ita ke nuna mata yadda ake sakawa da yadda akecirewaAhankali take nuna musu abubuwan zamani, yanzu dai sundan rage tsoro da kyauyanci, tinda har TV suke kallo lfy lau, hjy binta kuwa batayi kasa a gwiya ba tacigaba da wayar musu dakai seda ta tabbatar yanzu basuda matsala da komai sannan tashiga nuna musu yadda gyaran gida da yadda ake tsara parlour sundau kusan wata tana nuna musu abubuwa asarakam tashata agun joda saboda joda akwai barna kamar mage haka takeYanzu suna kan girki ne tinkan Su semo har zuwa abuncin zamani yanzu komai sun iya itada joda wata biyu kenan, hjy binta tace togwaggo yanzu ko yaushe zaku iya barin gidannan saboda yanzu nasan kun kware akowani fanni sannan kuma ni kunga tafiya zanyi so kafin in wuce zan nemo muku gidan aiki mai mutunci joda tace hjy mu munfi son zama dake kinfi kowa kirki aduniya hjy binta ta kyalkyale da dariya taceinjiwa keko joda har wanda suka fini akwaiAhmed zaune a garden yana shan iska yanakallon tsuntsayen dake wasa agurin zuciyarshi fall, gefensa tire ne shike da kayan marnari, kamar ance duba ya waiga bayan sa mezai gani, amina ce sanye da base iya cibiyarta se wando baiwuce gwiwarta ba, rike da kujerar roba zata shiga ruwa, baki yasaki yana kallanta Keee yadaka mata tsawa, seda ta tsorata Dan batama San yana gidan baWani irin iskanci ne zaki zauna ma mutane tsirara haka, Nan gidan kine ko dakin ki, amina tace to naga dai ai bamai shigo mana gida, Ahmed yamike tsaye zanci ubanki wlh, muba maxa bane ko angaya miki yahallata ko uwarki taganki ahaka ballantana mu mazaAmina ta murguda baki Kaji dashi can tafada cikin ruwa se ihu take, Ahmed yafusata ainun, ya zare belt dinsa ya nufi swimming pool din hannu sa yazura yacabko gashinta tuni tabuga ihu kafarsa yasa yabuge mata baki seda yamata liss sannan yabarta agurin馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�4鈨�Hjy binta tashiga tunanin inda zata kai Su gwaggo batareda sun takura ba gidan dai da bataso dole can zata kaisu, tagayamusu Su shirya zasuje gidan aikinsu ba musu suka shirya tin safe bayan sunkarya suka dau hanyar abj , hjy binta tayi horn mai gadi yabude gate din saboda yasanta bata bukatar wani bincike akai,A parlour Suka yada zango, hjy binta tadauko wayarta takira hjyr gidan, amma kafun tafito sunfi karfin minti talatin, sanye yake cikin riga red se wando 3 Q yasan ya Farin glass hannunsa rike da system yafito daga dakinsa,Hjy binta tace a'a Ahmed na baida go fuskarshiba seda yakai bakin kofa sannan yace ehh, tace ygd yakaratu, cike da haushin tambayoyin yace lfy, batareda yajira wani que ba yafice , gwaggo tace wannan kuma fa, ?Hjy binta tace dansu ne shine babba, gwaggo tace to allah yakauta, ameenHjy tafito se wani dagawa take tasamu guri tazauna, tace hjy binta yagari , hjy binta tacelfy lau, hjy dama bawani abu bane yazo daniwadannan dakike gani baki ne daga daji suka fito kuma mijinta yarasu bada dewaba amota na hadu dasu zuwa zauna gurina kusan wata biyu da Yan Kwanaki zuwa yanzu sun waye suna iya kowane ayki na gida, shine nakawo miki Su ko akwai bukatar Yan aiki nan gidan,Hjy tace no binta bana bukatar Yan aiki wadanda ma ke gidan wlh sun isheni, binta tace to hjy kozasu zauna gunki ne kafin in dawo daga zaria, hjy tace binta bana mgn biyu fa, hafsa dake saukowa downstairs duk taji abunda suke tattaunawa, taje tasame Ahmed tamasa bayani yace tomezan musu ne kiji ance fulanin daji ne me zamuyi dasu ne, Hafsa tace yaya taimako nefa kuma binta tace data dawo inba ma bukatar Su zata koma da abuntaAhmed yace Hafsa stay away 4rm here, hafsa da takaici yacikata garden dinsu kawai tawuce cike da takaicin halin yayanta, Ahmed kuwa glass dinsa yasaka ya nufi parlour din hjy nazaune tabawa TV amana, Yace lfy wadannan kuwa? Hjy tace aiki suke nema kuma bama bukata munada isassun ma'aikata, Ahmed yace wannan ba kawar ummah bace, binta tace ehh nice Ahmed ashe zaka shaida ni, Ahmed yace kije kawai za'a basu ai kinyi, binta tace nagode sosai Ahmed allah yaji kan mahaifiyarka ameenHjy tace yazance bana bukatar Yan aiki sannan kuma kadaukesu, Ahmed cike dagadara yace kozaki hana ne nan gidan ubana ne inada right din duk abunda nakeso , hjy tace kai kake da wannan right amma sauran basuda shi, Ahmed yace zakuiya jira inkira kanwata tamuku masauki kunjiko , se a lokacin joda tadago fuskar ta takalle shi, 馃槼 Iye makashi tuni ta kwala ihu, Ahmed yadafe kunnuwansa dajin wannan ihun abunda ya tsana hanyar dakinsa yayi se faman tsaki yakeBinta tace lfy ke joda gwaggo tashiga jijjigata ke lfy, tace gwaggo wlh mubar nan gidan, gidan makashi ne shine Wanda yakashe kada aruwa shine Wanda ya harbi ganbun mota kadan in mutu, binta tace kai joda akwai shiririta wlh yoshe akayi haka wanda baya ko fita kullum yana dakin shi in kuwa ki ganshi yafita Tokuwa gurin aiki zashi, dole joda tayi shiru cike da tsoron zama agidan,Hjy tabar parlour tayi dakinta, ba'ajimaba Sega Hafsa tafito, Lah inna kece dama gwaggo tace nan ne garinku dama, hafsa tace sosai nanma gidanmu ne ina joda, Gwaggo tace ta fita tayo fitsari, Sega ta kuwa ihu tasaki taje gurin Hafsa tace yar uwa, hafsa tace ashe allah zaiyi mugamu , hjy binta tayi musu sallama tawuce cike da jin dadi Dan tasan Hafsa akwai kirkiSeda Suka sha fira sannan Hafsa ta fita dasu zuwa sashin masu aiki tanuna musu masaukinsu, sannan takoma dakinta,dasafe tazo tanbayar Su abunda suka iya koda ta gwada Su sunsan abubuwa da dama, tayi matukar mamakin ganin yadda suka Dan rage hauka da kauyanciJoda ita ke taya mai gyaran gidan aiki gwaggo kuwa kitchen takebin mai aiki suyi tare, kwarai da gaske suke jin dadin zama da gwaggo saboda batada kissa ko kadan komai tsakani da allah take yinsa,Tin ranar joda batasake ganin Ahmed ba sedai tayi ta jin kamshin sa idan yabi ahanya , kullum da jacket dinshi take kwanako ana zafi seta sakata take iya bacci itamakuma Batasan dalilin hakan ba, tofah jama'akuji joda meke damunta ne oho 馃槦Muje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�5鈨� Joda har ansaba da gida ko ina shiga take har cikin parlour abunda sauran masu aiki basayi, hafsa tasa ta ajiki sosai, haka zata yitadibar kayanta tana bawa joda , Yauma kamar kullum tafito daga kitchen tanata wake2 abunta hanunta rike abunci, karab taji taci karo da mutum, gabanta yashiga dukan 3 Dan koba ta dagoba tasan ko waye, tsawa yadaka mata keeee mahaukaciyar inace kina gani kin takani kuma kin wani tsayawa sororo , jikinta yashiga bari tace Dan allah kayi hakuri wlh banganiba, mari taji mai kyau, to ubanwa zai goge mun talkamina,Dasauri tacire Dan kwalinta tashiga goge masa kafarsa bata ankaraba tashar awa wandonsa manja, yana dubawa yace bura uba wlh sena karya yarinyar nan, jikinta yakara bari tafara kuka, tashi tayi zata gudu taji ancabko gashin ta, kalansa take ido cikin ido, Yace ni zaki yiwa iskanci shin waima ubanwa yakawoki nan gidan shegiyamai fuskar jaba, joda tace Dan allah kayi hakuri ba a kaine ka karbemu aiki ba, yakarafusata, Dan ubanki yaushe kika taba ganina, yawulgata dakarfi, se asamam kafar waniDurkushewa tayi tana kuka cikin muryar Su ta fulani tace Dan allah kiyi hakuri wlh bada gayya namiki hakan ba, wanda tafada kan kafarshi yadagota idonta arufe yake tana hawaye jikinta se karkarwa yake, joda kuwa seta rike masa hannu, tana Dan allah kayi hakuri, abunda ya tsana kenan kalmar hakuri, Tasake cewa dan allah fah nace, wanda tarike yadaka mata tsawa you shout up, dagowa tayi tana kallan sa tuni ta ware ido ganinsa cikin kayan soldiers, ubanwa yabaki izinin shigowa parlour nan, Iye, mari yakai mata ba dake nake mgn ba, kucakar banza, hannunta yacire kan nasa, seyaga ta Su lale ashe har tasuma, tsaki yaja ya tsallake ta yawuce,Abdallah yace kai tafa suma, Ahmed cike da tsanar zancen yace to mezan mata, abdallah yace tsawar dakamata ne kana abu se kace wani lion, Ahmed yace shine ai, yayi gaba abunsa, abdallah yadauko ruwa a fridge yazuba mata, ahankali tabude idonta , tana ganin sa tamaza tarufe, abdallah yace kuji shegiyar yarinya to ai sekiyi ta, rufewa ya hankadata yawuce sama ,Ahmed kuwa tubewa yayi yasaka jallabiya zai shiga wanka kome yatuna sekuma yafito dasauri, a parlour yasameta ta kudundume guri guda se rawar dari take, Yace kee wai nan parlon ubanki ne da bazaki fita ba, joda takara matse jikinta, tadanne kunnuwata, abun se yakara fusata tashi , wato bata son jin zancensa kenan, Yace kee wlh zan karyaki kibar nan parlon nace, rerafe tadinga yi har takai bakin kofa sannan tawazga aguje se dakinsu tafada kan gado tana cigaba da rawar dari,Hafsa tadawo daga islamiyya tabiya dakinsu joda, a parlour tasamu gwaggo tana yiwa husaina kitso, tace inna ina JODAtaje, inna tace kishi ga daga ciki, Asaman gado tasameta ta yaye bargon ke lfynki kuwa, joda tace zazzabi kedamuna, hafsa tace Ayya sannu kinsha magani kuwa , joda tace a'a Hafsa tace to bara nakawo miki mgn kinji koh,dakin Ahmed tashiga tayi sallama yabata izinin shigowa dakin, kan gado tasamesa kwance yana shan wakar Kenny G , tace bros maganin zazzabi zaka bani, kina zazzabi ne? tace no bros joda ce ba lfy, Yace you get out banasan renen hankali, tace bros yarinyar daka..... Ahmed you yadaka mata tsawa shout up , bana bukatarsanin kowacce magani bazan bayar ba dz ollHafsa tafita daga dakin cike da haushi batama koma dakinsu joda ba, sallah tayi tayi wanka tasake kaya sannan tasauko kasa danyin lunch, amina na kan 3 star tanakallon star movies , tawuce ta ta hau dining tazuba crab cakes da honeydew peach cooler, tana ci cike dajin dadin abincin, taceamina wlh duk zaman husaina mai girki bata taba mana irin wannan ba, amina tace to waya tanbayeki da iskanciHafsa tace kece da iskanci wlh daga magana zakice mun da iskanci, amina ta taso ni kike gayawa mgn, hafsa tace angayamiki tsoronki nake, tuni hafsa takai mata mari abaki bata sauke hannunta ba, hafsa takai mata nanko fada yakaure atsakaninsu,Ahmed dake son yin bacci yahaniyarsu ta tada shi, fusace yafito rike da belt, turus yayi ganin Su hafsa na danbe , yadunfaresu tuni hafsa ta sake amina tayi hanyar waje tsalle daya yayi yacabkota yashiga zuba mata belt Dan ubanku da girmanku zakuyimana danbe agida Iye seda yamata liss sannan yabi amina da tun tuni tayi sama tasakama dakin hjy keyHjy tace ke lfy kika fado mun daki ko sallama babu, amina da idonta keta wani wuki2 tace bros Ahmed ne zai dakeni, hjy tace to me kika masa ne? Amina tace wai yar iskar kanwar shi ce take gayamun mgn nikuma na bibbigeta shine zai dakeni itama yazaneta, hjy tace to ai kinmun dai2 kada kitaba yarda taranaki.........馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�6鈨�Ganbun dakin aka bugo dakarfi bugu daya yayi masa da kafarshi amma yabude se huci yake , hjy tace wlh karka kuskura kayaba mun yarinya, cike da tsana yake kallonta koke idan kika kara mun zan dakeki balantana yarki, ke kuma ki kawo kanki inda keki inba hakaba wlh idan nakamoki da hannuna senayi miki wanda yafi wanda nayi niyyar miki, komawa tayi bayan hjy tana hararanshi,Ahmed yadunfaresu, hjy takara tareda mike hannayenta, Ahmed yace kijace wlh ko in hada dake, hjy da ranta yagama baci tace shege kake idan baka dakeni ba, tuni Ahmed yacabko ta tareda wulgata se kan gado yajanyo amina yashiga dukanta tin tana kuka har takasayi sannan ya yada belt yawuce yabarsu,hjy tayi ta kururuwa har tagaji, daga karshe tadauko phone takira abdallah ta tsara masa karya da gaskiya, abdallah kuwa yana zana wata exam baisan tym dinda ya yaga papers dinba yabar hall din dasauri baima tsaya Jan mota ba yahau Dan achaba yana zuwa gidan yabude ganbun parlour dakarfi, can gefe ya hango hafsa na kuka bakinta sejini yake, yabuga tsaki yawuce wato ko kanwarshi bai bariba, tun kan ya isa yakejin kukan aminaRungume da hjy yasameta tana kuka, abdallah yace hjy tell me meya miki hadda ke yadaka, amina tashare kwalla wlh bros hadda ita yayita zuba mata belt, abdallah yace to wlh yau gidannan za'ayi kashin kai , hjy tace look son kada kayi fada dashi wlh kasan yadda zuciyarshi take tamkar ta kafiriwlh zai iya illata mun kai abdallah yace komai zai faru sedai yafaru amma wlh ba shegen daya isa yataba uwata yakwana lfyFita yayi daga dakin yadum fare dakin Ahmed amma me seyaji kofar a kulle haushi duk yaci kashi juyowar da zaiyi yaci karo da dad dinsu, dad yarike kuqu yace kayo shan ne shi isa naga kazo zaka ballamasa kofa , abdallah yace dad bansha komai ba amma wlh za'ayi kashin kai agidan nan, dad yace subhanallah Abdullahimekake fada haka, abdallah yace yes dad , Ahmed yace shege kafasa nida kai , dukansu suka juya suna kallonsa yafito daga kitchen rike da cup din coffee,Abdallah yadunfaresa, Ahmed ya ajiye cup din coffee, yatartara hannun rigarsa , dad yace muhammad kada kasoma kaima Abdullahi kada ka fara wlh dukanku zan sabamuku kusameni after magrib, dukansu kowa yakama gabansa, hafsa kuwa tana tashi taje tahada ruwan zafi taga sa jikinta, se baccin wahala, amina kuwa ruwa hjy tahada da towel tagasa mata jikinta tahada mata tea tasha sannan tasauya mata kayaBayan magrib dad yabukaci ganin Ahmed da abdallah , yadau few minutes sannan yace, Abdullahi lfy kake neman fada da yayanka abunda baka saba yiba ? Abdallah yace katanbiyesa mana , dad yadaka masa tsawa, naki na tambiyesa kai dashi wanagani , abdallah yace dad ya za'a yi ace wai Ahmed yana dukan uwata ina raye in kyale ai wlh bazai yuba , dad yace ya isa kai muhammad meyafaruAhmed yazayyane ma dad komai yakara dacewa, dad idan yayi yunkurin tabani da sunan wai zaiyi danbe dani, am so sorry ku kunsan abunda zan iya yi dawanda bazan iyaba yana kai nan yafita dad yace muhammad na sallameka ne, Ahmed yace sorry dad ina bukatar hutu ne idan inajin wadannan abubuwan komai zai iya faruwa so allah ya huci zuciyarka , abdallah yace ahaka dad za kace mun yafini kirki dubi yadda yake gaya maka mgn sekace.......dad yace ina ruwanka tashi kabani guri kuma wlh kaji na rantse idan katada fitinar nan wlh sena batamaka raiAhmed dakinsa yafada kan gado yana maida nunfashi, gani nayi yatashi da karfi yadauko eviron drink yasha nan dannan yaji normal wayarshi yadauko yakira Mahmud, Mahmud yadaga man yatake ne, Ahmed yace mod kazo kadaukeni ina bukatar hutu ne bana bukatar zama agidan, Mahmud yace ok ina zuwa ko bai tanbaya ba yasan an taba Ahmed neMahmud yafito daga motarshi, yakira Ahmed yace gashi aharabar gidan, ko minti biyu ba ayiba Sega Ahmed yashiga mota, Mahmud yatada suka bar gidan se wani gurimai kyau nidai nakasa gane gurin kona Menene nadai ga decoration yayi yawa agurin mutane dai dai ne agurin kowa yana harkar gabanshihafasa tasame joda tace joda zoki gaida dad dina, joda tace a'a Hafsa ni ina tsoron in hadu da wannan yayan nakine wlh bashida maraba da nasara, hafsa tace ke baya nan, dakyar hafsa tashawo kan joda suka je, har dakinsa suka samesa yana karatun jarida, hafsa tace dad wannan itacenaje gurinsu sokoto, dad abun tausayi babanta yarasu, dad yace allah sarki allah yajikanshi ameen, joda tamike tace muje hafsa, hafsa tace kedai bakiyiba wlh daga zuwa, dad yadauko kudi yabata tace sam bata San zancen ba yayi yayi taki karba tacetagodeMahmud yakalli Ahmed yace man wai yaushe zamuyi aure ne nifa nagaji dazama ahaka, Ahmed yace mekarasa da zakayi aure, Mahmud yace tab ni gsky aure nakesoabunda matarka zata maka ba kowace mace zata maka shiba, Ahmed yace tomeka rasa ne arayuwa, Mahmud yace ahhh.....ina bukatar kadaituwa ne damace, Ahmed yace wannan kuma kai yashafa, Mahmud yace kaifa bai shafekabane? Ahmed yace kaga bana San wannan iskanciabar zancen kawai, Mahmud yace niko zanga randa Ahmed zaice wa mace ilove you , Ahmed yace bakuma zaka ganibaMahmud yace to bakasan babies ne kenan?Ahmed yace idan ka haifa naka ma x ok, Mahmud yace kayanka kenan bazaka ji abun ba, Ahmed yace kai bansan bura uba wlh, Mahmud yace allah yashirya ka da girmanka kake zagi, Ahmed yace kada kasake mun wannan zancen ka naji koh..........馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�7鈨�Joda tace hafsa kikaini dakinki ingani hafsatace to muje yanzu ma , joda tace yayanki bashi nan, hafsa tace eh muje kawai hafsa tarike hannun joda suka shiga parlour sukayi sama, a dakin hafsa joda se ihu take ganin yadda dakin hafsa yake tamkar a TV, seda Suka gama tsiyarsu sannan suka sauko kasa gurin saukowarta ne tahadu da amina, amina tadinga yimata kallan wulakanci, ke ubanwa yabaki izinin shigomana parlour kaxama kawai kucaka, tuni idon joda suka cika da kwalla, hafsa tace ni naba ta izinin shigowaAmina taci kwalar joda ta hankadata kasa goshinta yafashe tuni joda tabare baki, dai2 nan Ahmed yadawo, dafe kansa Yayi oh god wai wannan wace irin yarinya ce kullumzai hadu da ita kuka yake ganin ta nayi, yadaka mata tsawa kee uban me kike a parlour nan, tuni jikinta yadau bari yakankame kujera hafsa tasauko kasa tace joda zo muje ciki, Ahmed yace gidan uwarkizataje koya, shegiya, Yace kee wlh idan nasake ganin ki a parlour nan sena kare ki, amina tace yayi dai2 bros shi isa nake son......bata karasaba yace zan ballaki ina magana kina mgnYasaki kallon joda da ke makyarkyata yace kee bazaki bar nan gurin ba senaci ubanki joda kam har fitsari tasako, Ahmed ganin tamasa banza yasa yayi wulgi da rigarshi yadunfaro ta, joda dakejin kamshinsa nakara matso wa takara runtse idonta, cabko ta yayi da niyyar kadi da ita waje, seyaga tana laudi kamar matatta tsaki yaja yasaketa da karfi, Wata irin ajiyar zuciya tayi sekuma tayilamo kan carpet, hafsa tabuga kalima bros jifa yanda kasako yar mutane akasa, Ahmedyace kema wlh nakusa kakkaryeki idan nasake ganin kin shigo mana da wannan kucakar acikin parlourAmina dake tsaye tayi murmushin jin dadi, tawuce abunta, hafsa tarasa yanda zatayi da joda dakyar ta da gata ta kaita dakinsu tayi sa'a gwaggo na sallah, ta tsaya har tagama sannan tace ma gwaggo faduwa tayi gwaggo tace oh ni gurin rashin ji koh, gwaggo tana dubata tace amma dai taga wani abun tsoro koh, rabenta da irin wannan yanayin tun randa tafada kogi a dajin mu se shekaranjiya tace mun wai tagakwado ne,Hafsa tayi shiru to kadai Ahmed dinne tagani shine ta boye mata tace kwado, Su ina sukaga kwado, wanga gidan, hafsa tace gwaggo yanzu ba abunda za'a mata takomanormal , gwaggo tace tomezan mata tunda nan ku bakuda itace ballantana in hada mata magani , hafsa tayi tagumi tana kallanjoda tace to gwaggo Dan rufeta kamar zazzabi ne ya rufe ta haka kuwa akayi gwaggo tarufeta tayago kyalle ta dora gurin da goshinta ke fitar da jiniTin ranar joda batasake gigin zuwa parlon Su ba sedai hafsa ta cimmata Su sha fira abunsu, gwaggo tace joda nikam ba makaranta a unguwar nan dazaki rika zuwa ni banga amfanin zamanki anan ba , joda tace to gwaggo sedai in hafsa tazo musa tanbaya, haka kuwa akayi joda ta tanbayi hafsa, hafsa tace suje islamiyya dinsu yafi sauki, hafsa taje tasame Ahmed tace bros I need help plss, Ahmed yacire glass dinshi yace to ina jinki, cike da tsoro tace bros joda ce......hannu yadaga mata bana bukatar duk wani abu daya shafeta kibar mun dakina kawai, ba musu tafita cike da haushin abun to ita yanzu ina zataje ne?Abdallah yafado mata a rai , dakinsa ta nufatana adduar allah yasa bai sha komai ba, takuwa yi sa'a yana nan lfyqlw ahankali tagaidashi ya amsa tareda tsare ta da ido yana son jin abunda ketafe da ita, guri tamakanta tazauna, bros Dan allah joda ce keson asaka ta islamiyya kuma kaga islamiyyanmu dole se ubanka ko wani nmj yasaka hannu ake karbarta shine naxo Dan allah kataimaka wlh maraya ce kamata komai nasan zaka iyaAbdallah yagalla mata harara Ohh yayanki ya koroki shine ni zaki zomun, shinma wayejoda? Tace plss bros nasan kafi Ahmed tausayi, wannan yarinyar da aka daukesu aiki last time, abdallah yace kan uba yarinyar da hjy tace bataso yayanki yanuna mata isa, to wlh ko karye ta zanyi kibacemun dagani ba abunda zanmata wlh sumuy2 ta tashi tabar dakinHaka tasame joda tace mata se karshen wata za'a fara karbar new students, bayan kwana biyu shugaban makarantar Su yakira hafsa yace yana ana bukatar dalibar tazo dan amata enterview hafsa bayadda batayiba taji waya saka hannu amma malamin yace bai shafeta ba bata kawo kowaba illah abdallah Dan tasan shi da tausayi sabanin Ahmed...........Muje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�8鈨�Hafsa tasamu joda tamata bayanin komai tace tashirya ran asabar zasu fara zuwa domin a gwada karatun ta , tanason zuwa tayi wa abdallah godiya sekuma tafasa, tace nasan ma zaiyi domin shi baidauko halin hjyr Su duka ba hasalima Itake kara turasa ga aikin da bai dacebaJoda tafito da katuwar kula zata kaima masu gadi da drivers abincinsu tafe take tana wakokin Su na fulani, tana shan alawa, doguwar riga ce ajikinta wadda hafsa tabata kanta sanye da hula kanta kuwa kitso daya aka mata yaxubo har kan gadon bayan ta,sallama tayi musu mai gadi yakarba tareda fadan a'a yar fillo yau ke aka bawa kular ashe dai kinyi karfi, murmushi tayi tace kaifa kaci ka tsokana ita wannan kular ce bazan iya dagawa ba ta ajiye tajuya har tayi nisa yace kee yar fillo ba tire kodaya joda tadafe kai oh ni zainaba wlh namanta bara nakawo mukuTajuya aguje tana dariya, se jinta tayi kamartafada kan wani abu dago kanta tayi abunda tagani shine yai bala'in firgita ta, tuni ta San kare guri guda takasa motsi, kallo daya tayima idonsa tuni fitsari yazo mata, rike kugunsa yayi yana mata kallan wulakanci kamar wanda yaga kashi ,itakuma tariga ta sankare ko motsi batayi, hararar dataga yana mata ne yasata rufe idonta, tareda rufe kunnuwata, Ahmed abunyabasa mamaki wai Menene wannan jakar take nufi batasan jin muryarsa ne batasan ganinsa shine dalilin dayasa take rufe idonta da kunnunwata idan tagansaKarasowa yayi kusanta azatonsa zata gudu seyaga taki motsi, kafarsa yasa yataka ta, da shegun takalminsa huuww taja iska hawaye suka cigaba dabin fuskar ta idonta arufe, Yace Keee ni sa'ar ubanki ne dazaki rika bi hanyata nan ba'a gayamiki gurin zaman mota ta bane ba uban dake binsa,ko tsuntsu bai isa yabi wannan hayaba nabarsa balantana mutun, dakyar ta iya hada kalmar Dan allah kayi hakuri , Tau 馃槼batasan abunda yatsana ba kenan, Ahmed kee how dare you " ni ni zaki....sekuma yayi shiru ganin tanata langwadi da alama kasa tayi idonta se lumshe wa yakeTimm kakeji tafadi kasa, somammiya , tsakiyaja wannan yarinyar wlh na tsaneta bana San ganinta shegen kukan tsiya, tome ma yamata ne dazata suma mtsss yasake Jan wani tsaki yashige motarshi yayi gaba abunsa yabarta nan kasa zube ga kafarta daya taka har kumbarta ya sabule kefe ,Abdallah yashigo gidan asaban mashin dinsa, har yayi parking yasauka kamar ance juya, yaga joda kwance, ya salam meyasame wannan yarinyar, ganin layin motar Ahmed yasa shi cewa "oh gosh "ita wannan yarinyar batasan nan gurin Dan iskan yaron nan bane,I know shiyamata wani abu myb ma yataka ta da mota ne , ruwan dake hannunsa yadauko yazuba mata, bude idonta tayi tareda fashewa da kuka , Yace x ok2 meyasameka ne? tace bkomaie faduwa nayiAbdallah yace amma dai koma ya ne kada kisake, bi wannan hanyar kinji koh, Ta daga kai, Yace gud yanzu ina yake miki ciyo ne, joda tace bakomai lfy lau nake, abdallah yace ok tashi kishi ga daga ciki,kasa tashi tayi se cije lebe take, idonsa yakai kan kafarta yace no wonder nasan zaiiya wlh, kiyi hakuri kibarshi da allah kawai haka yarika hannunta har kofar dakinsu sannan yawuce side dinsu........馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 2鈨�9鈨�Tin kan uniform har zuwa sauran littafan makarantar bawanda malam bai bawa hafsa yace tabawa joda, hafsa abun duk yadaure mata kai aranta kuwa tace nasan abdallah ne akwai son taemakon jama'a, cike dajin dadin abun taje tasame joda takaimata uniform din joda kuwa se murna take tana fadan kai tufafin kyawawa ne , riga sawando ne red se hijab white, gakumaniqab black ,Yau tin safe tashirya tayi wanka dama kuwahafsa tagoge mata uniform dinta, jikinta harrawa yake tasaka uniform din, hafsa tashigo tasameta tana famar yin kwalliya, hafsa tace kaddai naga kinyi wannan digen2 naki na hauka, joda ta tabe baki nifa idan banyi wannan kwalliyar ba se inga kamar nakode hafsa tace bakuwa zakiyi ba bani powder nan, tasha famata powder tareda pink lipstick, hafsa tace kam kungan ki kuwa gaki dakyau amma kina bata fuskarki da haukaJoda tace ni wlh banga nayi kyau ba, fuska ta kamar anwanke Farin kyalle, hafsa ta kyalkyale da dariya tace to naji badai zakiyi wadda kike soba, yanzu zanje in shirya kafun nan kin karya , joda tace ke hava dai ba kisaka mun wannan bakin kyallen ba, hafsa Ohh. ..ni manga bani nan tinda ke komai bazaki dakanki ba gwanda ma ki koya tinyanzu bazan zauna zaman shirya ki ba kullum takarba tasaka mata sannan tawuceJoda tagama shirin ta tsaf hadda wani aza bag kan kafasa Su joda an waye 馃槀 kofar parlour Su ta tsaya tanata kwalama hafsa kira, Ahmed dake gurin fridge zai dauko ma dad lemo duk haushi yacikashi wai wacece wannan tsaki yaja yawuce dakin dad , hafsatafito tace to uwar Yan zanzana gani nafito, hafsa tace wai kinganki kuwa kamar bulaliya bakauri ba kiba se tsawo kamar jimina,joda tace to ai nafi wasu kuma ai kema duk gudanku dogaye ne jifa wannan yayan naki tsawonsa yakai na rakumi, hafsa tace allah yasa yajiki wlh yafasa bakinki, joda tace nidai muje Dan allah gabana ma keta faduwa,, abdallah dake fitowa yace to ay seki dauko shi, Karasowa yayi kusanta yabude nikab din yarabb yafada wow whatapp veuryfull, hafsa tace bros kodai2 abdallah yace zanci ubanki wlh kodai me , Ahmed dayake kallon duk abunda suke yasauko fuskar nan ba annuri yace kewai Dan ubanki ban hanaki shigowa nanba ido tazare tayi bayan abdallahAbdallah yace wai me wannan yarinyar ta tare maka ne inaruwanka da ita tinda ba akanka take saukaba, Ahmed yace zanfasa bakinka wlh nikake gayawa mgn, abdallah yace ke muje inyi drop dinku, Ahmed yace Hafsa wlh idan kika fita sena karyaki kinsan kuma zan iya, joda kam kasa motsi tayi still kuma idonta nakansa takasa daukesu ballantana tayi takanta, Ahmed yace mekinwani kafeni da mayun idonki, hawaye kadai kesintiri a idonta, Ahmed yace kobazaki fita bane, jus dinda ke hannunsa ya watsa mata a fuska gashi da shegen sanyiAtake tarufe idonta hijab dinta duk yalalace yayi colour din lemon , ganin taki koda motsawa yakara fusata shi, yadunfarota kamar wani lion, yana kawowa gurinta yacabko wuyanta sezare ido, yake yace keeee wlh sena.......baikai karshen zancen ba yaga tana lumsashe idonta tana wani laudi kamar taliya sekuma tayi kasa bata kai kasaba saboda yaci kwalar hijab dinta dogon tsaki yaja yasaketa carab abdallah yacabketa tafada kansa, cike da takaici yace amma dai wlh Anyi marar imani nan gurin , yarinyar nan totally bata San ganinka muryar ka tamkar aradu yake agurinka amma kuma duk bai isheka ba seka hada mata da tsawa wlh watarana kashe ta zakayiHafsa dake gefe se kuka take, Ahmed yace kasan zan iya kasheta koh? Abdallah yace I know wlh nasan zaka iya, Ahmed yace so keep mouth, yajuya ga hafsa keko.....sekuma yafasa fadan zancen yakama hanyarshi, abdallah yace Hafsa bani ruwa plss,Dasauri tadakko gorar ruwa aka watsa mata, dakuka ta tashi, abdallah shi yayi tabata baki akan abunda yake faruwa, hafsatadakko mata wani hijab tasaka sannan tace kije bros abdallah yakaiki ni inazuwa, ba musu tabisa, cikin motama hakurin yake bata har suka isa skull yaje sujira hafsa tinda banisa , akafa hafsa tazo sannan yawuce sukuma suka shiga skull din............馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�0鈨� Seda yaga sun bace sannan Yakoma gida, hafsa taja hannun joda se office din headmaster, shi dakanshi ya gwada karatunta Alhamdulillah tanada irin nata kokarin sedai batada tajweed saboda haka aka bata aji biyu, har dai aka tashi makarantar jikinta bai saku ba tana tinanin hali irin na wannan mutumsuna shiga cikin gidan joda tabi hanyar dakinsu dasauri hafsa tariko ta, tayi narai2 da ido, tace Dan allah joda kada ki gayawa gwaggo abunda yafaru Dan allah wlh koni zai iya yiwa abunda yamiki fiyema, joda tace karki damu hafsa bakomai muke gayawa iyayenmu ba, wani lokacin mukan manta damuwa ko bacin ran dawani yasa kamu amma iyayenmu basu manta ba, hafsa tace nagode a kullum ina mamakin kaifin hankali irin nakiJoda tace bakomai nakoyi hakuri daga gurin baffana , na kuma samu kyakkyawar tarbiyar da har karshen rayuwa ta bazan yada ba, ina fatar ma infi hakan, hafsa tace allah yajikanshi ameen, hawaye suka gangaro afuskarta Dan kar ta saka hafsa kuka yasa tawuce abunta itama joda tagoge idonta tashiga dakinsuHar tabude kofar dakinta taji anjawota dakarfi, Ahmed ne yace ke Dan gidanku ni zaki cewa wai haka halina yake koke zanmahaka? Meyasa kika ce karta gayawa uwarta zata rama mata ne Iye? Answer me, hafsa tace bakomai bros banason wani yaji haushin ka koya saka ka ranshiTurata yayi dakarfi , tareda Jan hancinsa tsaki yace nafi bukatar wanda zaiji haushinaakan wanda zai soni, nagaya miki bana bukatar ganin wannan yarinyar a parlour nanidan kuma nasake ganinta dake dakika kawota da itadin wlh duk sekun ji ajikinku ,hafsa batace komai ba har yashige dakinsa,sannan tashiga nata kan kujera tazauna tana tunani Anya Ahmed Dan ummah ne da dad, Wata zuciyar tace dansu ne mana ay zaka iya haifuwar mutun baka haifi halinshi ba , allah kanunamun randa bros Ahmed zaigyara halayyarshi ameenAbdallah yakasa sukuni , yarasa so" ko " sha'awa yake yimata, to inma sone mezai so ga village girl, inkuma sha'awa ce batadaabun da zaisa aga sha'awar ta yanzu tafara boobs sedai akwai baya, to kodai small lips dinta ne kejanka, mtsss a'a idonta ne, kai aykoni manyan ido ne dani, to inaga dimple dinta ne, can kuma yace kai natina wlh gashinta yayi tsawon na ameesha phatal , hmmm kuji abdallah fah 馃憟馃徎 dole dai kadauki daya ko so ko sha'awa "Amina ce rike da hannun saurayinta suna fira amota , Ahmed yashigo da motarshi yaje yayi yayi parking tuni tasaki hannunsa tace OMG, baby kaje gida wannan yayan nawa zai takura mun yanzu, wanda takira da baby yace akanme zanje gida sedai ko inkin gaji daganina ne, tace no wlh, Yace to sbd me zanje gida ba inda zanje idan zuciyar sojoji ne dashi nikuma ta kafirauna ce dani ( wa'iya zu billah) a kullum murika kiyaye harshen mu daga alfasha ko abun kiAhmed yashiga gida abunsa tamkar baigansu ba , Wata ajiyar zuciya tayi , suka cigaba da soyewarsu, can ajima kadan Segashi, yafito yacanza kaya, bainufi ko ina ba se gurin Su, yana zuwa yasamesu manneda juna wai Su kiss suke , baiyi wata2 ba yashiga jibgarta ita har saurayin nata seda yaci ubansu dakyau sannan yace ke kunnen kashi ne dake ko? Kaikuma idan aurenta zakayi ina bukatar ganin iyayenka idan kuma ba aurenta zakayi ba, to wlh kada ka kuskura nasake ganinka akofar layin nan,Yaron yataso se huci yake, yana fadan bari ganin kayi mana riske, wlh se in karya ka, Ahmed yazaro ido hava dai, yaron yace sosaima kuwa idan ka cika ka ajiye belt din ni bana fada da bulala, Ahmed wohoho wlh ina tausayin ka yoko ubanka ya isa yadunfareni balantana kai, ay nadakeka da belt shine sauki, Dan ina samaka hannu wlh zaka.......Hannun rigarsa ya shiga kwashewa amina tace sayyid wlh kada ka hada jiki da shi zai kasheka abanza, sayyid yakara fusata yakuwa yi cikin Ahmed, Ahmed Baiko motsa ba har yagama naushinsa Ahmed ko tangadawa baiyi ba, se abun yabashi tsoro Ahmed yace meyasa kake mamaki ne kagama, nan yamasa shegen naushi aciki tuni yadi kasa , Ahmed Au dasauri haka, hannu yadaga tuni sayyid yace plsss kar ka fidda mun yayan hanji 馃槀 Ahmed yace no its ollryt am leavingYamaida kallansa ga amina tuni tayanka aguje , yabita dai2 wata mota yahadu da joda kanta ba Dan kwalie Anyi mata kitso daya, dasauri tajuya yace Keee aykuwa ta tsaya bata juyo ba, yana isa gareta, yajanyo gashinta dakarfi, seda tayi kara mekike anan ne?Batace komai bah jikinta serawa yake gashiyaki sakin kanta kuma da zafi, hawaye suka fara mata zuba , Yace wlh idan kina mun wani wai sunanki na qarya sena idaki, ni dodo ne koya, idonta arufe, har yagama yaturata kan amota yawuce, joda tadade tsaye ahaka sannan takoma dakinsu abunda zatayi ma seta fasa.......Muje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�1鈨�Tin randa joda tafara fita islamiyya wani yasir yake damunsu haka zaiyi ta bibiyarta , tin hafsa na zaginsa har tagaji tasaka masa ido, Wata rana yakafe Su dole hafsa tabasu guri dai2 gate din gidan, Nan yagabatar mata dakansa , akan cewa shifa yana sontaso kuma da aure,joda tace gaskiya ke bakida hankali yanxu ni zakisewa aure yaushe na iya tuwo bare nayi aure, yasir kuwa yadinga dariya, Yace ke baku dade nan garin bane? Naga har yanzu hausar ki se ahankali , joda tace bansaniba, yasir yace yihakuri ranki yadadeAna haka se ga Ahmed yazo zai shiga gidantin anesa yahangota yana mamakin yadda wannan tsular yarinyar ta isa tsayuwa da samari wlh kuwa watan cin ubanta yatsa ya,har zai fito kome yatuna sekuma yabasar, aransa yace ko gardi goma zasu cita agabana baruwana tinda ba hafsa ce ba ko amina,Seda yakai dai2 Su sannan ya watsa musu ruwan cabi yashige gida abunsa tamkar baigansu ba, yasir yace amma dai wlh Anyi matsiyacin yaro nan gurin dubi fa yadda yalalace mana sutura, joda tace bakomai kayi hakuri baiganmu ba ne, yasir yace kamar ya baiganmu ba makoho ne shi koya? Joda tace to ai seka rama koh, yasir yace a'a yawuce, Nan yamata sallama yawuce,Joda nashiga dakinsu gwaggo tace to joda zoki tayani fura zanyi yau nagaji da wannan cimakar, haka kuwa akayi suka zage dantsesuka hada furar Su aka gyara nono aka zuba馃構 haka masu aykin sukayi ta santin furar kamar me,Joda tazuba ma hafsa a jug tabawa wata yar aiki takaimata, abdallah yafito daga dakin hjy shida amina yahango hafsa na shan fura, Yace iyyee hafsa ina kika samo kayan dadi? Hafsa tace wlh gwaggo tayi furar kamar ta ummah, abdallah yace hava dai , hafsa tace wlh fa bros akwai dadi, abdallah yace ok tashi ki karbo mun tawa hafsa ta ajiye cup din tafita aykuwa abdallah yadauko cup din yana sha baisan tym dinda ya shanye ba tassHafsa tashigo rike da plastic cike da fura, tace bros yau celebration na fura da nono 馃槅 abdallah yace nidai zoki zubamun , amina tace bros yanxu furar fulani zaka sha ' fulani ma na daji ne fa , abdallah yace wadannan sunada dffrnt ne basuda kazantar komai nagani da idonaAmina tace to nima asammin inji yadda take tana sha tafara woww wlh kamar furar ummah baqarya wlh hjy tafito tareda dad sewani manne masa take abunda Ahmed yatsana kenan yaga tana yiwa dad dinshi abu agaban su , dad yace bidirin me ake ne naga kun hadu haka, Hafsa tace dad fura muke sha zoka sha kar a barka abaya , Dad yace a'a nikam raben da nasha fura tin bayan rasuwar saratu Bankara shan fura ba duk wadda nasha bata min kamar tataAbdallah yace to kuwa banda wannan kamar hannun ta yake, dad yace ar u sure, abdallah yace yes dad, dad yace idan najita badai2 ba zanmuki duka, sukace sun yarda Amina ce tazuba mishi hafsa takai masaYana kai bakinsa yace wonderful diz x a great, wlh sak hannun saratu, hjy najinsu tayi musu banza, dad yace wa yayi furar haka, hafsa tace dad masu aikin da aka dauka ne last time, dad yace dz gud to ina son ganin wannan bafulatana domin ina son cimakar Su, hafsa tace to dad se randa kake free koh? Dad yace se 2morrow hafsaSallama sukaji anyi daga waje, tsalle amina tadaka antyba2 wlcm, hjy tace Oyoyo big sister, mansura tayi ma kanta guri tazauna , tagaida dad ya karba bayabo ba fallasa, hafsa tace barka da zuwa antyMansura ta ballamata harara, kamar batajiba , dad dake kule dasu yace zonan Hafsa yajata sukayi dakishi Mansura tace yo naji iskanci wannan fa bayarshi ceba, hjy tace Uhm haka yake banbanci yake nunawakiri2Mansura tace to ai laifinki ne anty kizo mukaishi gurin mai kwalshi aikinshi kamar yankan wuka ne , hjy tace kenifa nagaji da barnar kudina abanza aiki baya kyau Mansura tace tab wlh wannan ba kuskure, ana haka Sega Ahmed yashigo ko kallan inda suke baiyi ba yanufi kofar dakinshi hjy tace Ahmed........yatsa ya cak batareda yajuyo ba, tace bakagan mansura ba halan? Dogon Tsaki yaja yawuce dakin sa.........馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�2鈨�Mansura tace amma dai wlh so wawa ne inba hakaba ya za'ayi nmj yamun haka anty dubi yadda ake mun rushing amma ni duk duniya wlh banga namijin danakeso kamar Ahmed ba, abdallah yace yo naga maita tinda baya sanki ay seki kama gabanki ko nibanga abun so acikin Ahmed ba wlh indansaboda kyan sa ne, Tokuwa kisani kyan Danmaciji ne, gabansa fari bayan sa baqiKina auren Ahmed ina gayamiki kin gama yawo, hjy tace kai ya isa shasha ba uwarka ceba kawani tsayawa kana bata mgn haka, amina tace wlh da gaskiyar bros, anty surahidan idan kika aure bros Ahmed wlh kashin ki yabushe, to waima taya zai aureki bayan ko tantance fuskar ki baya yiHjy tace bawani nan fuskar kowa yasani iskanci ne kawai, mansura tace nidai anty kona hakura dashi kawai kada naje nadawose zanbaga ma malan kudi nake amma har yanzu ba labari kuma da alama wannan yaron bazai canza baHjy tace dubi ke Dan allah watsamana plan zakiyi? Mansura tace ohh. ..... namanta ne sam wlh, hjy tace iyye wato so ya rufe miki ido to wlh tin wuri kisake tunani abunda muka tsara shi zakiyi ba soyy ba kada kije kimanta shaukin so yadebeki , hakarmu takasa cimma ruwaMansura tadafa hjy tace karki damu antyna komai zai tafi yadda ki keso baxan baki kunya ba kinfi kowa sanin waye ni, abdallah yaja tsaki yace duk dukiyar da allah yamukubata ishekuba sekun kara da kwadayi, hjy tace me kuka cemaka zamuyi da iskancin ka abdallah yace mama niba yaro bane kuma nasan abunda nake, ko Dan primary yaji firar ku zai iya fassara ta balanta mai mastersHjy tace amina kema wai kin fassara Amin ta kyalkyale da dariya hava mamana namiji ma yafahimci firar ku balantana ni mace , hjy tace to wlh ku kama bakinku banason jinwani zancen, karku sake zanjen nan nasake jinsa kunan ta dashi kwata2Abdallah yata be baki yace whatever dai you shall remember Ahmed x solider, bazaku iya hada masa tuggu ba, sannan kwan wayo ne nagaske ko hanjin mutun yana gani, Ahmed zai iya kamaka yamaida laifi akanka tahanyar dakuke son bi, hjy tace munji dai jeka2 mungode da tunarwa,Abdallah yayi murmushi yace anty surah idan kika nace kan auren Ahmed wlh am telling you, u will on dy n regretting, so u hv to take a hrt, hjy tace kai bamusan iskancin banza ina ruwanka, abdallah yace mamma lamme tell her my point. hjy tace kai kabacemun dagani nace, abdallah yace ollryt am leaving, hjy tarakashi da harara Mansura tace anty aduba zancen abdallah fah! hjy tace idan zaki dinga biyewa zancen sa zai karya miki da zuciya, kada kiyarda ke macece kinfi kowa sanin namiji yaro ne dukyadda kikayi dashi haka xaibi , mansura tace anty ban katsekiba taya kenan?hjy ta harareta tace kidauki hankalinsa mana tahanyar shiga jikinsa duk yadda kika San kinsaba haka zakiyi masaMansura tace ohh.....antyna ay banfahimceki bane daga farko se yanzu, to ai anty kuma kinsan shi ko kallan mace bayayi bansan tayadda zan bullo masaba, hjy tace ke kizama mutun ayi mgn dake hava Dan allah, dubeki gafari gakyau kinadakomai da namiji yake buqata diri se Wanda yagani boobs gasunan kamar zasuyi magana, mansura tace kai antyna, kuma boobs dinfa sunsha mouth din guys amma ko kadan sunki zubewa, hjy ta zungureta ke dallah yimana shiru,Yanzu bazama zakiyi ba kitashi kishiga dakinsa kifara aiki, mansura kam wlh anty kwarjininsa yayi yawa har bana iya hada ido dashi, hjy tace to wlh kuwa dasake dole kicire tsoronsa zanyi wani abu akai, mansura tadauko wani tirare tadaka, takalli hjy sukayiwa juna murmushi sannan ta dunfari dakin Ahmed..........馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�3鈨�Tana isa tamurda kofar takuwa yi sa'a kofarabude take, da sallamarta tashiga ciki, bata samesaba gabanta se bugawa yake, kan kujera tazauna, tana karewa hadadden dakin kallo, se kamshi kakeji kala2, kofar toilet aka murda hakan yadawo da ita daga duniyar tunani , Ahmed kuwa baikula da mutun ba daga shi se towel iya cinyarshi, shafe jikinsa yayi sannan yafesa body spray kamar zai kare gwangwanin, sannan yashiga shafa mai , haka yake bin jikinsa kaba2 yana shafa masa mai sannan yadauko cum yataje sumarshi, kamahin mansa kadai da sabulunsa yasakata cikin wani yanayiYawunta tashiga hadiya lokacin datake karewa surarsa kallo, farine dogo Mai faffadan kirji jikinsa duk gashine Wanda yake kwance luf, duk gabobin jikinsa dogaye ne , idonta takai kan hancinsa dayake dogo tamkar na hrithic roshan , se manyan idonsa, ga eyelashes dinsa zara2 kamar namace, girarshi kuwa haka take kwance maiyawa da ita , lips dinshi takuarawa ido gasu pink sosai gasu very small , sajensa luf kan fuskarshi , aranta tace ance Dan Adam baicika goma ba Tokuwa yau naga 12 ma ba ten ba domin Ahmed ba abunda yaragu dashi kyau dukiyailimi, ni kuwa asea nace me ake da hali irin nashi mutun kullum kirarshi ahade yana shan naganitowel din yake kokarin cirewa har yaxare daurin, kamar ance duba, yaga mace acikinmirror takafesa da ido se murmushi take , ohh..shiit yafada tareda sauri yamaida daurin , wani karamun blanket yadauko yayi rufa dashi yaxuyo afusace, kee mekikeyi adakina? Mansura ta taso cikin wani tako taiso gareshi, Seda taxo daf dashi sannan tace hava my Ahmed kasanfa ina sonka meyasa kake son bani wahala ne, Ahmed yacije lebe yanunata da yatsa yace kinsan duniya babu abunda natsana sama da ace ana sona da cewa kikayi kinfi kowa tsanata toda zakifi burgeni, mansura kuwa taji haushin kalamansakwalarshi taciyo tace Ahmed look at me look into my eyes, babu namijin danakeso aduniya sama dakai wlh Ahmed ina sonka fiyeda yadda nakeson kaina, Ahmed yawanke ta damari Seda taga wata wuta, Yace nizaki ciwa kwala, agabana kike fadanwai Kina sona, to wlh ina gargadinki ki fita daga rayuwata, inbahaka ba wlh senasa kinyi nadamar zuwanki duniya , yahankada get out marasa kunyar yarinya komata sunkare aduniya Kina tunanin zan so kine, wawiya jahilaYa isheka Ahmed bari ganin ina sanka kanemi gayamin magana, Ahmed yace ohh to ay seki rama, hawayenta tagoge tace wlhAhmed baxan taba dena sanka ba har abada kuma wlh sena aureka zaka shigo hannu, Ahmed yajuya yacigaba da shirinsa tamkar baisan da mutun adakin ba, dole daidataga zaman baiyi tafito cike da kunci tanajin haushin kantaTsaki yaja yace mezanyi da wadda takusa zuwa age dina, wayarshi yadauko ya duba, 5miss call daga Mahmud, kiranshi yayi kamar zata tsinke sannan yadaga, Mahmud yace wai ina ka shiga ne inata call dinka , Ahmed yace ina toilet ne, menene schedulea yau ? Mahmud yace sekazo zakagan, Ahmed yace please kazo kadaukeni, Mahmud yace kaikuma fa sekayi me? Ahmed yace inzaka zo in kuma baxaka zoba shikenan, Mahmud yace aikuwa bazanzoba, Ahmed yace idan kazo bakamunba wlhTsab ya gama shirinsa yatada sallah azahar,sannan yabi lafiyar gado har yasoma bacci can yaji ring din wayarshi yadamesa tsaki yaja yakara shigewa bargo can kuma tasakeruri, dolensa yagada baima duba Wanda yake calling dinba, jin muryar commissioneryasashi tashi zaune, Yace Ahmed bakaji Kirana bane?Ahmed yace sorry sir " ina bacci ne, cmsner yace Mahmud baigayamaka ina nemanku ba?Ahmed yace ni baigayan komai ba, cmsner yace ollryt kuzo yanzu ba atare ina nemanku, Ahmed yace sir seyanxu2 kake buqata cos wlh bacci nakeji, cmsner aranshi yace inbanda kokarin yaronnan da davaru wlh dayanzu ya'ajiye aikinshi, cmsner yace yes yanzu nake nemanku bana bukatar sake nemanku,Ahmed yaja tsaki ya tsinke wayar yakoma kan gadonshi yacigaba da baccinsaHafsa tasame gwaggo taga yamata yanda sukayi da su dad, gwaggo tace bkomai ay aykinmune zanrika masa kullum hafsa tace yauwa gwaggo na wlh da dadi, gwaggo tamata dariya, yau harda danbun gero zanmuku, hafsa tace lah gwaggo Kin iya, gwaggo tace idan anyi zakigani hafsatu , hafsa tace to kiyi dayawa saboda kowa yanaso, gwaggo tace karma kidami kanki yanxu zantashi ba'afi awa biyuba gida yadau shegen kamshi ko ina jinsa kake, hjy tin asama takejin kamahin, tadauko taga me ake haka abun haushi taga gwaggo a kitchen tana kwashewa, tabuga tsaki , tace ke tsabar gidanku ce dazakiyi mana barnarta haka kiyi fura kiyi danbuGwaggo tace kiyi hakuri ranki yadade, hafsatu ce tace maigidan na buqata daku gabadaya, hjy tace ubanwa zaici muku wannan kazantar, dallah kifice mun dagani kafin inyi ball da abincin, gwaggo taraba tawuce, dai2 nan Ahmed yafito ganin hjy tarike kugu yasan rashin mutunci tashukawa gwaggo , baice dasu komai ba, yashige dakinsa can yaji hjy na zage2, hayaniyar ta tahanasa sakat yafito rike da new paper, Yace wai lfy kuka cikamana gidada hayaniya, ganin hafsa na hawaye yasa shi yin shiruGurinta yaje yaduka 6 lfy me akayi miki, tace bros dad ne yace yanason furar gwaggo shine tamasa kuma naga zatayi danbun gero senace tayi dayawa saboda nasan kunasansa nan gidan shine, hjy tabarar duka kuma tayita zagin gwaggoHannunsa taja bros zokaga danbun kitchen sukaje yaga danbun a kasa yasha vegetables da hanji, kamshinsa kadai yatabbatar masa yayi dadi , se idonsa yakai gun fura lumui2 da itaYajuyo yakalli hjy daketa kada kafa yadannabell din gidan segamasu aykin duka yakallesu daya bayan daya, Yace kada nagaWanda yagirka koda indomei ce, hjy tace toidan ba ayi abincin ba mekakeso muci? Ahmed yace kuci Wanda kuka barar ay ba'a banza muke nemaba, hjy tace to kai kake neman kudin da ranen sense. Ahmed yace kai kutashi , kundai jini da kyau wlh duk Wanda yagirka ko ruwan tea bakin aykinsa kuma wlh baxai karbi salary din wannan month baYakalli hafsa yace zeki kwashe danbun kifito da furar Seda ta gyara kitchen kamar ba ayi komai ba sannan yasakawa kitchen key yawuce abunsa , hjy tace billahillazi senayi maganin wannan yaron bayadda zai rika juyamu yadda yaga dama...........Muje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�4鈨�Hjy zaune agaban dad tana korafi kan Ahmed, dad yace wai ke yanzu dakika tasani agaba mekike son inyi masa ne dukansa zanyi kome, hjy tace bazancen duka bane, kawai kai kake dagidanka order kai muke gabadaya nmj har shi, nagaji da wannan zaman dole kowa yadauki matsayinsa, dad yace idan nafahimceki sokike kizama boss agidannan fada yadawo kanki umarni da order right? hjy tace eh to nidai baikamata ace ina matsayin uwa agaresa ba amma baya dauka ta da daraja baya bin umarnina, sannan ni ban isa Ince ayi ayiba ko nahana yahanu a'a dole sena rika bun umarninsa, why?Dad yace to hakuri dai zakiyi Ahmed koni karan kaina ban isa in sakashi dole ba yanada wata irin zuciya ne nibansan inda yagado taba, hjy tace shikenan zandau mataki da hannuna idan har kai kaka sa kwatarmun hakkina , dad yace fyn gaki ga hanya kindai sansa farin sani, tin farko dakin daukesa uwa shida kan warship ay dabai rainakiba, hjy taja tsaki tabarmasa roomdinsa, cike da takaici, aranta kuwa tadauki aniyar ganin bayan Ahmed koda kuwa zata rasa duk wani abu data mallaka, toh fah "Mahmud kwance kan gadon Ahmed yace wato mod ko wlh tin randa muka bar dajin nan nake cike da kwadayin fura bantaba shan furar datayi dadin wannan ba tin bayanta ummah, Ahmed yace toni me zanmaka ne? Mahmud yace I don't know Dan iska kaigoma ba'a zancen kirki dakai, Ahmed yace tona tanbiyeka ne? Mahmud yace nafa fika iskanci wlh, Ahmed ohh.....hava dae, Mahmud yagalla masa harara yagyra kwanciyarshi, Ahmed kuwa yadauko systemdinshi yana dubawa ,Hafsa nagani aguje se haki take tayi dakin dad, ko sallama batayiba tafada dakin sa. yadago kai yana kallan ta yace hafsa lfy naganki haka? Se shesheka take tace dad joda ce ba lfy wlh gatacan se murde2 take cikin ta ke ciyo kamar zata mutu, dad yace Subhanallah, Ahmed nagida? Hafsa tace ehh yana daga ciki, dad yace jekice yazo ya duba ta, hafsa tace wlh dad bazai dubata ba, sedai ko in kai zakamasa mgn, dad yaceshikenan jeki zanmar waya, haka kuwa akayi yasaka kiran AhmedRing daya yadaga tareda fadan yes dad, dad yace Ahmed kana inane yanxu, Ahmed yace am in home, dad yace gud, Ahmed kaje kaduba wannan fulanin da aka dauka ayki ance wai yarinyar ba lfy katacan ciyon ciki ne, Ahmed yace what dad, nizan dubatayanxun gsky ina ayki ne buh akira driver da hafsa sukaita hospital, dad yace hakan dakayi aganinka ka kyauta kenan Ahmed yace bahakaba dad inada ayki dayawa agabana so kuma ni.....Di. ....Di yaji wayar ta tsinke, tsaki yaja kawai saboda anrenan wayo nizanje induba ta, nikadaine doct agari ay wlh gwanda narasa komai akan nataba wannan najasarMahmud yabuga masa dogon tsaki yace in angirma asan angirma, Ahmed yace da buhun uba dawa kake, Mahmud yace kaidinwani abun zakayi ne, Ahmed yace kabarmun dakina kafin muyi kaca2 dakai, Mahmud yace ay kobaka fadaba nasan dakinka ne buh baxan fita ba kazo kafidda ni, Ahmed yaja tsaki yadauko rigarsa yasaka yace aysekayita zaman, yafice yabardakinHafsa tajasu se wata hadaddar hospital, suna isa wani nurse yazo da kujera suka axata, hafsa tace ina doct inmasa bayanin abunda kedamunta nurse din yace base kinga doc ba yana dubata zai gane matsalar, hafsa tace amma dama kunsan dazuwanmu ne, nurse din yakalleta yayi murmushi yacigaba da tafiya, sama yayi da ita gwaggo da hafsa suka rufa masa baya, room no 7 suka shiga da ita, bayan kamar minti goma yafito daga dakin yace doct na bukatar ganin mahaifiyar wannan yarinyar, den kuma dakinje kifara masa bayani kawaidoct din yana da matsala idan kikaga ya dubi kofa to yana nufin shikenan zaki iya fitowa, hafsa tace shikuwa wannan wani irindoct ne haka dayake da regulations, nurse din yace haka rules dinshi suke baya mgn a lokacin dayake duba patientsGwaggo tace bari inje hafsa , sallama tayi tashiga dakin sa a tsaye ta samesa yana kokarin sakama joda drip kujera yaturamatatazauna sannan shima yakoma mazauninsa, fuskarshi sanye da glass fari gakuma face mask, hannu yamata alama dashi akan taci gaba da basa bayaniGwaggo tace likita tun daren jiya takecemun kafafunta naciyo da cikinta kuma setakejin kasala sosae ajikinta doct yagyada kai yafara rubutu , tacigaba sekuma yau tawayi gari da tsara se murde2 take doct yadakatash sheta da a hannu alamun ya isa kofa yanunamata gwaggo tafito nurse din yashiga...........馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�5鈨�Doct din yacema nurse din nasakamata drip saboda tawahala den jeka dauko mun pad da pant, ka ajiye mata kan gadon tana farkawa ka kirani, haka kuwa akayi nurse yazauna zaman jiran tashinta doct din yafito, hafsa tabisa tana doct meke damunta ne ? doct yagada mata hannu alamar yana zuwa file din dake hannunsa yabata, yawuce abunsa,Hafsa nadubawa tace toh fah " gwaggo kinga al'ada ce tafara, gwaggo tace amma ay damun sani dabamu zoba se ayaga tsumma tasaka shikenan , hafsa tace ay gwara damuka zo domin kinga yaxomata da gardama , kuma ay andena saka tsumma a yanzu sedai pad, gwaggo tace komenene pad kuma ganin doct na sauri yasa suka rakashi da ido ,Dasauri yashiga tareda rufo kofar, nurse yagani rike da ita se kucce2 take tsawa yadaka mata kee ki mana shiru tuni takomakan gado talafe gashi duk tabata gadon, doct yace ungo wannan zaki iya shiga wannan toilet kigyara kanki akwai ruwan zafi , ahankali tace nifa wani abu yajimun ciyo gurin fitsari na jini kefita, doct yace kijekiyi wanka zan miki bayani kinji kanwata, tace bazan iya tashiba doct, likita yace nurse bamu guri toilet yakai ta yasata cikin baho wanka wata ajiyar zuciya tayi, Yace yade tace da dadi wlh, likita yace to kiyi wanka, joda tayi narai2 da ido likita yace menene kanwata tace bakomai kafita manakuma banda wasu tufafi, Yace tobari ayi mgn sukawo mikiBell yadanna, Sega nurse yazo yamasa bayanin abunda ake buqata, shima ya yiwa su gwaggo bayani bajimawa hafsa takawo mata wata atamfa riga da skit, dae2 nan kuwa tafito wanka lulube cikin katon towel doct yace ke ki kuma ciki mana akawo miki kayan, Seda tasaka tafito sannan tace nifa jinin bai dena zuba ba, likita yace tobaki saka pad din bane? tace nibansan ya a keyi baKarbar pad din yayi yalaka akan pant din yace kinga yadda nayi to haka ake jeki saka ba musu taja tasaka, taxo tazauna , Yace wannan jinin haila ne kika fara every month zakiyi daga kwana daya zuwa shabiyar, haka dae yamata bayanin komaiJoda tace nikam menene every month, likita yayi murmushi yace bakije skull bane, joda tayi shiru, yasake cewa bakije makaranta bane, joda tace bana boko islamiyya kawai nakeyi , Yace to meyasa bakiyi, joda tace babana yarasu ayki muke gidansu wannan yarinyar datakawo ni , likitayace a ina kike a hadda tace yanzu nafara mu fulanin daji ne, Nan likita yanemi sanin labarinta bamusu tamasa bayanin komai har zuwa yanxuYace to nikam wannan ya Ahmed din sonsakike ne koya, tace kam wlh karkasa yakasheni ni wlh natsanesa arayuwata tindanaga baya sona, likita yace taya kika San baya sanki, joda tace kaiwai bakaji yanda yake dizgani bane, likita yace toke meyasa kike tsoronsa dayawa haka, joda tace nima bansaniba, likita yace tym natafiya naso nabaki somes advice akan wannan guy , ga wannan magungunan dazaki rika Shane tayigodiya tafita yabita har waje yayi gyaran murya yace kikulamun da kanki plss kirika shan magani akan kaida inba hakaba, zaki jawa kanki problems dayawa, murmushi tamasa nagode likita mai kirkiHaka suka dawo gida dukda bawani kwari takejiba , hafsa kuwa senan nan take da ita, se kusan magrib sannan takoma side dinsu,sallah tayi tukun tafara cin abunci sannan tayi wanka tashiga bacci abunta, joda kuwa mararta talafa mata tasamu itama tayi bacci cike da mafarkin likitanta mai murmushi , tace wannan haka nakejinsa tamkar ya Mahmud shima haka yake cemun qanwata, ya allah kahadani da Mahmud ko a ina ne, ni kuwa nace shakurumunki joda, indai kere na yawo zabo na yawo to dole watarana zasu haduKoda akayi 12 joda tajita latsama acikin jinihaka tasaka kuka tana kiran gwaggo, gwaggo nabacci taji kukan joda, tasowa tayi tana tanbayar lfy joda tanuna mata jikinta, gwaggo tace tokekuma naki yanayi haka yake Muje bayi nagyaraki , haka gwaggo tajata sukaje toilet tawanke mata jikinta , sannan tasake bata wani pad talaka, aka canza kyallen katifar............馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�6鈨� Kwananta biyar sannan tasamu tsarki, ranar lahadi takoma islamiyya ,sun dawo sesauri take yunwa ta I sheta kamar me, hafsanata yi mata tsiya, sunkawo cikin harabar gidan taji wata murya dabaxata taba mantawa ba, yana cewa plss mod kayi sauri, jakar hanunta tayada, taje aguje bayan motar ta samesa kansa a kasa yana daure talkaminsa,Anatse tace ya Mahmud ga fura, 馃槄 dago kansa yayi dakarfi yana joda kece ina kika shiga naje dajinku bansameki ba, ya akai kikazo nan gidan naganki da uniform fin nurul kharim koday har kinzama yar abuja ina gwaggo da baffaAhmed yaja tsaki kai bani key din motar zan wuce, bansan iskanci, Mahmud yace Ahmed wannan sune wadanda aka nuna gidansu a TV Wanda akace akwai fetur, Ahmed garesu ne nakeshan fura a dajin , Ahmed yace towai natanbiyeka ne, dallah kabani key zanwuce, Mahmud baiko sauraresa ba yacigaba da tanbiyar joda tace ay baffa yacika, innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, allah yajikansa fita yayi yabar Ahmed suka shiga ciki domin ganawa da gwaggo, Ahmed yace wato ni yamaidani Dan iska akan wannan shegiyartsaki yaja sannan yatada motar, joda dagudu tashiga dakinsu, tana gwaggo zoga ya Mahmud, dakinsu yashiga yasame gwaggo na karatun qur'an Mahmud yazauna joda kuwa tafita takawo masa ruwa, gwaggo takai aya yajuyo cike da farin cikin ganin Mahmud tace yo wanake gani haka, Mahmud yace gwaggo nine dama nangidan kuke dazama, gwaggo tace Mahmud labari ne maitsayi, Yace gwaggo ashe baffa yacika gwaggo tace ka gani dae Mahmud, Yace to allah yagafarta yakyautata makwancinsa ameen,Mahmud yace ay bansan kunanan gidan ba kullum ina ciki, Ahmed babban aboki nane atare muka taso , atare muka je dajinku shidae yanada kyankyami shi isa bakya ganinsa, gwaggo tace ay base kamana bayanin saba munsan komai akansa, Mahmud yace Ince dae baimuku rashin kunya baGwaggo tace a'a ay shi haka yake kamar baya ganin mutun baruwansa da sha'anin mutun matar gidan ce dae wlh gata nan, Mahmud yace haka fah suke sea hakuri kawai, gwaggo tace yo mu ay bama shiga sha a ninsu kaga hafsatu itake sonmu wlh ta taemakemu sosae arayuwanta , Mahmudyace zata iya itafa batadauki rayuwa da girma ba, gwaggo tace haka ne fah sedae fatan dacewayinin ranar Mahmud dakinsu ya yini gwaggonabasa labarin su, Yace insha Allah zai binciko musu kudinsu, gwaggo tamasa fura,yasha se santin furar yake, hafsa ma tadiba takaima su abdallah da dad, dad yace yana buqatar furar a kullum da kuma irin danbun geron da gwaggo tamasa kwanan baya, haka kuwa akayi gwaggo takoma mai aykin dad dukda ko afuska baitaba ganin taba amma yana musu alheri sosae , duk wani abuncinsa yakoma hannunta, haka takemasa duk abunda ya buqata hafsa tajera masa kan dining kida dae rana ba'a taba samun mistake ba sabanin sauran masu aykin dazaiji girkin yayi yaji kokuma ancika mai dayawa............Muje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�7鈨�Yaune su hafsa zasu yi jararrabawar karshe kuma Yaune iyayen yara zasu hallara a makarantar , domin ganin yadda karatun yayansu yake tafiya, karfe 2 aka fara gudanarda taron da dae ake kiransu suna bada karansu kuma ana musu tanbaya, haka har a kazo ga hafsa inda ta uraemic Mahmud ido takasa yin komai Seda taga Ahmed nabinta da harara sannan tashiga taetayinta, harkuwa tacinye lokacin ta kadan yarage balaifi ba'a mata gyara sosae ba dukda haka kuwa Ahmed baiyaba da qoqararinta ba,Su joda aka kira domin su waqar da aka basu kusan su 5 joda ce mai rera waqar sekuma yan amshinta su 4, cike da kunya tafito filin tafara gabatarda waqar, cikin wata zaqakkar murya ke kyace balarabiya ce ke rera waqar nan , Ahmed yayi shiru yana saurarenta har taxo karshe sannan suka rufe da addua, guraren 6 aka watse joda kam tasha kyauta kamar me, allah kaday yasan iya adadin mazan dasuka koma gida da zakakkar muryar joda aransuAcikin kyautar hadda Wanda yabada 50k ten 5 gasunan dae, Mahmud kuwa duk murna tacikashi, suka dawo gida kowace danata kyautar, suna isa taruga aguje gurin gwaggo tana murna, gwaggo tace nidea kada ki karyani Dan allah nan tazubewa gwaggo kudin da sauran littafan data samu,Mahmud yashigo yasamu gu yazauna, Yaceaifa yau bakin yr fillo baya rufuwa, joda tacenifa banasan tsokana, Mahmud yace au wato ni nake tsokanarki koh? Joda tace a'a banceba yaMahmud yace ni kuwa gwaggo inba damuwa mezaihana kisaka joda a skull ne, gwaggo tace badae bokoba gurin yahudawaakoyamata miyagun dabi'u Mahmud yace ba abunda za'a ko yamata se dae2 kinga yanxu rayuwa bata tafiya yadda kakeso sekana Dan bokon nan koda or level ce tana amfani yanxu baga hafsa ba ay collegetake amma aybakiga hallayyarta ya canza ba muma kuma gamunan, joda tace nikuwada likita zan karanta saboda nawarkar da cutar data kashe mun baffa na, Mahmud yace kiwarkar kodai kibada naki gudummawa, joda tace ehh ay shine abunda nake nufi,Gwaggo tace tonidae senayi istihara akai naga yayadace, ayi idan alhkairi ne allah yatabbatar mana dashi idan kuma sabanin hakan ne saemu hakura , Mahmud yace insha Allah ma alhkairi ne agaremu , joda tace kai gwaggo sekinyi wani istihara, gwaggo tace yomekike son inyi bayan ita neman zabin Allah nefa, joda tace to Allah zabamana mafi alkairi ameenMahmud yasame Ahmed kan zancen yana son saka joda skull wace yake ganin tadaceasakata, Ahmed yace to waini ina ruwana da itane baruwana da duk abunda yashafeta kajiko kada kasakemun zancentabanaso, Mahmud yace to itakuma meta kashe maka, Ahmed yace nace maka bansan zancen ko dole ne hava, Mahmud yatabe baki Allah yashiryeka da wannan bakin halin, Ahmed afusace yace mutum nawa nakashe dazaka wani cewa bakin hali,Mahmud yace yo Ai gwanda wanda yakashe mutun idan akan kuskure yayi idan yatuba akankaAhmed yayi kadi da turaren dake hannunsa yayi cikin Ahmed yacabko wuyansa, idon nan sunyi jajir dasu, Mahmud yace wow shi isa nake sonka akwai zuciya kamar zaki, Ahmed yaqara matsesa da bango se huci yake tamkar wani maciji, Mahmud yakwacerigarsa dakarfi yatura Ahmed kan gado, yanufi fridge yadauko masa eviron drink, yamika masa Ahmed yawulgashi kasa yacigaba da kallon kafafunsa yana ajiyar zuciya, Mahmud yadafasa yace relax man, Ahmed yajanye hannunsa , dole Mahmud yabar masa dakinsa, yanufi dakin gwaggoMahmud yace gwaggo ya kin amunce zancen karatun, gwaggo tace toni dae ba abunda zance sedai allah yasanya alkairi yasa alhkairi ne, Mahmud yace to mungode gwaggo bari muga yaushe yakamata mufara apply din makarantar..........馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�8鈨�Mahmud yasame hafsa sun tattauna kan zancen karatun joda, hafsa tayi matukar murna, Mahmud yace yanxu se karshen zango kenan kafin nan ma akwai wani mission da za'a turamu, hafsa tace to ya sekun dawo allah yadawo mun dakai lfy, Mahmud yace iye mekika ce? hafsa tace no...eh. ...dama cewa nayi allah yadawo muna daku lfy, Mahmud yayi murmushi yace ameen 6terYau takama Friday Yaune ranar da su Ahmed zasuje yola state , tsaf suka shirya sukayi bankwana da kowa Ahmed yace hafsa inagayamiki duk shegen daya shuka miki rashin kunya to wlh kimun waya, hafsa tayi murmushi tace bakomai yaya komai zaitafi dae2 insha Allah, gud semun dawo, har mota tarakasu se satar kallon Mahmud take wanda baikosan tanayi ba, bayan sunwuce da kwana daya Sega wani David yazo akan maigidansa yaturosa zairika yiwajoda lesson kafun sudawo, ba bata lokaci yafara yiwa joda lesson kullum bafashi, idantagama lesson takoma gun hafsa takara koyamata ABCD suka fara, dayake bashida hausa, hafsa ke ko yamata hausa, haka zatayi ta masa zancen kurame idan bata gane ba, cikin sati ukku tafara ganewa, har anfara da party of speech, tin kan noun har zuwa karsehensu, kafun kace ha, Sega joda ana turanci, maths kuwa ta iyashi sosae ba'a barinta abaya dama takware agurin lissafi ,Daganan kuma se aka fara subjects, na primary, intro technology, P.H.E, science, social studies, cumputer etc, suma dayake ba wuya nan danan tagane, haka abun ketafiya, har zuwa wani Dan lokaci sannan akafara, na secondary skull, kafun su Ahmed sudawo joda komai fyn, turanci takebakama hannun yaro , abun se yayi tabata mamaki wai yau it ace kejin yaren yahuduSoyy takullu maikarfi tsakaninta da yasir domin kuwa yasir akwai kyawawan hali gakuma girmama naga ba, gwaggo har tasan dashi sun aje zance akan cewa za'a yimgn idan yakarkare aykinsa a suleja, hakan yamasa dadi shima kuwa yana karawa joda haske akaratunta ita kanta batasan tanada wannan ilimin ba seyanxu, hafsa ma abun namata dadi hadda ma ba'a barta abayaba, haka take yin abunta cike da haqazaAhmed haushi yacikasa, yadubi Mahmud yaxasuyi mana haka mun aje akan wata biyu da sati ukku zamu bar garinnan yaxasu sabamana alkawari su sake bamu wani aykin daban, Mahmud yace hakuri zamuyi nikaina inada important issue wlh, to ya zamuyi allah yasa hakan alkairi ne agaremu ameenDavid yacewa joda tashirya on Monday zasuje turkish intentional skull, acan akamata gwa akaga tawuce zama primary, secondary ma ko ss zataje, kasancewar batada, primary certificate ne aka bata jss3,murna gun devid ba'a magana koba komai oga zai ji dadi, joda ma haka itada hafsa sunyi matukar murna da hakan,Ran Friday aka gama komai nxt mndy tafarazuwa, skull cike dakunyar uniform din riga da skit ne iya gwaiwa yake se hula, haushinta daya gashinta dabaya shiga acikin hular , hafsa tace kifara retouching dinshi zairage yawa , joda tace kenifa ba yanxu ba segaba, zan rika sakamasa vatikadole zai kwanta , hafsa tace kyaji dashi ,Joda batada kawa kodaya, ita kadai ke karatunta, dukda akwai maza amma baruwata dakowa, dukda kuwa anason kawo mata hari amma ba'a ga fuska ba, karatun ta kawai tasa agaba, malamai namatukar alfahari da ita, hujjar joda nakin kula kowa shine, ganin duk makarantar daga yayan ministers se prop itakuwa bayarkowaba mezaikaita kawance dasuSati biyu da fara zuwan joda skull, Yaune kuma su Ahmed zasu dawo, batareda kowayasan da zuwansu ba, hafsa kuwa tanata kokarin zuwa skull dinta a saudia tazabe zuwa karatu, joda se korafi take akan hafsa zataje tabarta, ranarda zataje aranar su Ahmed suka dawo , dole tafasa tata tafiyar se bayan 2dyz,Mahmud sashin gwaggo ya yada zango yana shiga yabuda fridge yaga kuwa da akwai Yar gidansa, yawashe baki yadauko yazuba a cup yafara sha, joda tafito kenan daga wanka daga ita se zani, ita bata ganshi ba tafara shafe shafenta, Mahmud kuwa rudewa yayi ganin irin kyakkawar surarta............馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 3鈨�9鈨�furar dayake sha takamashi tuni yafara tari, joda tajuyo dasauri tabuga kara takoma cikin toilet, Mahmud yace sorry kanwata bansan kina ciki bane, a toilet take kyaro masa magana, yayana yaushe kadawo, Mahmud yace yanzun fa, anan nafara nayi missing din furar gwaggona, inama taje, joda tace tafita unguwa ne , uhm yaya zansa kayana fa, Mahmud yace oh so sorry kanwata bari ma zanje gun AhmedYana fita tasauke ajiyar zuciya, tafito takulle dakin ta Ida shirinta, akan dining yasame Ahmed Yana cin abinci, shima kuwa yarufa masa baya, Mahmud yace Ahmed dama kafada zamujo ne? Naga delicious haka, Ahmed yace a'a yanzun hafsa ta shirya mana su, Mahmud yace kai wannan hafsa tanaji da yayanta sosea,Gaskiya duk wanda ya auri hafsa yagama komai arayuwanshi ga tsafta ga iya girki uwa uba ga ladabi da biyayya, abdallah yacebawani nan bazan baka itaba , Mahmud yajuyo yana kallansa yace to wayace maka santa nake , abdallah yace oho dae nadae gano inda kadosa, Mahmud yace kae nifa wlh bakomai believe me, abdallah yace to naji daeDuk wannnan abun dasuke Ahmed baice musu uffan ba kawai abincinsa yake ci, har yagama yagoge hannunsa da tissue sannanyawuce room dinshi, Mahmud ma yagama yabisa, baisamesaba yasan cewa yana gurinwanka, sbd haka yahanye gado yana son yinbacciAhmed yafito sanye da jallabiya yace wannan iskancin fa, zakawani zo kahaye mun gado, bayan kasan ina fitowa bacci zanyi, Mahmud yabuga masa tsaki yatashi yashiga shima yayo wanka tareda alwala, sannan yabude wadrop yajanyo sabuwar jallabiya yasaka yatada sallah bayan yagama, yasakiran Ahmed, wanda har bacciyasoma dibanshi, Yace lfy malam kazo kana damuna bayan kasan natsani atadani ina bacci, Mahmud yace kayi sallah ne, Ahmed yace a'a banyiba kai nake jira , Mahmud yace kaifa Dan iska ne wlh, Ahmed yace idan iskancin kakeso sena koyamaka , Mahmud yagalla masa harara yadauki wayarshi yafita, se gidansuYana isa mom dinshi tafito tana oyoyo wazagani haka babu ko sanarwa, Mahmud yace mom nasameku lfy, tin dazu fa mukazo ina gidansu Ahmed acan nahuce gajiya, momy tace gidansu ubanka ko wannan Ahmed setayi tsamari nake ganinsa agidannan kaiko gakanan kullum yawon zuwa gidansu , Mahmud yace oh mom saunawa kikeson ingayamiki cewa shifa Ahmed haka rayuwanshi take se yayi sati agidansu ba'a San yadawo ba, rayuwanshi ce se addua,Mom tace shikenan jeka huta, Mahmud yace yauwa my mom ina shukra da Khalifa, mom tace suna dakin abbanku, Mahmud yace suwai sai yaushe zasu girma kullum suna maqale daku kamar sababbin haihuwa, mom tace ehh baruwanka kadawozaka fara takurawa, yayana koh, Mahmud yatabe baki yashiga daga ciki,Bayan magrib aka hadu falo domin dinner, abba yakalli Mahmud yace muhammad yaushe zaka fito da matane nifa nagaji daganinka a haka, mom takarbe ahto nima dae wlh inason ganin jikokina tun inada karfina inmusu goyo , shukra tace lah bros kanada budurwa ne? Mahmud yagalla mataharara tuni tacigaba dacin abincinta, abba yace wai badakai muke magana bane, Mahmud yace toni abba mezance maka banda wata yarinya danaga takwanta mun arai wlh, momy tace to idan bakada ita zamu nemomaka, Mahmud yace what? Niyarone ko kuma nidan dane dazaku nemamun mata, abba yace tokuwa idan bakaso kafidda mata kawai karshen zance, Mahmud yace bashine abunda yadace kuyiba addua zakumun allah yazabamun mafi alkairi agareni,Joda tagama shirinta tsaf zataje skull takarbi kudin adaidaita gun gwaggo tafita kenan sukaci karo da abdallah yace wow c diz gul, so cute n veuryfull, joda tace ina kwana, dkyar ya masa dacewa lfy , yaushe kika fara skull haka kuma turkish intentionalskull fah, joda tace ya Mahmud ne yasaka ni, abdallah yace Y? Joda tace kawai yanason ganin farincikinane, abdallah yace kamm Ai kuwa wlh dole nadauki mataki idan bahakaba zai karyatamun mafarkina, yarinyar Dana jima ina burin ganin girmanta, in cire sha'awarta dake dawainiya dani, joda taji shirun yayi yawa, tafice abuntaYauma kamar kullum tafito tasame driver yanajiranta, banza tamasa sannan ta mike titi tana neman adaidaita, driver yakarasa gurinta yace hava madam wlh idan kikayi late nizakijawa hasara Dan allah kada kisa narasa aykina, joda tace kainifa bazan shigamotarkaba sae kagayamun, waye wannan ogan naka ahankali yace Mrs marafa ne, idotazare Jin ance Mrs marafa tasan mutun dayane akecewa Mrs marafaCike da tsoro tashiga motar, tin ranar batasake yimasa musu ba duk yadda tayi sammako zata samesa yana jiranta haka kuma idan yakaita baya dawowa seya maidata gida, duk wannnan abun bata taba gayawa gwaggo ba aganinta bakomai bane, dama kuwa duk abunda ke faruwa na gidan dae2 dasau 1 bata taba gayawa gwaggo ba aganinta bakomai bane..........Muje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 4鈨�0鈨�Haka karatunta yacigaba da tafiya babu abunda ke takura mata , har tasaba da rashin hafsa, wata umma khalthum ce tindatafara zuwa skull din takeson kawance da ita ganin irin hazakar joda, joda tace lok kalthum kinganni nan nibakowa bace, banida kowa agarinnan se allah mu Fulanin daji ne dajin sokoto, mahaifina yarasu dalilin dayasa bana kawance dakowa, domin banaso indaukarwa rayutawa abunda yafi karfinaKhalthum tanisa shikenan joda dama dae bakison zama dakowa amma duk skull dinnan banga wanda yakaiki gata ba kodakuwa yafiki dukiya, dubi yanda malamai ke dar2 da bacin ranki , idan aka kawoki se antashi driver dinki yake komawa, breakfast sedai kizabi abunda kikeso abiya miki , shin intanbiyeki akwai wani gata dayakae wannan ? Joda tace shikenan idan baki yarda daniba , amma kisani ni ba kowa bace face Yar aiki agidan, khalthum tace naji dukda dahaka, ni I want be ur frnd, joda tace tom shikenan allah yabamu hakuri dajuna ameen, tin daga ranar suka zama wasu irin qawaye tamkar hanta dajini dukda basu taba ziyartar gidajensu ba, joda waya na burgeta amma bata iya maganaYasir ya gabatarda iyayensa gurin dad domin shine ya wakilce iyayenta anyi maganar aure ansaka, sora 2mnth dazaran tayi j . l . c , abdallah nacike da bakin cikin rasata amma yakudurci seya more ta kafun taje gamijinta, wata zuciyar tace taya hakanzae faru, okey Soyy zaka kulla da ita, to tayazan kulla Soyy da ita bayan tana tsorona, sekuma yace zan koyamata yadda zata soni da kyawawan halaye na nadaban kyautatawa tausayi kulawa etc, murmushi naga yayi na Jin dadi daga ranar yafara shirye2 yadda zae fara mataJoda anshirya cikin bakin yadi mai flowers red tayi matukar kyau kamar ba joda ba , wannan yadin yana dae daga cikin kayan daMr marafa ke aykomata tin kan kayan make up cosmetic kayan sawa duk wani datake bukata sedai kawai taganshi, gashi bata ganin dad balantana tamasa godiya haka abun ketafiya, joda tawaye sosae fiye da zatonkuTafito kenan zata tari taxi Sega driver dinta,dafe kanta tayi tace oh god, shi wannan driver sekace aljan bansan taya yake sanin schedule dina ba tsaki tabuga tashiga baya,basu tsaya ko inaba se gidansu khalthum, har ciki suka shiga, sannan tashiga parlour, wata mata nagani cikin shigar alfarma tareta da fara'a joda taxauna se kallon dakin take ruwa da lemu aka kawomata , sannan suka sake gaisawa, tace mama gurin khalthum nazo , mama tace ke kawarta ce koh ? Joda tace eh skull dinmu daya, mama tace ya sunanki, joda tace zainab muhammad, amma anfi kirana da joda,Mama tace eyya aykuwa inajin zancen ki gun khalthum kullum batada zancen dayawuce na joda, joda tayi murmushi nan suka sha fira kasancewar khalthum bata nan, atake joda tashiga ran mama dazata dawo kuwa tamata shatara na arziki , haka takoma gida cike da murna dukda bata hadu da khalthum ba amma ranta fes domin kuwa mama akwai kirkiTafito daga mota kenan sukayi kicibus da abdallah murmushi yasakarmta itama kuwatamaida masa, abdallah yace kanwata dagaina haka, joda tace gidan kawata, abdallah yace shine baki kirani narage miki hanyaba kona rakaki, joda tajuyo cike da mamaki tace kae ne kake fadan haka? Abdallah yace balaifi na bane sako ne daga zuciyata, joda tace zuciyar ka fah?Abdallah yace kwarai da gaske joda kinsan zuciya ta kan aykeka da sako a gurin da baka zato kuma ga wanda baka tsammani, joda tace lallai kam naga alama, dae2 nan takawo hanyar dakinsu tace ya abdallah sae anjima, abdallah yadaga mata gira c u ltr, ido da gangar jiki bazasu gaji da ganinki ba..........馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 4鈨�1鈨� Abdulmkibab.hexat.com Joda tashiga dakinsu kanta duk yadaure gameda zantukan abdallah ita dae a iya saninta wanda ake so akeyiwa wadannan kalaman to amma koma yane zata jira yafurta sannan ta yanke hukunci, har tafara bacci taji muryar mai gadi yana fadan tafito ga yasir can yaxo , joda tace kainifa bazan iya tsayuwa ba kace yashigo , haka kuwa akayi yashigo dakin su gwaggo tabasu guriAcikin firar sune sune yake ga yamata yagama gidansa kaf, gobe zasu kawo lefe, 3week masu zuwa za'a daura aure, joda tasadda kai kasa tace allah yakaimu, haka suka sha firar su har zuwa wani lokaci sannan yamata sallama, tsalle tabuga sannan tashiga kwalawa gwaggo kira, gwaggo tace ke lfy wannan Kiran haka? Joda tace albishirinki gwaggo gobe za'a kawomun lefe, gwaggo tace wani lefe kumabayan nace bana bukatar kowace bidi'a , joda tace ay yace dakanshi zaikawo, gwaggo tace to Allah yakaimu ameenTa shirya tsaf zataje skull tayiwa gwaggo sallama, kofar dakinsu ta hadu da abdallah, joda tace a'a ya abdallah ina kwana kaine anan, abdallah yasakarmta murmushi nine kanwata kintashi lfy, joda tace lfy lau, yasu hjy, abdallah yace qlw, yanxu se ina? Joda tace skull mana, abdallah yace ok toh Muje narakaki koh, joda tace dakabarshi , abdallah yace oh...nadae gano bakya San ganina atare dake, joda tace bahakaba ne, nagode kawai tacigaba da tafiya har gate sannan tashiga motar ta driver yajata suka wuceAbdallah yayi murmushi yace da sannu zaki shigo hannu yarinya, yajuya yashiga side dinsu, Jin ihun amina yasa shi tsaki yasan waccan antyn ce taxo, yana isa yagansu a parlour se hauka suke tsaye yayi akofa yana saurarensu, mansura na fadan magani yafara ci tinda Ahmed yafara daga wayana, tace anty kinsan me hadda tanbayana yake yagida, amina tace kai amma dae wannan malamin yayi wlhAbdallah yabuga tsaki yashiga dakinsu ko gaisheta baiyiba, hjy tace ni wai narasa kan wannan yaron wlh, 2dyx dinnan yacanza hali, mansura tace yaji dashi can Dan iskan yaro kinaga ko gaidani baiyiba fah , hjy tace barsa zanji meke damunsa , mansura tace anty koh wlh har na hangoni kan jikin Ahmed, amina ta kyalkyale da dariya wlh kuwa anty zaki sha kamashi da laushi,hjy tace kai bansan iskanci maita zaki muna masa kiri2 koya, tin wuri kisake tunani kisauya ra'ayi kar kiyarda ya gane kina son yatabaki idan ma yatabaki kiyi masa bala'i kina jina koh, mansura tace inaji antyAbdallah kuwa dakinshi yafada kan gado yarumgume filo duk juyi joda yake gani da murmushinta yana tuna dimple dinta, hakoranta fess ga wushirya atsakiyarsu, wanda takara mata kyau sosae da sosae runtse idonsa yayi yana hangosa manne da ita, lips dinta yariko yasaka anasa wani yarrryaji ajiikinsa jikinsa narawa yakai nasa bakikan lips dinta ahankali yake tsotsensu tamkar mai shan minti, yana kara lumshe ido can yaji anvude ganbu firgigit yabude idonsa uban tsaki yabuga ganin an katse masa tinaninsa, hjy ce tasamu gu tazauna, tace abdallah meyake damunka ne plss, abdallah yace plss mamma ki kyaleni plss, ganin haka yasa hjy fita dakin tareda cewa allah yahuci zuciyarka DanaTana fita yabuga tsaki yacigaba da juyi yanaganin kamar yana tareda joda, gwaggo ta aika ma dad sako cewa za'a kawo lefen joda, dad yaji dadi yabada 30k yace a basu idan sunkawo , gwaggo tasha godiya kamarme, dasafe gwaggo tashiga kitchen tareda hasana mai ayki sukayi snacks da miya se meetpie, gwaggo tabada kudi aka siyo matabiyar malt ,exotic,hollondia, se 5 alive, hakaaka hada kayan abun sha'awa , karfe hudu narana Sega yasir da abokanshi su biyu, sunkawo lefe 1 set kaya tubarikallah dae2 buqata..........馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 4鈨�2鈨�Shirye2 kawai akeyi gobe daurin auren joda da yasir kasancewar tayi junior weac , joda ansha kunshi da kitso dukda kitson fulani ne amma tasha kyau, dad yayi tsaye yagyara ma joda dakinta balaifi duk wannnan hidimar da ake hjy batada lbr abdallah kuwa kamar yayi hauka domin kuwa san joda yake kamar me , yayi kudi ringayamata komai zaifaru yafaru , amma yagaji da dakon sontaJoda takira khalthum da telephone tagayama mata, khalthum tayi matukar mamaki mezaisa amata aure daga yin j.l.c dinsu , cike da alhini tagayawa mamanta, haka suka dungumo suka zo tare, mama tayimata tirarika dayawa, da humra su kulacca da sauransu , koda suka isa gidan yafara jama'ar gwaggo da makota dayake bakowa yasan suba, khalthum kuwa fushi take da joda akan me zata boye mata har Seda akaxo finalDakyar gwaggo tashawo kan khalthum tahakura suka ci gaba da hidimar biki , duk inda joda tasaka kafa khalthum na biye da ita, joda tace nikam wannan makalen name ne, khalthum tayi rau da ido hava joda ke bakya Jin kewar kowane, joda tace to ay bayau zanje ba yasir yace sena girma sosae, khalthum tace hmm wlh wanaki yakeyau dinnan zakije gidan yasir kuma baxai sarara miki ba,Joda tace kamarya kenan, khalthum tace a'a abun ma aurata mana, joda tace kenifa banganeba khalthum tace zokiji taje hannunta sukaje garden tashiga zayyane mata komai, joda kuwa tasamata kuka, khalthum tace ke dallah kimun shiru, dae2 nan abdallah yashigo dama kuwa yana kallon su ta window, yadauko kyalle yabata cak yatuna mata da Mahmud takarva ta goge hawayentaAbdallah yace yace joda rana bata karya sedae uwar diya taji kunya, ranar wanka ba'a boyon cibi, joda ina sanki ina sanki ina sanki 4rm d bottom of my heart, joda tace what? Ya abdallah kasan mekake fada haka, abdallah yaduqa kasa yace hava joda so baruwansa da nasaba kudi ko mulki wlh ina sonki so bana wasaba,joda tace amma meyasa ka boye mun seyanzu dabamuda abun yi, abdallah yadago da sauri yace u mean kema kina sona kenan?Joda tashige cikin khalthum, tace ya abdallah ban isa ince bana sanka bakaine mutum nafarko daya ji tausayina agidannan bayan hafsa, abdallah yayi murmushi yace nagode dakika fahimci haka kanwataAtake taji tausayin sa naratsata , tace kayi hakuri ya abdallah kaddara tariga fata, kobakomai nasan kafi karfina, abdallah yace nagayamiki so baruwansa da nasaba kudi ko mulki, joda tace hakane ina maka fatan alkairi allah ya zabamaka wata wadda tafiniameen, Jin sukayi hasana na kwalawa joda kira hakan yasa suka juya gabadansu, tace ya abdallah sae watarana nagode, abdallah yayi mata murmushi yadaga mata hannu, tuni hawaye suka ciko a idonta , khalthum dae sae binsu da ido take, wanka tayi tasake shiri abunta , sannan takoma takwanta, ahankali takira sunan khalthum, khalthum kinsan wani abu wlh tin safe nakejin faduwar gaba narasa dalili inata maimaita innalilahi, nakaranta qur'ani amma kuma se abunda yacigaba tsoro nakeji yana shigata se wani sanyi nakeji kamar zazzabi hakaKhalthum tadafa joda tace don't worry besty fargaba ce kurum kike yi insha Allah ba abunda zaifaru, kat agogon dakin yabugadasauri tadaga kae tadubi agogon, khalthum tace kinkusa zama mallakin yasir nasan yanxu ana gama sallan jumu'a za'a daura auren , joda tayi murmushi tarungume filo tace khalthum kamar baxai yuba wlh mafarki nake khalthum kitada ni, khalthum tayi jugum tana kallan joda, can kuma seta tashi tadauko mata ruwa tabata tasha , tsam naga ta tashi taje tashiga dudduba wadrop dinsu dkyar taganta, wata jacket ce tadauko tasaka, tareda saka kanta aciki tana shakar turaren daya kusa shekara bai cire kamshi ba2:30 dae2 kamar yadda aka tsara za'a dauraauren joda da yasir akofar gidan Mrs marafa , dad shine wakilin joda se alh baushe shine wakilin yasir akan sadaki dubu 30, liman yafara gabatarda komai davada joda a mana kan yasir yasir , yace yakarba , dad yace dukda bani bane mahaifin wannan yarinyar ba, amma nabawa yasir gidana dake kan kasuwa, baushe yace bamu gane bakai bane mahaifinta, dad yace dama azatonku nine mahaifinta ay mahaifinta yarasu ayki suke agidana,baushe yakalli yasir yace yasir dama kasan dahaka Yar ayki zaka aura, liman yace Dan allah kubari ashafa fatiha mana, baushe yace shikenan allah yasanya alkairi har liman yafara bismillah se baushe yace dakata, Mrs marafa daga ina take, dad yacefulani ce Fulanin daji ne dajin sokoto, baushe yace what? fulani yo meya hadomu da fulani wlh Sam nafasa baxan bawa Dana izinin auren taba yasir yace hava baba miye aybun su? Baushe yace kai rufe mun baki babu aure tsakanin mahauta da fulani, Sam bazaka aure ta ba bada yawuna ba, haka yaja hannun danshi yana ta kuka suka bar gidan, duk yadda jama'a sukayi dashi Sam yaki yafahimta, dad yahasala matuka ga shi yagayyato abokanshi, dad yakira liman gefe zasu tattauna banjira Jin abunda zasu tattauna ba nagudu ganin irin facin ran da dadi yashiga gud uwa nayi se gurin su AhmedAhmed yace Mahmud narasa meke damuna yau natashi da faduwar gaba , inaji kamar wani abu zai faru sedai bansan komeyi ba, Mahmud yace ka dauko al_qur'an mana ka karanta, Ahmed yace nifa inajin tsoro kuma sanyi nakeji sosae kamar zazzabi, Mahmud yace to Allah yakawo komai da sauki, nan Mahmud yafitashikuma yadauko jakarsa yabude yafidda wani dankwali na tsofaffi yadaura akansa, tareda wasu duwatsu kamar abun jigida yajimke sosae a hannunsa zuciyar shi na cigaba da bugawa......Muje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:37 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 4鈨�3鈨�Haka yawuni aranar cike da tsoro ga wani irin sanyi dayakejin na ratsa shi dakyar yasamu yayi bacci sannan komai yalafa masa, gurin joda ma haka abun yakasance bacci mai nauyi yakwasheta, acikin barcin ne taji hayaniya yayi yawa, tafarka hannuntarike da jacket tamanna ta akirjinta tafito waje Dan Jin meke faruwa, khalthum taganizaune jugum, karasawa tayi kusanta tace lfykhalthum meke faruwa naga gwaggo tayi tagumi? Khalthum tace joda duk abunda yafaru ga bawa mukaddari ne, duk abunda allah yahanama hakan shine alkhari agareka, joda tace hakane wani abun ne aka rasa ?Gwaggo ce tadafa joda tace zonan autana daki tashiga da ita taxaunar da ita kan cinyarta tace joda tin randa kuke haduwa da yasir bakitaba sanin Dan mahauci bane joda tace me? Mahauci kuma wlh bansaniba, gwaggo tace to mahaifinsa yahanashi aurenki saboda kinfi kowa sanin ba aure tsakanin mu da mahauta, joda tace iye yanxun yafasa kenan gwaggo ina son yasir fah, gwaggo tace hakuri zakiyi ba mijinki bane, joda tace gwaggo nikaina baxanso na aure mahauci ba yadda naga suna kiyayya damu,Gwaggo tace yauwa yata naji dadi dakika fahimceni, joda tace yanxu gwaggo zai karbe lefensa koh? Gwaggo tace yace ya yafe amma ba abunda zamuyi dasu zansa amaida masa kayansa, joda takoma kan cinyar gwaggo tana ta murmushi wanda nakasa gane kona meneneJoda takankame gwaggo tanacewa gwaggo kirufeni sanyi nakeji, gwaggo tace sanyin lfy joda awannan yanayin na zafi joda tace gwaggo kisaka mun jacket dinnangwaggo tadauko tasaka mata, tarufa mata bargo sannan tafita, joda tacigaba dafadin, sanyi2 inajin kamshinsa nazuwa, sannnnnnnnyiiiii ahaka har bacci ya kwasheta, Ahmed kuwa haka yawuni rike dawannan dankwalin tareda wani stone nikamnarasa kona miye ne,Dad yasa Kiran gwaggo yanabata baki akan abunda yafaru yace kiyi hakuri komai mukaddari ne watakila hakan shine alkhari, gwaggo tace kadena bani hakuri alh kai yakamata nabawa hakuri saboda ankunyataagaban jama'a, dad yace bakomai hakan shine dae2 allah yamusanya mata da mafi alkairi ameen, dad yace yanxun tacigaba dazuwa skull har muga abunda allah zaiyi zuwa gaba, anawa ra'ayin kibarta tayi sc skull sa'annan kimata aure, gwaggo tace bakomai indae hakan bazai janyo wani batanci agaretaba, dad yace bakomai insha Allah zan saka ido akan tarviyanta tamkar yayana, gwaggo takara rusinawa tana godiya, dad yace ay yiwa kaine wannan sedai fatan dacewaKusan sati guda joda nafama da kanta kwata2 takasa gane wannan yanayin, dkyar gwaggo tasamu taciyo kanta takoma skull bayan exam dinsu tafito murna ba'a magana domin tafito da 5 credit 3 A etc, malaman sun buqaci abata ss2 amma David yaki amuncewa yace oganshi yace abari tayi karatu mai kyau, dama joda bawani dadi tajiba domin bataso arabata dakhalthum, haka rayuwar ketafiya ba laifi komai datake buqata tana samu, duk inda zataje, driver dinta shiyake kaitaJoda tace khalthum yakike gani wai nayarda nakarbi Soyy abdallah kar nafada tarkon so daga baya kuma nazo nasha wahala domin wlh hjyrshi batada kirki ko kadan, khalthum tace kada kiduba wannan so baruwansa da wadannan ababen kedai kawai idan kina sonshi to fine, joda tace wani na isa ince bana sonshi handsome nefa, khalthum tace hmm joda kenan wlh kinyi saurin fara Soyy da wuri haka nifa nan dakika ganni senagama skulk kozanfara sauraren samariJoda tace kekike ce ay badaya muke ba, ni nasan dakyar ne gwaggo zata bari inyi karatu, kinga kuwa gara nakula saurayi musa danta tin wuri khalthum tace gsky idan kikayi aure kin cuci kanki awannan tymdin sc skull bakomai bane, kije kiyi karatu sosae kigan yadda jama'a zasu rika girmamaki, bama shegen dazai kara cewa wai ke Yar aiki ce wlh sedai a rufe zancen , joda tace allah koh? .............馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 4鈨�4鈨�Joda tace lallae kuwa zan same gwaggo wlh natsani abunda akecemun wae Yar aiki sekace wata barauniya 馃槄 , khalthum tacetosae me Dan ance miki Yar aiki, ay ba shegiya aka ceba, joda tace kam yo ingamaDan kutumar uban daxae cemun shegiya wlh bakinshi yayi tsami, khalthum tabare da dariya, kae joda akwaiki da fada wlh , joda tace ahhh.....ay gsky ne, mu za'a nunawa asali, mahaifina Dan asalin Dan binji ne, gwaggo kuwa wani zubin ma, balarabiya ce Dan Yar masina ce kusaga Sudan , fulani neamma ruwa biyuKhalthum tace lallae iyakar asali kenan, joda tace ke bawannan ba, nifa wlh phone kebani sha'awa, khalthum tace kae joda akwai ki da kiriniya kinganni nan inada phone yakae biyar wadda abbana kisayaminamma suna a kwati na, ajiye se nagama skull, joda tace kae amma bakiyi ba wlh , khalthum tace nadae ji tashi Muje Dan allahtym x overDriver ya ajiyeta dae2 gate tahangi abdallahrungume da hannayensa , yana mata murmushi, joda ta karasa cike da nishadi, tace kaddai ni kake jira haka? Abdallah yace kwarai da gaske kenake jira since bakidawoba yakarashe zancen cikin sigar shagwaba, joda takallesa ta kyalkyale da dariya, tace kae abdallah abun yara kakeyi , abdallah yace ay idan ina agabanki ni yaro ne seyanda kikayi dani, joda tace kana fasamun kae fah, abdallah yayi dariya yace hava dae my queenHaka suka jero har kofar dakinsu yarakata yace idan kinshirya ina jiranki a garden, jodatace ok 30 minutes, abdallah yace hava Danallah har 30mnt, joda tace bayawafa yanxunzanfito, tashige abunta ta barshi gurin murmushi yayi a ransa yace tafara kamuwa fah, gaba kadan zan cimma burina , yasosa kansa yashige side dinsu, mansura yasama kan dining tana lunch, yatabe baki sannan yace anty barka dazuwa, mansura dason girma tace qlw son hw x 2yd? Abdallah yace cool, mansura tace gud, yanxun Muje zaka kaini kadunaAbdallah yazaro ido what, kd at diz tym mudawo yaushe, mansura tace kai dallah bansan iskanci zuwan Dan wa za'a yi badan kaba , abdallah yace kamar ya Dan ni? Mansura tace wannan kuma ba dole kajiba kawai kaje ka shirya, abdallah yace anty wlhba inda zanje karshen mgn kenan yana kae nan yayi downstairs yabar ta, cike da alhiniMansura tasami hjy tagayama ta duk yaddasukayi da abdallah, hjy tace kibarshi badai sahun kafarshi akesoba kije garden gefen tanki akwai kasa kidebo seki zuba akofar shigowarshi dakinshi , mansura tace wow dz x my 6 kae anty kin iya hadoshi wlh, hjy tace nifa akace ay basauki ingayamiki, ni wannan shegen sudawo ma, muga ya nashi yanayin zai kasance a kankiMansura tace ohh...anty wlh gavana har faduwa yakeyi idan natunasa, kunsan me tinranda mukayi waya aranar ko baisake daga wayata ba kuma yayi blocking dina a WhatsApp yaki accept request dina a fb yaki following dina a instagram, bbchat snapchat, wechart, soma , imo palmtchart, hjy tace kai ya isa haka duk wadannan chrtsdin takeson kinayi ?Mansura tace eh mana danma Kin katseni ay basu kadai bane akwai twitter....hjy tace ke barni haka Dan allah dama acan kike karar da kudinki gurin siyen data, mansura tace kai anty akwai dadi fah baki da wata damuwa idan kina chrt, hjy tace allah yataroki charting ko sallah baya barinki, mansura tace kae anty inayi fah, Hjy tace kina me yau sallah kodaya bakiyi ba, mansura tasosa kae to ay zanyi, hjy tacekedai kika sani duk lalacina sallah baya wuceni, mansura tace inayifa anty se zani kwanciya nakeyi, sena hada duka, hjy tace kyaji dashi allah baya san hakan gwanda kigyara tin wuri shi isa ma kika kasa samun Ahmed nasan baxai rasa Jin lbrnki agari ba, tin wuri kisake tunani, dole kizama kamila kiyi watsi da samarinki kikama sa shi kadai hakan zaisa yatsaya kulaki.............馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 4鈨�5鈨�Tafiya suke ajere suna shan ice cream abunsu kae kana ganinsu kasan suna cikin farin ciki, abdallah yadubi joda yace bae zanyi tafiya fah, joda tace me? Tabata fuska yaushe, abdallah yace gobe amma bazan dadeba sati daya ne, joda tace sati dayafa ni wlh baxan yarda ba ay sati daya tamkar shekara daya ne agureni, abdallah yace calm down mana nagaya miki baxan dade ba kuma zamu rika waya da telephone, jodatayi kadi da ice cream dinta tanata buga kafa ni wlh baruwana dakaiAbdallah yadafe kanshi, Yace oh gosh ni yaxanyi da wannan yarinyar ne, nifa kawai saboda tayi missing nawa yasa nakirkiri wannan tafiyar, ina dawowa zan gama aiki, murmushi yayi yawuce hanyar gate, anan neyahadu da dad, Yace ji man abdallah yafito amotarshi yace ahhh....abdallah yanzun daean shiryu an daena shaye2 koh ? Abdallah yadafe kae yana wani murmushi ehh dad andeana, dad yace to yayi kyau allah yakarashiryamun kae ameenAbdallah aranshi yace hmm nadae na me. uhm ay badan allah nadae naba inasamun bukata ta gun joda zan koma ga halina yanxun ma a matse nake, ina zuwa kd zancigaba da harkata ( Allah ya shirya abdallah ) ameen, dad yace mene kake tunani haka? Abdallah yace no ntn dad, dadyace to shikenan jeka allah yamaka albarka ameenSu Ahmed angama wannan mission din murna gun Mahmud ba'a magana kullum baida zancen dayawuce na joda, haka zasuyi tafada da Ahmed domin shikuma in da wadda yatsana a duniya baifi joda ba, acewarshi itace sandin mura yakamashi, shirinsu sukeyi bawasa tin safe suka hawo jirgi sea birnin tarayya, Ahmed yakalli Mahmud yace kayi waya zakazo gida kuwa?Mahmud yace a'a kaifa? Ahmed yace dsame, Mahmud yace to ya kenan, Ahmed yace kainifa banasan wannan bahon yaganeyau muka dawo yatsaremu agidansa, Mahmud yace waye bahon lallae Ahmed wlh bakada kirki, ina laifin Dan yakula damu ay bamukaday keyin tafiyar ba amma mubiyu kadae yake ma hakan tink mana sone kokuma me?Ahmed yace kae dallah shut up ina ruwana dawani kulawarshi, nafi bukatar nasauka agidanmu , Mahmud yatabe baki okey sekayi waya azo adaukeka, Ahmed yace kaidae zakayi wayar idan driver ka yaxo sekuyi dropping nawa, Mahmud yace wannan kuma karyanka sedai kowa yanemi nasa driver n, indan kawai kayi waya kace azo adaukeka shine kake Jin haushi , Ahmed yace kae ya isheka fa haka, wani soldier dake jinsu yaxo yace A marafa kazo nayi dropping dinka manaAhmed yace kae kuma waya tasaka aciki dallah malam bace mun dagani, Mahmud yabuga tsaki yace ahaka din zan yi drop dinka, Ai wlh sedai kowa tasa tafish shesa, Ahmed yace dayake kasan gidanmu ba motor shine zaka wani tada ji jiya banza kawae , Mahmud yace oho dae nidae bazaniyaba indae baxaka iya waya azo adaukeka ba sedae ka tabbata anan gurin, Ahmed yajuyo afusace yace wlh zamuyi kutumar uba anan gurin idan baka mun shiru ba Dan iskan kawai, Mahmud yayi murmushi yafidda wayarshi yasaka kiraJoda tafito daga dakinsu kawai taji wani irinsanyi na ratsata, ta lumshe idonta tacigaba da tafiya, dama kuwa tafito ne kawae saboda tasha iska, Jin karar Bude gate yasata Bude idonta dasauri, wani murmushi tasaki wanda yasa dimple dinta lotsawa ta dunfari motar aguje, tsayawa tayi jiran abude , motar kusan minti biyar shiru ahankali ta yi knocking din ganbun motar tana baxaka fito bane , Jin shirun yayi yawa yasakata lekawa amma kuma ba'a gani, atake tashiga buga kafar ta ni wlh kabude mun motar kona fasa glass dinHuuuuuu........taji wani sanyin nakara ratsatasakamakon, bude kofar da akayi idonta arufe ahankali tabude tana fadan kae koh 馃様Kammm waxata gani 馃槼 , harara kallon tsana tsangwama bawanda Ahmed bai bita dashi ba, idonta kafff kan nasa takasa saukewa fuskarta cike da tsoro, tsawa yadaka mata Dan ubanki kibani hanya kafin in yi ball dake , ko motsawa batayiba balantana insaka ran zata basa hanya, hakan yakara basa haushi gashi dama yadawo da takaicin Mahmud kafa yasa ya turata dakarfi, kara tasaki tareda rike hannunta tana wayyo gwaggo nah.............Muje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 4鈨�6鈨�Seda taci kukunta mai isarta sannan ta kamo hannun ta , tanata hawaye har tashigadakinsu tasamu gwaggo bata waje, taje kankatifa tanata kukanta, har tayi bacci bata farkaba se kusan 3:30 zata mike tsaye ne setaji hannun yamata nauyi koda taduba yajuya gaba ya koma baya, jikin ta yahau bari wani zafi takeji har cikin zuciyarta , kuka yadawo sabo, azatonta zata iya daga hannun tafita aykuwa tana tabawa tabuga wata shegiyar kara duk wanda kegidan Seda yaji, gwaggo tafito da sauri tana fadanlfy , joda tafashe da kuka wayyo gwaggo hannuna zai cire gwaggo taxo tana dubawa tafara salati itama din rudewa tayi,Tace joda meyasameki haka dakyar ta iya furta faduwa nayi ,gwaggo tace subhanallahAi karyewa kikayi amma yanxu ay nabaki kina baccinki, joda tace tin dazu ne, nazata bkomai bane shine nazo nayi kwanciya ta, gwaggo tace yau na shiga 3 yanxu hannun yayi tsami sekinji azaba wlh, joda takara fashewa da kukaKansancewar dad yace duk abunda ake bukaqata anemesa, shi isa gwaggo takira hasana mai ayki tagayamata itama arude tashiga babban falon gidan tadanna bell, Ahmed dake saukowa downstairs yace ke lfy kike nemanmu, arude tace ranka yadade joda ce.....ya isa banason Jin wani bayani, hasana tace ranka yadade karyewa tayi ahannu kuma wlh hannun yabaude sosea, Ahmed yace what!?馃槼 karyewa garin ya, hasana tace faduwa tayi daxu shine tayi baccinta yanxun tafarka ne hannun har yayi kunburi, Ahmed yasaka hannu a aljihunsa yazaro bandir din yan dari biyar yabata yacegashi ku kaita clinic hasana tarisina tanata godiyaKaro nafarko da Ahmed yasaurari zancen daya danganci joda, dakinshi yakoma yacigaba da harkokinsa, kamar bashi ne silaba, hasana nazuwa tabawa gwaggo kudin tareda mata bayani, gwaggo tace bara nadubo katinta na asibity, hasana da gwaggo suka kamata akafito da ita, Sega driver dinta yazo basuyi wata2 ba suka shiga se clinic dinda sukaje kwananan baya, suna fidda ita Sega nurses sunxo dakujera aka axata, sewani room asama, Su gwaggo suka rufa masu baya, gurin wanidoctor aka kaita, suna ajeta zasu juya yace duka su tsaya dole se anriketa, joda kuwa tagalabaita se nishi take, hannun kadai yariko amma Seda tasaki wata qara, tuni gwaggo tafashe da kuka hasana tajata sukafita waje , doct din yace abasa allurar bacci kusan ukku ana mata amma taqi bacci se nishin wahala take dole suka kama aka riketa sosae bismillah yafara sanan yajanyo hannun yajuya shi dasauri yakoma qattt kakeji tuni joda tasume hakan yabasu damar daure hannun da kyauDayan nurse din tace sir amma yakamata abasu gado saboda taji jiki sosae kar sukoma gida alalata daurin, doct yace ehh ay se anwarware daurin duka zasu koma, anan suka fita suka barshi da ita, fuskanta yashafa yace allah yabaki lfy kanwata, bansan wani irin so nake yiwa yarinyar nan ba, tin randa nafara ganinta amma zanyi kokari in koya mata sona, indae har zata cigaba da zuwa nan asibitin,Zan samu information akanta naji koyar waye miye asalinta, cikin wannan tinanin neyaci tafara motsi, dasauri yataso yace sannu kanwata daga masa kae tayi, idonta duk sunyi jajir sun kunbura, tea ya hadama ta mai kauri yabata, takauce fuskarta, Yace hava kanwata ki sha mana, Jin yakirata da kan warshi yasa tadubesa sedai bata ganin fuskarsa tinda yasaka face mark ,abaki yadinga bata har ta qoshi sannan yabata ruwa, zae fita ne tace likita sallah zanyi, cak yatsaya yajuyo yace kanwata sedai kiyi sallah aranki amma kinga bakya iya tashi alwala ma baxaki iyaba, joda tace toni ina gwaggo na, likita yace bari akira miki su yanxun idan su kike buqatar gani.............馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 4鈨�7鈨�Nurse yakira yamata bayanin komai sannan yakoma office dinshi , akasa tasame gwaggo tamusu bayanin komai gwaggo tace nidae wlh zaman asibity badadi, hasana tace hakuri zamuyi za'afi kula da ita anan sabanin can ,gwaggo tace hakane yanxun tinda ga driver ke kije gurinta ni saena je nadauko mana abubuwan buqata, hasana tace hakane kiyi sauri ,gwaggo tashiga mota hasana kuwa tayi sama gurin joda,kwance tasameta idonta arufe ahankali ta janyo kujera taxauna Dan atunaninta bacci joda keyi , segata tabude ido , dasauri takarasa gunta tace sannu joda, joda tace yauwaBayan kamar minti shabiyar Sega gwaggo tadawo, harda abunci, joda naganin gwaggotafashe da kuka, hasana tace yo naji munafukar yarinya tindazu muna qlw Dan kinga uwarki zaki saka kuka, gwaggo tace kodai kin kwance tane , hasana tace cizonta dae nayi bare kwanta,Ferfesun hanta da cabeg ne yaji sinadaran dandano se kamshi ke tashi, ga kuma sakwara da miya ogun, gwaggo tazuba aflate tabata, joda taki karba, gwaggo tace kae na manta hannun dama ne, amma wlh akwae aiki kafun ki warke , joda tace nifa banaci, gwaggo tace karyanki wolla dole kici, akayi2 amma joda taki ci, hasana tace bara akira likitanta, aikuwa segashi, hasana tace likita gata nan bata cin abunci , likita yanuna masu kofa alamar su fita, hasana taja hannun gwaggo suka fita , gwaggo taceshi kadai zaisa ta taci ayadda yake dinnan fuska ba annuri, kwananan baya ma shine muka samu yaduba ta kinga ko yanxu shine,amma fa likitan yasan aykin shi yana lallabamarasa lfy Kujera janyo daf da ita yasaka spoon acikin abuncin yafara bata abaki , tanata yamutse fuska bai kulata ba, yacigaba da bata har abuncin yakare yazuba mata lemu da ruwa tasha sannan yakawo magani yabata, Yace ar u okey? Joda tace I think so, doctor yace menene? Joda tace bkomai ay bana Jin dae2 ne, doct yace taya kuwa xakiji dae2 bayan bakida lfy,Yanxun gayamun taya kika fadi ahannu haka har kikayi muguwar karyewa? Joda tafashe da kuka, doct yace plss kanwata yihakuri bansan kuka zakiyiba ay da bazan tanbiyekiba , joda tace shine yaturani akan dakalin gidansu baya sona yatsaneni baya san ganina muryana ma bayaso, doct yace ya isa haka waye wannan damugunta haka? Joda tace Dan mai gidan ne shine babba wanda nabaka lbr abaya, doct yace au ashe kingane nine nazata baxaki ganeba, joda tayi murmushi tace nagane ka magana, doct yace taya kika ganeni , joda tace wannan kamshin iri dayane Dana wancan tym din kuma kae dogone kamar wancan mugun, doct yace hava kidena hadani da mugu manaYanxun kibani labarinki, joda tace kamarya kenan ? Doct yace garinku asalinki skull dinki an others, joda kuwa tafara basa lbr kamar yadda tamasa ada, Yace anya wannan Ahmed din ba sonki yake ba, joda ta rufe bakinta Dan allah rufamun asiri kar yasake karyamun kafa, doct yace ina zaiganki ay duk wannan abubuwan take2 sone, sonki yake bilhaqqi amma yakasa yarda da hakan inaji yanada feelings akanki soseashine abunda kedamunsa,Joda tace in possible wlh, ba yadda wannanyaron zai soni, yana Jin kanshi kamar wani sarki baya tsoron kowa ni wlh bana fata ko hanya tasake hadamu bare zuciya doct yayimurmushi shikenan naga kin tsorata a bar zancen kawai tinda baki so, amma meyasa kike tadi da abdallah, joda tace ay nagayama komai sona yake nima kuwa haka,doct yarike baki yace ikon allah yanxun ke kinsan so, joda tasa hannunta tarufe idonta, Yace dama kin bude ni baruwana, amma kiyi hankali da abdallah nasanshi farin sani ba shida kyau wlh, joda tace lfy lau yake nidae banga wani aybunshiba dayaga dae bata son zancen dole ya bari amma koba komai yaji relief akanta sakamakon Jin lbrnta da yayi...........馃巹 FULANIN DAJIN@ B aleeyu 馃挄 page 4鈨�8鈨�Haka abun ketafiya kullum wannan doctor din shiyake kula da ita tinda sassafe zaizo yabata breakfast, haka lunch ma zaizo hakaidan dare yayi shiyake bata har tafara sabawa , Mahmud nazuwa kullum dubata tareda yan tsarabarshi, se sun sha fira sannan yakoma, joda tafara Jin sauqi,khalthum kuwa kullum tana hanyar asibity duba joda, ta tsinewa Ahmed yafi aqirga, joda tace kenifa na barshi da allah kifita harkanshi kawai, khalthum tace wlh joda daace nice ke to wlh kuwa kodan uban waye bai isaba yatakani shi har ya isa ba soja ba bura'uba, joda ta rufe mata baki kae khalthum kiyi hakuri Dan allah kiyi shiru banasan irin wannnan zage2Doctor ya ajiye biro dinsa yabi khalthum da ido to itakuma wannan wacece? Tambayar dayayiwa kansa kenan wadda ba'a amsa, yana saurarensu duk firar dasuke, sedai bai tanka ba amma yafahimci wannan khalthum din akwai zafi dukda joda ma nada nata zafin, shakuwa mai tsanani tashiga tsakaninsu da doctor dinta, sedai tana cike da kewar abdallah , ana haka Sega shi murna gun joda ba'a magana,Seda tagama yimasa shagwaba sannan suka sha yabata hakuri kan dadewar da yayi, yana fita gwaggo tace joda wai ni miyetsakanin ki da wannan yaron ne? Joda tace bkomai gwaggo cewa yake ni kanwarshi ce gwaggo tace to wlh kiyi hankali dashi nidae wlh dama kin yanke wannan alakar atsakaninku, joda ta juye baki a ranta tace kuji gwaggo fah Dan baki san miye so bane shi isa kike cewa na rabu dashiGwaggo tace mekika ce? Joda tafara a'a in in dama cewa nayi, gwaggo tace dallah yimun shiru shasha yarinya ana nuna miki gsky kina kaucewa, joda tasadda kanta kasa tace Dan allah kiyi hakuri gwaggo, gwaggo tace bkomai ina kara jadda da mikibana San tarayyarki dashi karshen mgn kenan, joda tace gwaggo Dan allah kibani lokaci yadda zan koyawa zuciyata rabuwa dashi bazan iya farat daya ba, wlh tausayin shi nakeji har kuka yake mun , gwaggo tace oh yaro man kaxaAhmed zaune kan gadonsa yana latse2 awayanshi, Mahmud yashigo yazauna, Ahmed yace daga ina haka, Mahmud yace daga gurin joda nake har tafara Jin sauki, doct din yasan aykin shi wlh, ni naso na ganshi na masa godiya, Ahmed yatabe baki yacigaba da aykinsa, Mahmud yace kozaka je ka dubata, Ahmed yagalla masa harara yace inje inyi uwarme acan? Mahmud yace uwarka xakayi acan da iskanci Dan kawai kaje dubata shine wani abun bayan koba komai akwai lada acikiAhmed yace ni kake zagin uwata akan watabanza , Mahmud yace yihakuri banji dadin zancen kabane shi isa, Ahmed yasadda kaeyacije lebe yacigaba da aykinsa, wayarshi ce tadau ruri uban tsaki yabuga ganin wake masa waya , daga ganin yanayin shi Mahmud yagane ko waye kemasa waya, Mahmud yace da kayi hakuri dae kadaga wayar ka Mai sonka yafi makiyinka, Ahmed yace agareka hakan yake ni agurina gwara makiyi akan masoyi .......Muje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 4鈨�8鈨�Mansura nagani anci ado tamkar wata amarya se kwarkwasa take tana juya duwawuna, dakin Ahmed tanufa ba fargaba ko darr azuciyarta, knocking tayi nayi kusan minti biyar shiru ba'a bata izinin shigaba, hakan yabata damar murda key din dakin tareda sallama, Ahmed na zaune kan kujerayana kallo a system dinshi baida go ba , ya amsa sallamar tsaye tayi tana jiran dagowarshi, can da taga tsayin bamai karewa bane tace barka da hutuwa ranka yadade, banza yamata yacigaba da harkokinsaAhankali tasake cewa Ahmed ya hutuwa, nanma shirun ne yabiyo baya , mansura kam tadan tsargu , tasake cewa Ahmed mgn fah nake maka amma kamyimun shiru, Ahmed yadago afusace yace waeke mayyar ina ce, mekikazo yi a dakina na nemiki ne kokuma ya? Mansura tajuya masa baya gudu kar yaga hawayenta, tace hava Ahmed kaso mai sonka koda kashi ne,bare mutun,Ahmed yace ay kashin ma yafiki daraja agurina, da zanga kashin da kuwa zakiga yadda zan daukaka darajar shi sama da takiwawiyar banza jahila kawai get out yanuna mata kofa, bamu su mansura tafita amma me? Tana kae kofa tatsaya batareda tajuyo ba tace wlh Ahmed ina mai shaida maka cewa sena aure ka kota halin kaka, ka soni koka kini bashine damu wataba burina naganni a gidanka amatsayin mallakinkaAhmed yace shege kafasa idan kika cigaba da cusa kanki a rayuwa ta to wlh zakiyi Dana sani na har a bada , mansura tace ok toh shikenan Muje zuwa nida kae, kasani bazan kara kawo kaina agareka ba, dakankazakaje neman aurena, kasaka wannan a ranka!!! Ahmed yayi murmushin mugunta yace duka bokayen duniya da malamanku basu isa suja daniba, ki koma kigayawa bokanku yayi kuskure da yayi tunanin zai iyagalaba akaina, malaminki yaudaran ki yake ba abunda zai iya yimun, mansura tayi shiru Jin kalaman sa kana tafice daga dakinDakin hjy taje tafada kan gado, hjy na sallahta Idar tace lfy mansura kika fada kan gado dakarfi haka ? Mansura tace inafa lfy anty kinji yadda Ahmed yace, nan ta zayyane mata yadda sukayi dashi, hjy tace indan wann karma ranki yasosu ina baki tabbacin Ahmed naki ne har kin samesa, mansura tace allah ko antyna, hjy tace sosea ma dubi nan, wani Dan karamun kwalba ne da turare aciki, hjy tace yana Jin kamshin wannshikenan angama dashiMansura tadaka tsalle wayyo dadi kasheni , hjy tace ungo kiyi hankali dashi dashi bakaramun kudi nazuba aka bani shiba har Niger aka karbo mun shi, mansura tace to ya ake amfani dashi? Hjy tace ajikinki zaki sakashi kisamesa, seki gayamasa cewa yaushe zae turo ayi mgn, mansura tace kae anty wlh ina Jin tsoro kinga yadda ya wulakanta ni yauHjy tace hakuri zakiyi tinda kekike nema ba'a gaggawa, idan kika bi komai ahankali zamuyi nasara, mansura tace to yanxu yaushe zan saka hjy tace bayanzuba se bayan kwana biyu, ni bani turaren kar kije garin rawar kan tsiya kifashe shi , mansura tace wae anty ina amina tin danazo bangantaba yanxu har 10:30 ace bata dawo ba, hjy tace ay wlh bataji ne nayi2 ta dena yin dare se ayita zagina agari bataji ne yanxun idan Ahmed zai fara yiwa mutane iskanci....shiru tayi Jin ihun amina gabadansu suka fito agujeAhmed suka tarar yana dukanta yana ball da ita hjy tasaka salati na shiga uku Ahmed kashe ta zakayi, Seda yamata lis sannan yace Al qur'an idan nakara ganin ki kinfita da irin wann shigar ta yayan arna wlh sena kakkaryaki bare kuma har kiyi dare haka tukun na ma gidan ubanwa kika fito?馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 5鈨�0鈨� HAUSA NOVELS SOKOTO WHATSAPP 07068808039 Cikin muryar kuka tace gurin bithday din saurayina Ahmed yakara hankata saurayi koh, to wlh kishiga taitayinki idan nakara ganinki kinfita koda get ne batareda izinina ba wlh se jikin ki yagaya mikiKuma kisani kitattara kayan ki ki koma islamiyya on Sunday, hjy tace kae ya isa haka sekace wani ubanta zaka wani gindaya mata sharudda haka, Ahmed yace inada ikon yin hakan ne kuma babu ubanda ya isa yajanye wann tsarin, hjy tace koda uwarta ne, Ahmed yajuyo afusace yace koda ubanta ne!Dae2 nan abba yashigo yace tabbas ko ubanta bai isa yajanye wann dokar ba bare kuma uwarta, hjy tabuga tsaki taja amina sukayi sama Ahmed yamaida kallansa ga abba yace abba barka dazuwa, abba ya amsa da lfy lau Ahmed yagajiya, Ahmed yace ba gajiya, abba yace Ahmed kayimun dae2 kacigaba da hukunta kannenka wann shi zai tabbatar mana dacewa koda mun mutu mun bar baya muna da wanda zai tarbiyan tarda yayanmu, Ahmed baice,komai va yashiga maida belt dinshi daya ZareJoda kam jiki Alhamdulillah tafara warwarewa, har wata kiba naga tayi yan kasusuwan jikinta duk sun bace, tayi cif cif da ita, yau satinsu biyu kenan, idan anyi lesson a skull khalthum tana tashi seta biya gurin joda tamata bayani sannan ta wuce gida, abdallah kuwa kullum yana kan hanya shida Mahmud narasa wayafi bata kulawa acikin mutun uku doctor ko abdallah kokuma Mahmud dukda khalthum ma ba'a barta abaya baAbdallah yakalli joda yace bae yaushe zaki koma gida? Joda tace nima bansaniba ask doct, abdallah yace okey ana haka Sega doct ya shigo, abdallah yabasa hannu suka gaisa, Yace doct yaushe za'a bata sallama ne, doct yace itace tace maka tana bukatar sallama? Abdallah yace no, doct yace gud taji sauqi ne har tana iya komai sa hannun koh? Abdallah yace no hava gashi kana gani, doct yace to me kake bukata da abata sallama tinda ba kula zakuyi da ita agidaba kamar yadda yakamataAbdallah yace shikenan allah yabaki lfy kanwata ameen , joda tace doct mura kakeyi ne, doct yadaga mata kae yacigaba da rubuce2 joda ta tabe baki bansan meyasa yake bata ranshi ba idan yaga abdallah agurina , sedai kayi ni bamai rabani dashi shine hasken idaniyata abdallah yace bae zanwuce sekuma night, joda tace tom amma Dan allah karkayi daresosea kamar yanda kakeyi, abdallah yace kinsan fah inada abubuwa agaba nane matse wa nake ina lekowa gurinki,joda tace nadae gayama idan nayi bacci karka kuskura katadani, abdallah yayi murmushi to ranki yadade , yana fita doct yarufo kofar dakarfi har Seda joda ta tsorata, tace lfy doct? Ba lfy ba shine amsardaya bat! Joda 馃槼 meyafaru? Kace mura kake kuma gashi muryanka ayanxu qlw, docyace yess , ba lfy ba, banason ganinki da wann yaron zai bata miki tarbiya yaron dakeshaye2 , joda tace ya isa haka bakada wannhurumin na shiga tsakanina dashi koma daemeyake sha ina sonsa ahaka kuma babu wanda ya isa ya rabani dashi , doct yadaka mata tsawa dacewa how dare you ni zaki gayawa mgn tuni joda tashiga taitayintaDoct yace b carefull you do not know me , joda ta kankame jiki tafara kuka abunda yatsana kenan kukunta glass dinshi yasaka yabar mata dakin , yana fita tafara tunanin anya kuwa ta kyauta hakan datayi, yinin ranar baidawo ba baixo bata lunch ba bare na dare haka tawuni da yunwa , damuwa fal aranta duk wanda yaxo dubata haka zai hakura yakoma anrasa kanta ,Mahmud da abdallah atare suka zo tana Jin shigowarsu ta lafe kamar mai Jin bacci...........馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 5鈨�1鈨�Ahmed yafito daga room dinshi zai shiga kitchen yahada coffee , mansura kuwa dama tana labe kawai segata aguje dae2 nan Ahmed yafito suka hadu da juna dasauri Ahmed yaja dabaya yana kokarin rufe hancinsa 馃檴 Jin wani kamshi tareda wani yanayi yana shiganshi, ganin haka yasamansura yin sauri takarasa kusansa ta warehannayensa Ahmed yashiga juye2 da kanshiyarasa inda yake masa, dadi kasa yadinga yi har yakai kan carpet yazaunaMansura tace yade Ahmed, ahankali yadago idonsa dasuka kada sukayi jajir yace bakomai ina son na kwanta, mansura tajanyo hannunsa sukayi room dinshi, kan gado ta ajiye shi , ido kawai yake binta dashi, mansura tace mekake bukata ne, Ahmed yace bacci nakeson yi , mansura tace bismillah , kwantawa yayi tareda wasu tinanin wadanda yakasa gane kansu, mansura tadaka tsalle tayi dakin hjy da gudu tafada kanta I love you my cwet anty wlh yakamu, anty kinga kuwa yanda yake kallona, hjy tace dakyau seki fara aykinki bawasaKarfe 2 dae2 Ahmed yafarka tareda rike kanshi dayakejin yana juyawa , yana son tuna abunda yafaru amma yakasa , wanka yayi yashirya cikin kananan kaya , yana kokarin fita wayarshi tadau ruri, new number ce saboda haka baidaga ba Seda tayi kusan 3 miss call sannan yadaga tareda fadan yess, Jin muryar mansura yasashi Jan tsaki tareda fadan ya ake ciki? Mansura tace inaso karakani shopping ne, Ahmed yace kinga na miki kama da mai rakiyar maceMansura tace shikenan tinda baka sona, Ahmed no kigane banda gud tym ne amma zan baki driver, mansura tace ni idan baxaka kai niba kabarshi kawai kafi driver agurina, Ahmed calm down mana zaki iya barin firar har zuwa night yanxun inada abunyi ne, mansura tace allah yakaimu, my man Ilove you.....Ahmed yace uhm.....Thanks mansura tace au baxaka cemun you love me ba, Ahmed yace ay base nafada ba fadanshi bashi yake tabbatar dashiba, mansura tace dukda haka nidae nidae inason Jin wann kalma daga bakinka , Ahmed yace sena dawo I'm busy ya tsinke wayar yafitaMansura tace ay day tinda baxaka iya cewa baka sona ba komai yayi nakusa kammalawa da matsalar ka, Ahmed kuwa yana Jan mota yana mamakin kanshi shi kam yarasa meke damunsa akan mansura yana Jin wani feeling akanta yarasa ko miye, yafe yake yana shan wakar ice prince. Waya yake da hafsa cike da kulawa yanata tambayar yakaratu ba abunda kike bukata hafsa tace bakomai bruhh , sedai ina neman wata alfarma guda daya Ahmed yace yes go on " hafsa tace bruhh plss ina son mgn da joda, Ahmed yace hafsa zaki fara koh? hafsa tace sowie bruhh, Ahmed yace dont lemme warn u again , hafsa tace bruhh.....shhhh yafada bana San Jin komai dole tayi shiru tareda Jin wayar ma ta tsaneta dukaJoda kwance abun duniya duk ya isheta tin ranar bata kara saka doct a idonta ba sedai yaturo wata likita tadubata idan joda ta tadubata ya doct baya xua se tace mata yana busy ne, gashi ankusa bata sallama tinda hannun yayi kyau yanxu tafara motsa shi da kanta yau sunada text skull saboda haka tin wuri tashirya driver yaxo yakaita a skull se xua dubata ake ana mata sannu karfe 12 dae2 suka fito exam principal yatava izinin komawa gida ganin yanda takeDama kuwa driver na jiranta tana fitowa suka sa kae se asibity dae2 kofar shiga asibity tahadu da Ahmed Yana fitowa dumm taji gabanta yafadi dasauri take ja dabaya baya, Ahmed kuwa yatsuramata idoyana kallan shigarta acikin uniform, ido yazare 馃槼 naga ya yada key din motar shi ya na fadan jodaaaaaa鉂� wani rin tsalle naga yayi yacab kota suka fada gefen titi , mai motar yafito da niyyar basu hakuri sekuma yayi turus ganin irin kallon da Ahmed kebin joda dashi ita kuma idonta arufe..........Muje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 5鈨�2鈨�Joda ta turasa da karfi da koma gefe tana maida nunfashi , Ahmed yamaida kallansa ga mai motar yace kae mahaukacin inane kana ganin ta tana yowa baya da baya baka iya yi mata horn ne? Mutumin yace to ay laifin ta ita batasan kan hanya take ba , Ahmed yace bazaka gane laifin ta bane Seda ace ka maketa wlh daka san katakarowa kanka bala'i,mai motar yace yi hakuri ranka yadade, amma dae kanason matar nan taka dayawa, Ahmed yace what? 馃槨 ubanwa yagaya maka cewa matata ce, Mutumin yace am sorry irin yadda ka tsorata ne da kuma yanda naga kana kallanta yayi kama da yanayin so mai babban Al amari aciki , Ahmed yace bansan raini kagan namaka kama da banza ye ne, wann kanwata ce yanuna ta batareda yakalletaba Mutumin yace ayya gsky kana son kanwar nan taka dayawa, shi isa kuke matukar kama big eyes dinnan naku iri daya da sexy lips dinn , Ahmed yadaka masa tsawa, tuni yashiga motar shi yabar wajen ganin yanayin AhmedTin randa Ahmed yafurta cewa kanwarshi ce takasa daena kallanshi se mamaki take yau itace Ahmed ya kecewa kanwarshi ce, murmushi naga tayi wann shine nabiyu ko menene oho" Ahmed yadauko jakarshi ko kallan inda take baiyiba yanufi motar shi Kamar ance yajuyo, yagan tabishi da ido wata harara yaballa mata tuni tajuya da sauri, ashe akwae ruwa agurin jinta kakeyi tisss tafada aciki kuka tafashe dashi wayyo gwaggo hannuna wayyo hannuna Ahmed yayi Jim kadan sann yafito yaganta se hawaye take, tsaki yabuga yace zakumin shiru kosaena kara karye miki hannunJoda ta dukadda kanta se sheshsheka take wayarshi yaciro yakira wata nurse cikin kankanin lokaci Sega su su uku yace ku kaita sama a dubata yana kai nan yafice yayi gurin motar shi " joda kam se kuka takehar suka isa da ita sama, cikin muryar kuka tace Dan allah kukiramun likita nah, dayan nurse tace karki damu yanxun zaizo zanmasa waya, joda tacigaba da kuka sunata bata hakuri, kwance daurin sukayi sann suka duba, dayar tace anisa dubamun ay kamar taji sauki,Wani doct ya izo mata yace bashida lokacinzua, shi yaduba daurin yace base ansake wani ba taji sauki sedai kawai Dan wann faduwar datayi ne amma zua 5dyz za'a batasallama, joda taji dadin Jin hakan Dan kuwata qagu da zaman asibityn, baccinta tayi na kusan awoyi biyu se kusan la'asar tafarka sann taje tayi kowace sallah takoma kwance tana tunanin irin yadda doct yadau abu dazafi haka, abunci aka zuba mata amma bawani cin kirki tayi masa ba sama2 taci takoma kan gadoAbdallah yashigo rike da Yar ledarshi, yanata fa man yiwa joda murmushi joda kuwa ta kawadda kanta gefe, Yace kanwatanayi laifi ne? Joda tace a'a kawai banajin dadi ne, abdallah yace meyake damunki, joda tace bakomai kawai dae bana Jin dae2ne, abdallah yace ayya bae konakira doct neadubaki, joda tace a'a bana bukatar hakan bacci zanyi, dayaga dae dole bata san firar ya ajiyemata ice cream dinta yayi mata saeda safeMansura tareda amina suna saukowa downstairs, dae2 nan dad yafito room dinshi aikuwa yayi kamar baigansuba, amina tace dad barka da fitowa yaamsa da yauwa, mansura ma tagaidashi yakarba bayabo ba fallasa, mansura tace jeki kiramin Ahmed amina tace what? Ahmed fah sokike ya bibbigeni a banza wlh baxan jeba yaushe ma kikayi wann matsayin keda ko Kin samesa a dakinsa wulakanta ki yake bare kuma ya amsa kiranki ay seki saka ya sanbadeni wlh yanxun zaifito ya shuka miki rashin kunyaMansura tace dakata kiga, wayar ta taciro tasaka kira Seda tayi ring yakai biyar sann yadaga, amina tace ahto, dama dae kin hakura da wann miskilin dayafi, mansura tace hava babyna yabaka daukan waya, Ahmed yabuga Dan tsaki sann yace ina toilet ne, mansura tace ok kasameni a dining akwai maganar da zamuyi, Ahmed yace bacci nakeji sedai kayi bari har natashigobe kenan understand? Mansura tace hava kae wae goma mutun yake da bukatar ganawa dakae seka kawo masa naka uzurinna daban idan baxaka zo yanxuba abar zancen kawai............馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 5鈨�3鈨�Ahmed yadaga kafada yace alright , amina tabushe da dariya tace mena ga yamiki antywlh ko dad baya masa wann ikon kince dolese yanxu, ay wann dolen dakika ce shizai hanashi xuwa koda kuwa yayi niyyar xuwan, mansura tace ke wlh zanci ubanki kikama mun bakinki Yar iskar yarinya....shiru tayi Jinkamshin turaren sa nadosota , dukansu suka juya Dan ganin ko waye amina ta Zareido 馃槼 can a maqogaro tace bruhh, binta yayi da harara tuni takama hanyar dakinsuMansura ta washe baki tace ashe zakazo durling amma Seda kabatamun rae, murmushi yamata wanda yafi komai ruda ta, kujera tajamasa yazauna sann tadauko lemu tazuba musu tareda cup, bismillah tace masa Ahmed yace thanks. menene maganar? gabanta yashiga faduwa tadaure dae tace Ahmed nasan kasan cewa babu wani namiji danakeso a duniya sama dakaeakanka zan iya komai zan iya bada rayuwa ta akanka banajin......ya isa yadaga mata hannu, let go 2d strength point, mansura tanisa sann tace Ahmed inaso katura gidanmu neman aurena! What aure kuma? dama nace miki zan aure ki ne ? Mansura tace fyn yanxun katabbatar mun dacewa baka sona, Ahmed yace bahaka bane amma naga dae bawani dating muke dake ba kuma ni bantaba yimiki zancen aure ba hasali ma banida ra'ayin aure ayanxu, mansura tace lamme ask you menene ribar Soyy? Ahmed yace aure, mansura tace gud sbd haka aure zamuyi bafashi shine zaibada tabbacin muna san Juna,Ahmed yabita da kallan mamaki kana yace umurni kike bani ko kuma shawara ? Mansura tace shawara dae Ahmed yace gud to zanyi shawara da zuciyata, mansura tace hava Ahmed nida kae munasan juna tome nawani shawara, Ahmed yace ni bance ina sonki ba shawara kuma dole ce adukkan lamari, mansura tace kenan baka sona Ahmed yace waeke meyasa kincika mita ne hava yaja tsaki yayi dakinshiAmina dake labe tace tirkashi kenan angama da bruhh amma wlh baga badae base yayi kamar zai warware komai sekuma yakasa, amma anty zakici ubanki wann ba namijin so bane, mansura tace mekike sakawa ne haka, firgigit tafarka daga dogontunanin da take, , tace bakomai anty ina mamakin yadda bruhh ke yarda da bakon Almarin dake zuwar masa , mansura tace nangaba sekinga yana driving dina, amina tace hehehe aykuwa da nabada gold dina sadakaAhmed yafada kan ga danshi se juyi yake meke damuna wann bakon Al amarin fah meyasa bana iya gaya mata bana santa , meyasa zanbiyewa umarninta allah kamun gata fadawa yayi kan gadonsa yana Jin haushin kansa meyasa ma ya amsa kiranta sekace wata u warshi, wayarshi yajanyo yakira Mahmud ring biyu yadaga hello mah kazo yanxun ina gida akwai matsala, Mahmud yace subhanallah ganinan zuwa momy zankai unguwa idan nasauketa zan biyu , okay sann ya tsinke wayarHar bacci yasoma dibanshi Sega Mahmud yashigo zaune yatashi, Mahmud yace gani mod ince dae ko lfy daga ninka nasan ba lfyba meyake damunka, Ahmed yace wato Mahmud narasa abunda kedamuna wlh nakasa yimata gardama ina biyema umarninta Al hali basanta nakeba nakasa furta mata cewa bana santa bansan meyasa ba, Mahmud yace waye ita haka ? Ahmed yaja dogon nunfashi sann yace mansura kanwar hjyr gidann, Mahmud yayi murmushi yace why not ka aureta tinda tana sonka koba komai zaka moru domin mace idan tana sanka zata iya yimaka komai arayuwa sabanin hakan kuwa se hakuriAhmed yace kana ganin aurenta zai zamemun alkairi senake ganin kamar batada kyakkawar tarbiya Mahmud yace shedanne ke kawo maka wann aranka koya take auren irinsu jahadi ne babba yafi auren wadda kake da yakinin cewa tana da gud behaviours, Ahmed yace amma dae nasha gayama maka nafi ra'ayin mace karama wann kam ay kona girmeta kadanne, Mahmud yace karka duba wann ba'a kanka aka soma ba.............馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 5鈨�4鈨�Ahmed dae abubuwa sun kwance masa , yana Jin tsoron yadda zai tinkari dad da wann zancen kae bama dad ne matsalar ba a'a abba ne keda tsaurin ra'ayi , bakinshi yatabe yace anyhow dae ni ita nakeson aure, dama kuwa aure suke son inyi sabodahaka ba fashi aurenta kadaine kwanciyar hankali na, ayadda nakeji dinnan kamar anamintsilana dole na aureta da wann tinanin bacci yayi a won gaba da shi, uhm....tirkashimasu karatu yakuke hango wann Al_amarin?Yau dae kam ansallami joda, amma bawani nishadi a fuskarta, dayan nurse tace hava joda ko bakya farin ciki da wann rana ne allah yanuna miki kin bar asibity nan lfy tareda sa'a, joda tace ina muryana sedai kawai damuwana daya ne ina son likitana domin in mishi godiya, dayar ta kalli daya sann tace keday kiyiwa allah godiya kawai , amma wann likitan dakike ganin bahagon namiji ne ba'a iya yimasa dae2Gwaggo tashigo tace wae mekike jira ne tindazu driver yake jiranmu awaje haka dae tafito asibity bada san ranta ba, jikin ta bakwari , driver yagida ta asma dae wani iri,suna isa gida tabude ganbu tafita bata jira gwaggo ba, amma me takasa gane kofar dakinsu yadda taga angyara shi dole ta tsaya jiran gwaggo taxo gwaggo taja hannun ta tace zonan joda , suka shiga ciki joda kam se bin gurin da kallo takeYadda taga ansaka musu furniture, da set din kujeru masu kyau ga kayan kallo da fridge, komai dae angyara gakuma akwatinta biyu cike da kayan sawa tin kan jallabiya atanfa shadda less material, ga cosmetic nan, atake taji damuwarta ta yayeGwaggo wayamana wann hidimar haka, gwaggo tace bawan allah yawuce mai gidann ne nidae gani nayi kawai ana shigowa da kaya ance za'a gyara nazata makorarmu akayi ashe azziki ne ke bibiyarmu joda tace allah yasaka musu da mafificin al_khairi ameenWanka tayi tadakko daya daga cikin kayan da aka kawo mata tasaka doguwar riga ce red har kasa takamata sosae simple make up tayi taje gun gwaggo tace Dan allah gwaggo kirabamun gashinan nawa biyu ya isheni wlh, gwaggo ta taje mata kan sann aka mata kitso gida biyu haka tazubo abunta agaba kamar wata babyn india, hakakawai taji tana sha'awar fita waje, dayake weekend ne ba skull kuma ana hutu islamiyya,Dae2 swimming pool tazauna tasaka kafafunta acikin ruwan tana wasa dasu, wani iska yakada tareda sanyi da kamshi hannunta tasaka ta kankame jiki sosae tareda lumshe idonta, Jin takon mutum na zuwa yabata damar bude idonta, takasa tafara kallon mai xua murmushi tayi ganin kafafun Abdallah tace kaidae kullum cikin saka wando 3Q kake , tasaye ta tashi da niyyar kara masa wata magana abun data gani yasa ta shan jinin jikinta, dasauri tajuyabaya tana komawa da baya bayaWani shu"umin murmushi naga yayi wanda na tabbatar na mugunta ne, bata ankara ba taji yafada tussss acikin ruwa dae2 nan Ahmed yajuya baya zai tafiyanshi joda ta kwala mishi kira yayan hafsa......Dan allah kataimakamun ban iya fita ba, tana mgn tanayowa saman ruwa cak yatsaya batareda yajuyo ba sed yadade ahaka shi baitafi ba kuma shi bai dawo baHar tacire ran zan dawo sekuma taga yajuyo fuskar nan ba fara'a kamar baitaba dariya ba, Seda yakawo dae2 ruwan sann yaballa mata harara dasauri tadena kallanshi, hannu yamika mata tamasa banza takara kankame jikinta, Seda yadaka mata tsawa zaki zo kona tafiyata, cike da tsoron abunda zaimata, tabasa hannu yatashi tsaye yacabko ta dakarfi, Sega joda kan kirjin Ahmed 馃槣 dasauri yatureta yanamata wani mugun kallo yanunata da yatsa, sann yace Dan kince yayan hafsa yasaka nataimakeki, domin ni bayayanki bane, karma kiji ranan nace miki kanwata kizata ko dagaske ne taimakonki nayi kawai..........Muje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 5鈨�5鈨�Ahmed yajuya yabarta sororo, aranta kuwa tace koma dae menene badae ka fidda nibatoh Alhmdllh , dakinsu taje tacire rigar tacanja wasu kayan tashanya rigar , zazzabiyasoma rufeta, ga mura atake tafara sneezing, telephone tajanyo tasaka Kiran likitanta cos yagaya mata cewa duk abundayafaru shi zata nema, Seda wayar tagaji da ringing sann aka dauka wata nurse ce tace baya nan ay bakowane tym yake xua asibity ba, seyaga damaAmma zan miki wata nasifa zan kira miki shi, mexa'a gaya masa, joda tace mura da zazzabi kedamuna ga ciyon kae , nurse din tace alright, zangaya masa allah yasama zaidaga wayar, joda ta tsinke wayar takoma kwance, gwaggo tashigo tasameta cikin bargo, tace lfy joda, joda tace gwaggo mura ne da zazzabi, gwaggo ta dafe kanta tace ohhh ni manga ke kam gakinan kullum ciyo kamar Yar kaza,joda tace gwaggo ruwa fa nafada aciki, gwaggo tace toh garinya hakan tafaru? Joda tace tintibe nayi, gwaggo tayi tsaki ayke bakya rabuwa da tsautsayi sekace amarya , joda tayi murmushi tace nidae gwaggo fura in akwaita, gwaggo tace babu sedai in miki yanxu idan ita kike bukata tinda akwae garin tsaba, joda tace gwaggo bansaki wahala ba, gwaggo tace shin fura dae kikeso koh? Joda tace eh, gwaggo tacetoh shikenan sedai xua magrib kam, joda tace toh gwaggona ngdGwaggo tashiga kitchen tareda hasana dayake duk aykin da gwaggo zatayi se hasana ta ta yata, ruwa aka fara dorowa atukunya sann aka dama garin, suna fara boiling aka zuba mulmulen garin kafun kace me har yadafu , hasana ce ta daka shi sann gwaggo takarba aka dama tareda nono, plastic aka cikawa dad aka saka masa a fridge , joda nasahan fura taji sallama kuma da alama namiji ne dasauri tasaka hijabi wanda tagani ya sata yin murmushi lah馃槉 doctor ashe zaka zo , Yace ba wann ba kan hanya nake allura zan miki ga magani sena wuce atake joda tafara 馃槴 ni wlh bazaka mun allura baBaki yasaki yana kallanta can kuma se tace kae wae koba a asibity ba seka saka face marks , kuma kullum da glass a fuska, doct yace eh haka nake, joda ta tabe baki shikenan dkyar tayarda yamata allura da kuka da komai Seda gwaggo tafara yimata fada sann tayi shiru magani ma dakyar tasha shidae baice mata komai ba sedai yayi murmushiYagama yayiwa gwaggo sallama, gwaggo tace nikam dann wayake biyanka ne ? Doct yace allah, gwaggo tace shikenan kuwa ka gama mgn, yana fita abdallah nashigowa, bae yade yau banganki ba joda tace kaedai wlh zazzabi da mura, abdallah yace ayya baby na allah yabaki lfy ameen, bude bakinki nabaki chocolate, joda Jin ance chocolate da sauri tarufe idontamurmushi yayi yauwa babyna yasaka mata dae2 nan gwaggo tashigo mugun kallo tabi abdallah dashi sann ta kwalawa joda kira dasauri joda tabude idonta , gwaggo ta bala'in daure fuska kana tabita da harara joda tashiga rawar ido jikinta yadauki bari,gwaggo tarungume hannuwa tana musu mugun kallo , Abdallah yashiga soshe2 gwaggo ina wuni? Gwaggo tace da ban wuniba zaka ganni anan, meyakawoka dakinmu, kaxo ka koyawa yata lalaci koh? Abdallah yace a'a wlh inna kiyi hakuri ni sonta nake bakomai baGwaggo tace dakyau idan sonta kake nabaka sati daya katuro mun iyayenka, idan kuma rayuwarta zaka bata tokuwa zan hadaka da mahaifinka, joda tace gwaggo wace irin mgn ce wann abdallah baya nufina da komai wlh ko yatsana baitaba tabawa ba wann ma shine nafarko kuma shaukin so ne , gwaggo tawanke ta da mari,lallae na yadda so makaho ne, tinda har joda take kallon idona tace shaukin so.........馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 5鈨�6鈨�Abdallah yace allah yahuci zuciyarki gwaggo yaraba ta gefen joda yawuce, gwaggo tarakashi da harara , joda tafada kan katifa tana kuka, gwaggo tayi waje tabarta cike da haushi, abdallah kuwa naxua dakinshi yadauko win yasha yace lallae wann matar zata kwabsa mun baxata watsar mun da plan ba nan da sati dayan data ce zan cika mata ayki , wani guntun murmushi yayi yacije lebeAhmed yashirya tsab yanufi dakin dad dinshi, zaune ya samesa yana karatun jarida, Ahmed yayi sallama dad yakarba tareda murmushi, Ahmed yace dad gud mrng, dad yace mrng hw ar u son, Ahmed yace am glad 4u dad, dad yace gud, Ahmed yakallesa yaga shi yake kallo , dad yace yess kae nakeji yau nasan akwai mgn daga ganin wann bakin naka , Ahmed yace eh dad dama wae zancen auren nan ne dakace , nasamu mata, dad yace wow I can't believe you fah, Ahmed yace serious dad ay bana wasa dakaeDad yace gud 4u son a ina take kuma Yar waye, Ahmed yace kasanta dad, mansura ce, dad yace eye wakace kamar banji da kyau ba Ahmed yace itada din da kaji mansura, dad yace wace mansurar, Ahmed yace kanwar hjy ta nan gidan, dad yace what ar u in sense ? Mansura fah kace yarinyar da bata ganin idon ubanka da gashibare kae wai tsayama tukun yaushe kuka fara dating da ita da har abun yakae ga aure, Ahmed yace oho dad ni bansaniba kawai abunda nasani aure nakeso kuma mansura zan aura dz ollDad yace how dare you ina mgn kana mgn to baxaka aure taba indae nine mahaifinka aure tsakanin ka da mansura babu sedae kuwa in wasu iyayen zaka canza , amma matukar uba ke nemar wa yayanshi aure , towlh bazan nema maka auren mansura ba , ina auren yaya kaikuma zaka aure kanwa, bad脳 Ai abun yama kazanta wlhAhmed yatashi afusace yace find dad, nikuma idan har ba'a auramun wadda nakeso ba, to wlh baxan yarda da auren kowace mace ba, kuma baxan taba aure ba har abada, dad yazare ido, son ni kake gayawa mgn ? Ahmed yace sorry dad amma idan har kadaga bazaka bani abundanakeso ba to wlh zaka cigaba da ganin irin haka ni kawai abani abunda nakeso yana kae nan yafice daga dakinHjy dake labe tana jinsu tayi murmushin mugunta tace yauwa Ahmed aranta yana wucewa tashiga dakin, kamar bataji komai ba tace alh yana ganka wani iri ne? dad yace no bkomai kaina keciyo hjy tace shikenan idan taruba maji, dad yakalleta ya girgiza kai, sann yace ina bukatar hutu zaki iya fita, hjy tace basae ka koreniba dakai na zan fita, tafita dakin tana murmushi, tana isa dakinta tasaka Kiran mansura nan tazayya nemata komaiMansura tahau ihu tace kae anty kice nakusa zama amarya wayyo dadi, hjy tace nadae gayamiki wlh kikama kanki kizama Yar mutunci, mansura tace hava anty sedai a rika sakayawa amma ko 2dyz baxan iya yiba ba'a yi abun nan ba, hjy tace kyaji dashishegiya kinzama taxi motar kowa kowane kato hawanki yake, mansura tace no anty manya dae kinsan nifa nafison yara sunfi iya sarrafa ka dakyau, hjy tace dallah yimun shiru marasa kunyar banza idan dae kika je kika nuna masa maitarki afili kekika saniMansura tace inahhhh anty ay sekinga yanda nake kamewa amma wlh ina cike da kwadayin wann yaron zai yi cwet馃槝 sosaehjy tace tirrr da halinki kekam kinma guce harija idan da abunda yafi haka tokuwa kin kai can, mansura tace yp anty kinsan bana wasa da fruits dz y always akwai ni'ima har tsiyaya nake, hjy tabuga tasaki irinku ake rabawa aure idan kuka hadu da wanda bayaiya daukar dawainiyarku, mansura tace kamm anty wlh baki saniba randa naja hannunsa zua dakinshi koh uhm..wani unexpected shock naji baki ji yanda nayi release ba nan take aranar kuwa koh.....har safe dreaming dinshi nake amafarki ma ya iya rolling din mace bare kuma afili kae I like him so so so much.....hjy tabuga dogon tsaki takashe wayar...........馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 5鈨�7鈨�Dad zaune a dakinshi shida abba suna tattauna matsalar Ahmed, abba yakirasa yace komai kake kaxo yanxu kasameni a dakin mahaifinka, Ahmed yace ganinan xua dama yanxun na shigo wanka kawai zanyi se nafito, dad dajejin komai yace kagan rayuwar shi koh ace muna matsayin iyayensa muce shi muke jira amma yace se yayi wankaAbba yadaga masa hannu ya isa bayadda muka iya dashi se addua tin haihuwanshi haka yake, Ahmed kuwa yana shiga dakinshi ya jona kettle yayi wanka yasaka jallabiya sann yasha eviron drink, kana yanufi dakin dad dinshi sallama ya musu sann yagaida kowa yama kansa gurin zama, abba yace kasan meyasa muka kiraka, Ahmed yace no, abba yace gud, mgnce akan auren dakace kanaso , nayi matukar farin cikin Jin wann zancen koba komai zaka zama babban mutumAmma wani hanzari ba gudu ba meyasa kace mansura kakeso , bayan akwai yan mata tsaranka sann idan ka duba abun ta wata fuskar mansura antynka ce tinda kanwar matar ubanka ce bai Haram taba amma abun yakazanta, Ahmed yace gud abba tinda har kagane bai Haram taba toh bakomai nidae kawai auren nakeso kuma ita zan aura , abba yace katabbatar ita kakeso, Ahmed yace eh, abba yace shikenan zaka auri mansura matukar mahaifin ta yabaka ita, amma karka kuskurakaxo mana dawani zancen abaya komai yafaru after weeding dinku ba ruwanmuDad yace yaya meyasa zaka biyema ra'ayin sa to nidae ba daniba kuma bazan je nemanaure ba gidan surikina, abba yace dama wayace kae zaka je ay ni zanje ba kunya tinda addini bai Haram taba koh? Dad yaceamma dae Ahmed kasan foundation dinda yake kasa koh? Ahmed yace banmantaba abba kuma baxan bijerewa hakan ba, nidae kawai abunda nakeso tinda nafaranta makakaima kafaranta mun , dad yace hakane shikenan jeka allah yasanya alkairi yazaba mana mafi alkairi ameen , abba yayi murmushi yace ko kaifaAhmed yana fita yasaka Kiran mansura dama kuwa tayimasa 7 miss call yana kiranta bata wani Jan epixy ba tadaga wayar, hava bae tindazu fah nake kiranka, Ahmed toh sarkin mita zaki fara koh, mansura tace yi hakuri ranka yadade, Ahmed yace better yaushe ake samun ubanki agida, mansura tace bangane ubana ba, Ahmed yace ur father nake nufi, mansura tace shine zaka wani cewa ubana abun kamar zagi,Ahmed yace toh yakike son ince inba ubanki ba, ko karya nayi ba ubanki bane? Mansura tace naji ya isa ubana ne, ko yaushe zaku iya samunsa sbd yadena fita outside sedai inza a duba lfy shi, Ahmed yace ban tanbiyeki wann ba iya abunda na tanbiyeki zaki amsa ,mansura ta bata fuskakamar tana ganinshi ....nidae asea ina gefe ina dariyar manya , Ahmed yace alright kigaya masa su abba zasujo neman aurenki, what? Mansura tace kae wayyo allah nah, yaushe ne bikin dear nah, Ahmed yabuga tsaki yace wato har murna kike zaki bar gidanku koh?Mansura tace no inadae murna zan je gidanhabiby na hubby na my soul my gentle my......Ahmed ya katse ta keeee ya isa sarkin zuga zaki wani cika mun kunne da surutan banza, mansura tace au bakaji dadin kalamai naba kenan ?Ahmed yace yo wani dadin zanji acikin wann surutu kinwaniwae my me my me 馃槒 mansura bawani kaedai dadi ne yakasheka, Ahmed yabuga tsaki ya kashe wayar, sann yakira Mahmud yace man akwae story fah kashigo gida yau,Mahmud yace ina kan hanyar xua fah na biya market ne zan siyowa joda chocolates kasan akwaita dason chocolate, hello hello tasaki yabuga wato na dauko masa zancen makikiyarshi shine ya tsinke wayar , dae2 nan yakawo kasuwar chocolates kaday yashiga siya kala2 Seda yasiye kusan kala yakai goma se flower mai kyau da greeting card dauke da luv quote 4 my 6 tareda tirare jidda mai shegen kamshi ..........Muje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 5鈨�8鈨�Joda zaune kan dakalin gidansu tana shan alawa 馃嵀 tana yan wakokin Justin B, driver dinta yazo yace barka da hutawa madam, joda tadago cike da girmama wa takarba, Yace madam kishirya xua 12 zamu fita dake , joda tace kamarya fita xua ina? driver yace kedai kishirya wann umarni ne daga oga nah, ga wann yamika mata wata pink gown, da pink shoes, sarka da yan kunne ma pink se wani katon ribbon pink, yanuna mata wani pic. kinga madam yanda kikaga wann baturiya haka zakiyi shigar shi plss karki bata mana lokaci oga ni zai yiwa fada ,Joda tace nifa banganeba waye wann ogan ne, shiru tayi ganin yajuya yace mata no African tym madam, joda tayi tagumi a iya tinanin ta abdallah take zargi domin kuwa yasha gayama ta zakiga ina ta yimiki abu amma bazaki gane ya abun yakeba, murmushi tayi ta shiga daga ciki, tanuna magwaggo kayan gwaggo tace toh amma dae zakisa ka mayafi koh joda tace no kam gwaggo wann rigar ba'a saka mata mayafi ,gwaggo tace gsky ba'a San raina zaki fita haka ba amma kije kishirya tinda yanxu kinga 11 tayi, ba musu tashiga wanka tana fitowa tasaka Kiran khalthum tace plss khalthum kizo kirakani wani guri yanxu2 ni ake jira , khalthum tace kamar ya yanxu nifabacci nake kintadani, joda tace plss khalthum kizo Dan allah nima bansan ina zamuje ba an kawo mun wasu kaya kamar wata india, khalthum ta kyalkyale da dariya wow kice party zamujeJoda tace party kuma wae iskanci tona ubanwa zamuje nidae kawai kishirya, khalthum tace wait kada ki tsinke wayar gaya mun wani irin kaya ne Dan nima nasanirin shigar dazanyi, joda ta zayyane mata komai, khalthum tace kambu allah har na hangoki amma pah simple make up yakamakiyi kisaka pink lipstick karki saka eyeshadow kisaka eyeliner white seki saka maskara ki gyara idon ki karkiyi brow , taki kullum kamar anyi shape dinta dae2 kawaikigyara ta da brush amma fah kisaka blush sae kinyi Dan smiling sann zaki shapa, joda tace ohh ni Yar fillo, naji Mrs make up,Duk yanda khalthum ta zayyane mata haka tayi, tsayawa tayi tana kallon kanta ta mirror, tana murmushi ina hafsa ta itake son ganina haka aranta tace da inada camera danayiwa kaina hoto na ajiye mata, sallama taji anyi dasauri tajuyo tana dariya yayana kaine, Mahmud yabita da kallo duk yarude yana domin kuwa da batayi mgn ba bazai gane ko ita bace, gashinta yake kallo a iya sanin shi bata retouch or something like that, buh yagan yayi wani murde2 kamar anmasa wani abu se sheki yake babuabunda yafi burgesa irin yanda tayi parking dinshi atsaka takawo wann ribbon tasakaJoda tace yayana mekake tinking haka? Mahmud yace no nothing kanwata nagan kinyi kyau ne waya koya miki dress da makeup haka? kinsan allah idan kika fita za'a zata india ce, joda tace kae yayana bana san zolaya wlh, Mahmud yace allah, ungo wann wata irin jaka ce mai kyau, dasauri takarba tashiga budawa tirarika ne dasauran abunda yasiyo mata, tuni tashiga wangale baki nagode yayana kae naji dadi wlh, wata mp yabata tareda kunna mata wata romantic songs mai taken valentines day , joda takara rudewa yayana bansan mezan cemaka allah abun yaburgeni ashe Yaune valentines day inaji anafada a skull dinmuMahmud yace zomuyi selfie pics joda tazo dasauri Mahmud yadan matsa kadan yaddajikin su bazai goguba yafara daukan su pics,ana haka Sega khalthum cikin wata gown itama tasha kyau dayake khalthum ma ba baya ba gurin kyau, sungaisa da Mahmud nan, shikuma yabasu guri, joda tashiga nunamata kayan da Mahmud yabata , khalthum tace kaiii anya kuwa ba so" ana gurin yanda ma yake kallonki daban ne, kai amma pa ni kaina abun yaburgeni wlhJoda mayyar chocolate tabude tafara ci, gwaggo tashigo tace lfy nakejin ihun ku , joda tace zokiga gwaggo ya Mahmud yabani, gwaggo tace iyye Yar yayanta kinsha godiya aykuwa ki kawo chocolates dinn inba haka ba kafun gobe duk kincinye shi , idan watan Al_adanki yayi kice maranki keciyo bayan ke kekike cin kayan tsaki. ...........馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 5鈨�9鈨�Joya ta bata fuska hava gwaggo nifa bashi yake sakani ciyo ba allah ne yake kawo mun, gwaggo tace eh allah yake kawo miki amma ke kike kara wahalar da kanki , gwaggo takarbe chocolates din tasaka ajaka, tace keda sake cinsa se jibi, iddanana ( kina jina ) joda tace Dan allah gwaggo munyu ( kiyi hakuri ) kibani, gwaggo tace bazan bayarba, khalthum tace gwaggo kara mata daya manaGwaggo tace ware ja'u ( zo karbi ) joda ta gwaguda baki tace midamu wara ( banason sa ) gwaggo tace kekika sani dae tajuya tafice tabar joda na kunkumi, dae2 nan driver yaxo yace madam time x over fah, joda taja hannun khalthum suka shiga motar tafiya sukayi mai nisa, sun hau wani sabon titi tsitt yake bakomai se kukan tsuntsaye kake ji,joda tace wai ina zamuje ne ? driver yace sorry madam har munkawo fah , wani gate suka Parker wanda yasha mayun flowers , joda ta kalli khalthum tace badae nan zamushiga ba, khalthum tace to ki tanbiyeni nacemiki what? Joda taja hannun khalthum sukashiga driver yace bismillah madam, joda tace bangane ba kaifa, driver yace iya nan kadae aka bani umarnin na kawoki plss kishiga daga ciki ,joda takalli khalthum, khalthum tadaga mata kae, suka shiga, khalthum itace ta iza gate din yabude , wani kamshi da sanyi ya ratsa zukatansu ji kake suna taka wani lallausan carpet , cak suka tsaya ganin danja takawo ko ina se ga wasu flowers dake xua daga sama joda ta daga kae tana kallo , tareda murmushi atake taji wani nishadi yana ratsata, khalthum tace joda kinga wani guriCake ne agurin mai shegen kyau babba ansaka happy birthday joda, joda tace wow hw cwet 馃槝 allah nama manta Yaune bithday dina, khalthum tace nifa narude wann surprise haka, daga ina? Joda tace oho nima bansaniba, shiru sukayi Jin waka na tashi ta happy bithday to you, joda tace ohh gosh, joda tace khalthum mu yanka cake din. joda ta yanka suka ci ga lemuka nan birjik, gakuma naman kaji, se su greeting cards sunfi biyar Dana valentines day Dana bithday ,joda tace khalthum bansan mezanyi ba gurin nan yahadu ko ina mayen decoration ne akayi, komai na sukayi gurin pink ne, ta zagaya gurin duk inda suka leka zasuga flowers da rubutu valentines day, ko birthday, khalthum tace kenan kekam a 14 February kikazo duniya, joda tace eh fah nazo ranar masoya gaba dae suka sa dariya, khalthum tace zomu fara karanta cards dinn joda tace dayawa fah, khalthum tace ni zan karanta idan baxaki iyabaNa valentines suka fara dauko wa, joda tace lah kinga wani littafi cikin leda yake joda ta yage ledar sann ta Zare flower din wani rubutu mai kyau da biro kam akayi shi amma yayi matukar tsaruwa ba mistake ko daya aciki , joda tafara karantawa Sallama agareki tauraruwar zuciyata kece farin cikin rayutawa, kamar yadda taurari ke haske gami da kyalli asararin samaniya to haka fuskanki take haske famida kyalli acikin zuciyataKhalthum tace wow bana Jin dadin hausa quote amma gsky wann yamun dadi, joda tace nima fah , khalthum tace oya buda mana next page . joda tace to kinga wann da English ne, kezaki karanta mana khalthum tace ok bani nakaranta, joda tamika mata, khalthum tafara " 4u see each dy I luv u more 2dy more than yesterday and less than 2morrow so happy valentines day " khalthum ta kalli joda tadaga gira ya kika ji wann, joda tace Muje next nidae khalthum tafara " life is a journey, so enjoy every mile happy birthday "馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B aleeyu 馃挄 page 6鈨�0鈨� Haka suka ci gaba da karantawa har kusan 2 suna gurin sunma manta da tsawon lokacin da suka dauka agurin joda harda su cire takalmi, kwance sukayi kan carpet din suna karanta cards din idan joda taduba wann tabawa khalthum wann , Seda suka gaji Dan kansu suka kira driver yakaisu gida,badan ransu yasoba sedan kawai lokaci yatafi joda kam Seda ta ebo flowers din dasauran kaya ga uban chocolates da biscuits, khalthum kanta bata taba ganin irinsu baKhalthum aka fara saukewa itama ta ebi nata kayan sann tawuce, joda ta isa gida se faman cin chocolate take kafun su isa gida tacii biyar duk girman su , sadaf2 tashiga dakinsu taje taboye chocolate din kar gwaggo tagani takarbe, wanka tayi tacanza kaya, atampa tasaka riga da Zane tayi daurin Dan kwalinta oll back. Sann tayi sallan azahar da la'asar,hasana tashigo tace joda Dan allah kimikawa su isa driver abuncin su, joda tace yana ina nifa tsokanar shi ce banaso, hasana tace hava dae kiyi hakuri ni yanxun cake zanfara toyawa waccan masifaffiyar kafun tazo tacimun mutunci, joda tasaka dariya tace gsky kam, kular tafara kaimusu sann takoma tadauko plates da spoons, takai musu , zata juya ne taji ance kamar yanda taurari ke haske gami da kyalli asararin samaniya to haka fuskanki take haske gamida kyalli acikin zuciyata,joda tajuyo dakarfi abdallah dama kaine kayi haka, abdallah yadinga mata murmushi, Yace zomuje bae kigan wani big surprise , joda tace a gain kuma Zagaya yayibaya da ita yabude wata kofar sann yace rufe idon ki tarufe kyalle yasaka yadaure mata idonta hannunta yaja sukayi Yar tafita sann taji kamar ansake buda wata kofar sekuma aka rufe, abdallah yakalleta yayi murmushi yace oya bude idonki, tana budewa taga flowers ko ina jajaye bedsheets shima ja, tace wow ya abdallah amma nadazu yafi kyau shi komai pink ne, abdallah yace dazu kuma joda tace eh mana, abdallah yace ok naji yanxun ba wann ba mezaki bani as my valentine , joda tace mekake soAbdallah yace duk abunda kika bani inaso, joda tace a'a nidae kafada kawai, abdallah yace ok ke nakeso, joda tace nima kai nakeso, abdallah yace kanki zaki bani koda 15 mnt ne, joda tace yo ay dama ni taka ce ,abdallah yace ba wann ba ina nufin kibani jikinki na more ki koda na 15 mnt ne, joda tace nifa wlh banganeba , abdallah yace ok lamme proof it" fuskanta yajanyo yafara shafa bayan ta jikinsa kuwa se bari yake " joda ta turasa dakarfi abdallah mekake nufi ne , abdallah yace plss joda just in seconds mun gama wlh zan miki ahankali, kwalla yacika idon joda tace abdallah dama Amma jikina kakeso bani ba, allah ya isa tsakanina dakai,kacuci Soyy ta kayaudareniAbdallah yadaka mata tsawa ni kike kira da mayaudari, to yau zan nuna miki yaudara, yafara kiciniyar cire mata riga dayake zif ne har kasa baisha wata wahala ba yazare shi joda ta kankame jikinta tafara matsanancin kuka , kaji tsoron allah dadin da zakaji na kankanin lokaci ne yafita nikuma kagama bata mun rayuwa abunda iyayena sukayi she karu suna tanadi , wace amsa zanbawa mijina alokacin daya kusan ceni yajini ba'a cikakkiyar budurwa ba , wa'azi tashiga yimasa kota ya amma ina wanda yakauce hanya ya kauce kenanKanta yabuga abango tuni ta buga wata shegiyar kara yazare rigar takasance daga ita se vest, kuka take har muryanta baya fitakan gado yakada ita yahanye ta, tuni ta gan tsara masa cizo, Seda yayi Yar kara turasa tayi takoma kan ganbu zata bude, abdallah yataso dasauri yafizge key din yajefa a window yarufe , ganin haka yasaka joda buga shegiyar kara amma dayake sama ne suke ba'a ji sosae kan gado yamaida ta, joda kam ta sadakar rufe idonta tayi, tana adduar neman tsari........馃槶Muje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page6鈨�0鈨�Kiss din wuyanta yake kamar zai cinyeta jikinshi se bari yake yagangaro abakinta joda ta rufe shi gam yadda bazai iya saka nashi ba, rigarshi yake kokarin cirewa damakuma bx ne ajikinshi , yana kokarin zare wandon ne sukashi an wani irin hankado ganbu, abdallah yajuya dakarfi, 馃槼 Ahmedmekazo yi dakina, Ahmed yawankeshi da mari zai kara wata magana yasake marinshijanyoshi yayi yabuga kanshi a bangoDuka yake kaimasa ta ko ina seda yamasa lilis sann yace kajira sammaci akotu, Dan wlh sena bimata hakkinta, shikenan kawai kaga yarinya yar kauye zakazo mata da yaudara ke kuma yanunata......shiru yayi ganinta kamar a sankare hawaye na zuba amma jikinta baya motsi, dasauri Ahmed yadaukota se jijjigata yake amma taki koda tari sema kara faduwa tayi ajikinsa,Ahmed ya azata akafada bai tsaya ko inaba se dakinki, kan gadonshi ya ajiyeta, duk yawani rudewa, dakyar yasamu yadauko jakarshi yahada mata allura, yamata aykuwa anan ake yinta, randa taga allura tafara motsi, Ahmed yabita da kallo da harara, juyata yayi baya zai mata allura amma me tajuyo da karfi ni wlh bana son allura kakaini inda gwaggo naAhmed yace gud tashi muje daganan sena gaya mata abunda kuke aykatawa keda Abdallah , joda tace Dan Allah karka tona mun asiri wlh baimun komai ba, Ahmed yace nidai baruwanka kijuya amaki allura, joda tarike gado gam, yana sawa tawani irinajiyar zuciya harda su hawaye, tsaye tamikezatabar dakin sekuma jiri ya ebeta Ahmed yana kallonta yabarta tafadi akasa, sekuma tasaka mishi kuka, tuni yadawo real Ahmed,yadaka mata tsawa joda tace, dama yayan hafsa ne nazata ma ya Mahmud ne "Ahmed yace wlh idan bakimun shiru ba zan hadaki da bango jikinta yadau rawa , tayi shiru Dan kwalinta tacire tadaura shi a kirjinta, Ahmed na kwalinta yabuga tsaki duk daya tuna irin yadda yasame Abdallah kan jikinta se wani bakinciki yaziyarci zuciyar shi , tsanarta kuwa tadawo masa sabuwa Joda tana son fita amma kuma taga yafita harkanta yakoma kan system yana ayki, lokacin sallah yayiyafita xua masallaci yadawo yasa meta zaune se kuka take tana yiwa Abdallah Allah ya isa, Ahmed yace ke kimun shiru kafun na fasa bakinki ubanwa yakaiki dakinsa ay kina so din " joda tadago dasaurini wlh cuta na yayi mugu azzalimi Allah yahadashi da bala'i da masifa, Ahmed yace kuttt nakara Jin kinma Dan uwana muguwaraddua sena saba miki Joda tace ni zanfita inyi sallah Ahmed yamata banza yadauko abincinsa atake away yaci tareda soya milk,joda tasake maimaitawa nifa banyi sallah baAhmed yaballah mata harara dole tayi shiru,seda tacire ran zai yi mgn sann taga yabudewadrop yadauko mata wani katon hijab yajefamata, joda tace ina ne toilet? Ahmed yace toilet din ubanki, kucaka dake katsama xaki shigarmun toilet wato kizubarmun da najasar dinda kika fitar koh " joda tashiga girgiza masa kai, yadaka mata zaki wuce kose na ballaki, joda tara ba, bayanshitafita , har takai kofa yace jimana " tajuyo, dettol yajefamata zaki iya hadawa da warmwater kizauna kar HQ din taki tayi xafi koh " sann ki tabbar kinyi wankan janaba b4 ki kusanci ubangijinki"Joda ta aza hannu aka tafashe da kuka shikenan Abdallah yagama da ita , yacuceta, tafiya take se famar matse kafafun ta take gudun kar agane halin datake ciki, tana isa tayi sa'a bakowa tafadatoilet tayi wankan tsarki sann ta hada ruwanzafi da dettol tazauna, kuka take kamar zata shide tana fitowa wani zazzabi yarufeta " kan gado tafada ko sallar batayiba, tafara kuka ciyon kaine mai tsananin gaske yataso mata har bata iya gani batajin zancen mutane sosae, gwaggo tashigo da nufin tadata tazo taci abinci amma kuma sae tasameta tana kuka kadan2 alamar tayi harta galabaita kenan,馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 6鈨�1鈨�gwaggo tace lfy "yan nan ? Joda tashiga nuna mata kanta, idonta arufe gwaggo tace subhanallah sannu joda, joda tace gwaggo mutuwa nakeso rayuwa ta batada amfani aduniya, gwaggo tace yau na banu ciyon kanne yafara gusar miki da tunani haka baraakirayo driver muje asibity , joda se nishi take, ba'a Fi minti biyar ba Sega gwaggo da hasana suka sata a mota sann sukayi asibity, dazuwansu suka hadu da wata aisha da suka sani I tace tamusu jagora xuaciki, aisha tace gashi nikuma lokacin tashina yayi amma bara akira likitanta tinda yace kome yasameta anemeshiDoctor aysha takirasa amma yace bazai samu damar xua ba tamasa nasiha ta dubata dole badan tasoba ta tsaya tadubata , bayan tagama gawaje2 tace jodamesa jininki yahau? Joda ta gwale ido hawakuma nima bansaniba, doc aysha tace shikenan Allah yasauwaka, tabata magunguna suka dawo gidaZancen auren mansura da Ahmed ya kankama , amma me jikin Ahmed yayi sanyiyakasa sakin jikin sa, bayan da har anbiya sadaki da kudin aure ansaka time wata mai xua, mansura kuwa anshiga gyara bakama hannun yaro, matsi take har na fitar hankali ,magani ba'a daina yiba amma har yanxu Ahmed yaki zama yanda akesoTin ranar da abun ya faru joda batasake haduwa da abdallah ba kuma bata daina tsine masaba, abdallah kuwa yayi regrettingyafi dubu, gashi based samu abunda yakesoba gashi yarasa soyyr joda, kuka yake yi sosae yana alawadai da zuciyar shi, se yanxun yakejin sonta sabo na ziyar tarshi , ya daina fita ko ina saboda kunyar Ahmed da joda amma zuciyar shi takasa sukuni yana son gafarar joda koda zai samu nutsuwa aranshiYau tin safe yashirya yayi wanka yanufi kofar dakinsu joda ay kuwa yana xua segatazasuje skull, joda na ganin shi takurma ihu takoma ciki aguje, ganin haka yasa abdallahyabar gidan, hasana tafito aguje tana tanbayar lfy? Joda tace kunama ce nagani, hasana tarakata har mota sann tadawo neman kunamar bata gantaba aranta tace yanxu haka wani kwaro ne anma tace kunama, nidai asea nace eh yes kwaro ne amma babba uban kwari baDae2 gate tahangoshi yadaka tarda driver, joda tace kai kadesa muwuce, driver yace hai madam sokike oga ya korani , joda tace okay budemun motar natari keke, yace wann kuma bazai yuba ki tsaya kiji abunda yakeson cewa mana, joda tabuga tsaki tajuya fuska , abdallah yakaraso yace plss kabamu guri zamuyi mgn, joda tace wlh idan ka fita nima fita zanyi dubifa 7:30 nayi late sosae, abdallah yace shikenan zan jiraki ki dawo koba komai naji sauki dalilin ganinki lfy lauJoda tabuga tsaki zaka gama borin kunyarka kadena macucin banza wlh nafison ganin fuskar gorilla akan taka sautinzaki yafinaka dadi azuciyata, abdallah yace Allah yahuci zuciyarki, joda tacewa driver zaka wuce kose na ballah ganbun " kuji jodakamar wata kakkarfa " abdallah yabuga kanshi a bango yanxu gashi duk soyyr datake yimasa tarikida takoma kiyayya tsantsar ki nake hangowa a idonta , ya AllahceceniAhmed yakira Mahmud yaxo akan suje zabagidan daya masa a cikin gidajen dad dinsu, Mahmud se tsiya yake masa ango2 kasha kamshi nifa baxan yarda kayi auren nan bada niba, gwara nima na nemi tawa, Ahmed yace wann kuma kaitashafa, Mahmud yace nifa kanwarka tamun, Ahmedyadaure fuska wace daga ciki, Mahmud yace D cute be dinn amina, Ahmed yace to badaniba jeka same ubanta, Mahmud yace kaima ubanta ne..........馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 6鈨�2鈨�Ahmed yace baruwana fa wlh yarinyar batada kamun kai you know agabanka nazaneta kwanan baya, Mahmud yace saimi toh iyakacin iskancin mace ace tayi cikin shege to so what " virginity dinta ba shine abunda nake bukata ba, in har tana sona zan iya canza ta daga mummuna zuwa kyakkawa, Ahmed yace lallae se yau na tabbatar baka San mekake baMahmud yace kai bafa budurcin mace shine abun bukata ba obeying kawai indai zata mun da'a to wlh tafimun virgin dinda zataxo tana Ci mun mutunci, mu maxa se muce dole se virgin wlh watarana wata kaddara ce kawai wadda baka Fi karfin yarka" matarka" kanwarka" uwarka" tafada aciki ba , idan bama auren irin wadann matan lalaci bazai taba kaura ba a duniya , aurensu jahadi ne babba " kuma bana Jin auren irin wadda kakeso zaifi wann lada dakyar ma idan ba wann yafi lada baAhmed yace ya isa Dan Allah el_sheek , kazo kacikani da wani zancen banza kowa danasa ra'ayi kagane koh " Mahmud yayi murmushi yace Wanda yayi nisa baya Jin kira, dae2 nan suka kawo wani gidan , sun shiga ciki suna dubawa amma Ahmed sae complain yake yana kawo matsalar gidan,Mahmud yace dakata malam wlh nagaji da yawon nan iskancin banza tin dazu muke yawon duba guri amma duk inda mukaje se kawo matsalar shi, Ahmed yace duk basumin ba ne , Mahmud yace gud saboda kagansu ne inba dad ba waxai tsaya tawa kamarka gida kuma har se kazaba, Ahmed yace karfa kafara zubamun bansan zancen banzaJoda sun fito skull itada khalthum, suna fira, khalthum tace joda ga nakin nan yaxo, joda tace plss kibarshi bashida ayki ne, khalthum tace tohfah yaukuma keda kanki, joda tace ehh kibarshi kawai munyi break up ne kuma wlh baxamu taba dawowa nomss ba, khalthum tace insha Allah joda har yanxu kina sonsa na tabbatar abunda yamiki bakai kimasa wann horon ba, joda tace plss khalthum bakisan abunda kefaruwa ba just leave me alone, plss khalthum tace shikenan Allah yasauwakaJuyawar dazatayi taganshi agabanta idonsatab dawaye yace plss joda karkiyi judging dina tahaka zuciyata bazata dauka ba, Dan Allah kisaurareni wlh tin randa kika shigo skull dinn nake jiran fitowarki banji yunwa ko kishi ba, ganinki da yafiyarki shikadai ne abunda nakeso arayuwata, joda tabuga tsaki tace abunda baxaka taba samuva har abada baxan yafe maka ba tana kai tajuya dakarfi tashiga motar suka wuce, khalthum dake kallonsu hawaye tab a idonta itama tajuya zata wuce abdallah yace plss kitayani bata hakuri, khalthum tace insha Allah batareda ta juyobaYau kusan kwana biyar currr abdallah nabin joda anma wulankancin yau daban na gobe da ban. yauma kamar kullum tafito daga skull, dasauri yaxo yarike mata wando duk yarame yayi baki, joda tace malam wai lfy kake neman taramun jama'a, abdallah yace joda ko ubangiji munayiwa laifi ya yafe mana bare kuma Dan Adam, joda tace ayya Wanda yasan Allah shiyake da wann sanin bakaiba, abdallah yaduka har kasa yace DanAllah3 joda kiyafemun, hannu bibbiyu yasaka yariketa joda tawankesa da mayen mariDuk jama'ar dake wurin seda sukaji kukan marin khalthum tazare ido gamida juyawa abaya, samarin makarantar suka yo kansu, wani daga ciki yace ke dabbar inace zaki dubi girman wann mutun kimaresa aganan jama'a bayan da duk wulakanta shi da kike a kullum bai miki ba se kin hada da zagi, joda tace ohh....kazo rama masa ne ? Yaronyace kuttt yarinya karki kuskura kigayamun rubbish wlh yanxun jikinki tagaya mikiJoda tace bismillah shege kafasa, yadagan hannu zai mareta dasauri abdallahdakansa yake kasa Yadago yarike shi yace kana tabata wlh jikinka zai gaya maka yaronyace yi hakuri bruhh ashema kaine, abdallahyace kasan nine? Yace eh ay abokin bruhh dina kake hafix, abdallah yasosa kai hakanejeka bakomai zan gyara lamarin , yaron yace sure bruhh gsky yarinyar nan batayiba Sam batasan zafin soba, abdallah yace anjiya jeka dae sae anjima,Yana wucewa abdallah yajuyo fuskar sa adaure, yace joda Allah yagani na name gafararki iya abunda zan iya " kuma Allah yagani har zuciya ta nayi nadamar abunda na aikata, kisani baxan kara biyarkiba akan kiya femun , zanje nacigaba da rokon Allah akan yasaka miki jinkaina kiyafe mun , kodabazaki soni ba burina kawai kiyafemun, amma kisani daga yau duk abunda yasameni kece ko yaushe zuciyata zata iya bugawa ayadda nakeji dinn bana tunanin zankai safe da rayuwa,idanma har narayu to kuwa nasan se an gwammace mutuwata akan rayuwana yana kai nan yajuya yabarta atsaye tana hawaye.........Muje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 6鈨�3鈨�Wani gida aka Ahmed yazaba ba nisa da gidansu dukda bai masaba sedan kawai yanada side dinda yakeso, tini aka shiga gyaran gidan, hjy tazo tasame Ahmed da dad a palor , tace dama kunake nema, dad yamaida dubanshi a kanta, Ahmed kuwa ya cigaba da rubutunshi, tace alh dama nace kaida Ahmed waxai hado lefe ina nufin kai zaka masa ko kuwa shi zaiyi abun shi,Ahmed yakalli dad ya girgiza kanshi, dad yace kamar wann zanmasa komai yanada abun shi shizaima kanshi lefe, hjy tace toh Ahmed wai dama nace kasan mata sunfi sanin abunda yadace , shine nakeson ka kawo kudin se muje dubai muhado komai nida amina, Ahmed yace dakata kinfi kowa sanin bana son shishshigi alamurana, nizanhada abuna bana bukatar kowa yasaka munhannu aciki yana kae nan ya ajiye biro dindayake rubutu dashi kan table yafita a dakin , hjy tarakashi da hararaCiyo mai tsanani yakama abdallah yarufe kanshi adaki bawanda yasan halin dayake ciki, amina ce talura kwana biyu baya fitowabreakfast, tayiwa hjy mgn, hjy tace waya sani ko yana can gurin iskancin sa ba mamaki ba ace baya gidann tin shekaranjiya, amina tace anya bruhh baya kwana biyu ba'a gida ba bara nadubo shi, side dinshi tanufa, tamurda ganbun atake kuwa yabude, kara tasaki ganin shi akasa yana murde2 da alama cikinshi keciyoDasauri takoma tasanadda hjy, hjy tin a dakinta take ihu da kuka, koda su kazo yanata kwara amai, dasauri hjy takira dad tasanadda shi, ba'a Fi minti uku ba se gashi tareda Ahmed sukazo aka saka shi a mota se asibity , ana xua Ahmed yakira wani likitasuka shiga tare aka basa taimakon gaggawa, atare suka fito, Ahmed yace kamusu bayanin abunda kedamun dansu, likitan yace ulcer ce tamasa mugun kamu har zuciyarshi tafara ciyo, da alama yau satidaya baici abuncin kirki ba Wanda zai Gina masa jikiHjy tace shikuwa meke damunsa har dazai kauracewa abinci, dad yace ay laifinki ne kina matsayin uwarsa ace yadaina cin abinci amma baki lura da hakan ba wann kenuna cewa baki kula dasu yanda yakamata watarana seya mutu bada sanin kiba, aminatace dama kasan koyanxu nice na lura yadena fitowa, Dana mata mgn cewa tayi kila baya gidan danabi takanta sedai muji warin gawarshi, dad yace kajiko, hjy tace kaji munafukar banza wlh sena ballaki sgegiyar yarinya kawai, Ahmed yabuga tsaki yaraba tagefen su yawuceKwanan shi 7 sann aka bashi sallama ko yaushe damuwa fal aranshi, joda kuwa tin ranar bata kara saka abdallah a ido ba , khalthum kuwa tayi tamata fada akan bata kyauta ba, joda dae jinta kawai take Dan batasan meke faruwa ba , sun fito exam yautin 12 suka dawo gida dae2 kofar gate tahango abdallah yana tafiya shikadai amma se hawaye yake joda ta tsaya tana kallansa jikinta duk yayi sanyi shikuma kamar an ce yadago yahaganta, tana kallansa dasauri yakaraso zaizo gurinta, ganin haka yasaka joda juyawa dakarfi tareda bata fuskaAbdallah yace joda idan baki ya femun ba banga amfanin rayuwa taba, mota na xua gurin shikuma abdallah yatsaya kan titi, kiyyy!!! Kakeji dakarfi tajuyo tareda aza hannu aka tayada jakarta tana wayyo Allah, jijjigashi take amma ko alamun motsi ba yayi , se jini ke fita , duk ta haukace se ihu take da gudu tashiga cikin gidan, gefen garden ta hango Ahmed dasauri taje gurin shi tana hakiAhmed yajuyo Jin ana xua aguje, jaridar hannun shi ya ajiye, yana kallonta jikinta dukjini ne " kanshi tafada tana kuka, yayan hafsa, mo...mo....tahhh.....ce takade shi baya motsi ya mutu, Ahmed yace waye dallah ki daga mun shegiyar yarinya , se a lokacin joda talura da tafada ajikinshi.........馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 6鈨�4鈨�Atare suka fito da Ahmed waje se kuka taketana fadan na shiga uku, Ahmed ya daka mata ki koma cikin gida kafun na halaka ki wlh kokuma se kin taramun jama'a , joda tace yazan koma navarshi ajikin wann halin" Ahmed yace gud karkije wlh idan nataso se jikinki tagaya miki dajin haka takoma ciki, aguje tafada kan gwaggo tana sanaddaita abunda ke faruwaAhmed kuwa motarshi yadauko yajashi sukayi asibity, dazuwansu aka karvesa emergency, seda aka masa dress aka sakamasa drip sann Mahmud yace yakira yasanadda su halin da ake ciki, hjy kam tayi ta masifa akanme Wanda yakedasa bai tsaya koda hakuri ya bayar ba, dad najinta yamata banza, abdallah kuwa ciyon zuciya ne yakamashi bayan da jininsa ya hau sosae ,Ahmed yatasashi agaba seya gayamasa abunda kedamun sa, abdallah yayi shiru se hawaye yake, dad yace wai bada kai ake mgn ba, abdallah yace ba abunda kedamun sa , Ahmed yace wlh karya kake wani dalili ne zaisa ka kulle kanka har kwana biyar bacibasha, ina hankinka yaje da har mota ta kadeka , tunanin me kake meka rasa arayuwa , dae2 nan joda tashigo ita da hasana, ganin joda abdallah ya kirkiri murmushin dole yana kokarin tashi, Ahmed da dad suka maida kallon su ga kofa Dan ganin meke faruwa, joda ta karaso tagaida dad da hjy dad ya amsa ciki da fara'a , hjy kuwa tabita da yatsina , abdallah yanunata yace itace itace dad wlh itace ciyona nasanna mata laifi na nemi gafarar ta har kasa naduqa na nemi, gafararta amma Sam taki Dan Allah dad kace taya femunHjy tace what? Kaduqawa wann al majirar uwarta ka kashe ko ubanta? Dad yace ke dallah kimun shiru, joda gaya mun meke faruwa, joda tayi kasa dakai tayi shiru dad yace kigayamun idan cutar ki yayi wlh zan bimiki hakkinki, abdallah yace dad naso na bata rayuwar ta amma allah baisa nayi nasara ba plss dad, tayi mun kowane hukunci amma banda takini wlh idan ban auretaba gwara kawai na mutuHjy tace kuttt馃槨 wlh kar in kara Jin wann mummunan zancen wazaka aura din wann baran namu dasuke under mu, never wlh bakaxa taba auren taba kwarya tabi kwarya, dad yace ke kifita daga dakinnan kafun inyi mummuna saba miki, dad yamaida kallansaga joda yace joda hakane yaushe kuke soyyda abdallah banda masaniya ? Joda tace tinbayan rabuwarmu da yasir, dad yakalli Ahmed yaga shi yake kallo, yace Ahmed kasan da wann zancen Ahmed yace no nima dae yanxu naji cos bantaba ganin su suna tadi baAbdallah yace bruhh Dan Allah kashiga lamarin nan nidae so nake aha da auren nan da naka idan ta amunce, Ahmed yace ke kina sonsa ne " joda tarike hasana kam atake taji kanta yayi nauyi wani irin sanyi yafara ratsa ta sekuma taji takasa fada tanaji aranta kamar akwai wani abun datakeson fada amma kuma takasa, Ahmed yadaka mata tsawa ba dake nake ba, dad yadaga masa hannu yace kabita a hankali yarinya ce karama, joda tafashe da kuka, dad yace yi hakuri haka yake kinsan soldier se a hankaliJoda takaras kusaga abdallah tarike masa hannu ba hasana ba hatta dad da Ahmed seda abun yazomusu abazata ga badai suka samata ido " joda tace abdallah zan aureka idan kabi sharuddana , zaka dena shaye2 da xua club, zaka daina bin mugayen abokai , karika bin umarnin iyayenka kazama kamilin mutun gentle kamar.....takalli Ahmed da gefen ido Ahmedya balla mata harara, joda tace kamar ya Mahmud. Abdallah yace shikadai ne joda wlh zanyi na tabbatar ke alkhairi ce agareni, tin farkon ganina dake nake tsoron kiganni a maye abunda bana tsoron kowa yaganiAbdallah yace dad abamu sallama naji sauqi, dad yayi murmushi yakira doctor, doctor yace yanada yamike, ana auna bf dinshi a kagan yasabko sosae, doctor yace woww wae menene sirrin ne " abdallah yanuna joda yace itace ciyon itace magani, joda tasadda kanta kasa, dad yace lallae joda kinyi abunda muka kasa akai tsaye wato raba abdallah da shaye2, ha kika banida bakin gode miki, joda tace dadyn hafsa idan kayi mun godiya kayi haramun, nice yadace a koda yaushe na gode maka abisa dukkan alkhairan da kake mun馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 6鈨�5鈨�Ahmed yabuga tsaki yace kusameni a waje idan kun gama, dad yace bawani zama zamuyi ba kutashi muje gida , kayansu sukahada sann suka fito, joda na makale da hasana suka fito driver dinsu nanan suka shiga motar har abdallah yabisu hjy tadaka masa tsawa, dole yadawo yabisu dadSuna isa gida hjy takira mansura tazayyane mata komai mansura tace impossible, yama za'ayi abdallah ya auri yan DAJI Sam baxata sabuba, wlh kiyi gaggawar jamusu kunne, hjy tace toh yanxun makuwa, tana tsinke wayar, tanufi sa shen su joda , duk Wanda yaganta seya Duka ya kwashe gaisuwa amma ko kallan banza , tana isa taci karo da gwaggo, tace ke kuma matsiyaciya ina gargadinki daki jawa yarki kunne akan tarabu da Dana wlh har abada Dana bazai auri yar matsiyatava,dangin tsiya, gwaggo tace Allah yahuci zuciyarki, zan jamata kunne Dan Allah kiyi hakuri , hjy tace oho dai kinji nagaya miki idan bahaka ba wlh zakuga tashin hankalin dabaku taba gani ba arayuwa In banda kwadayi ina abdallah ina wann kucakar duk yaushe ne kuka dena tsoron mutane, wato ansata a makarantar manya ta waye ko, to ahirr dinku zata juya kenan Sega joda, joda naganinta takoma aguje dasauri tacakumo wuyanta tace munafukar banza munafukar wofi wato kun shanye mun da baya ganin kowa seke harda wani gindaya masa sharudda koh "ku kiyayeni fah, ta ture joda tafita tabar dakin, gwaggo tabi joda da harara kinga abunda nake jimiki koh mutunci yafi komai yanxun gashi anci zarafinmu harda ubanki dayake kasa, ina amfanin hakan , mema zai saka kiyi sarakuta da wann masifaffiyar matar , kikama kanki wlh idan bahaka ba abunda zasu mana agaba seya Fi wann , joda kam se famar kuka takeTin a ranar abdallah yamutsu yade na duk wani abu mara amfani dashi ake sallar asubah hasalima kowace a masallaci yake yinta, yamaida qur'ani abokinda carbi abokin firarshi, ita kanta hjy shi taji dadin yanda yakoma barinma dataji dad yace zai basa day an company dinshi na sarrafa fata, Ahmed kanshi na mamaki aranshi kuwa yace Allah rabamu da masifar so " nidae asea nace ameen " so fah badama"Soyy kuma se abunda ya cigaba sedai aboye suke yin abunsu, joda kam jitake kamar inba abdallah bazata iya rayuwa ba, khalthum se tsokanar ta take dama a naso ana kaiwa kasuwa , joda tace naji dae kemazan rama watarana ay, haka abun yake tafiya bawani takuri duk yanda hjy tasaka musu ido takasa gano su, amma wani gefentana cewa hegiyar yarinya tamana rana tinda tarabashi da shaye2 yanxun ne yakamata na ne masa auren yar commissioner wato safina, toh fahAhmed dae sae shirye2 zuwa dubai ake hado lefe duk yanda mansura tayi dashi yaje da ita amma firr yaki xua da ita yace zasuje after weeding dinsu, mansura tace ok dear kabani key din dakinka kafun kadawo, Ahmed yace kajimun rubbish akan wane dalilin zan baki key din dakina, mansura tace gyaramaka zanyi idan zaka dawo, Ahmed yace kibarshi ngd, idan nadawo zaki gyara, fushi tayi tabar masa dakinshi , Ahmed kam ko a jikin shi danko bayau suka saba ba itake gajiya tadawo neman shiriJoda tafito xua skull ba driver dole ta tsayacike da mamaki Dan baisaba hakan ba, tanatsaye hannunta rike da textbook tana dubawa, kamshinsa kadai yaganar da ita waye, joda tace doctor kaine da sassafennan, doctor yace eh wlh wata patient naduba nan bayan layin nan , zan wuce na hangoki zo in rage miki hanya ba musu joda tashiga suka dau hanya, can yakira sunan ta, joda antaba gayamiki kinada kyau? Joda tayi murmushi tace tosaunawa ma , doctor yace amma fah ni wlh bantaba ganin kyawunki ba hasalima muninki na firgitani fari se kace yar aljan, joda tayi Jim tace nagode amma plss zaka iya saukeni anan, dasauri yade na kallonta sbd dariyar da yaxo masaYace yi hakuri fah gsky nake gayamiki wlh su basu San kyau ba, amma dakinga matatakoh wlh sekin raina kanki fara se ba irinki bake komai nata fa special ne " joda tace koxan iya ganinta? Doctor yace tabb banaso irinku munana kuna hada hanya da ita sbd tsaro amma ke kanwata ce zan baki tym dae2 nan suka kawo skull din........Muje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 6鈨�6鈨�Tin ranar joda tashiga tinking kullum hanunta rike da madubi tana kallon kanta, aranta kuwa cewa take kila dai kowa kallon mai kyau ake mun shi isa ake ganin kyawuna, amma shi yaganemin gsky, sundawo daga islamiyya, tadauki tell phon takirashi , bayan sun gaisa take cemasa plss doctor yaushe zaka kaini gurin matarka, yayi dariya sann yace bayauba kam inada ayki sedai ko zuwa jibi, idanma nasamu tym dakaina xanxo in daukeki inkaiki gurintaJoda tace Dan Allah kada adauki long time wlh na kagu naganta, doctor yace ayku dama mumuna jikinku har rawa yake kugan masu kyau, sukuma masu kyau yan hutu ne" itama komai batayi daga skull se bacci fatarta kamar auduga idonta kamar madarabakinta kamar na jinjiri, dimple dinta tamkarna pretty , yatsunta zara2 doguwa ma'abuciya tsayin wuya, hips da boobs kuwa yanxun suke ta sowa amma abun se Wanda yagani,joda tace nidae ya isa duk wann abun ace mutun daya aiko hurul'in ce iyakacin kyanta kenan, ita kenan komai nata indeed be batada miskila ko kadan aikam baxai yuba , doctor yace alright idan kin ganta zaki tabbatar da hakan, joda tace to ay nagama kamar rowar ta kake, yace ba dole ba saboda irinku karku sakamata asid a fuska, joda tace uhm...gamu gani daeKarfe 7:30 nasafe jirgin Ahmed yace yadagaxua dubai , kafun yaje seda yajawa masu aykin gidanshi kunne kafun yadawo komai ready. dukda yadamka komai a gurin Mahmud , mansura awaya tana soyewa da wani honorable, yace hava sury wlh kinsan ina cike da kishirwarki Dan Allah kibari muhadu, mansura tace kaga honorable wlh nafara matsi ina tsoron ka lala tamun shiri gaka in kafara se mutun yaci uban shi kamar Wanda yakama wani nonoHonorable yakyalkyale da dariya, to ay kecetamkar Zuma wlh bantaba ganin wadda takaikiba kuma bakya tsufa, yanxun dae zanbada , 1m mansura tace dagaske, yace sosae ma kuwa kedai kawai kisama time, mansura tace gove dama fa nima amatse nake wlh sati daya babu abuncin zuciya 馃槀 Allah ka shirya su mansura ameen "Joda suka hada appointment da abdallah akan zasuje kasuwa su siyo littafan addini, tareda wasu ababen, haka kuwa akayi dakanshi yajasu suka fita bayan tacewa gwaggo gidansu khalthum zataje, yar karamar market ce sukaje, sunsiyo littafai da dama ya kuma kwaso mata chocolate da cake, dae2 wani hotel suka gameda mansura tana rike da hannun honorable, abdallah yaja tsaki Allah yashirya anty sura, itakuma duk tagansu anma se tayi kamar batagansuba , wayarta tajawo takira hjy tashai damata sann takira AhmedAhmed yace toni ina ruwana rayuwar shi ce, nahanashi soyy ne " mansura tace to yarasa waxaiso se wann kucakar yar village,Ahmed yace oho tsakaninku ni kinka karki kara kirana in har kinsan soldier tsegumi zaki kawo mun, mansura tabuga tsaki ta kashe wayar tace Dan iska goma aka kawo maka mgn seka gwalashe mutun , abakin gate suka hadu da hjy taci damara se huci take kana ganinta kaga bala'i, tuni jikin joda yafara rawa tace Dan Allah abdallah saukeni anan, abdallah yace y" joda tace nidae bakagan hjyr kubane, abdallah yace naganta menene tohJoda tace Dan Allah abdallah " banza yamata seda yashiga har harabar gidan, hakan yakarawa hjy haushi, ta dososu dasauri, tana nuna joda ke Dan uwarki bana hanaki hulda da Dana ba, abdallah yace ni zaki hana hulda da ita domin sena kulata take kulani, hjy kamun shiru mutunin banza ,ke kuma tanuna joda wlh wlh wlh nawa uku koh idan naqara ganin ki da dana to kikarasa sauran zancen kawai馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 6鈨�7鈨�Joda kam tashiga dakinsu aguje tayi sa'a gwaggo na bacci, abdallah kuwa palor yashiga se wani huci yake, wayarshi yaciro yasaka Kiran mansura tana dagawa yace to munafukar uwa nizaki hada da uwata koh " Allah dae yasaka ba fasikanci akajimu munayi ke kuma gaki nan ansaka rana amma kina yawon dadiro wlh idan kika karamun haka sena dauki duk wani move naki nakaiwa Ahmed se inga abunda zakiyi dake har antyn taki marasa tarbiya da tsoron Allah kawai,Mansura tayi sororo rike da waya lallae dole adaukarwa abdallah mataki idan bahakaba zai bata mata shiri, sann bazai taba auren joda ba wlh watsatstsiyar banza,Lefe naji nafada Ahmed yayi tsayawa ma fadansa bata tym ne kawai ku kissima abunaranku, hafsa ma haka yahada mata nata Dan karamun lefen abun gwanin sha'awa, Mahmud kuwa yayi tsayin daka akan gidan Ahmed dukda yace agyara kowane side, haka kuwa akayi ko ina an gyara side hudu ne har gefen yara gidan ba'a cewa komai, daga India yasaka akayomasa order takaya ga baki daya su suka tsara masa parlor dinshi dakuma room dinshi sekuma wani dakin da'a ka gyara abun dae se Wanda yagani duk wann hidimar Mahmud ke yinta Ahmed yana can dubai , yana hado lefeAbdallah yasami dad dinsu akan zancen joda yanaso anemamasa auren ta , dad yace abdallah bayanzu nakeso kayi auren ba nafison seka kara nutsuwa tukun sann kafara aykin company dinka gadan2 kaga a lokacin zaka iya rike iyalanka kome kace? Abdallah yace banida zabin daya wuce zabin iyayena dad duk yadda kayi dae2 ne aynasan bazaka cuceni ba, dad yace sosae ma kuwa son Allah yamaka albarka yatabbar da farin ciki arayuwarka Allah yasakawa wann yarinyar data zamo silar shiruwarka ameen " yana fita dad yacire glass dinshi yafara share kwalla, tausayin dansa fall aranshiMahmud yaxo gaida gwaggo kuma yasha fura, yakuwa yi sa'a anyi furar kusanma kullum se anyiwa dad furar, gwaggo tacikamasa kofi yana sha yana zuba santi, joda kuwa se dariya take masa, Mahmud yace idan kinamun dariya zangayawa matata tabaki Duka, joda tace lah ya dama kanada mata bansaniba, a nuna mun ita nagani, Mahmud yace kambu ayganinta se an shirya yarinyar tayi tsada dayawa , joda tace nidae ya Mahmud kaki ka kaini inda mom dinka, Mahmud yace kinshir yanxu? Joda tace eh ashirye nake, Mahmud yace ok dakko mayafinki kizo mutafi, joda tabuga tsalle bara na yiwa gwaggo sallamaHar zata bude mota taji ance yaukuma se ina naga har wani rawan jiki ake, murmushi tayi tin kan tajuyo tasan abdallah ne " gidan su yah Mahmud zanje in gaida momy sa, abdallah ahhh.....wann yanada kyau, se andawo Allah yakiyaye hanya, yadagawa Mahmud hannu bruhh Allah yakiyaye, Mahmud yace ameen bruhh, abdallah yace wait bruhh akulamun da matata fa kar abi hanyar duwarwatsu da ita , Mahmud yace okay kamanta tana tareda yayanta ne ' abdallah yace hakane se andawoTana shiga yatada mota, amma kuma me yanayin sa gabaki daya ya canza , joda tace ya lfy naga kadan canza, Mahmud yace bakomai joda kaina yake ciyo, joda tace ayya yayana Allah yabaka lfy, joda tadakko wata game acikin motar tana bugawa se murna take idan tacinye idan kuma aka cinyeta seta bata fuska, Mahmud dae yana kallonta ta glas sedai yayi murmushi amma shikadai yasan iya adadin son dayake yiwa joda amma yakasa fada mata yanagani kamar baxata dauka na amma gashi abdallah yakowa mata sonshi ,joda tace lah ya Mahmud mekake da dettol acikin motar ka? Mahmud yace kinsan ko yaushe bukatar shi yana tashi, kuma x gud ma ace ollwyz kana tareda shi koda bukatarshi yaxo , tayi shiru tana tuna wata maganarda doctor dinta yamata abaya yana cewa x gud ki rika yawo da tissue kokuma pad , period dinki batada tabbas koda bukatar hakan yana tasowa, A'a confuse yana ji zancen yaxo iri daya, joda kam ta tabe baki tace anyway dae nasan su manyan maxa tsarin su daya ne馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 6鈨�8鈨�Atare suka shiga a gidan Mahmud yana gaba tana biye dashi, joda se bin gidan takeda kallo aranta tace ashe ko ya Mahmud Dan maikudi ne amma baya nunawa kome yasa " Mahmud yace zonan, wata kofa sukabi segasu awani lungu yace nan kofar parlornan kuma idan kika bi hanyar dakin abba damomy ne inazaki fara shiga,joda tayi shiru tace ya Mahmud kafini sanin dae2 mana, Mahmud yace ok shiga parlor ina xua nayi mantua a mota ,joda tace idan na shiga Ince ni wacece,? kawai zan jiraka , Mahmud yace joda baki saba yimun musuba, meyasa zaki fara yau , joda tace yi hakuri ya Mahmud bara na shiga yajuya yakoma itakuma tashiga cike da tsoro2 sallama tayi tinda ga kofa tayi sa'a Shakur nakusa ya amsa sallamaJoda tashiga daga ciki tazauna se bin shakur da kallo take kamarsu daya da Mahmud ana haka Sega shukra, tazo tace lah baquwa muka yi wuce daga ciki, joda tabita har cikin palor, ruwa da lemu takawo mata sann tace bara na kira miki momy, atare suka dawo da momy, momy ta tarveta da fara'arta tana tanbayar ya gida yakowa da kowa, joda tace duk lfy lau sukeshukra kam se makalewa joda take tana janta fira , can dae momy tace yasunan ki, tace joda, momy tace kiyi hakuri fah banganekibaJoda tace tare da ya Mahmud muke yana waje, momy tawa she baki iyye ashe sarakuwata ce, shkura tabuga tsalle, takwalawa shakur kira, zo ga matar bruhh, joda kunya yakamata tadukadda kanta kasamomy tace shukra jeki kawo mata abunci, joda tace a'a nakoshi, momy tace ba'a yihakaba shukra kuje dakinku se taci acan kafun yashigo , har suka shiga taci abuncin tayi sallah Mahmud bai dawoba seta fara tunanin kodai tayi masa laifi neShkura taja hannunta sunkoma parlor, suna tsakar kallo a system Sega shi yashigo, shukra tace bruhh matar nan taka akwai kunya wlh, Mahmud yace zanci ubanki wlh ita tagaya miki matata ce ko ni? Momy dake saukowa downstairs tace indai tarubamaji, Mahmud yace look mom wann fah kanwata ce, mom tace ayshi so dama yafi dadi idan akatafi dashi ta hakan , zallar so gashi a I donka kana wani boyewa, gara daekasanar da ita kar kamun asarar sarakuwar kirkiMahmud yace joda tashi muje gida, joda tayiwa momy sallama, shukra kam ansha magiya akan Mahmud yabar mata joda har xua night amma yaki sema zaginta daya fara yi , joda kam duk jikinta yayi sanyi haka suke tafiya amota kowa da abunda yake kissimawa aranshi, sunkai wani shago ya Parker yace me za'a siyamiki ixecrem ko chocolate, joda tace ko daya ba naci, Mahmud yace shikadai yajuya motarshi suka isa gida, sunfi minti goma da kawowa gida amma bawanda ya fitoDakyar joda tabude ganbun motar amma kuma seta kasa fita , a hankali har muryarta narawa tace ya Mahmud dagaske ne abunda momy tace, yah Mahmud dama kana sona amma baka taba nuna munba , Mahmud yace joda ki shiga ciki zamuyi mgn ltr, joda tamike se hawaye take shikuma yajuya motarshi , jodaaaaa nahhhhh. ....taji ankirata dasauri tajuyo Jin muryar hafsa,da gudu ta sheka tarungumeta, tana hafsa na yaushe kika dawo, hafsa tace bajimawa, kinsan ankusa auren ya Ahmed shine naxo biki Allah ma yasa muna hutu, joda tace aure kuma nikam banjiba, hafsa tace kamarya gaki acikin gida, next week fah za'a fara bikin joda tace lallae ma ashe kunfitadda anko, hafsa tace eh munyi waya da amina tace anfitar amma zamuyi namu daban kinji, joda tace Allah yakaimu tym din........Like 馃憠馃徎@ RUNBUN ASEEYAH BASHEER fb. Com zaku samu complete FULANIN DAJI 馃巹Muje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 6鈨�9鈨�Hafsa da joda ne tafe suna fiarar yanda bikinsu zai kasance, Sega amina tazo wucewa takira hafsa zo muyi mgn, hafsa taja hannun joda suka tafi, amina tace ke kuma ubanwa yakiraki nagadai yar uwata nakira bakeba, joda tace hafsa idan kungama kyasameni aciki, hafsa tace to shikenan Dan Allah kiyi hakuri, amina tace iyye wato ma hakuri kike bata, yanxun dae bama wann ba, Allah kada kije mana da ita abikin bruhh in bahakaba wlh se in diz gata a bainar jama'aHafsa tace akanme nagadai itama ta zama tamkar yar gida, amina tace to shikenan zaki gane wann shegiyar yarinyar dakyau kamar aljana ay se gabaki daya hankalin samarin yakoma kanta, hafsa ta kyalkyale da dariya, to kindaiji abunda zakije jealouslykawai, amina tace wlh zan jimiki ciyo mezanyi wa wann banxar kishi akai, hafsa tace ay sedai kiyi amma joda kamar taje biki ne ashobe bawanda ban mata ba , hakama head ba abunda zaki nuna mata inmadai bakiyi hankali ba tafiki haduwa domin make up artist zan dauka har agama biki, amina tace bura'uba wlh se in gayawa bruhh nasan shi baxai bari aje da ita gurin bikinsa baHafsa tajuya tareda Jan tsaki tayi gurin joda, koda taje tasameta suna dama fura da gwaggo, joda tace hafsa zoga fura ke nake damawa, hafsa tace kai my joda naji dadi wlh, joda tace hafsa plss kirakani gidansu khalthum inkaimata ankon nan , kartayi fushi dani, hafsa tace ok yaushe zamuje, joda tace bayan sallah magrib driver nakaimu seya dawo damu, hafsa tace toh shikenan Allah yakaimu lokacin joda tace ameen " gwaggo tace hafsa ungo wann ta abbanmu ce kije dakinshi kisaka masa a fridge amma fa karkibari yayi kankara zai lalace, hafsa tace lallae ma dad, yazarce da shan furar gwaggo, joda tace kinsan me, allah duk randa ba'a masa wann furar ba dakanshi yake xua tanbaya kuma wae duk wann plastic din kafun gobe yakare, hafsa tace uhm aikam dad zai iya yanaso fura ne sosaeAgidansu khalthum se tsokanar joda take tana cewa matar abdallah, hafsa tace nifa banganeba wane abdallan, khalthum tace yayanki mana shiyake son joda harda ciyon so yayi, hafsa tace iyye shine ba'a gayamun matar yayana ashe zamusha liki jibi , joda tace kinga hafsa banaso ki dena, hafsa tacetab aikuwa yanxun ma nafara kice munada shagali agaba mune yan amarya mune yan ango, kaiiiii abun zai bada ma'ana......shiru tayi ganin joda na hawaye, khalthum tace lfy joda? In dae kan wann mgnr ne to mun daina tinda bakyaso, joda tace a'a khalthumbashine abunda yasakani kuka ba,Hafsa tada fata to menene joda, hawaye dake fuskarta tagoge sann tace hafsa wlh inason ya abdallah kodan shiruwar da yayi aka ina amma nasan niba matar bace inaji ajikina kamar ankusa rabamu dashi, hafsa tace wakuwa zai rabaku bayan da kunason junanku, joda tace a'a hafsa hjyr abdallah tayiwa gwaggo dani kaina garfadi akan danta, gwaggo ita kanta ta gayamun bata son ganina da abdallah takaras he zancen cikin kukaHafsa tace clm dwn, joda addua zakiyi kowane aure se yaxo datashi gaddama wani yaxo dasauki wani kuma yazo da tsauri addua itace magani kiyita tsayuwar dare kina kaiwa Allah kukanki akan yazaba miki mafi alkhairi muma kuma zamu tayaki da addua amma kisani duk abunda kika ga Allah. Yayi toshine dae2 mafi alkhairi agareki, gara kisakawa zuciyar ki salama tinyanxu, kikoyi yanda ake danne so ayi biyayya ga u waye, joda tace hmm Allah shigemana gaba ameenTin randa hafsa tamata wadann maganganun seta kara Jin kamar zata rasa abdallah ah yan kwanakin nan, shikanshi abdallah yana yawan Jin faduwar gaba a duk lokacin daya tuna joda , yaukam yashirya fadamata komai, zaune suke a garden kowannensu yayi shiru da abunda yake sakawa aranshi, abdallah yafara dacewa joda bansan meke faruwa ba se intajin faduwar gaba aduk lokacin dana tunaki, joda tace nikuma jinake kamar sanadin rabuwarmu natare damu, abdallah yace kamarya kenanJoda tace abdallah ji nake ajikina yan kwanaki kalilan suka rage mana murabu da Juna, abdallah yace hava joda yakike irin wann zancen ay seki saka narasa dayan side din jikina, domin ke rabin jikina ce , joda kam fashewa tayi da kuka, abdallah yakaraso kusanta yadan janyota ajikinshi yana lallashinta ana haka Sega gwaggo tazo wucewa tsananin bacin rai taji lokacin data hangesu rungeme da Juna , jodaaaaa takirata da murya mai karfi, dasauri joda tadago tareda janye jikinta abdallah kuwa zare ido yayi, gwaggo tace wlh baxan taba yafe maka ba idan ka lalatamun "ya , abdallah yace Dan Allah gwaggo kidena mun kallon ma yaudari wlh son tsakani da Allah ne馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�0鈨�Gwaggo tajuya afusace danko zuciyarta takawo baxata jure tsayuwa ba , joda tamike aguje zata bita abdallah yarike matahannu joda ta girgiza masa kae , abdallah yace karki bata hakuri yanxu ki bari harta huce joda tace koma yane yanxun kasakeni hankalina at ashe yake inajin tsoro, abdallah yace shikenan ,tana wucewa yadafe kanshi omg ya Allah kamun gata a wann lamarinGwaggo kam share joda tayi gabaki daya tadena shiga lamarin ta, joda tin tana hakurihar tafara kuka da rashin cin abinci, hafsa talura da halin da halin datake ciki, tayi2 da ita taki gaya mata komai, dole tasamu gwaggo itama din cewa tayi kibarni da ita hafsa dole badan tasoma tafidda kanta a lamarin, daga lokacin tafara tsoron tsayuwada abdallah shima haka dukda cewa kuwa tana missingdinshi sosae da sasae, yau sundawo islamiyya itada hafsa tafe suke suna firar bikinsu joda tace nidae hafsa inajin tsoron xua bikinku kinsan yanda yayanki yatsaneni hakama su hjy barema amaryar inkinga yanda take hantarana ma basauki , hafsa tace hava joda bruhh batsanarki yayi ba rayuwar shi hakanan kowa yana iya yiwa hakan Dan Allah kiyi hakuri kicirewa ranki hakan, bashida sabo ne barema nacemiki idan kun saba zai bari, joda tace hmm bakisan wasu abubuwan dasuka faru ba bayan tafiyarki, acikin ranta take wann zancenganin abdallah yasaka ta manta duk wani bacin rai, dasauri ta isa gareshi , ya abdallahshine kagujeni koh " abdallah yace joda bana son naja miki matsala ne tsakaninki da mahaifiyarki, hafsa ta karaso tace zanshiga ciki kisameni, joda tace toh ganinan xua fiarar su suke gwanin sha'awa kowannensu yana nunawa Juna irin son da yake yiwa Dan uwansa, joda tabuka sgegiyar kara sakamakon bulala dataji a bayan ta haka adinga zuba mata dorina,abdallah yaturata da karfi mamma kashe ta zakiyi ne kome? Hjy tace abdallah wlh zan kashe ta matukar bata rabu dakai ba, abdallah yace niyakamata ki kashe ba itaba domin ni nake biyar ta ba itaba, hjy tayi tsalle tasake bugawa joda dorina joda tazube kasa, hafsa tafito aguje tareda sauran masu aykin gidan , gwaggo tafito tayi tsaye tana kallon su, abdallah yace wlh hjy idan kika jimata ciyo agidan nan kowa bazaiji dadi ba wlh zan to tonawa kowa asiri sekuma yafashe da kuka jikin hajiya yayi sanyi gwaggo kanta ya bata tausayiA yanda taso zata karawa joda wani dukan amma kuma ganin yanda abdallah yake kuka da sanbatu yasaka jikinta sanyi, joda takara fashewa da kuka saka makon jinin data gani akafarta hjy tayi fuuu tawuce tareda yada dorinar hafsa tazo dasauri tajanyota abdallah kuwa yabisu har daki yana dada basu hakuri, a hanyar garden ya hadu da gwaggo dasauri yaduka yana bata hakuri tareda zayyane mata yanda sukayi da dad dinshi, yakara dacewa zan dena kula joda har se randa aka mana baiko,Gwaggo tace tashi bakomai Allah zaba mana mafi alkhairi ameen " Joda kam kuka take kamar me badan komai ba sedan in ta tuna kiyayyar da hjy ke mata, dakyar aka samu tayi shiru, abdallah kuwa doctor yadauko yadubata aka mata dress din gurin,kulawa yake bata kamar me abu kadan zaice me, me kikeso, hafsa kanta tana tausayin yayanta yanda duk yawani canzawa lokaci guda yazama silent fiyeda tunaninkaBayan kwana uku tawarware har takoma islamiyya , iyakacin su gaisawa da abdallah joda najin tsoron tasake cin wani dukan , abdallah kuwa bayaso yasake jamata wani abin , gamida gwaggo kuma bayaso tasake kamasa da wani laifin baya da abin Kare kansa , joda takira doctor dinta tace wai nikam se yaushe zamuje gurin matarka ne " dariya yayi sann yace kefa kin cika azarbabi, ba nagaya miki cewa dakaina xanxo muje tare ba, idan nasamu chance. joda tabata fuska tamkar tana ganinsa nidai idan aka wuce wann tym din banaso I mean cikin wann satin...........馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�1鈨� Yau Saturday yaune Ahmed zai dawo, kumayaune za'a fara biki, hafsa tazo tacewa jodaDan Allah zoki rakani mugyara dakin bruhh Ahmed, joda tace aza hannu aka, tace wah ni tufa mun asiri wlh ba inda zanje mezanyi a parlor dinku kuma har dakinshi sokike yakasheni tabb kedai Allah kiyaye hanya , bayan da hafsa batayi ba amma firr taki xuadole taje ita kadaiBayan tagama ne tazo ta kawowa joda kayan da zasu saka, English wear ne riga daskit sekuma Dan kwali fari riga baka skit pink, da talkami farare da baki komai iri daya, khalthum kam kamar tasan abunda zasu saka itama tasaka nata amma ita shigar marron colour da milk bakaramun kyau tayi ba , hakama joda yaran kamar"yayan turawa khalthum ce tanada musu dankwalin kamar head.A motar hafsa sukaje basu bari angansu ba"nice day" ce saboda haka kowa irin shigar yayi barinma amarya abun basauki, hotel suka dauka babba a nata ciye ciye ga lemuka kamar ruwan panpo, duk inda sukayi idanun jama'a na kansu, musamman joda ana son sanin ko yar waye yanda suke kama da hafsa dakuma Ahmed, mansura tadauki loudspeaker tafara godiya ga kawayenta yan uwa da abokan arziki sann takara da yan gayyar sodi, khalthum tace kaddai dani take billahillazi bana daukar kaniya ba shegiyar data isa , hafsa tace clm dwn mana khalthum bada ke take ba mutunnawa yake gurin nan taya zaki gane hakanKhalthum tace to meyasa taje an mata pics da kowa banda mu, nida joda idan bamuda alaqa da ita kefa, hafsa tace duk ba wann ba yanxu tashi muje kugaisa, khalthum tacebanda kyau fa wlh idan tamun rubbish ramawa zanyi, hafsa a'a khalthum Dan Allahkiyi hakuri abun a kaina zai dawo bruhh yacikaniyata , khalthum tace shikenan muje, joda kam jinsu kawai take haka suka jera suuku anata kallon su, gurin amaryar suka nufa ankunna wakar JustinB suna Dan taka rawa, hafsa tace anty ga kawata seda ta maimaita sann tace toh ya akayi, hafsa tacewae nace ku gaisa ba, mansura tace ok ina jinta, khalthum seda takalleta sama da kasasann tayar, tajuya abunta,joda tace ina.....bata karasa ba tace Dan ubanki bance miki ko kallona kada ki kara ba shegiyar yarinya kamar mayya sewani barawon kyau take kamar aljana, hafsa taja hannunta suka koma mazaunin su haka bikin yakasance se hantarar su ake barin amina ma dataki yiwa kodayansu mgn , suna zaune Sega Mahmud shida wasu kawayensa, sun zo kawo flowers da chocolates, Mahmud tin daya ga joda yake kallonta dakyar yabar hall din yakirata taxo ,khalthum tashiga tsokanar ta yarinya mai maxa biyu abdallah da Mahmud nikuma asea nace harda Ahmed 馃槼馃樂Hafsa gabanta yayi muguwar faduwa dasauri takauda kanta lokaci daya taji gurin ya gundureta , khalthum tace lfy hafsa, hafsa tace bakomai kaina yake ciyo inaga zankoma gida, khalthum tace ayko se muwuce nima naqagu da gurin nan, amota suka same Mahmud da joda ,dasauri hafsa takauda kanta daga dubansu, harzata tada mota, Mahmud yace akulamun da joda nah fah karki bi hanyar duwarwatsu,Hafsa tayi murmushi taja motar dakarfi, segidansu khalthum duk firar dasuke bata jinsu , suna isa gidan hafsa tafito tareda banko ganbun dakin dakarfi, joda tamaza tafito tariketa tace hafsa na lfy waya bata miki rai, hafsa tace bakowa joda kaina yake ciyo ina son nakwanta, joda tace ok toh muje narakaki hannunta tarika suka shiga parlor anan tahadu da hjy dakuma abdallah ko kallanshi batayi ba, abdallah yace lfy naga kinrikota haka joda tace batada lfy kanta yake ciyo, abdallah yace ayya Allah yabata lfy " jekikaita kizo kikarbi magani abata,Bayan takaita daki tafito tasamesa shikadaiyabata magani yace tabata takoma tabata magani tasha tamata Allah yakara sauki sann tafito dae2 step tahadu da abdallah yakuramata ido itama haka, haka suka dinga karaso wa har takai suna Jin nunfashin Juna, bakinsa yakai anata tuni talumshe ido da niyyar karbar sakon kiss dinshi , lebensa ya aza anata "馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�2鈨�Abdallahhhhhhhhhhhh sukaji ankirata dawani irin lion voice dika gidan seda yadauka dasauri suka janye tareda juyawa domin sanin waye Ahmed yasha bala'in toka fuskarshi ba annuri , yace abdallah kakiyaye kanka gataba matata nayimaka lamuni har nagaji kaki fahimtar hakan Sam baxan jure ganin kana tabamun mata ba, abdallah yace Ahmed yaushe kafara shaye2 joda dince matarka yarinyar daka tsana bakaso ganinta, Ahmed yace komadae yane baka bukatar bayani daga yau nayanke duk wata alaka atsakanin kuAbdallah yace wlh baka isaba bruhh idan bana maka musu yau zanfara, dae2 nan hjy tafito itada dad meena ma tafito tareda mansura Jin hayaniya tayi yawa, joda kam ta tsorata, dad yace meke faruwa Ahmed? Ahmed yace dad kaga yawa abdallah yafita harkar matata nagaji da wann wasar "yayan karan , dad yace kowa yaxauna , mansura tace wae matakarka honey koday kasha abun ne " Ahmed yace zanci ubanki wlh ubanwa yake shaye2Dad yace ku min shiru hafsa tafito rike dakai tazauna kusaga Ahmed tamika masa eviron drink , ya balla mata harara, ta girgiza masa kai hawaye na fita a idonta, shikuma abunda yatsana kenan kukan ta dole yakarba ya shanye atake yaji relief " dad yanna bell din gidan Sega kowa da kowa, hjy tace wae lfy ake tara mana bayinmu anan, dad yace karki sake mgn kinji nagaya mikiBayan kowa ya hallara harda su gwaggo, dad yayi gyaran murya yace toh ranar wanka dae ba'a boyon cibi, a lokacin da za'aauren joda da yasir, suka watsa mana kasa a ido suka wulankantani agaban abokai na a ranar nadaurawa joda aure da Ahmed tareda amincewar mahaifiyarta , Ahmed yafirgita kwarai lokacin dayaji hukunci na batareda neman yardashi ba, amma dana bashi mgn nida yayana seya dauka ya kumahakuraMansura tace billahillazi bazai taba yuwaba mijina shine mijin wann tanuna joda, waddaita Sam bata san yaren da suke ba , hjy taceyasaketa kawai aydama kunya kake gudu kuma yanxu komai yawuce, Ahmed yace bawanda ya isa yasaka nasaketa , joda kanwata ce jinina ce da uwarta da tawa uwa dae uba dae! Gwaggo tace yaushe muka hada jini dakai ? Ahmed yace tin randa nafidda joda aruwa nake tunanin akwai wani abu a tsakaninmu domin yanda nakejin hafsa haka nakejin taDaga ranar nake bibiyar asalinku har naganekece hafsatu kanwar mahaifiyata saratu asalin masina tashin nija, gwaggo tace koshi yasa nakejin hafsa sosae ashe munada alaka, Ahmed yace ni nayi tsaye aka kara muku kudin barin gari dayake ma lokacin bansan waye kuba inadai cikin bincike, kudinku suna account koyaushe kuka bukata za'a baku, mansura tace kai bamasan iskancin banza anjiya uwarku daya ubanku daya wlh matukar baka saki wann jahilar ba baxan aureka ba, Ahmed yatabe baki it's up to you "Abdallah yadora hannu akanshi yana maimaita innalillahi wa'inna ilai'hir raji'un, mike wa yayi atsaye yana shikenan narasa joda narasa raina da farin ciki na, timm Kakeji yafadi kasa somamme joda tabuga wata sgegiyar kara seda kowa yafirgita domin kuwa sunma aza iska ne da ita, da gudu tadunfaro gurin abdallah tana karka tafi kabarni abdallah na rayuwa ta bazata in ganta ba idan bakai, Ahmed yacabketa tafada kanshi, bude idon dazatayi taganta ajikin Ahmed luuuu tayi itama ta some akasa............( zanbada hakuri akan 2dyz kunjini shiru muna ta hidimar biki ne kunsan sa'a nin bikin mata so plss amun afuwa dalilin dayasa kenan nayi page 4 sbd baxan yi gobe ba se jibi )Abu nabiyu shine :- akwai wani dayake juya mun novel yacanza shi daga yanda nayi nd kuma yasaka sunanshi, ni nakirkira labarina dakaina , so plss idan bakada basirar yin naka badole bane ka yi satar nawani ba, baxakace dole se kayi abunda bakada shi ba, seka duba idan Allah baibaka wann baiwar ba to yabaka wata kowane Dan Adam yanada tashi baiwar sedai rashin maida hankali yakansa mutum baisain baiwar da Allah yamasa ba { a gaskiya baxan yafewa duk wani mai juyamun novel baMuje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�3鈨�Dad yayi gurin abdallah dasauri yana jijjigashi, hjy tace billahil'azim idan dana ya mutu senayi kararku akotu Sam baxan ragawa kowa ba, kuma wlh kigaggauta karye asirin da kikayi wa dana Dan banga abunda yake cikin yarki ba da har zata sakashi ciyo, gwaggo tace nagadai ba danki kadai ne yashiga tension ba harda tawa yar,amina tace dallah yimun shiru, Ahmed yace kee zan tattakaki wlh, da ke ake mgn , mansura tace nidae ba wann ba wlh kawai kasaketa,tsaki yabuga mata ya cakumi joda aka fadarshi se dakinshi hafsa tarufa masa baya , dad kuwa yakira family doctor dinsu domin yaduba abdallah hjy tabarsa dashi sekuma amina data tsaya domin tana Jin tausayin yayan nata, mansura ma tabi hjy, hannu ta aza akaii na shiga uku anty yanxu yazanyi da son Ahmed wlh bazan jure ganinwata a matsayin matarshi ba, hjy tace ke kinutsu,ni wlh dadi naji anraba dana da kaya, yarinyar batada wayo ga shegen tsoro, kawai yanda zakiyi kimaidata boyarki itama dole as an abunda aka kulla mata shikanshiAhmed din bafa sonta yakeba, kawai sbd tana yar uwarshi ce, kokin manta yanda yake wulakantata, kedai kawai yar ayki kika samu kinfita waye wa dakomai se yanda kikayi da ita, kinga wann abun tawarware mana hanyar rabasu da abdallah, ga abu yajo mana asaukiMansura tace hakane anty kwakwal warki naja wlh, se yanxu naji hankali na yakwanta da kuwa har jinina yahau, to yanxu ya zancen abdallah, hjy tayi murmushi har nake yanke masa shawara sati mai xua yabar Nigeria kawai myb acan yasamu reliefbafa karamin so yake yiwa yarinyar nan ba , mansura tace bari anty wlh yabani tausayi yanda yake kukamatsalar yarinyar ce kyakkawa gata da shiga rai komai nata abin birge wa ne koke mace zaki so ace yarki ce bare kuma namiji, hjy tace sosae yanxun dae karki yarda ta waye agidanki duk abunda zai kawo mata cigaba karki yarda dashi Hjy tace yanxun kije kibashi hakuri kice bakomai zaki riketa amatsayin kanwarki kinjanye zancen sakinta adauraaurenku kawai, Mansura se antyna "fitilar Sheri ko babu mai kina kai safe" hjy tayi dariya kedai jeki tuggu xamu hada mata da kanta seta gudu agidan , mansura ta daga hannu a gaida sarkin mugaye, dakin Ahmed yace tanufa , shiga tayi kawai batareda sallama ko neman izini ba, hafsa da Ahmedsuna kokarin sake mata wasu kayan sakamakon zazzabin datake amai kawai take batama san waye kanta ba,Ahmed yadago yace kinbiyoni danki karamun wani rashin kunyar koya Mansura tace a'a dear hakuri naxo baka akan abundanamaka agaban siblings dinka, kasan kishi irin namu na mata daga baya kuma naga bakomai bane joda batada matsala indae har na riketa amatsayin kanwata, Ahmed yace wai an gaya miki ina sonta ne? Mansura tayi murmushi dukda baka santa dole kadauki kaddara da baka santa ay bazaka yi kishi taba,馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�4鈨�Ahmed yace luk mansura bakishinta nake ba zunubin da zasu dauka ne abun duba, ciki kuwa harda ni sbd basu San da wann auren ba, mansura tace toya zancen tarewaatare zamu je, Ahmed yace fuck you wazata zauna mun a gida ay wlh seday ta tabbata anan auren dai akeso ko totayi , to taya ma zan dauki wann amatsayin matata na karamar yarinya tazo tarainani Hafsa tayimurmushi tace bari in fita bruhh,Ahmed yace au dama zama kikayi kina saurarenmu munafuka ba tace masa komai ba tafita abunta, mansura ta karaso kusaga Ahmed tace hup komai yawuce, Ahmed yamata banza ya cigaba da gyara fuskar joda mansura tace tokadaina tabata mana, dasauri Ahmed yadauke hannunsa afuskarta, mansura tamatso tajanyo fuskarsa tana masa wani kallon Ahmed yace kee lfy miye hakamansura kam data gama tafiya tace just once Ahmed, Ahmed yace kee wai mekike nufi, kafun yagama fada yaji bakinta anasa tana masa wani ka ruwancin, Ahmed dayagama rudewa domin kuwa kankanin abu yana saka shi fita a hayyacinsa , a hankali yafada kan gado tarufa masa baya, dakyar yasamu ta sakesa tana kokarin yin wani abu Ahmed yace plss mansura kibari muba muharram Juna bane, mansura tace au to menene yayi saura kwana uku kaday, Ahmed yace ayseki jira tym tinda naga har sokike mansura tace noo hava dae shaukin so ne kawaiDae2 nan joda tafarka da kuka ta farka abunda tafara fada shine, abdallah! Abdallah nah! Kana ina lalube tashiga yi tsavar kukan dataci har bata iya bude idonta, carab ta cabko hannun Ahmed dasauri tarungumesa abdallah wai mafarki nake ko gaskiya ni nakasa gane yaren dasuke, abdallah karka bari ahadani da yayan hafsa , bana sonsa natsanesa kamar yanda baya sona yatsaneni, abdallah mugu du adaura mana aure , yayan hafsa wulankantani zaiyi Sam baisan darajar Dan Adam bazanso ace shine uban yayana baTass Kakeji Ahmed yawanke ta damari, mansura dake kallonsu tayi murmushin Jin dadi, ubanwa ne baisan darajar Dan Adam ba, angaya miki ko mata sun Kare aduniya zan soki bare harna hada zuri'a ta dake kazama kucakar banza jahilar yarinya kawai, joda tace wlh banice jahila ba inada ilimi, Ahmed yayi ball da ita ta saiwa ina mgn kina mgn bell yazare zai fara dukanta dasauri mansura tazo ta tare hava dae dearyazaka biyewa wann yarinyar kasanfa akwaikuruciya acikinta,joda ta balla mata harara, ta cigaba da kukanta Ahmed yace mansura bani drink a fridge. mansura tace ok dear soya milk tadakko masa, Ahmed no ba ita energy drink nakeso, seta sake dauko masa rabenadrink, tsaki yayi yakarba yasha sann yace tafita yana son hutawa , mansura tace hava baby na wai meyasa kake illegal ne seka korani, Ahmed yace to ay seki tsaya inyaso semu shiga wankan atare,joda najinsu se kuka take, mansura tace hmm ok zan fita wann jikin da ake boyo yakusa xua hannu, Ahmed yabuga tsaki aranshi kuwa yace mara kunyar banza, mansura tabude kofa zata fita joda tabita zata fita Ahmed yadaka mata tsawa ubanwa yabaki izinin fita, mansura tawaigo hava dear karika mata a hankali mana yarinya ce joda kam batasan randa tafadi ba yanda yabuga mata tsawa, mansura tafita cike da Jin dadin data kasa sanin iyakarshi, direct dakin hjy taje, tana bata lbrn yanda taga Ahmed nayiwa joda hjy tace za'a rina Ahmed da kyankyamin yan kauye,dama dae zumuncin da yace ne yasaka ya yarda da auren su kinsan fah baya wasa da jininsa duk yanda yake dinn yana da son jininsa , sekinga yanda ya yiwa wani ranar daya mari amina kadan yakaishi kotu, mansura tace tohhh ashe kam idan nayiwa joda mugunta zai rama mata tinda ita jininsa ce ,馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�4鈨�hjy tace kamm wai bakiga yanda yake tsanar tabane mansura tace nagani mana Ahmed yashiga wanka yabar joda akasa tana darzar kuka, net yasaki agadonsa sannyashirya bayan ya fito yace keee zonan, joda taki xua tana dinga kankame jikinta , Ahmed yace zaki zo kose na ballaki, joda tadinga matsowa kadan2 tana rawar jikiAhmed ya kamo kunnenta idan nakara jin kinkira sunan abdallah kowani da sunan Wanda kike so sena fasa bakinki kar in kara Jin wani iskancin koke bakisan darajar aure ba joda kam takara fashewa da kuka, Dan Allah yayan hafsa tinda baka sona nima kuma bana son ka Dan Allah kasakeni na aure abdallah shikadai ne farin ciki naAhmed yace anki asakeki yar iskar yarinya inkika kara mun irin wann zancen wlh sena fasa bakinki ,anan zaki tabbata da aure a kanki keba gidan miji ba keba gidan ubanki ba, joda takara fashewa da kuka Ahmed yace kefitar mun adaki kafun in kakkaryaki joda ta dinga bin Gina har tafita a dakin, dakyar takai dakinsu tafadi a kasa tana kuka , gwaggo tazo tadagota joda tafixge hannunta tana cigaba da kuka , tace gwaggo ashe bakya sona kinfi son farin cikin wasu akan nawa kika badani ga Wanda baisan darajar Dan Adam ba baya sona hasalima kyamata yakeyi ya maidani kashiGwaggo kokin san duk sanda nayi ciyo tasana dinsa abun kefaruwa, shine voice dinshi yake sumaddani shine, shine yakaryani da gangan yataka mun kafa shine shine sekuma tafashe da kuka, gwaggo tarungumeta tana shafa bayanta kiyi hakuri yata ina sonki fiyeda komai nawa insha Allah bazakiyi dana sani ba , joda tace na yaushe kuma har abada baxan daina dana sanin auren yayan hafsa ba, gwaggo kema kinsan bamu dace da Juna ba girman kai dagawa daukar mutane bakowa duk halinshineGwaggo tace bakomai zai canza, indae har kin iya shi namiji kamar yaro ne se yanda kikayi dashi , joda tace gwaggo kina karawazuciyata zafi ay se kana son mutum zai yadda kamasa haka ni bana sonsa shi baya sona yatsaneni 2 sekuma tafashe da kuka, gwaggo takara janyota tana lallashintaKuyi sorry muna biki bazan samu damar idawann page dinma, dakyar nayiMuje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�5鈨�Tin randa abun ya faru joda tazama kamar wata tababbiya , hakama abdallah an rasa gane kanshi dole dad ya yanke shawarar dazaran angama bikin Ahmed zai tura shi Malaysia kozai samu relief. khalthum kanta tagirgixa dajin wann zancen hafsa kuwa tana maijin dadin kasancewa yar uwar joda koba komai yanxu tagane dalilin dayasa bata iya barin joda acikin wani hali itama haka, wani gefe na zuciyarta kuwa yace shikenan Mahmud yakusa xua agareki , murmushi tayi Allah ka mallaka mun yah Mahmud amatsayin mijina ameenYaude itace ranar daurin auren mansura daAhmed, kofar gidan dad, cike take da Dan mutum dangin mansura danasa sekuma abokan arziki gakuma yan semun gani a gefe akwai yan kwadayi dasuka zo dan su samu garar biki, ciki harda su oo da oo , Alhmdllh angama daurin aure lfy anguce gurin cin abunci babba hotel ne dad yadauka domin mutanensa hakama Ahmeddanasa daban, tsayawa fadar irin dukiyar daaka batar bata lokaci ne ku kissima aranku,Karfe 3 aka shirya domin xua gurin walima, joda nakwance dakinta har yanxu takasa sakuwa , hafsa da khalthum sun zo suka ce tazo su shirya amma seta fashe musu da kuka , khalthum tace iyye wato kina kishin mijinki koh? Joda taballah mata harara Allah sauwake nayi kishin namiji irin yayan hafsa, hafsa tace tome aybunshi, joda cikin muryar kuka tace dallah ku matsa kubani guri kafun muyi masifa , hafsa tace muje khalthum yau tafullo ta motsa zuciya ba kartamana sanda 馃槀Khalthum kuwa ta dinga dariya hakane fah kin san FULANI da zuciya kamar zauna, joda tace billahil'azim idan baku bar mana dakinmu ba ....sekuma tasaka kuka, hafsa tace ohhh my joda clm down mana kisakawa zuciyarki salama, rayuwa komai seda hakuri , bakomai muke nema musamuba watakila akwai alkhairi acikin aurenHaka suka gama zancen su joda ko motsa wa batayi ba bare nasaka ran zata tashi , dole su biyu suka shirya sukaje gurin walima ba jimawa amarya tafito shikin watashiga ta alfarma se kyalli take wuyanta tasha zinari da awarwaro, hjy tamata iso zuwa gurin decoration din daka tanadarwa amarya ,mansura ta duba ba joda tashiga Kiran hafsa, hafsa tazo tace ina uwargidanahafsa tayi murmushi anty tana ciki sekuka take har yanxu taki sakuwa, mansura tace ollrt jeki kawaiMalama uku sukayi walima amarya kam batajin su domin ana walima tana soyewa da Dan jeneral , dayake akwai net ba'a ganinta dakyau se itace take ganin mutane , anraba kayan walima a bun badama anci ansha an watse sekuma dinner wadda abokan ango suka tanadar , Karfe takwas akafara xua dinner din joda tafito zata gate kamar daga sama taji muryar abdallah yanacewa zaije dinner, abun yabata mamaki wai har yasaki, aranta tace aikuwa nima se naje nagan ko zai kula wata budurwa neJoda nah ango cikin wani red nd white din led tasha head karami Wanda khalthum tana da mata purse dinta red takalmin ma red ne, haka hafsa da khalthum sunyi masifar kyau khalthum ce kejansu joda na baya hafsa naga ba tareda khalthum馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�6鈨�Katon guri ne Wanda yaji decoration gurin amarya da ango basauki lemu ka gasunan da kaji nama ko wanne iri kakeso, kowane grp din kujeru da kafar rago agurin gakuma pizza da cheese se abunda ranka yaso nikaina yawuna seda ya tsinke kadan nace a sammun , su joda sun shigo sun yiwa kansu guri itada su khalthum da hafsa, bayan minti biyar Sega ango yashigo rikeda amaryar sa sunyi shigar fararen kaya weeding gown ce tasaka da net a kanta bakaramun kyau mansura tayi ba bare kumaangon daya hade cikin mayyar shadda da hula baka bantaba ganin Ahmed cikin manyan kaya ba, khalthum tace woww joda dubi mijinkiJoda tabuga tsaki wlh banaso khalthum wlhzamu saba dake waye mijina ay dae agama biki ni wlh seya sake ni nakasa In auri wanda nakeso , ana haka Sega abdallah, tamike dasauri ta taresa, cak yatsaya yana kallanta dae2 nan aka fara kidi light tafada kansu tinda atsakiyar guri suke , dasauri tajuya zata koma ma kidan yafara kanwar ango da kanin ango subuda fili da rawa , joda taware ido abdallah kuwa yajuya mata baya kidi akasa joda kam tashiga rawar jiki se juye2 take ana haka Sega wata yar kwalisa tazo tana zuba musu kudi dole abdallah yajuyo yafara takawa joda kam tsaye kawai take takasa motsiHafsa taji tausayin ta tazo tajanyota zuwa kujerun dasuke zaune khalthum kuwa mezatayi inba dariya, at kinga masoyinki koh? Joda tafashe da kuka se hafsa ke lallashinta, duk abunda ake visa idon Ahmed da Mahmud Wanda yagama kuluwa, mansura kuwa se murmushi take na mugunta, haka taron yakasance Ahmed yazuba dala kamar ruwa haka yake barin kudi agurin Mahmud ma ba baya ba,Hafsa tace kuzo muyi wa amarya da ango liki, joda tace wah ay wlh dana zuba musu kudi na gwara na zubasu a shadda, khalthum tace kyaleta hafsa kishi take ,jodatace tupp Allah sauwake inyi kishin wancan mai mugun halin , hafsa tace nidai yayana bayada mugun hali kema Dan kinki kwantar da hankalinki ne " joda tace nace dai bazaniba sekun dawo dole suka kyaleta sukaje suna yimusu liki,Wucewarsu keda wuya Sega wani yazo yaxauna baby tin dazu nake neman tayaddazan sameki mugaisa , joda tadago tace lfy? Yace lfyr ce dai wlh kawai kimun kuma ina sonki in bazaki damuba muje filin rawa, joda tace amma wlh kai bakada kunya nizaka cewa muje filin rawa namaka kama da mai rawa ne iye , Mahmud yaxo wucewa yagansu dasauri yadawo baya, yace kai malam lfy? Yaron yace lfy qlw bros dama naganta ina sone, Mahmud yace itakuma bata gayamaka cewa ansaka muna rana ba,joda tadago tana kallonshi yace to maxa kabar nan gurin wann matata ce, yaron yabashi hakuri sann yawuceMahmud yaja hannun ta yace zo muje gurin rawa joda tace a'a ya Mahmud ni ban iya rawa ba , Mahmud yace sekuma kinje dole, haka sukaje yasakata dole tayiwa amarya da ango liki, Ahmed se bin ta da harara yake mansura na mamakin yanda yarinyar tahadu amma Sam bata gaban Ahmed duk yan matan gurin babu wacca tafita yayan masu kudin gurin da kowa , dayake khalthum ce ta gyara ta, khalthum akwai duniya ci dason wankaMahmud yace kiyi rawa mana se in miki liki, joda tace kunya nakeji ya Mahmud bantaba rawa ba ni banma iya irin wann ba, Mahmud yace shikenan toki Dan taka, haka kuwa akayi yafara mata liki, abdallah na hango su nashi kishin ya motsa shima yaxo yana mata likin kudi, aykuwa se abun yazama kishi dollars, aykuwa mai kidi yakoma kansu yana xuba kirari joda kuwa duk ta tsarguHankalin kowa yadawo kansu, Ahmed yarungume hannuwa yana kallonsu khalthum da hafsa sukayi jugum suna kallo, sukuwa sunki daina mata liki duk da barawatake ba, hafsa taje gurin mai kidi tace yasaka musu kidin FULANI, aykuwa Sega joda tafara motsawa duk Wanda yake FULANI agurin seda yaje filin rawar saboda yanda suke Jin kidan ajikin su...........馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�7鈨�Joda tafara wani irin rawa yanda kidin ke tafiya haka rawar ta ke tafiya kowa yakoma kallonta hafsa takalli khalthum ashe ta iya rawa jita kamar macijiya, kowa yamatsa yabata guri Mahmud ya cigaba da liki hakama abdallah, gumi se karyemata yake amma taki bari shikuma mai kidi yakara da busar FULANI, nan joda tafara ajujuwa har takai gurin Ahmed anan tafada kanshi tareda rungumesa da hannu bibbiyu, hafsa tace yayi dae2 khalthum tace yo naga soyy,sun dade ahaka sann Ahmed yadago fuskarta yaga idonta arufe Jan ta yayi yanda take rungume ajikinsa har mota, abdallah ya dinga ja dabaya yana dana sanin abunda yayi, mansura tabiyosa dear ina zaka ay seka bari hafsa ta maidata gida, Ahmed yace noo kikoma ina xua, gudun yamata wulankanci cikin kawayenta yasaka takoma, Mahmud yaxo yace man......baikarasa ba Ahmed yasaka hannu agabanshi batareda yajuyo ba yace enough enough Mahmud,yana kai nan yasa kai yawuce cikin motarshi ya ajiyeta yazagaya yatada motar se gida haka ya rungume ta tamkar jaririya, se dakinshi ya shimfideta kan gado sann yadauko mata ruwan sanyi yabata tasha tareda wani kyalle yagoge mata fuskarta, ar u ok? Naji yafada joda ta girgiza masa kai, sekuma tasamasa kuka, Ahmed kam shiru yayi yana kallonta can yace kinsan Allah Zane ki zanyiYanxun Dan bakida mutunci kikaje karti suka tasaki a tsakiya suna tabaki wann yatava boobs wann yataba hibs , kowa na kallonku, joda tace na shiga uku ni wlh bawanda yatabani acikinsu, Ahmed yace yimun shiru munafuka dama ay haka kikeso, ke baki San hukuncin aure ba koh " joda tace toni ay bana son auren ,Ahmed yadakamata tsawa zanci ubanki wayake son auren daga an taimaka miki akayi, joda tace toni nagode da taimakon, Ahmed yace keee wlhzakici ubanki yanxu get out b4 nabata miki rai shegiya mai fuskar agwagwa ," nikuma asea nace ay fuskarku daya ehe 馃槒Fita tayi takoma dakinsu, gwaggo tace au har kun dawo inasu khalthum da hafsa, jodatace basu dawoba, seni kadai, gwaggo taceke kuma ana zaune qlw sekika yanke jiki kika dawo gida, joda tace toni nadawo ne ay yayan hafsa ne ya maidani gida, gwaggo tace tsakaninku baruwana, joda tafashe da kuka ni wlh an cuceni kawai baza'a bawa mutun Wanda yakeso ba mezanyi da wann Dan bakin rai, gwaggo tace kyaji dashi in ni nacuceki toki gayawa Allah inyaso seya saka miki, joda ta zunbure baki tayi cikin dakinTellphone tajanyo takira doctor bayan sun gaisa, yace toh ganinan xua nadai san abunda kike jira, joda tayi murmushi yauwa likita kagane, bara nayi sallah kafun kaxo , sallah tayi sann tasake wanka sabuwar atanpa tasaka ta cikin kayan bikin super ce tamata kyau sosae sann tasaka gyale kalar atanpar se takalmi flate, gwaggo sallah takesaboda haka ta lallaba tawuce batareda taganta ba , tana kai gate yana fakawa da mota kawai tashige, suka tada hanya , wakar flavour yasaka mata mai taken vewrifull" joda najin dadin wakar sedan mamin take dikda bata iyaba , har suka kai wani gida mai kyau, yakalleta yanaga jikinki yafara bari zakiga queen of beauty " joda tace uhm..Muje dai , shi yabude gate din abunda yabawa joda mamaki kenan sann suka shigaKaramun gida ne amma yahadu komai naciki sabo ne " binsa kawai take itakam bataga alamun wani mutum agidan ba, jodatace nikam bakowa ne agidan, yace bana son azarbabi fah muje dae, wani daki suka shiga se kamshin sababbin kaya yake , yacetazauna yakira mata matar tasa joda tazauna cike da kaguwa, ba'a Fi minti uku ba se gashi yadawo da drink yana sha yace dubo nan joda ya nuna mata mirror wakika gani, yarinyar nan tafiki kyau luk at pinky lipsdinta bakinta kamar cokalin tea gashin ta har gadon baya komai nata enough ina kewar ganinta nanda shekara daya , joda tajuya tarufe idonta, da hannuwanta, likita yace hakika joda so yawuce afadesa da fatar baki ina sonki joda tin randa nafara ganin ki, joda kam kasa tsayuwa tayi aranta tace shikuma wann nasa style din daban yake..........Muje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/28/16, 9:42 PM - Queen Safiyyert馃憫: 馃巹 FULANIN DAJI 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹 馃巹馃巹 馃巹馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�7鈨�Haka suka dawo gida Zancen namata yawoakai, kowannensu da abunda yake sakawa aranshi, joda na tunanin makomarta shikuma yana tunanin karta ki karban soyyr shi, joda tace nikam likita se yaushe zanga fuskar ka? Dasauri yataka burki seda ta tsorata, yace no joda bayanxu ba lokaci baiyi ba , joda tace towae mekake boyewa ne acikin wann fuskar, yace bakomai joda mamaki ne kawai aciki dakuma tsoro,Joda tace tsoro kuma kamar ya? Yace eh tsoro nasan idan kika gan fuskar nan komai ma zai iya faruwa idan ki kaga hallitar da Allah yamun wann dalilin ne yasaka nake saka face mark nafi son kiso zuciya ta sama da fuskar nan tawa ganinta bayada wani amfani Watakila ma idan kika ganta bazaki sake yarda ko hanya ta hada mu ba, joda , kam dole ta hakura ,yana ajiyeta Sega su hafsa dasauri joda tashige gida batareda sun ganta ba, tayi shiru kamar mai bacci, koda su kazo tana bacci khalthum tasha dariya sann suka fita, wanka tayi sann tasake wasu kaya , tana cikin shiri segasu sundawo , hafsa tace muje gurin kae amarya, joda tace wah zaije kai amarya din. hafsa tace tome ne aciki Dan kinje, joda tace Allah sauwake mun naje kaima wani mugun amarya toni waemamiye ruwana dasu nifa danke nake xua bikinnan hafsaHafsa tace ollrt yanxun ma kije danni okey, joda tace wlh ba inda zanje kubace mun dagani, khalthum tace muje hafsa kar mu rasa motar hawa mudae baza'a bamu lbr ba, joda tace safe journey. khalthum tace oho dai kedai kishi ne kurum bazaki iya ganin mijinki dawa ta ba amatsayin matarshi, joda taadauko filo ta jefa mata sann tafashe da kuka dasauri suka bar dakinGwaggo tace to lfy sarkin kuka, joda tace ni wlh ki musu mgn sudena tsokanata wae daga nace bana xua shine wae ina kishin yayan hafsa ne " gwaggo tace yo dama meke cinki inba kishi ba, joda takara fashewa da kuka tana bubbuga kafa , ko Dan kwali bata saka ba tafito waje tayi hanyar garden tana kuka, bayan wani window ta tsaya tana kuka tana zance ita kadai, kamshin tirare taji dasauri tadago taga waye fararen kafafun sa ta zubawa idosann tayi sama light din wurin yaki kae ga fuskarsa amma dae tasan abdallah ne sbd shiyake saka irin wann kayanDagudu taje tayi hugging dinshi tana kuka, ya abdallah shikenan kahakura dani, Dan Allah mugu du daga gidann, bana son yayanhafsa natsanesa kamar yanda yatsaneni, sekuma tasaka kuka, tareda kara kankame shi, shiru taji yayi a hankali ta sakesa, tana son ganin wani yanayi yake ciki , amma fuskar shi bama ita yake kallo ba kujera tajawo tahau yanda tsawonsu zaizo daya , na shiga uku tafada 馃檰馃徎 tareda zare ido " Ahmed yakura mata idonsa masu ban tsoro fuskar nan ba annuri acikinta , yasaceki kugudu yafada acikin lion voice dinshi? Wato ke yar iska tantiriya koh har kinsan saurayi ya daukeki kugudu domin kuji dadin aykata masha'aJoda tace wlh a'a bahaka.....bata karasa ba yabuge mata baki sann yakwabe kujerar tafadi akasa, joda kam tini tasaka mishi kuka, Ahmed yace wlh yanxun zakici ubankiidan bakimun shiru ba shegiya munafuka , musa afuska fir'auna azuci, joda tashiga girgiza masa kai hawaye na fita a idonta, dagota yayi sama sann yace idan bakiyi hankali ba wlh boarding skull zan mai daki tinda ke ta tacciya ce. ..........馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�8鈨�Joda tace ni wlh bazanje boarding ba haka kawai arabani da gwaggo na, Ahmed yakwabe mata baki ina mgn kina mgn koh? Joda tasadda kae kasa tana hawaye kafarshi yasaka yayi ball da ita sann ya juya yabarta agurin kuka take kamar me, aranta kuwa cewa take Allah yasa yafusata din yasakeni , nidae nace ameen kufa 馃Tin lokacin joda bata kara zancen abdallah ba koma ganinsa bata sake yiba sema lbr dataji cewa yatafi Malaysia gun hafsa dagaranar tafidda shi aranta amma can kasan zuciyar ta na sonshi, hafsa ma takoma skull, su joda ansha kuka kamar me, dakyar ta hakura itama hafsa din tasha kuka ciki harda kukan rashin samun soyyr Mahmud da tayi, atunaninta kafun tadawo yayi sabuwar budurwa,idan yafahimci joda nada aure, wata zuciyarkuma tace koday kigayamasa, can kuma tace noo bana kishi da yar uwata, to ammakuma miye amfanin boyewa din dawann tunanin tabar gidan Gwaggo tagama fura tamikawa joda tace takai a fridge din babban palor na gidan, a hankali take tafiya har ta isa gurin tabude fridge ta jiye furar sann tajuyo, dae2 nan suka ci karo da amina nanko joda ta tsaya cike da tsoron abunda zata mata, amina tadinga zunburo baki kamar mai shirin daukar selfie,joda tarava gefen ta zata wuce amina ta tare hanya, sann tace sannu anty joda matar big bruhh, sekuma ta kyalkyale da dariya , joda kam tini tafara ruwan hawaye, amina tace au kuka ma zakiyi, dubeki Dan Allah wae ke kin waye koh? tobara kiji maganar da bata tashi wlh wlh wlh sau nawa? Joda cikin muryar kuka tace uku, amina tace gud to wlh kar na sake ganin kinyi kwalliya kokuma kinsa ka kayan masu kama da na yayan manya danke bayar manyan bace tsiya gaba tsiya bayaKuma daga yau kexaki riga gyara mana dakinmu nida hjy sann kirika wanke mun under wears dina okey tareda jamata kunne, joda tace ollrt anty amina ta mata soko alright, ni zaki yiwa speak yaushe ma kika shiga skull din. kar nakara jin kinyi speak wlh sedai kiyi hausa ko kuma kiyi fulatanci ay muma munaji , joda tace insha Allah zan kiyaye, tajuya zata wuceamina ta janyota zo muje na nuna miki toilet dina akwae pants dina uku dasuka baci da mensis dina zaki wanke kitabbatar kinsaka Gishiri kadan da dettol akwae warm water dasu zakiyi amfani idan kin gama ki dauraye da hypo dauraya na biyu zaki gan tirare Wanda ake sakawa saboda karnin sabulu ko karnin blood din understand? Joda tace yes, amina kuwa tabuge mata baki wato har kin manta**** abunda yakamata kowacce mace tayi kenan domin Kare kanta daga cutar infection sann zaki iya insert na miski fari ko zaitun da habba domin kara tsabtace HQdinki musamman matar aure ko budare suna yi infection base mai aure ba so kowa seta kiyaye marta barta , gyaruwar HQ dinki shine martabarki ( Allah yasa mudace ameen )****馃巹 FULANIN DAJI 馃巹N@ B Aleeyu 馃挄 page 7鈨�9鈨�Haka joda taje ta wanke pants din xuciyartase tashi yake sann tagyara mata dakin Tassko ina seda tagyare tsab ta kunna tirare , tafito kenan tahadu da hjy a downstairs, hjy tabita da muguwar harara dasauri joda ta nemi sauka, hjy tayi saurin jawota inazaki munafuka,mekikayo adakin yata, amina tace kyaleta hjy ni nasaka ta ayki, bara naduba wlh idan baimun ba sekin kara wani, dakin tashiga tana Kare masa kallo yanda yadawo Tass harda can zamata jerin daki kuma bakaramin kyau yayi ba, tafito tana kinci sa'a yarinya yanxun sora dakin hjy, joda tace lokacin sallah yayi fah,hjy takai mata ran kwashi lokacin sallah dayake mu kafurai ne koh? Joda tace a'a bahaka nake nufi ba hjy takwabe mata baki yimun shiru makirar "ya , maxa jeki gyara mun nawa, tana shiga amina tace wlh hjy ta iya gyaran daki dubi fah yanda dakina yadawo harda canza style aikam da baimunkyau ba senaci ubanta tinnda bansakata janzamun kaya ba,hjy tace ohhh....kice munsamu yar gyaran daki, amina tace sosae ma hjy kinga munsamu hanyar cin ubanta , da aeki kadaesemu maidata tsofuwa wahala tamaida ita baya daga baya dole mijin yasaketa inyaga ko kallonta baya iyawa Bari kiji hjy nahana ta saka kayan kirki sann nahanata make up da wann shegen speak datake yanxu kuma bara taxo sena hanata daka bra yadda boobs dinta zasu zube awar silifa ,sann wanka a sati sau biyu banda saka tirare, hjy ta kyalkyale da dariya kae amma dae se yau nakara tabbatar ni na haifeki wann bala'in haka yo ay kice yarinya tazamahoto duk wata hanyar gyara kin tosheta, amina tace baki wasan wann ba sena gusturemata gashin nan nata yanda natsaninagan ta zuvo shi, hjy tace nagode yata nabaki dama kiyi duk abunda yadaceTana fitowa amina tasata agaba da scissors, tagutsire mata gashin ta yakoma kamar nawata baby, sann tabata wata sabulu tace dole da ita zaki rinka wanka kuma nagaya miki sau biyu ko uku zakiyi wanka asati daya , sann tabata baseline dinda zata shafa dakuma man kitso joda kam ba tagane kona miye ba, bacin ranta daya ashe wae bata wanka kullum amma inbancin haka babu abunda yamata zafi gashin ta kuwa dama ya isheta daGwaggo tasama zaune tana karanta iziya, gwaggo tace ke kuma daga kae fura sekika maida gari naku joda tace wlh a'a gwaggo anan takwashe komai tazayyane mata amma taboye zancen wanka da gutsure gashi duk taboye kawai dae tagaya mata cewa itace zata rika yimusu gyaran daki, gwaggo tace to miye aciki ay duk acikin aykinmu ne " kodan kinga sunbarmu muna cin bulus, koba komai ma kinga zaki kara kwarewa da ayki a yanda kike da shegen son jikin nan, joda kam tabe bakinta tayi tashige daki tayi alwala ta tada sallahSu mansura kuwa se zagwadi ake an shigo gidan Ahmed, randa aka kawota bai shigo gidan ba se kusan 12 shima itace tamatsa mashi da kira danko yamanta cewa shiwae angone duk wata waya tashi daya san za'a nemeshi kashe ta yayi, yana kuwa xua ta taresa da hugging, hannunsa take kallo bataga ledar kaji ba, aykuwa tasa tanbaya Ahmed yace nasiyi miki kaji sekace wata mayyar nama kaxarma wace iri ce bakiciba, mansura tace hakane honey muje daki na, Ahmed yace to mezanyi a dakinki nifa baccinakeji seda safe, mansura tace bazamuyi sallar godiya ga ubangiji ba, Ahmed yace kyayi ke kadae danni na rigada nayi shaf'i da wut'ri.........Muje zuwa 馃巹ASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/29/16, 12:04 AM - Queen Safiyyert馃憫: FULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�0鈨�. Hausa novels sokoto . Daga ranar joda tazama kazamar karfi da yaji tingwaggo bata damuwa har abun yafara cinta, askull ma haka khalthum kefama da ita idantamatsa mata seta saka mata kuka, gashi lokacinzafi ne " haka zakiji tana ta wani tsamin ba dadiduk yanda khalthum taso daure wa amma inadole ta canza site ,Ba abunda yafi damun kh irin bakin da joda keyiskin dinta duk ya takuje yayi wani iri dashi harmakara gwaggo da ita, abu dayane bata bari bashine karatu dukda suna gab da fara paper, agidakuwa tazama boya tana dawowa skull sometimeko sallah batayi zakiji anzo nemanta hasanamaiayki kuwa tayi ta masifa acewarta wahala cetamaida joda hakan, yau Mahmud yakawo musuziyara tareda chocolates dinda yasiyowa joda,bakaramun mamaki yayi ba ganin yanda jodatadawo kamar yar 60 , dakyar yake iya zamaatareda ita, Mahmud yace joda ke kuwa waniirinciyo ne haka kinbi kin rame kinyi baki komainakiyacanka, meyasa kike zama da datti nehaka,Joda kam tagumi tayi tana kallon sa dukyanda yaso takar bamasa amma taki, yana fitakuwa yawuce supermarket yasiyo mata sabulunhimalaya tareda mansa dakuma tiraren smartcollection,yakawo mata joda tayi godiya aranta kuwa taceina ni ina wann sabulun mai kamshi ina wankadashi zasu tsigeni idan sukaji kamshin sa ajikinahaka takaisu daki acikin akwati ta ajiye batasake waiwayarsu ba , mansura kam abu yafaradamunta yau kwana uku Ahmed yaki kulata sedaisu sha fira itadinma ita kadai ke zuba bada shiba,idan ta tabasa komai baya cewa , gashi amatsetake koba komai tasha abubuwa barekuma yandatake da bukata Yau kam tasha al'washinnemamsa da kanta domin kuwa bazata jurehakanba, Ahmed kuwa yana lure da take2 tashiisa yamata banzaarayuwar shi yana son mace mai al kunya da Janaji , bayan sun gama dinner sunyi kallo kusan har12 mansura tacanza tasha zuwa wata ta shar daake sako BF, aikuwa tayi sa'a ansaka wani, tunitafara murmushi aranta kuwa tace yanxun zakajifeelings. Ahmed kuwa yi yayi tamkar bai ganekomai ba , seda tamatso a kusa dashi tafararomancing dinshi, sann yadaka mata tsawa miyehaka? Dallah kicire mun wann iskancin kawai zakisa mutum kallon haram, mansura tace havadearduk kauce war danake kaki kagane iye, yaukwana biyar ace babu wani abu da muka gudanaramatsayin mu na ma'a u rata ,Ahmed yace ohhh....ay seki fito fili kigayamuncewa namiji kike bukata ba kizo kina kunna munbf ba kokuma a zatonki shi zaisa nakulaki ,mansura tace sorry dear yanxun muje daki,Ahmed ya ballah mata harara muje daki inmikiubanme acan, mansura ta kimtse fuska tacekabani hakkina, Ahmed yace hakki koh? tobangadama ba, sena tashi yana kai nan yafita , hakamansura ta kwana daddafe da mara tsananinsha'awar datake ji, Ahmed kuwa tin safe yafitadomin baya son wata maganar Mansura nafitowataga baya nan, tsaki tabuga ni wlh bazakakasheni ba da lfy na wanka tayi ta sauyakaya.........Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�1鈨�tazare key din motar ta se zaky hotel, tana kaetasa Kiran sabon saurayinta kamal, shikumadama yana expecting kiranta tinda sunyi dashi2ydx idan angon yafara , haka yaxo yasametasuka aikata masha'arsu, kamal yace sury kin jikikuwa billahillazi kinfi korama kinji yanda najisama na yawo dani,mansura tace dole nefa kasan nasha gyarakamar mutuwa shikuma angon Dan apixy ne "baitashiba gara kawai na nema Dan bazan iyakoda sati dayaba batareda naji ehem ba, kamalya kyalkyale da dariya bakida dama Karfe 1 dae2tadawo gida tasake shiri sann tafito parlor domintasan yanxun Ahmed zaizo,amma shiru ba labarin sa, bai dawo gida ba seguraren 11 yana xua ya hau dinner bayanyagama yaxauna parlor , ganin fuskarsa adaureyasaka mansura low tasan tin abun jiya ne "wato kar nasake tambayarshi koh " ay nasanmaganin ka Daki taje ta dauko wani caset, dakakanta yabata wa'azin gombe ne " tasakaananan suna saura re Ahmed dae baice kala ba ,se gashi ana fadan hukuncin Wanda yaki bawaiyalanshi hakkinsu alhali yana qlw, da matardata guje mijinta,Ahmed yakalleta yaga shi take kallo, tsakiyabuga yabar gurin se dakinshi wanka yayiyasaka jallabiya sann yadawo parlor koda yazohar tafara bacci, bubbugata yayi firgigit tafarka ,kisameni adakina yafada kawai seya koma ,mansura tayi jugum tomeni Allah yasa daekudine zai bani da wann tunanin tabisa baya,suna shiga Ahmed yarufo kofa yanuna matagado, ba musu mansura tazauna, Ahmed yakashe light din. aykuwa gabanta yashiga dukanuku Mansura tace lfy Ahmed menene, Ahmedyace hakkinki zanbaki tinda kinkai karata agurinAllah.mansura tace no wlh bahaka bane Dan Allah Kayihakuri kabari se gobe ni yanxun ban shirya bakuma bana Jin dadi, Ahmed yace ni dinma bashirine daniba amma naga alamar ke zaki iya kaucehanya idan baki samu biyan bukata ba , mansuratafashe da kuka na shiga uku, Ahmed kam kosauraran ta baiyi ba yashiga aykinshi ayaddayake sarrafa ta kadae yasaka ta manta dawaniabun, Ahmed kuwa yakudurta aranshi Yau setarana kanta har kusan 3 bai wani abu ba, mansurakuwa tasha gurza tin tana nishi har tafara kukayanda yake mata ne basauki ,lokacin da yafara ibadar aure kuwa ihu takekamar zata shide Ahmed kuwa bai mata a saukiba kuma yaki saurara mata, har kusan safe abuguda ake seda yamata lissss ko yatsanta bataiya dagawa sann yabarta yaje yayi wankayawuce masallaci yabarta agurin , yana dawowayaganta a yanda yabarta wata irin tsawa yadakamata seda tamike zaune bata shirya ba, Ahmedyace maxa kificemun adaki kafun nayi miki Danbaxan Duka fasika jahilar yarinyaSanin dalilinsa na kiranta fasika baisa tayikokarin cemasa kala ba illah kawai tafita adakindakyar take takawa tsabar azabar dataji, kusankwana uku tana jinyar jiki Ahmed kuwa bai sakebi takanta ba, dukda baya ganinta, mansura takirahjy tayi mata bayani, hjy tace ay kinga irinta kewlh shegen kwadayin tsiya gashi duk kudin damuka batar sunje abanxa, mansura tace Allahanty bakiji yanda naji bane bana iya jurebukatataHjy tace to ay ga abunda kika jamana nan, nantalabar tamata yanda suka maida joda, tuni ciyonta yabace, mansura tace kae amina shegiyace,tamun dae2 karku bari yagane kuma karkusakata ayki agabanshi, hjy tace ay bama zai ganiba wlh haka nake son ji, kinga ma naji yana wayada Mahmud cewa wae zamu je Egypt honeymoonkafun mu dawo tazama kiyashi gabadai suka sadariya...........Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�2鈨�Joda tagama gyaran dakin amina dana hjy sanntakoma yimusu wankin underwears, danko har nahjy itake wankewa, joda tana wankin pants dinhjy kawai seta saka dariya, tace yoni wai dukwann wake ken wandon duwawu kecikashi....nima dae asea abun yabani dariyaAshe afili take zancen kawai taji ana fadanduwawun uwarki shegiya , joda ta tsorata dajinmuryar hjy, danko tasan makomarta abi kadantayi setaci Duka bare kuma irin wann subul dabaka , tsawo ne mai kauri tasaka tadinga dukantaseda ta mata liss sann tabarta tsabar tasaba daDuka ko kuka batayi, tagama aykin ta tsabdasauri ta tsere batareda tasanar tagama ba,tana xua tasame gwaggo zaune tayi tagumi,jodatace hey gwaggo lfy? gwaggo tace ina lfy jodanarasa meke damunki duk kinbi kin canzaJoda tayi ajiyar zuciya tace gwaggo lfy na qlw kisakani a addua, gwaggo kam seta fashe da kukajoda ma haka ba mai lallashin wani acikinsu,Mahmud ne ya katse musu kuka, dasauri gwaggotajuya ta share hawayenta, Mahmud yagaidagwaggo sann ya dubi joda yace yadae yar kanwa,joda takirkiro murmushi tace qlw yayana,Mahmud yace gurinki naxo gwaggo , gwaggo tacenikuma Ince dae ko lfy? Mahmud yace qlwgwaggo se alkhairiGwaggo tagyara zama, joda kuwa tamike zaunedomin tashi, Mahmud yace a'a yi zamanki joda,takoma kusaga gwaggo tazauna, Mahmud yacegwaggo gidanmu ne anmatsamun akan nafiddamatar aure musamman da aka ga Ahmed yayiaure, nikuma arayuwa ta babu wadda nakesokamar joda tin kuna yan DAJI gwaggo tace ayyaMahmud dacan kana sonta kaja baki kayi shiru ,har aka maka riga yeMahmud yace bangane rigaye ba, gwaggo tazayyane masa zare da abawa , dogon nishi yajatare da hawaye har cikin zuciyarshi yaji kishinAhmed , Mahmud yace dacan Ahmed yasan daauren kuma yakara mata? Gwaggo tace au damaitakadai akace ya aura ne " Mahmud yace gskygwaggo joda matar mutum daya ce sann batacancanci rashin kulawa ba , naso ace ni aure tadomin in zame mata gata , gwaggo tace hakurizakayi Mahmud Allah yahada ka da wadda tafitaameen "tin da suka fara joda take kuka , meyasa nakesamun masu sona tsakani da Allah amma anacemin akan Wanda baya sona, sekuma takarafashewa da kuka, Mahmud yashiga lallashintadakyar tahakura, yana fita Sega khalthum taxo kokallon joda batayi ba taje inda gwaggo takaimata korafin joda , gwaggo tace nikaina narasagane kanta dazaran na matsa mata kuka takesakawa, khalthum tace kodai aljanu ne sukashafeta, gwaggo tace to waya sani nibangaalamar aljanu ba kawai abunda nafahimta akwaiwani abu dayake damunta bata san fada kedakike kawarta kexaki san kome neneKhalthum tace nayi2 gwaggo taki sanar danikomai, abun nabani tsoro yanda joda tazamakamar wata kaka , abun se an hada da addua,mansura taxo gun hjy gaishe su tareda musubankwana, anan tasame joda na goge2 mansuratace keee biyoni toilet ki wanke mun kafa na, bamusu joda tabita toilet mansura tamika kafa jodata wanke mata tanayi ana mata ran kwashi waezata balla mata kafa , tana gamawa takomayiwahjy guga aykin datake agidan har yazarcetunanin mutum,Karfe uku Ahmed yashigo gidan, direct dakinshiyaje yakwanta baitashiba se kusan 4:30 dajinmotsinsa , mansura tace wa joda taje takai masaabunci , cike da fargaba taje dakin bata ganshiba Dan haka tayi gurin table din dakin ta ajiye,bata Ankara ba taji ta tayi tintibe da mutunaykuwa abuncin ya bare Akansa tuwo da miyarkuka , taji dad dawa , Ahhhh......naji Ahmedyafada dasauri joda taja dabaya , fitila yakunnaDan ganin waye. Ahmed yayi toilet Daguduyadunga sharara amai kamar zai a mayehanjinsa, joda takara tsorata tashiga kwasheabuncin ,Ahmed kuwa wanka yayi kamar zai yi wankanzallar tirare ajikinsa, yana fitowa yartada joda nagoge gurin, keee ubanwa ya izoki da wannabuncin adakina jikinta narawa tace antymansura ta amina su kace nakawo maka, Ahmedyace ke kuma Dan ubanki sekika zo kinga namikikama da mai cin tuwo da wann shegiyar miyar,joda tace kayi hakuri, abunda yatsana kenan,cikinta yayi yacabko rigarta amma tsabar tsaminjiinta yasa kashi sakinta, joda ta bare baki xuakuka carab a idon Ahmed yellow teeth dintasukamasa arba da wani warin daban aykuwa Ahmedanan yadin ga kwara amai harda su sheshekaJoda tafito dakin aguje, tayi inda gwaggo ,Ahmed kuwa yana gamawa yasake wankaarayuwarsa baitaba tsanar abu kamar yandayatsani joda ba musamman a yau, parlor yafitofuskarsa ba annuri , amina! mansura! Hakayakwala musu kira atare suka zo, seda yagamayi musu kallon wulakanci sann yace wato Dankun rai nani zaku ay kamun tuwo da miyar kuka,amina tace tuwo kuma wayayi tuwo agidannAhmed yace ubanki ne yashiga tsula mata beltmansura tace hava Ahmed meta maka aykuwayahada su subiyu ya dinga Duka yana ball dasuyanata hada kansu yana bugawa tunikowannensu tafidda jini, hjy tafito dasauri tarikemasa hannu itama ya wulgata gefe sedayasumadda amina mansura kuwa da alamayamata targade a hannu.......( please masu cewa ina Jan aji akan novel dinakokusa bahaka bane. Kurika uxuri akwai aykingida ga karatu, sann yanxu lokacin biki nemunata lalura idan nasamu tym wlh bazan kiyintyping ba, kuma kunfi kowa sanin typing akwaewuya, abunda zan gaya muku idan nayi yaubaxan yi gobe ba sbd rai nason hutu , pleaseayihakuri da tsarina 馃憦馃徑 )Muje zuwaASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/29/16, 12:09 AM - Queen Safiyyert馃憫: FULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�3鈨�Joda tafito rike da boket zatayi shanyar tufafi,Sega Mahmud yaxo gidan ko kallonsa batayibata cigaba da aykin ta. Mahmud yamatso yacemata, kanwata karki damu zan same Ahmed muyimgn in har baya sonki tokuwa ya sauwake miki,joda tadago idonta dasuka cika da kwalla tace yaMahmud kana ganin zai iya, baya son farincikina, ya rantse seya dauwamar da bakincikiarayuwata sedai Allah baya bacci baregyangyandi Allah zai saka mun , Mahmud yaceno joda kar yiwa yayanki mijinki Allah ya isaJoda takallesa ta girgiza kai sann tawucetabarsa, Mahmud yayi jugum koshine dalilindayasa duk tabi ta lalace batada wani sukuni,direct gidan Ahmed yaje, yakirasa awaya, Ahmedyace tokashigo mana kokuma sena maka isosekace baqo, Mahmud yashiga har dakinsa,bayan sun gaisa yace Ahmed yanxu ashe harakwai abunda kake boye mun, Ahmed yacedakata inada aure bakasaniba shine zancenkoh "Mahmud yace yes amma hakan da kayi kayidae2 ,Ahmed yace to menene amfanin gayama kabayan kana son yarinyar, Mahmud yace aykuwadaka gayamun daban bari sonta yayi zurfi azuciya taba, Ahmed yace ohh....ashe hakane,Mahmud yace Ahmed al_hakika bakaine mijindayace da joda ba Sam baku dace da Juna bajoda na bukatar mai lallashin ta mai kwantarmata da hankali bamai wulakantata ba kamar kaiAhmed yace dama wann ne yakawoka? Mahmudyace kwarai dagaske naxo karba mata yanci neeither ka maidata gidanka kokuma kabatatakardarta inhar kasan bazaka iya xama da itaba,Ahmed waxai kawo wann kazamar kucakaryarinya agidansa yarinyar da ko.....sekuma yayishiru,Mahmud yace kadaiji tsoron Allah, Ahmed yacedama wann ya kawo ka gidana ? Mahmud yaceehh shine yakawo ni, Ahmed yace please get outtareda nuna masa kofa b4 kowa yaji mu agidann,Mahmud yace idan ba'a fita dinma saime, Ahmedyace wlh kasan abunda zan iya da wanda baxaniyaba so mind yourselfHaka sukayi challenge daga karshe Mahmudyabaro masa gidansa, yana fita Ahmed yafaukoeviron drink yasha sann yaji relief " Mahmudyafito kofar gidan anan sukayi karo da amina zatagidan kallon kallon suke yiwa junansu dagakarshe amina tajuya dasauri tashige gidan,Mahmud yace fine gul inaga nan zan maidasheqata , tin daga ranar yake Jin feelings akanamina itama haka dayake Mahmud akwai kyaukadan Ahmed yafisa , gidansu yake xua kullumgurin garden anan yake haduwa da amina ammasedai su yiwa Juna kallon kallon amma kogaisawa basayiYau kam Mahmud yaci al_washin yi mata mgnbayan yazuna yafara kara tin jarida Sega aminatazo wucewa, Mahmud yace jimana, aminatajuyo tana masa wani kallo, Mahmud yacemezai hana mufitar da sakonnin dasukezuciyoyinmu , amina tace kana da saqo ne dannidae banida shi, Mahmud yayi murmushi yace Ihave mssg, I love you daz oll na kwana2, aminata kyalkyale da dariya lallae kayi kokari............FULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�4鈨�Daga ranar soyy tabar ke tsakanin amina daMahmud kudi yake kashe mata kamar me, shi isata makale suka samu nonon ta tsa, joda nakuledasu kishi fall aranta dukda tasan tanada aurekuma bawani dating suke ba amma tana Jinkishin sa aranta, jama'a kuji jodaYaude su Ahmed anvar Nigeria, yaune kumasujoda zasu fara exam karatu take bakama hannunyaro, Sam bata kula da yanda jama'a ke hantararta, karatunta take ba ruwan ta har Allah yasasuka gama WC, agida kuwa tanan amatsayinboya se abunda yakaru Wanda yasan joda bayaganeta a yanxu sedai yayi la'akari da muryarRayuwa suke ba laifi a Egypt mansura bata sakeneman Ahmed ba shima haka, kuma ba abundayake nuna mata sedai tafahimci mayen boobs neidan tayi kwalliya sukadai yake kallo hakan yasatakara yin shiga kala sometime baisan randayake tabawa ba seyayi nisa kuma seya tura tagefe abin na damun mansura gashi batasankowaba bare tabiya bukatar ta gashi tana tsoron saketinkarar Ahmed kar yasake gurzarta kamar kayanwankiMuje zuwa gobe zan cigaba zanyi page 4 "banda complain please, bakusan uzurina baLike 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�4鈨�Ahmed yafita siyo musu abunci, joda yadawomansura na dakinta yafi minti biyar baigan tazotarvonsaba, hakan yasa yashiga dakin, kanagadoyasameta a dukul qule se wani nishi take, Ahmedyace lfy dae ko? Mansura tace marata yake ciyoAhmed, Ahmed yace ohhh....sorry month dinkinekenan, mansura tace no Ahmed bashine neba ,Ahmed yace to menene kinsamu ciki ne koya?Mansura tace nima bansaniba plss help me,Ahmed yace with what? Mansura tafashe dakuka, wlh Ahmed kana cutuwata, kasan menakenufi amma seka saka nafada sannAhmed yace mekike nufi, mansura tacebansaniba aciki tsawa, Ahmed yazare ido nikkeyiwa ihu? Mansura tace ehh anyi kayi duk abundazakayi Ahmed yayi kadi da hularshi yabita kangado ya cakumi wuyanta dagota da zaiyi blanketya zube akasa bakomai ajikinta, Ahmed yabugatsaki sgegiya mayya kawai randa nake bantabaganin mace jarababbiya ba irinki ke kinma guceharija wlh , ni Sam baxan iya daukar hakan ma,ko abinci yana kosadda mutun bare mace,mansura tace nadaijiya join me kawai, Ahmedyabuga tsaki , kindai San aure na mutuwa akanhakan al qur'an idan kika matsamin kotu ce zataraba aurenmuSam bana iya wann jarabar , mansura tace okeyayi timetable. Ahmed yace bakida hankali wlhtimetable sekace a skull, dahaka dae tashawokanshi sedai koyau ta gurxu, aranta tace kowaniirin karfi ne da Ahmed oho shi Sam baya gajiyabare ya kasa tashi sekace wani inji, tin ranartsoron nemansa takeji aykuwa tafara zancen gidatinda bawani yawo suke ba bare tasamu ta tseretanemi wani awaje , Ahmed kuwa yace se sunyi2month zasu koma gidaNote.....wann isuwar page din jiya ne danayikadan. Okey....?FULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�5鈨�Alhmdllh su joda ankammala paper lfy sedaifatan nasara aciki, suna waya da hafsa dintasosae har ta labar mata zancen amina daMahmud, baqaramun rudu hafsa tashiga ba,sedai taboyewa joda bata son agane tana sonMahmud daga ranar tashiga damuwa karatuntama duk yaja da baya , taqaqu hutunta yaqare,joda kuwa nanan yanda take se abunda yakaru,Mahmud yayi iyakacin kokarinsa amma yakasagyara ta dole yasaka mata ido " gwaggo kantatadena kulata abubuwa duk dunbi sun matayawagashi tadena samun wayar doctor bare tagayamasa halin datake ciki shikadai yarage matamasoyi, khalthum , gwaggo, Mahmud duk sunguje ta , batada wani hutu sena ayki idan takwana tokuwa dare ne yayi asuba nayi sallahkaday take watarana ko karyawa batayi za'azonemanta haka rayuwar ketafiya ba dadi agurinjoda, hjy kuwa da amina sunma daina kulatasaboda ta rigada tazama yanda sukesoWata daya da tafiyar su mansura, joda takamu daciyon kazuwa, gakuma kwarkwata akan ta, sukansu su hjy kyamarta suke dole su kace sundauke mata aykin kafun taji sauki suna tsoronkwasar cutar, gwaggo tafidda ita waje tana mataferfita, Sega hjy binta tazo dasauri gwaggo tajeta tarveta tana mata sannu da zuwa, amma Samhankalin ta na gun joda tace gwaggo meyasameta ne haka, gwaggo tace oho gata nankitambaye ta , hjy tace gayamun joda kinyiwanka da ruwan gulbi ne kodai wani kwaroyatava kiGwaggo tace kodaya tsabar zama da datti ne darashin wanka, hjybinta tace bangane rashinwanka ba joda dana sani tsab2, gwaggo taceasaninki nada ba, hjybinta tace joda ke kuwameyasa zaki jawa kanki bala'i haka keda kika fitodaji bakiyi wann ba seyanxu dakika zo birni,birnin ma capital city . joda tafashe da kuka,tace wlh ba laifi na bane su suka sakani hakan,hjybinta tace su waye ?anan joda takwashekomai tagaya musu duk wahalar dasuke bataTake idon gwaggo yacika da kwalla shine bakitaba gayan ba, joda tace sunce zasu ballani idannagaya wa koda tsuntsu bare mutum, hjybintatace to menene silar hakan, gwaggo tabatalabarin komai tin zuwansu har auren ta daAhmed , dakuma zumuncin su, hjybinta tayimurmushi kice alkhairi ne yakawoku nan, aykojoda kinyi miji, shi isa suke miki hasada , inamatar Ahmed zata zauna da datti Wanda bayasan ganin abun kaxanta ko kadan, yanxu yandaza'ayi, ki hado mun kayan ta tsab, bandawadanda tasaka acikin wann aykin sababbinkawai zanje da ita gidana bayan munje asibityangama kula da ita tinda bai fito dayawa baGwaggo tace ayi haka zaki dorawa kanki nauyi,hjybinta tace bakomai yayarki margayiya saratubamaijin kanmu kodanta zanyi haka, haka kuwaakayi gwaggo tayi yanda tace, sann tace kartagayawa kowa cewa ga inda joda take kice musuDan gin mahaifinta suka dauketa har taji sauki ,gwaggo tace insha Allah. bawanda xaiji Allahyasaka miki da aljanna mafificiya ameenMeena hospital aka kaita kwanan ta shida sannaka bata sallama jikinta yawarware sosae, sunadawowa hjybinta tasaka aka hada mata sabulunwanka mai kyau sann aka tsefe kanta aka wankeshi Tass aka yi kala ba hudu, haka hjy bintatasakata a toilet ta gurjeta son ranta da sosoSega joda anfara haske ,haka aka dawo kanteeth dinta tamkar dae wata yar kauye komaiseda aka maidashi sabo, kullum da sabulu maikamshi take wanka ga turaruka, tasha dilka dakulacca,Sati uku joda tazama balarabiya nikaina tsorotake bani yanda tadawo kamar ba itaba jikintakamar auduga, gashinta aka shiga gyaran shimaba laifi yadawo , hjybinta bata bartaba seda tagatadawo dass da ita sann tadawo teaching dintaakan yanda zata ja hakkinta akan mijinta dakuma su mansura , fita take da ita gurare dadama tana ganin abubuwa, yanda rayuwa ketafita ana haka joda tace mota takeson koyo hjytayi matukar murna dajin hakan............Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�6鈨�Aykuwa tuni tafara koyo dayake joda akwai kainan danan ta iya, tayi wasu kawaye a unguwarsamira dakuma yuhana wadda take christa ce, dataimakon su joda takara wayewa , waya gwaggota aykomata wadda dad yabata dadewa, iPhonece mai kyau, yuhana itace ke koya wa joda wayatabuda mata wp , fb imo, soma, Instagram,snapchart, dasauransu, joda kam kallonta kawaitake tinda batada numbers din kowa , a hankalihar tafara iya yiwa kanta komai make up damalight kawai take yi, amma seya karbetaWatanta biyu agidan ta waye sosae tadaukimanners dayawa agurin samira da yuhana,barinma yuhana data koya mata yanda zatajaapixy da kuma yanda zatayi mgn atake ta basulbrn ta tsab hakan yakara sakasu suka bata tipsdayawa akan Ahmed da matarsa, aykuwa jodataji harta kaqu takoma gida sbd tara ma zaluntada a kaci , magana wann da kwarkwasa sedasuka nuna mata yanda zatayiSu mansura andawo Nigeria murna gunta ba'amgn, gidan su Ahmed suka sauka anshadelicious kala2 Ahmed kuwa dakinsa yaje yayibaccin sa mansura kam wanka kadai sukayitacanza kaya suka yi gurin malaminsu, maganiaka bata Wanda idan tasha alawar zasuyi kissmatukar hakan tafaru tokuwa komai takeso zatasamu agurin sa ko nawa tayi tambaya zata samuagurinsa ba gaddama da murnarta tadawo gidaYau kam joda ta matsa gida takeso tana songanin gwaggonta, mota hjybinta tafiyar matasabuwa gal fara kirar jar chavarolet, acikin gadonmahaifinta murna gun joda ba'a magana, wankatayi tasaka prom gown green da ratesen blacktayi parking gashinta atsaka yazubo har gadonbayan ta rolling kawai tayi ta dankwali tayi lightmake up sann tasaka katon madubi Wandayakara fito da ita ga takalminta heel shoeskamfanin prada, se yar jakarta wadda tada ce dashigarTana fitowa hjybinta tasa shewa woww yatakinganki kuwa, har mota yuhana da samira sukarakata sann tajata se gidan horn uku sann akabude mata gate din direct tawuce gurin parkingdin motoshi kuma gurin da Ahmed ke ajiye motarshi inda yataka mata kafa , horn tabuga dakarfintsiya kasancewar ta hango Ahmed a gefe yanashan iska, Jin horn yayi yawa yasaka mansura daamina gamida hjy fitowa domin ganin waye.tafiminti goma kafun ta fito a motar tana chrt dintatamkar bazata fitoba shikanshi Ahmed yakaguyagan kowane ne kaddara takaishi gurinJoda tabude ganbun motar ta zunburo kafafun tataki fitowa Ahmed yatsurawa kafafunta ido kamarbana mutum ba, nanma tadade kafun tafito sanntafito gabadai batareda tajuyo sun gantaba,amina tace wai waye wann sekace yar shugabankasa wann shegen apixy, dakyar joda tajuyo,tadau minti uku sann tafara tako dass dasskamar hawainiya tanata zunburo baki kamar maishirin daukar selfie, gabadai mutuwar tsayesukayi danko basuma gane ko wacece ba hjytace Allah yasa dae amina ba saurayinta kikakwace ba bashakka wann yar shugaban kasa ceSeda takawo gab dasu sann tacire glass tanamusu wani irin kallo, a hankali tace hello, sanntakalli mansura data mutu atsaye danko kamshinjoda kadae abun firgitarwa ne " joda ta matsamata kumatu yade in law, na sameku lfy? tanakai nan tayi wani juyi dogon gashinta yamarimansura, takara rike kumatu kasa tayi dasauriamina ta janyota.............FULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�7鈨�Tin a kofa tafaran gwaggo na gwaggo na zogajodanki really miss you my cweet mother, hjytace shikenan wlh itace ayko wlh sedai idanoutside taje tayo wann wayewar duk ma watanawa kuma yarinya tadawo dawani fitsara hardasu mota, lallae Ahmed muna fuki neAhmed kam mamaki yacika shi yarinya daya barikamar kayi amai itace haka kamar wadda tayirayuwa aturai, lallae da sake, kuji Ahmed pah馃憟馃徎 gwaggo kam bakinta yaki rufuwa ganinjoda tace lallae hjybinta ta iya kiyo kinganki kuwajoda tace Allah koh gwaggo? Yanxu na wuce aykibare hantara, matar big bruhh dole abini a sannusann nice uwargida, gwaggo tace kiyarda daauren kenan, joda tayi wani shu'umin murmushinayarda mana gwaggoXua anjima kadan tayi wanka tasaka riga dawando leggings sann ta tubke kanta guri guda ,tanufi parlor gidan, TV ta kunna tayi zaune tanacin apple. Sega amina tafito amina tace keeubanwa yakawoki nan harda su kunna TV, jodatace kinsan Allah aminatu idan kika kara kiransunan ubana sena fasa miki baki, amina tacekam nizaki mara wlh kuwa dako ubanki dakelahira seya ji kukanki dasauri joda takai matamari aykuwa anan suka dinga ko kuwaHjy da mansura suka fito aguje suka rabasu,hjytace ke ubanme kike a parlor dinmu da har zakiyidanbe da ita, joda tace myb ubanta ne silar zuwana parlor dinn domin shi ne ya daura mun aureda dansa, dae2 nan Ahmed yashigo parlor, hannuwansa yarungume yana kallonta yanda takemusu iskanci , Ahmed yace ke lfy? Joda tayitamkar bata jisaba , Ahmed yace ba dake nakemagana ba, joda tadaga masa hannu wait badakai nake ba ay xanxo kanka, Ahmed yazaro idoyana kallonta , tace hjy kiyiwa yarki gargadi akanambaton sunan ubana inbahaka ba takusa rasahakorantaGa hanya amma tabi tsakanin mansura da hjyzata wuce mansura ta cabko ta ina zaki, jodatace sake ni kona balla hannun. ....kujimun jodakamar wata kakkarfa " mansura tace sekingayamun inda zakije, joda tace dakin mijinazanjekozaki hana, mansura tace waye mijin nakiyaushe ma ya yarda cewa ke matarsa ce, jodatace ohh....wann kuma shi zaki tambaya baniba,mansura tace bakisaba wlh ba inda zakije,yaushe kika tare agidann bare har ki isa shigadakin mijiJoda tace wann kuma yarage naki yaudae kwananane dukda banida interest da kazamin gidankuamma nan dakin komai shi bai isaba tana kai nantafice , Ahmed yadaka mata tsawa ke gidanubanwa zaki, dasauri tasakata amma seta basartace idan ka biyoni kaji " Ahmed yace metakenufi zanyi maganin wann kwailarAkan gadon sa yasa meta tana wakar JustinB,Ahmed yacakumo wuyanta ke ubanwa ya izokikimana rashin kunya, joda tace no no it's mytime kunyi naku yanxu kuma ni nakeyi Ahmedyace keee nikike gayawa magana , jodaohhh.....na manta ur my husband koh " Segajodakasa sannu da xua oga na, Ahmed yafusata yajanyota dakarfi suka fada kan gado , ido suka kurawa Juna dasauri joda takauda idonta bazatajure hada ido dashi ba sun dade ahaka sanntaceay dai seka matsa mun kawani hayeniDa sauri Ahmed yadaga mata, yace to ay sekifita adakina, joda tace wlh ba inda zani yau baccinane adakinka zan kwana, Ahmed yace wa yacemiki haka , joda tace tin randa ka aureta nakekidaya bantaba mantawa, Ahmed yaceohhh....dama kina son tarewa ne abaki hakkinkikenan, joda tace tuppp mekake dashi dazakabani.......Muje zuwaASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�8鈨�Ahmed yakwabe mata baki aykuwa tasa kukatanata bubbuga kafa, ni wlh ban yafe maka ba,Ahmed yace ni kike yiwa Allah ya isa, joda taceehh....ni ay marainiya ce amma baka dubimaraicina ba ka dinga zaluntana kana kyamatakana kushe halitta na goma muka hadu sekacucenini wlh banyafe maka Allah zai......bata karasa baAhmed yarufe mata baki, ni yayanki ne bazancucekiba nan gaba kadan zaki gane dalilin hakan,joda tabuge masa hannu tuppp Allah sauwakekazama yayana sedai yayan hafsa baniba wlh , niMahmud ne yayana bakai ba se abdallah sukadaisuke tausayina,Ahmed ya bata fuska yace wlh wlh wlh, nawanayi joda tace u..u uku ne muryar ta narawayace gud idan nakara jin sunan abdallah koMahmud a bakinki se kinyi nadamar sanin suarayuwa , yana kai nan yawuce yabarta atsaye,tana hawaye, yunwa takeji kuma tasha al washinanan zata kwana ,Ahmed kuwa bai sake bitakanta ba yayi gidansa yabarta anan joda kuwatashiga yimasa bincike har taga cornflakes nachocolate aykuwada murnarta tadauko shi tahada abunta tashasann tayi sallah tabi lafiyar gado ,bata farka base kusan asubah mamaki yacika ta ganin anyimata rufa da blanket , sann anrage sanyin AC dafanka, alwala tayi sann tayi sallah sann ta hadatea tasha kasancewar akwai komai adakin,baccinta takoma se 8:30 tafarka brush tayi sanntawuce dakinsu inda gwaggoGwaggo tace kewai ina kikaje ne naga Ahmedyafita shikadai jiya, joda ta sosa kai gwaggoshine yace duk ran girkina dakinsa zan kwana,gwaggo tajuya tawuce tana dariya sann taceAllah yakyauta ameen " agurguje tayi wankatashirya cikin atampa red nd blue tayi daurin Dankwalin ta Ali_yaga_Ali , se purse dinta redtakalmin ma red flate shoes tazuba tiraren nanbasauki light make up ne tayi tazubo gashintahar gadon bayan ta .inda gwaggo taje tace mata zataje gidansukhalthum, gwaggo tace kin nemi izinin mijinkiJoda tace zamuyi waya after yanxu sauri nake,gwaggo tace kitabbatar baya fada, joda tacekoma zaiyi wann yarage nasa ba'a gida sa nakeba bare yasaka mun gate , gwaggo tace kidaijitsoron Allah ko a ina kike aljannarki akafarsatake, joda tace bara kuma yatake ba yahani nishiga, tana kai nan tazare key din motar ta tayigaba, gwaggo tace ohni manga Allah yashiryamun wann yarWakar gfresh take sha kano to califonia tanamamin abunta dae2 wani titi ta tsayakasancewar motoci sunyi yawa, zata daga Segawani yaxo aguje yasha gabanta hakan yasakayabugi motarta har yafsa mata gaban mota,jodatace kambuu, dasauri tasha gabansa tafito sanyeda katon glass dinn tana tauna alawa, tace kaimahaukacin inane dazaka fasan mota sann kakibani hakuri kawuceFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 8鈨�9鈨�yaron yace keee kinsan koni waye kike gayamunmgn , joda tace Allah yasa kaine Dan sarkinmakka baka isaba, yaron yace ke karki kawomunrashin kunya yanxu zanyi maganinki joda tacekodai nayi maganin ka ba, yacee kewai yarubanwa ne " joda tace yar ubanka matar soldieridan kamun zancen banza wlh yau seka kwana aS,Ahmed dake gefe duk tacika shi da mamakiaranshi kuwa yace duk ina tsoron yarinyar nanyaje dubi yanda ta yafa mayafi akan kafadakuma tafito atiti tana challenge da wani doleyadauki mataki akanta, joda tace ko kana musuyanxun sena nuna maka waye, hannuta tanunadae2 motar Ahmed batareda tajuya ba,Ahmed yazaro ido danko baisan taganshi ba ,yana Saye da kayan soja, dasauri yaron yaceplss sorry madam dama ke matar oga Ahmed ce,joda tace kwarai dagaske , to Dan Allah kiyihakuri, joda tace sekayi kneel down. dasauri yayijoda taja masa kunne sann tace be more carefulokay?tana kai nan ta maida madubinta tashige motartabatareda takalli Ahmed ba, shikam dariya tabashiwann acting din nata kamar a film mace ammatana wani irin abunda bakowane namiji keyi ba ,sewani iskanci da rashin kunya takeji, Ahmedyace towai kuma harda proud ita matar soja,yace zaki gane ke matar soja ce idan kika shigohannuDaga nan se gidansu khalthum, maman khalthumtasama a parlor tana cin abunci, joda tace guntadasauri ta rungume ta, mama tace kaikai wacecezata idani haka, Joda tace yarki ce mamana,mama tace Ahhhh.....joda kece, khalthum jinance joda tayada plate ta ballo aguje tarungumejoda, tana wayyo Allah nah joda na kece kuwaina kikaje, joda tace ayseki sakeni tukun sann kijikomai ,khalthum tajata kan kujera suka zauna, khalthumtace joda ina kikaje kika barni, joda taballahmataharara dama kina sona kika kyama Ceni,khalthum tace wayyo joda na wlh bahaka banelamarinki ne abun tsoro nima ba'a San rainanabarkiba a sedan kawai bana iya kallon ki acikinwann halin "joda tace aykuwa masu iya kallona sun nemanmun magani , khalthum tace kigayamun mana ,nan tabata labarin komai, khalthum tace kan"ubawato so sukayi su kasheki da ranki , allah yafi sumama tace seki dage da addua irin wadannmutane ba'a zauna haka kawai dasu dole kanemi tsarin kanka sabd zasu iya halaka mutumtinda ba I mani a zuciyoyinsu,Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 9鈨�0鈨�amma gud karki yarda araina ki har mijin kicigaba da bin hakkinki agunsu, amma pa bancekiyiwa manaya rashin kunya ba kokuma mijinkiagabansu kinuna masoyinki ne " se kun kebesann kibasar tinda bashi yake bukatar zamankuba karki taba nuna masa kindamu dashi hakanzaisa yayi kishin ki har yanemi baki mazauniagidan sa, joda tasauke ajiyar zuciya sann tacewlh mama bana sansa kallonsa ma dakyar nakeyinatsanesa tamkar yanda natsani mutuwa naMama tace subhanallah joda mijin naki gara tinwuri kikoyawa zuciyarki sonsa danko bana Jinaurenki akwai saki aciki koba komai ga zumuncinku , kezaki gyara masa zama tinda yafara lowyanxu kiyita yi masa tsiya kina zuba shagwabadama ke gwana ce gurin shagwaba , joda tacetoh mama zan gwada Allah yashige mana gabaameen "khalthum tajata sukayi daki, suna kara wayekanjunansu, joda tace kinsan Allah khalthum yanxuwann doctor din nake bala'in so, komai nasadaban ne dana sauran maza ya iya soyy kamarme, khalthum tace garama kicirewa zuciyar kisonsa kimaida shi ga Ahmed yafi miki sauki, jodatace uhm....abar zancen kawai bazaki gane baneBata dawo gida ba se bayan magrib atare sukadawo da khalthum sann driver din joda yamaidatagida, bayan kh tawuce tayi wanka tasakanightwear sann takwanta, Ahmed kuwa dukhankalinsa na gun joda yana tunanin yanda zaiyida ita, wann renen datake ji, tabbas turo ta akayitayi masa wann iskancin amma yasan maganinta,mansura tayi bacci tazo takwanta kusagaAhmed baice mata komai ba, a hankali tacedearplease inason canjin mota kuma inason kudinasiye gwala gwalai Ahmed yace banganki dakodaya ba naci kin lefenki zaki ce nabaki kudikisiye wasu, mansura tace shikenan , kasiyawajoda mota ka kaita wani gun angyarata nikumanice banza, Ahmed yace bansan komai a kantaba gadon ubanta ne take amfani dashi,mansura tace amma dai kafara santa tinda hartake iya daga maka hannu agaban kawarkakamata banxa , Ahmed yace yafusata yace waike bakida hankali ne " yarinyar da kuruciya keciidan nabiye mata ayseta re nani, mansura tace tomeyasa ka kwana adakin kamar yanda taceAhmad yaballah mata harara ubanwa yagaya mikicewa agidan na kwana ma bare na kwana dakidaya da ita , mansura tace hava dae naxata aycan ka kwana , Ahmed yace ehh akanta manakwana da iskanci ,zatayi mgn yadaga mata hannu dallah kije kinxokin dameni da surutun tsiya, mansura tacetokabani kudin, Ahmed yacefaya check yacegashinan sora ki zare Duka kudin Dan naga kebaki San miye duniya ba , kudi ne kawai agabankitin xuwanki agidann banga kin dauko qur'ankinkaranta ba bare azkar sallar ma bayi ki kebasekin ga dama, mansura tadafe kai hava Ahmedsallah fah sekace kafuraAhmad yace ok karya nakeyi kenan, mansuratace wlh ina sallah, Ahmed yace ay zaki ganeranda kika isheni wlh dukan tsiya zan miki Dankin wuce a miki nasiha ko gargadi kinsan komaikike take wa yar iskar banxa bace mun daganikafun in sharara miki mari dasauri tabar masaparlor dinAhmed yace gaida dad gidansu sun gaisa yadancibreakfast. nan dad ke masa zancen joda, Ahmedyace tunani na kenan dad amma nafison takarahankali yarinya akwai kuruciya acikinta, dadyaceshikenan har kullum dae ina kara jadda makacewa kayi adalci kuma kasa ido akan matarka,Ahmed yace karka damu dad komai dae2 yaketafiya, dad yace gud son Allah yamaka albarkayatabbar da farin ciki arayuwarka Allah yajikanmahaifiyarka Ahmed yace ameenA garden ya hadu da joda tana sanye da rigarbacci duk ta lafe a jikinta , yayan hafsa yajitafada yatsaya cak batareda yajuyo ba, jodatacigabansa, tana marmada ido " ay baka bani kudingirkina ba kuma ni har yanxu banyi breakfast bayunwa nakeji, Ahmed yace to ubanme kike haryanxu baki karya ba joda tace badai ubana ba,Ahmed yace to senawa? Joda tace kila naka,Ahmed yajanyota dasauri ta rufe ido tana jiransaukar mari sekuma taji shiru tana bude idontayana turata gefe , joda tace nifa abuncin gidannbaya mun sann baxan iya girkawa ba dole kagirka mun kokuma kabani kudi asiyimun, Ahmedyace zan ballaki wlh kinga namiki kama da maigirki ne.............( karfa kuga nayi jiya nayi yau kusa ran zanyigobe, a'a tym ne kawai nasamu nayi gobe maidan ina free zanyi idan kuma banyi ba toh "hannuna nason hutu,Love you all my fans much loveMuje zuwaASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/29/16, 12:14 AM - Queen Safiyyert馃憫: FULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 9鈨�1鈨� Joda tace oho dai ay cina da shana duk a kankayake sena gadama zan tausaya maka in dafa ifnot kuma either ka girka mun kokuma kasiyomun,Ahmed yace gud kinyi gsky niba jahila bane,abunda kika saba ci gidanku shi zanbaki idannaso xan kara daga hakan , so zan kawo mikibuhun tsaba da dawa, joda tace kambu yausherabon tsohuwa da sukuwa a gado, Ahmed yadafebakinsa dariyar da tazo masa, joda tace kodaizuwa na gidanga yanxu shekara nawa soninamanta dawani abu dawa kayan dadi nakesoAhmed yazaro kudi a aljihunsa yabata joda taceda dai yafi maka kuma yau kwana nane dole kakwana agidann, Ahmed yace kee wlh nakusakaryaki, da aurena zandawo kwana agida , jodatace oh dai wann yarage naka, Ahmed yakwadamata wayarshi atake ta bare baki, yace idankwana kikeso tare dani Dan naga alamar namijikike bukata seki sameni agidana, joda tace iyeeenamiji Allah sauwake na name namiji koma inaneman maza bakaiba se wanda suka amsa sunansu na maxa ,Ahmed yafusata yacakumo wuyanta yabatamaribiyu kyawawa , kidena ganin ansamiki ido kizatatsoronki ake wlh zan gyara miki zama niba sa'anwasanki neba, ubanme ma zai kaini hada jikidake, joda cikin muryar kuka tace nadaifitsohuwar matar ka da kuka kusan zuwa agedayakuma ka duba dakyau har abada baxaka samu komaikama da joda ba bare joda, Ahmed yabita,aykuwa tace kafa minaci ban bakiba se dakinsuaguje tafada kan gwaggo tana maida nunfashiKusan 5 millions mansura taxara a account dinAhmed ta turasu anata , haka take kwasar kayanabincinsa tana aykawa kasuwa ana seda mata,hjy kuwa itama tazage dantse tana kwakwulalaljihun dad, se abunda ya gagareta, amina mahaka take ta tsan Mahmud shikuwa bai ganekomai, gwaggo tagama fura tabawa joda takaiwa dad, joda tasaka karamun hijab taje harkofar tayi Knockin akabata izinin shiga , fridgetakai masa furar sann taxo suka gaisa dadyamata nasiha sosae akan mijinta da rayuwar taJoda kwance dakin Ahmed kan gado tayi rufa dablanket, tana wasa sa flowers din bedsheet dindae2 nan Ahmed ya fito wanka Wanda baisanshigowarta ba itama kuwa batasan yana gidanba, lafewa tayi kamar bata agurin tana kallonsa,key yasakawa kofar sann yadawo shiri joda naganin ya cire towel tabuga ihu sedai bakintaadafe ba'a jinta, rude idonta tayi gam jikintasebari yake , Ahmed kuwa boxer dinshi yasakasevest yafeshe jikin shi da turaruka kala2 mouthspray yafesa sann ya kashe light, joda tazaro idoyau na banu na kawo kainaAhmed yafada kan gadon aykuwa joda tasakakara seda yaji tsoro yakoma baya dasauri ,yanunata da yatsa yace you! mekikeyi adakinayaushe ma kika shigo bayan nasaka key ? Jodatace yo ni ay banma San kana ciki ba se ganinayi kafito agurin wanka, Ahmed yazaro idowhat? kina nufin koda nafito toilet kina nan, jodatace ehh mana, naganka ma. Ahmed yace kingame? Joda tace naganka ba kaya kato kato dakai ,Ahmed yace kallona kikayi ina shiri yadafe kaiohh...gosh wann yarinyar tagama dashi Ahmedyace shine baki rufe ido ba koh? Joda taceoh..dai yaudae naga komai bawani dae2 dazakasake mun naga ciki naga waje joda ana tsulatsiya wollahAhmed yace kuttt wlh yau sekin gane, jodatace mezan gane nadai ganka ciki da baya,Ahmed yarasa mezai yi, yadafe kai, sann yacekema wlh sena miki tsirara, joda tace wayyo niAllah nah wayyo gwaggo wlh ban ganka ba kanazare towel na rufe ido yaushe idona ya isadaukar halittar namiji katoto dashi , Ahmedyadanne dariya yace ohhh...zama ki fadi gsky ,wato karya kika mun, joda tayi shiru, can kumatace nidae budemun daki in fita Ahmed yacewann kuma baki isaba........FULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 9鈨�2鈨�Joda tashiga bubbuga kafa ni wlh kabudemunkokuma namaka ihu " Ahmed yazagaya bayayahau gado yayi rufa yabarta agurin tanata mgnita kaday, can tajishi shiru ta yaye bargon tagaashe har yayi baccin sa, joda tace toni ma aybaccin nakeji bara na sauka kasa, pillow tajanyoda bargo tashinfida kasa tayi kwanciya ta , hadarine yafara haduwa iska da kura suka taso,abubuwan dakin suka fara rawa joda tabude idotaga duhu yakaru gakuma abubuwa na rawa,aykuwa ta takure guri gudaCan plate yafado akan table dasauri joda tabugatsalle tafada kan gado se ajikin Ahmed, Ahmedyace ke ke lfy? Joda tace wayyo ni yayan hafsaka kaini inda gwaggo na aljanu suka shigodakinka , Ahmed yace ke dakata mun dallahruwa ne ke zuwa, joda tarike shi gam a'a nidaeyayan hafsa, dakyar yabanbare ta yaje yarufewindows,wani kyalle yafado mata aykuwa anan tadakatsalle se gurin sa, tarike shi , Ahmed yace kewaibakida hankali ne bazaki sakeni ba joda tamasabanxa sema kara kankame shi tayi, Ahmedyabuga tsaki yace kisakeni nace kobakya ganinabunda kika rika joda tadago idonta dasauritasakesa taja dabaya Ahmed yagimtse fuskayakoma kan gado yayi kwanciyarshiJoda kuwa tabisa Ahmed yace ke kikuma kasakokuma ubanwa zai kwanta dake guri guda,jodatace al qur'an ba inda zani sokake a wurgo munwuka, Ahmed yace toh shikenan, joda kam gadotahaye tayi kwanciyarta, ba'a Fi minti uku babacci yayi a won gaba da ita , Ahmed yarufamata bargon shikuma yajuya baya,can cikin bacci ko mafarki tayi komeoho....kawai ji yayi yarikesa gam tana kuka,Ahmed yajuyo da nufin zai bigemata hannu seyaga hawaye a fuskarta idonta rufe bakinta namotsi, a hankali yakai kunnensa gurin bakinsa ,mezaiji tana fada....,yayan hafsa ka cuceni ka wulakanta ni kanunamun kiyayyar badan taba ganiba , bazan tabayafe maka Allah zai kamaka da cin zalun dinahakama maraicina baxan yafe maka ba baxanyafe maka ba......Ahmed yasaka hannunsa yarufemata baki aykuwa tasa kuka Dan Allah kadakadokeni, Ahmed yace kee keee, dasauri tabudeidonta, Ahmed yace mekikecewa ne acikin barcimafarkin wa kikayi ?Joda tayi shiru ba tace masa komai ba sehawaye take, Ahmed yayi shiru aransa yacedama haka yarinyar nan tarikesa yaxamematadodo har mafarki na take zanci zalun ta. lallaedole nabi mata wata hanyar da zata ya femundanko baxan iya neman gafarar taba, hakan zaikara sakawa tarainani, akan na yanxu , joda taceidan angama ruwa kabudemun daki inje indagwaggo na,Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 9鈨�4鈨�Ahmed yace ba'a gamaba bakya jinsu ne " watatsawa aka daka joda tayi bala'in rikesa tana kuka,Ahmed yace lfy kewai komai kuka, joda taceyayan hafsa wlh bana sanka banason kallonkaamatsayin mijina Dan Allah kabani takardartainada masoya, Ahmed yace nikuma maqiyinkikoh?Joda tace koma dai yane nidae nagaya maka wlhbana son ka bana son ka, Ahmed yace shikenannaji zan baki takardarki amma sekin yafe munJoda tace kambuu ay wlh sedai in tabbata daaurenka aka ina mara amfani amma baxan tabayafe makava,Ahmed yace auren ne mara amfani? Joda taceeh mana miye amfanin hada makiya guri guda,Ahmed yace toh naji ya isa haka, me kikesoinmiki seki ya femun joda tace babu shi, Ahmedyace idan nace zan baki takardarki fah Jodatajuyo da murmushi har dimple dinta ya lotsadagaske zaka bani takardarta,Ahmed yace of course idan kinbi tsarina, jodatace me kenan , Ahmed yace zaki koma gida nama'ana ki karbi aurenki na tsawon wata biyarnikuma namiki al_qawari suna cika xan bakitakardarki , joda tace shikenan na yarda, Ahmedyace kuma baxakimun fitsara ba komai nace dolekiyi, joda tace na yarda, kaikuma idan ka cuceniAllah baxai barkaba, Ahmed yace naji, dokatafara daga yanxu,Tashi kihadamun ruwan wanka, joda kamm nifabansaba da aykin wahala ba, Ahmed yace lallaeyarinyar nan mijinki fah, joda tace wai mijina ,mijin mansura dai Ahmed yace au zaki sabadokakenan, joda tace shikenan ina ne toilet din Ahmedyanuna mata tashiga ciki seda tafara wankewasann tahada masa ruwan, bayan tafito tace masagasu can ,waima bayanxu kafito ba daga wanka ba, Ahmedyace ehh ay wann ma kece sila, joda tacenikuma kamar ya? Ahmed yace manta kawaisena fito kifidda mun kayan sa zansaka, jodatace kai wlh baxan iyaba dama haka ne aurenkomai se anma mijiAhmed yace bakya son lada kenan Joda taceinaso mana , yana shiga seta gyara gadon tsabtagyara dakin ta kunna tirare bayan tagamatajanyo wadrop dinshi tafidda masa wando 3Q,da riga tafashesu da turare,Ahmed nafitowa joda tajuya bayanta, yace no fahay baki gamaba zoki gogemun jikina ki shafamun mai, sann kisaka mun kaya, joda tacekai_ka_kai sekace wani jinjiri, Ahmed yace yo aymiji jinjiri ne idan yana agaban matarshi kumakince zakiyi duk abunda nasaki joda tace ni wlhtsoro nakeji bana iya saka maka kaya , Ahmedyace shikenan wasa nake zo kiyi alwala kiyisallah kinga 4:20, ba musu tashiga toilet dintayialwala ta tada sallahBayan tagama Ahmed yace zo nan joda zantambayeki, joda tazo tazauna Ahmed ya kamohannunta yace gaya min meya sameki abayabayannan naga kinyi wani iri kina zama da datti,joda tafara kuka, Ahmed yace ba fah kukanakeso ba kigayamun naji, joda tafara basalabarin komai bata boye masaba, ran Ahmedyabaci matuka idonsa sukayi jajirhannunsa nadama yafara rawa joda kam tatsorata dashi, baya baya tadinga yi karyanausheta, se wani gurnani yake like a lion. Jodatabisa a hankali takamo hannunsa tahada danatata rike gam sann tafara shafa bayanshi a hankaliya lumshe ido yakwanta kan kafafunta, jodatacigaba da shafa masa kansa , sunfi minti gomaahaka sann tada gashi taje fridge tadauko masaeviron drink tazuba masa bamu su yakarba yashanye TassYana gamawa yakirata joda zo naga jikinki, Dankwalinta yacire yana taba gashinta yaga makamar yafi da tsawo sann yafi jikinta da kallobawata matsala, yace meyasa baki gayawa kowaba, joda tace sunce zasu ballani idan nagaya wawani sekuma tafashe da kuka, Ahmed yarungumeta yana shafa bayanta it's ok kinji..............Muje zuwaASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 9鈨�5鈨�Ahmed yaje yaga dad yamasa magana kan cewaran Friday joda zata tare gidanta baya bukatarkomai shi zaizo yadauki abunshi da dare, dadyayi matukar murna dajin hakan, shima yajeyasamu gwaggo yamata bayani, itama din murnatayi sosae daga ranar aka shiga gyaran jodaanatirka mata kayan fruits, hjybinta kuwa gyaran jikitake mata kafun kwana shidan suzo sekungayanda joda tadawo abun sewanda yagani skindinta kamar zai fashe idan katabaJoda tasamu khalthum tayi mata bayani,khalthum tace aykuwa yafi ma seki kara wanasa, khalthum a ranta tace lallae joda bakida wayokafun 5 month din yakoya miki yanda zaki soshi ,ni hakan ma yayi mun ina sonki da, Ahmed kodanki gyara masa zama kamar yanda kika gyarawaabdallah nasaAngama hada komai tsaf dad yakira joda yayimata nasiha kamar haka , joda ina son kirekemundana amana kamar yanda nabasa umarnin yarikeki amana nagayama sa tabbas idan yacucekitokuwa ban yafe masa ba , inaso kiyi amfanidailiminki da tarbiyar dakika samu kigyaramunwasuhalaye na Ahmed, tinda kika gyara abdallahAhmed baxai miki wuya ba , ki daure kiyi ibadaraure kisamu aljanna iyayenki ma zasu samuBanda fitsara da shashanci dukda nasan wannbahalin ki bane idan kika iya Ahmed bayadawuyar zama, ki kama kanki daga matarsa karkishiga lamuranta inso samu ma kada ki hadahanya da ita seta kama dole , allah yabakuzaman lfy da zuri'a dayyaba ameen " dakyarakabanbare joda daga jikin gwaggo, ita kuka gwaggohawaye, gwaggo takasa mata wata nasiha kawaitace mata Allah yabaku zaman lfy yakaudashedan azamanku ameenTin da Ahmed yatada mota takara wani ihu kukatake kamar me, Ahmed baice da ita komai ba,har suka kai gidan yafito itakuma taki fitowazagayowa yayi , yabude ganbu yajawo hannuntasukayi cikin gidan , kwance take kan kafadarsatana kuka har suka kai dakinta yabude mata"suka shiga yanuna mata komai hadda lefen taagurin sak irin na mansura babu banbanci ,dakinta kam ko makiyin Allah yagani yasananhadu se kamshi yake joda tafada kan gadotacigava da kukantaAhmed yace mata shikam seda safe, aykuwa tataso dasauri ni kadai zan zauna anan ni wlh tsoronakeji, Ahmed yace to sokike in kwana adakinkikoya? Joda tace eh kokuma nabika adakinka,Ahmed yace yo na banu muje din . dakinshisukaje takwanta shi kam toilet yaje yayi wankayasauya kaya sann yasha coffee. se yakwanta,joda na karshe Ahmed na farkon gado hakasukayi baccin su , anfara kiran asuba Ahmed yafarka koda yaduba joda tadawo ajikinsa ta lafemasa kamar mage aransa yace wann yarinyarkodai mage ce iyakaci kenan wann shegen sonjikin nataA hankali yasaketa ajikinsa yaje yayi wanka yayibrush yawuce masallaci yabarta tana bacci,kodayadawo yasameta kan sallaya tana karatun alqur'ani, tana juyowa tace ina kwana yayan hafsa,Ahmed yace lfy lau kn tashi lfy joda tace lau,bayan ta ida karatu tace yayan hafsa ina nekitchen in hada mana breakfast, Ahmed yace noan yafe miki kibari se zuwa gaba kadan............FULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 9鈨�6鈨�Su hafsa andawo hutu, taji dadin wann lbrn waijoda ana gidan Ahmed, gun khalthum taje sukayo inda joda, Sallama sukayi mansura na falotana kallo, kallon banxa tamusu sann ta cigabada kallonta, hafsa tace anty mansura ina wuni,mansura tace yana gidanku daban wuniba da zakiganni anan, khalthum taja hannun hafsa sukayisama,mansura tace gidan ubanwa zakuje khalthumtace gidan uban mai tambaya, mansura tazaburodakarfi, hafsa tace Dan Allah anty kiyi hakuri,khalthum bata sauraretaba tayi ciki, mansuratakoma dakinta tacigava da hutawarta ba sallahbare salati Ihu joda tadauka ganin su hafsa duktarude tama rasa abunda zatayi aykuwa tashigajibgo musu abunci pizza da kaji se lemuka,hafsa tace iye sukike ci ne " joda tace eh waibaya bari inyi girki ni bantaba sauka kasa batinranda naxo gidann, khalthum tace kenan bakutaba haduwa da fitsararriyar amaryarki ba , jodatace aifah ina side dina ina Jin motsinta sometime, hafsa tace ay haka yafi, joda tace nifainaga bata san da zuwa na gidann ba yandanakejin tana waya da karti datasan ina nan doletarage wani abu " hafsa tace uhm..allah yakyautaFira sukasha sosai se kusan mgrb sann suka fitojoda tahada musu kayan make up na cikin lefenta. hafsa tace a'a baxamu karba ba, joda tabatafuska to mezanyi dasu sunmin yawa wlh, dolesuka karba badan sun soba, har gate takaisusann tadawo anan taci karo da mansura taravata gefen ta tawuce mansura tadakamata tsawa ke ina xua, joda tabuga mata tsakisann tayi wuce wata sama, mansura tabitadasauri wai ina zakije nace basu hafsa sun wuceba ke kuma pa meya dawo dake joda tace eh sunwuce zasu gida nikuma nadawo saga rakiyarsuna shigo gidan mijina kuma habibiy na, hannutadaga zata mareta sega Ahmed yace ke kelfy?Mansura tace wann marar kunyar yarinyar manawai gidan mijinta, Ahmed yace eh karya tayinenan ba gidan mijinta neba, mansura tace waibala'i billahil'azim baxan zauna da ita ba, Ahmedyatada kafada fine kofar gidan abude take damani kawo ki ne ? Joda tace kuma kadaya matatabini sau dakafa Dan nice uwar gida nice babbabazan cen shekaruAhmed yaje famata key din mota dake nakemagana, joda ta bare baki wlh ban yafe ba,Ahmed yabita dasauri ta rufe ganbun dakindakarfi, mansura tajuya afusace tahada kayan tatafito taja mota tabar gidan, Ahmed na kallon tayamata banxa gidan su taje tazayyane wa uwartakomai, innasarsu tace to miye aciki tindabakulata yakebana tabbatar ubansa ne yace dole yamaida tagidanshi kedai kawai kikoma ki cigaba da ya gomana shi, dahaka aka batar mata da kishin ta.zuwa 11:30 tadawo gidan, shiryawa tayi cikinkayan bacci taje dakin Ahmed ko kallonta baiyibataduka tabasa hakuri , Ahmed yace shikenanyawuce daga nan suka lula wata d9/29/16, 12:24 AM - Queen Safiyyert馃憫: FULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 9鈨�7鈨�Tin randa joda tazo mansura take samun biyanbukatar ta agurin Ahmed har se ta ki wanilokacin, dalili kuwa joda ce keruda shi ammatsabar jinkai da karta renasa yasaka yake nemanmansura dukda tana gamsar dashi 70% amma kokadan ba itaba sha'awar taba , mansura kuwaansamu yanda ake so har anfara wani epixyepixy ,joda kuwa al amarinta take baruwanta da kowaagidan barinma yanda taga Ahmed ya shareta.itakuma tafita har kanshi ko mrng tadena yimasa,se hadu tarava masa hanya amma bawanda zeroyiwa wani mgn Kullum safiya seta zana da birokwana Kin da tayi agidan , yau Watanta biyucif,joda takara cika yanda take cin kayan dadigakuma hutu aykin komai batayi se gyarandakinta, yau tashirya cikin wata atampa browntayi kyau, tanada dankwalin ta simple taje dakinAhmed tareda mansura tasamesu suna iskanciinji joda aranta tace tanbadaddu kawai se ayitata shafe2 iskanci , baya tabasu sann tace inason zuwa gida inga gwaggo na, Ahmed yamatabanza, mansura tace honey ana mgn fah kayishiru, Ahmed yace ni Dan iska ne dazan amsamata mgn tabani bayaJoda tace nima kuma ba yar iska ceba dazankalleku kuna tanbadodi , Ahmed yaxuburamansura tarikesa yi hakuri cweet heart, Ahmedyace sekin dawo out kuma daga dakina joda tacekoma baka ceba , ba tsayawa zanyi ba kalloniskanci, allah yashirya wanda yabata tana kai nantawuce, Ahmed yayi tsaki sena karya wannyarinyar wataranaZuwa aza har tagama shirinta tsab ta rufedakinta tadauko kasa, mansura tace har kinfito,kigaidasu Allah kiyaye joda ta yatsina fuskaameen idan dagaske kike, Ahmed yace kewaibakida hankali koh se kiyi ta yiwa manya fitsara,joda tamasa kallon banxa tawuce abunta,mansura amma dae honey baida ce kabar ta tajegida ita kadai ba zuwan fari kuma ni banga tayiwani tsara ba ba hannu rabbana zataje, Ahmedyace hakane ina zuwa, ciki yakoma yasauyakayan shi sann yabita dae2 gate yayi wa maigadihannu alamar kar yabude gate.Ahmed yasameta yace mata kee fito mujeamotana , joda tace why bayan gatawa, Ahmedyace to haka nakeso, joda tace nikuma bahakanakeso ba , Ahmed yace zan ballaki fah ki fitokafun na saba miki Joda tace ni banidahannuwan tuka mota ne se anjani, Ahmed yaceshikenan karki fito wlh ba inda zakije, joda taceso what? Fitowa tayi a motar tarufe ganbun dakarfi tabuga masa dogon tsaki sann tawuceciki,Ahmed yabita da kalloHafsa tafito zata inda gwaggo ana tahadu daMahmud, yana waya da amina dae2 kunnenta tajiyace I love you amina more than you could think" wani kololo taji yana taso mata a zuciya zafizuciyar keyi aykuwa tadafe ta anan tafadi timm,Mahmud yajuyo yayi kadi da wayar yace hafsakoda yadago ta jini abakinta dakyar ta iya furtaya Mahmud kawai seta yi baya , wayarshi yaciroyakira Ahmed, Ahmed baijira yagama bayani baya tsinke wayar, motarshi yafiga yazo gidan Allahne kaday yakaishi lfyBasu tsaya wata mgn ba, aka wuce asibity da ita,duk atare suka shiga, Ahmed da Mahmuddasauran likitoci dakyar aka shawo kanta jinintane yahau sosae ga dunbin damuwa yamata yawa,Ahmed yace wai menene silar wann abun ne "anan Mahmud yagaya masa yace nikam inawayada amina kawai se jinta nayi akasa tafadi ammako menene zai saka mata damuwa haka hartahaifar mata da hawan jini , Ahmed yace shut upMahmud b4 I kill you, kasan komai duk ciyon 6tera kankane kokuma kanaso kace mun bakasantana dauke da cutar sonka ba , yarinya na nemanmutuwa a kanka taboye sbd kunya da kawaicikasani baxan taba yafe maka ba idan ta mutu akanka sann kotu ce zata rabamu, dae2 nantafarka da tari.........Muje zuwaASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 9鈨�8鈨�Dasauri Ahmed yaje gurinta yarungume ta yanashafa bayanta sannu 6ter kinji, hafsa tashigeajikinsa taki kallon Mahmud, shikuma jikinsa yayisanyi, a hankali tace ya ina son ganin joda na,Ahmed yace mezatayi miki anan, hafsa tacenidae kawai joda nake son gani, Ahmed a'abayanxu ba kibari har ki kara samun sauki , shirutayi Dan bata san musu sekuma tadinga kuka,Ahmed oh god wai mezata miki ne iyeMahmud yace joda kika gani? Tagirgixa masa kai,wayarshi yaciro yasaka Kiran joda, tana dagawayace mata kizo hafsa batada lfy tana asibityketakeson gani, baikarasa ba ta tsinke wayar hijabkawae tasaka tarufe dakinta tafigi mota aguje seasibity, tana xuwa tayi tambaya aka nuna matadakin da suke, Sallama tayi sann tashiga dagaciki, dasauri tayi bayan hafsa tana meyasa mekihafsa naHafsa tace bruhh zamuyi mgn plss " Ahmedyaceno hafsa zata tsira mana koke koke anan,Mahmud yace mubasu gurin Ahmed dole sukafita, Ahmed yace karki manta bai dace kiyidoguwar mgn ba kokuma ki tada hankalin kikinsan dae condition dinda kike ciki , hafsa tacetou bruhh, hannun joda tarike tace plss jodakarkibawa kowa labarin wann buk din plss, joda tacehafsa so kike ki kashe kanki da kanki, yazaki taboye so azuciyarki yana neman kai ki lfr kisaniidan kika mutu kece kika kashe kanki da kanki,hafsa tace ay dama akan hanyar mutuwa nakeJoda tace ni bazan bari ki mutu ba, hafsa tacejoda kada ki fallasa sirrin buk dina har se bayanraina, daga nan tafara tari jini yana fita Da gudujoda tafito dakin tana kuka Ahmed da Mahmudsuka bita da kallo Ahmed yadan bi bayanta, motatabude tadauko wani littafi, tazo dae2 gurinMahmud tajefamasa, ya Mahmud ka karanta kaji, komai yashafe hafsa na wlh kaine Mahmudyaduka yadauki littafin yana budewa yanakarantawa har karshe, joda tace u see koh "wuyanshi ta cakumo tana jijjigashi wlh idan kakashe mun hafsa na baxan taba yafe maka baKuka take sosae, Ahmed yaxo yajanyota yarungume ta ajikinsa yana bata mgn, joda kiyishiru hafsa bazata mutu ba seta auri Mahmudsun haifa babies. dasauri joda tadago tace DanAllah yayan hafsa da Dan murmushin ta, Ahmedyace eh , cike da Jin dadi, joda tarungumesa,harda basa kiss a cheek wanda yasaka Ahmedsusu cewa, duk lokacin da yahada jiki da joda sehakan tafaru, wani abu yakeji baisan ma koyanebaMahmud kuwa dakin yashiga dasauri yadagohafsa yagoge mata bakinta sann yabata ruwa tasha, Mahmud yace hafsa meyasa kika boye munsoyyr ki har kika bari nafara son joda by denkuma yayarki, hafsa shiru tayi ba tace komai ba,Mahmud yarungume ta, I love you hafsa I loveyou so much. dasauri ta banbare jikinta anasa yaabunda kake fada har zuciya yake kome?Mahmud yace wlh 4rm d bottom of my heart ne "Ahmed ne baya son yaga ina nuna zake wata akanki shi isa na boye sonki araina haduwa dajoda sonki ya narke mun, rashin samun ki yasakana nemi amina dukda kamarka afuska nehalayenki basa kama da Juna , hafsa takararungumesa ilove you more than you think.Mahmud yace it's ok love you too. Okey " hakasuka dade suna fa ranta ran Juna Mahmudnacigaba da lallashinta har bacci ya kwasheta.......9/29/16, 12:27 AM - Queen Safiyyert馃憫: FULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 9鈨�9鈨�Ahmed yadago joda yagan har tayi bacci,murmushi yayi wann yarinyar kamar jinjira takedaka sakata ajikinka yanxun zata maka bacci,Mahmud yakira awaya yace masa zai maida jodagida tayi bacci, Mahmud yace hava kae jodaakwai son jikiMahmud yace kana fama fah, Ahmed to yazanyiyarinyar ce se a slow yanxun natada ita tasakamun kuka , Mahmud yace c Ahmed woooo, kaineyau kake gudun kukan joda da , lallae so baiyi ba,Ahmed yace bansan iskanci fah kanwata cefahko ka manta ne " Mahmud yace no I remember.amma ay ada din da kake cutarta kasan kawarkace yanxun dae kagan ta waye kuma ta iya fitsarashine kake zaka matmata halin maxa na yaudaraka koya mata sanka koh? Ahmed yace kaifaDaniska ne so ya eh . kai kasan wann kalmar kumakaika ke amfani da ita, Mahmud yace naji dae najodaTsaki yaja ya tsinke wayar tadauketa cak seamota, har yakai gida ko motsi batayiba, hakamanan yadagata cak se dakinta ya shimfideta kangado sann ya juya, dakinsa yaje yakwanta haryafara bacci kawai seya farka yana son shanlemu, murmushi yayi ganin mansura har ta ajiyemasa Lemun kan table wanda yake sha idanyadawo daga aykiDauko sa yayi ya shanye Tass aransa yace tasanabunda nakeso wato yau zata fita shine takawomun kar na duba babu raina yabaci, mtsw yajatsaki zan koyi sonta"! Tass ya shanye yakomakan gado amma me wani iri yakeji yama rasamenene wann yanayin wayarshi yaciro yasa kiranmansura amma taki dagawaMansura kuwa ana can gurin boka ana aykatamasha'a, daya ga dae abun bana Kare wa banedole yashiga toilet ta watsa ruwa, amma kamarabun karuwa yake mace yake bukata kowace irice, marar shi ce tafara murda Ahmed se cijelebe yake duk yanda yaso yadaure amma yakasayanda gumi ke karyo masa gakuma jikinshidayake bari sewani jiri yakejiJoda ce tafado masa arai " a daddafe yakaikofardakinta rike da ciki, yamurda kofar dakin yacisa'a kuwa tabude ganbun, dakyar yasamuyashiga ciki , dae2 nan joda tafito wanka daureda towel. ihu tasaka ganin Ahmed a dakintaayanda take " dasauri tajawo hijib tasaka ' se alokacin talura da halin dayake ciki , dasauri tayogurin sa tana yayan hafsa meyasa meka lfykuwa? Ahmed yakasa amsa mata sema wanikallonta yake gumi nata keto masa , wani karayayi sakamakon murdawar da marar sa tayi,jodakam tini tasaka kuka wayyo Allah na yayan hafsaAllah yasa dae ba mutuwa xakayi ba kabarni plssyayan hafsa I beg.Ahmed yace yajawo ta yarada mata a kunne,plss joda help me mutuwa zanyi, joda takara barebaki wlh baxaka mutuba yayan hafsa ina nantare dakai, Ahmed yace help joda help plss ohhhgod, joda tace wani iri taimakon kake so, dakyarya iya furta joda I need you koba keba kowacemace inada bukata yanxu yanxuLike 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANINDAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�0鈨 joda tace dafe kai tadinga yi baya2 tanagirgiza kai baxan iyaba yayan hafsa baxan iyaba" so kake kara bani da mutunci na, never....,ganin tayi Ahmed kansa takai kasa dasauritadawo ta cakumesa dakyar ta do rasa kan gadotana masa ferfita dukda ga sanyin AC adakin ,Ahmed yalumshe ido tamkar yayi bacci jodakuwa ta tafi wata duniyar, hijabinta yacire ,afirgice joda tajuyo tafara kuka Ahmed kuwaidonsa yarufe ya walwale towel dinKiss romance ba abunda baya mata kuka taketana turesa amma ina baya ma jinta nikamtausayi ya hanani tsayawa dole nafito, sunfikarfin awa uku sann yabarta shikanshi ya wahala,rungume yake da ita bata koda motsi bare tari ,sunkai 30mnt sann ya daure yatashi a toilet dintayayi wanka yaje dakinshi yasaka jallabiya sannyadawo yahada mata ruwan zafi da dettol,dagota yayi cak se abawon wanka kara tasaki takankame shi sosae Ahmed yace yihakuri zakisamu relief dakyar takai 8mnt aciki Ahmedyahada mata ruwan wanka yafito yabata guri,kafun tafito har yacanza bedsheet ya kunnatirareKayan bacci ya fidda mata shine yataimaka matatasaka, a hankali tafada kanshi Ahmed yajata agado ya kwantarda ita, sann yahada mata teamai kauri, dakyar tasha kadan. sann yakomadakinshi yadauko mata magani seda yafara matafada sann tasha maganin , shikanshi seda yashasann yabita agado ya rungume ta yana tancuukanwata kinkawo yancinki agidan mijinki nagodemiki Allah yayi miki baiwa sosee wanda bakibaxai furta taba ,Allah yamiki albarka, joda najinsa tamasa banxajitake bawanda ta tsana aduniya Sama da shi,kuka take ciki2 har bacci yakwasheta shimadinbaccin yayi, se wani lokacin suka farka atarejoda takasa hada ido dashi se wani kasa dakaitake Ahmed yabar dakin ta yakoma nasa " dakyarta tashi tayi sallah tahada lipton tasha sekumatakoma bacci tsantsar bakin ciki dayake damuntaidan ta tuna abunda Ahmed yamata harmatakasa kukaAhmed kuwa jinshi yake tamkar me tsabar farinciki, daga ranar bata sake bari sun hadu daAhmed ba, shima haka ita tana cike da tsanarsagamida kunyarsa shikuma yana gudun tamasakallon raini, Mahmud ne suna waya da aminatake gaya mas cewa ya hakura kawai ya nemiwata itakam Dan gov garin zata aura , Mahmudyayi murmushi dama yana tunanin yanda zaibullo mata, se bainuna mata komai ba, kawaiyasamu iyeyensa aka je nema masa hafsa waddaxuwa yanxu takoma garau, aykuwa tasha arashida habaici akan cewa amina tayi yayin Mahmudtagama sann tabar mata " jifa sekace waniatampaAykuwa dad yayi matukar murna hakama gwaggowadda yanxu taxamo uwar hafsa, akasa bikiwata daya, shiri suke kamar me, hafsa dakhalthum da joda , duk yawon datake bata nemanizinin Ahmed danko yafita harkanta aranta takecewa yasamu biyan bukatar shi ay dole yamaidani shara, koma dae yane nakusa cikawatannina agidan, mansura kuwa se abundatacigava kullum Ahmed yafita seta kira watakawarta siddiqa wadda take asalin namiji ne yakeshigar mata suna iskanci suYaune za'a fara bikin hafsa, gashi kuma jodaantashi da ciyon zuciya ga yawan zuvadda yawusekuma jiri datake ji, haka dae take daure watana shiga mutane, salad suke gyara akace mataAhmed yana nemanta aykuwa gabanta yashigadukan uku2 danko kwanta uku agidan bataredatasanadda shiba, tana xuwa tace gani, Ahmedyace wato ke ko......baikarasa ba yayi shiruganin tana dade hanci tana masa alamaryamatsa, Ahmed yayi cikinta yacire hannun yaceke lfy? Joda tace plss kaje bana son wann warinna tiraren Ahmed yazaro ido yace medame kedamunki, joda tace jiri kasala....bata karasa batafara kwararo masa amai kamar zata mutuAhmed yana ya isa daena kakaroshi,Joda ta lafe ajikinsa Ahmed yace yarungume tayana murmushi...........Muje zuwaASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�1鈨�Dakinshi yaje da ita yakaita toilet yawanke matajikinta sann shima yayi wani wankan, akwatinshiyajawo yabata magani da Dan tea sann takomakwance, bayan yayi sallah yadago ta zai matamagana kawai tafara turashi Dagudu tayi toilettana kwara amai, Ahmed yadafe kai ohhh...goshwann aman yayi yawa gashi ba taci wani abunkirki baDole yaje gida yadaukota mata wasu kayanbayan tayi wanka tasaka su, yana fita itama tayidakin Gwaggo kan capet tazube , tana maidanunfashi, gwaggo tace ke lfy anata ayki kinxonan joda tace gwaggo wlh banda lfy bansanmeke damuna ba, gwaggo tace bangane bamekike ji, nan tazayyane mata duk yanda takejigwaggo tajuya tayi hamdalasann tace yanxun mekikeso joda tace ni pizzanakeson ci kokuma Dan wake gwaggo tace badamuwa yanxun za'a miki, akwai garinsa agurina,aykuwa ba dadewa aka gama mata tana Ci Segahafsa da khalthum sun zo, hafsa tace ke lfy kikecin Dan wake da sanyin safiyar nan ga breakfastcan mun hada,joda tace nikam banson sa wann nakeso,khalthum tace kaddai babynmu yasamu shigamusaka lissafi, joda tace kamar ya babaynkuHafsa tace wayyo dadi I'm gonna be mammabajimawa zaki sankado mun baby ammafa boinakeso mai kamada yayana,joda tace wai mekike nufi ne hafsa ta kyalkyaleda dariya, khalthum taje akunnenta tace yaAhmed yayi ajiya a jikinki, joda tace lez go to dstrength point mana , khalthum tace ciki nedakai, dasauri joda takalli hafsa itama tagyadamata kai, joda tace billahillazi karya ne anashanciki aruwa ne? Khalthum tace oho dai komayanedai dubi yanda kika fara fresh dole akwai ciki ,joda tace tobara kiji ni wlh baitaba kusanta ba ,kosau daya,hafsa tace ohhh..kenan maxan banxa kike bi jodatace hava hafsa yazaki mun wann kalamin, hafsatace yo inba maxan banxa kike biba me zaisakisamu ciki inba na mijinki bane, aykuwa tunijoda tafara hawaye to wlh sau daya ne shima wlhbada son raina ba dakarfin tsiya yamun , aykuwasu hafsa suka saka dariya harda su bingirewazama ki fadi gaskiya inji hafsa , yayana yacikaayki gwarzon namiji ne yi daya fah wuhuhuJoda taqulu matuka tayi kadi da tiren Dan waketafita Dagudu tana kuka karab sukayi kabra daAhmed tafada jikinsa tana kuka, Ahmed yace tomenene kuma joda cikin muryar kuka tace tobasu hafsa neba wai inada ciki, Ahmed yaceubanwa yagaya musu haka ?Joda tace ohonmusu, Ahmed yashigo dakin rungume da ita yacewahafsa ubanwa yace miki tanada ciki, khalthumtace yo metake ciwa Dan wake da sanyin safiyarnanAhmed yace zanci uwar yarinya yaxu wlh feverce ke damunta, gwaggo tayi dariya to munjiyanxu dae tace pizza takeso Ahmed yace waniirin pizza bayan taci Dan wake, gwaggo kada akara bata Dan wake gaskiya banyarda ana bawadana ko "yata wann abun ba, joda tace whatcikin ne dani kenan , khalthum tace au zaka fadama...........FULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�2鈨�Ahmed yace no ina nufin idan ansamu, jodatacebillahil'azim se ancire shi ciki dawa zan haihuaykuwa tafadi akasa tadinga birgima , dasauriAhmed ya dagota ke wasa nake miki fah , jodatace karya kakeyi tasss kakeji gwaggo tawanketada mari mara kunyar banza mijinki kike cewayana karya saboda bakida mutunciJoda tafashe da kuka Ahmed yajata sukayi sidedinshi tabaya sukabi saboda mutane suna isatafada kan gado wlh wlh seka cire mun cikin nankokuma na kashe kaina Ahmed yace bismillahbansan kincika jahila ba sekin kashe kanki yanxuyanxu , joda tace ay dai so rana wata dayaagidan ka kasa keni koh? wlh kana sakina zanjeacire mun cikin Dan ba karka shin ikon ka nakeba lokacin " Ahmed yace kinyi kuskure dakika yitunanin zan sakeki da dana ko yata a jikinki kicekihalaka ta , amma kisani kina juye mun dana tinagurin zan sakeki Dan bawani amfani kike munbaJoda tace so what? ay haka nakeso ammakasani da nacika wata na biyar wlh baxan karabiyarka amatsayin miji ba wai nabi umurninka,Ahmed yace wann kuma keda ubangijinki " sannkuma watannin zasu dawo baya, joda tace muguazzalimi haka zaka tayin zaluntana har nafishekara agidan ka , sekuma tafashe da kuka niwlh ban isa haihuwa ba Dan Allah ka duba nidagaske cikin ne " Ahmed yace bafa komaiiskanci ne suke miki , joda tace to ay kaima najikace danka, Ahmed yace ohh...god ke bari kijiciki ne dake kiyi abunda zakiyi faqadJoda ta dora hannu aka tafashe da kuka macucikawai azzalimi.....shiru tayi jin bakinsa anataseda yatsotse lips dinta tass sann ya kyaletayana sakinta tana kuka , aykuwa bakinta bayamutuwa tace Allah yasa zaka ga annabi muguka.....wani kiss din yadora mata sedanunfashinta yakusa daukewa sann yasaketalipsdinta har wani zogi suke akan tsotsa kamaryakama pop, seda sukayi jajir dasu " Ahmedyacewann shine hukuncin ki dazaran kin sake mgnDole bata kara magana ba , yana fita bacciyakwasheta koda tafarka har anfara zuwa gurinparty aykuwa agurguje tashiga wanka a toilet dinAhmed towel tadaura babba sann tasaka karamiakanta tana tsane ruwa , dae2 nan Ahmedyabude ganbun dasauri takoma toilet gurin rufeganbun toilet ne hannunta yamatse aykuwatasaka ihu , dasauriAhmed yaxo ya riketa yana mata sannu, cikinfada yace mekike yiwa gudu ne kinje kinji wakanki ciyo abanxa, joda kam kuka take barinmadata ga jini nafi ta se wani tsalle2 take Ahmedyajawo akwatinshi yayi mata dress din gurinaykuwa ansha kuka da gurje2 duk seda ta ciretowel din nakanta ma seda tacire gurin gurje2nta gashinta dayake ajike duk yarufe mata fuskasekuma yabada sexy act! Ahmed yatsaya kallonta sann yace mata miye haka zaki muntsirara........Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�3鈨�Se a lokacin ta tuna halin datake ciki, aykuwatasa lalube takasa da go idonta shikuma Ahmeddayaga haka kawai seya janye towels dinyamaida su toilet yayi tsaye yana kallon ta, zaningado tajanyo tarufe jikinta dashi, Ahmed yatabebaki sann ya kashe light din yabita agado, jodataji ana lalubenta dasauri takwabe masa hannumiye haka? Ahmed yace shhhhh......zo kiji cizoyabata akunne kadan, tasaka kara nikam fitowanayi na basu guri , joda taci kuka kamar rantazifita sann Ahmed yasha tsinuwa abakinta,dakyar tasamu ta tashi tahada ma kanta ruwandettol bata raba wann dana fari ba duk zafindayane, amma wann karon tafi Ahmed saukidanko shi yama kasa motsi har tasake wankatayi sallah bai daga va, a hankali ta yaye masabargon aykuwa rawar dari yake jikinsa yayi zafisosae , joda tace subhanallah yayan hafsa mekedamunka, Ahmed yanuna mata akwatinshi namagani ta dauko masa yanuna mata wandazatabude masa, lemu ta tsiyayo masa a cup tabasayasha sann tahada masa ruwan wanka dakyaryasamu yayi wankan yana fitowa joda tahadamusu tea suka sha, zata fita Ahmed yace inazua, joda tace gurin party zamuje nama san kowayabarniAhmed yace jeki shiryo ni zan kai ki , joda taceno tanks da mota na zanje, Ahmed yace bansanmusu fah kin sani joda tajuya tana ta tunxurebakinta , takuwa yi sa'a basu tafiba, daganintakhalthum tasaka ihu ohh maman baby anfitobarayar oga shine kika sharemu ke mai miji bakoh? Joda tace bansan haka khalthum kidena,hafsa tace nidai ga kayaki nan kisaka tana karbazata saka kamshin less din yabuge ta aykuwatuni tafara amai, hafsa da khalthum suka rude,dasauri aka kira gwaggoGwaggo tace lfy " khalthum tace daga an bataanko dinta shine kawai fah inaga bata san warinsababbin kayan gwaggo tace tabb ke kuma hakazakiyi mana naki cikin da yawan amai kukiramijinta, hafsa takira Ahmed tagaya masa yace ayyana gidan gashi nan zua " koda yazo joda nakuka tabata kayan ta da amai, khalthum tace yihakuri ganawa kisaka amma ina riga batayi Coxboobs dinta yafara cika, hafsa tace ganata jodatakara fashewa da kuka kayan amarya zansakane? Ahmed yace muga less din yana dubawayace to ay tanada irinshi akayanta na lefebabban wann flower ce kawai banbanci, gwaggotace to ay shikenan kuje ta dauko joda tace nifabana iya fita yanxu, Ahmed yace nikuma baron kibane da zaki ayke neDole badan tasoba tabisa sukaje gidan, dakintatabude dakanshi yajawo mata less din ganin irinkyanshi yasaka ta rungume Ahmed tana tancuuyayan hafsa, Ahmed yace jimana kirika kulaminda dana fah naga kina wani rawar kai kinfi ubankowa tsalle2 da guje2 Allah idan kika sakeabunda ke cikin ki yasamu matsala kema zakisamu, bakinta ta tabe tacigava da shirinta tsab,Ahmed yakalleta yace amma kam yau uhn ue kindanyi kyau kadan, joda tabuga tsaki wlh nadai Fimatarka kyau, Ahmed yace wakike yiwa tsaki?Joda tace ahh...wanda yatanka aykuwa tajiunexpected kissa seda takasa daukar kafafuntaHaka bikin hafsa yakasance ma joda bawanikwarin kirki ajikinta se yawan amai ga jiri, dukabunn mansura bata saniba, waya suke da hjytace kinsan me hjy yanxun haka inada over 20million a account dina duk ajikin Ahmed suka fito,hjy tace yauwa ki cigaba da kwakwularsa ,mansura tace ke pa hjy tace ay nikam ba wasayanxun nasaka yacika mun duk wasu kadarorinasa yanxun haka nasaka masa maganin a teana tabbatar yasha, bajimawa zakiji ankira Ahmedance yamutu, tuni suka saka shewa, unnnnnallah ka shirya mu baki dayanmu ameen........Muje zuwaASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�4鈨�Ahmed rungume da joda tagama amai , xuayanxu ba damar yayi nisa saboda yanda takeyawan amai ga jiri dole koyaushe yana tareda ita,sekuma me shakuwa tafara shiga tsakanin su,har idan Ahmed yakai 10 PM bai shigo dakintazaka gan joda nata yawo dole se yazo yabatabreakfast , hakama lunch haka dinner , dukabunda ake mansura bata san wainar da ake toyawa ba , pizza yake bata tanaci wayarshi tadaururi , baiduba ba, bare nasaka ran zai daga wayarhaka wayar tayi ta ring. joda tace yayan hafsanaga kamar dad ne yake kiranka, dasauri Ahmedya ajiye abunda yake yadaga wayarMuryar amina yaji tana kuka bruhh kazo dadnebashida lfy sosae yama kasa motsi, what!?Dasauri ya tsinke wayar yasaka takalmin sa zaifita joda taci gabansa lfy yayan hafsa? Ahmedyace dad ba lfy da alamu jikin nasa yayi tsanani,joda tace subhanallah Allah yabasa lfy ameen "gudu yake tamkar zai tashi sama , yana shigagidan yabude ganbun motar baiko rufe bayashiga dakin dad dinsu tin a kofa yake Jinkukan hjy da aminaGunsa yayi yadaga hannunsa yaga baya motsisann jikinsa yayi sanyi, innalillahi wa'inna ilai'hirraji'un naji yafada, hjy tace ya mutu koh? Ahmedyace noo dasaura amma sedai munje asibity,dakanshi yacakumi dad dinsu xua mota sannyakira Mahmud yagaya masa yace kar yafada wahafsa tinda tanada hawan jini, a asibity sukahadu likitoci dayawa Akansa ciki harda Mahmud,Ahmed kam kasa shiga yayi saboda yanda yaluracewa ciyon yaxo da wani abu kamar dayan sidedin jikinsa yamutu, haka kuwa ta kasan ceDaga ranar Ahmed yazama wani iri gashi nandae, ga joda ga dad dinsu, dole Mahmud yadaukohafsa yaxo sa ita asibity, bakaramun tashinhankali tashiga ba yanda taga abbansu bayakodamotsi ne " kusan wata uku ana fama dole akadawo gida Ahmed yace lallae baza'a fita waje dashiba se maganin sa yakare na wata hudu, dolebadan kowa ya soba ya hakura, abdallah matuniyadawo gida , hjy da amina ne ke kula dashiyanxu kuma sun daina sedai idan Ahmed koabdallah ko Mahmud da yanxu yazo shine zaicanza masa kayan su suke yimasa wanka sannkuma su wanke masa kashi da fitsari , joda maitada hafsa agida suke wuni kullum saboda dadsu suke ragema si abdallah ayki,Hjy tashigo dakin tasame bakowa a hankalitakalli dad, tayi yar dariya sann tace se yaushezaka mutu ne " rayuwarka batada wani amfaniaduniya oxygen dinda yake bakinsa tajawo zatacire se taji anbude ganbu, dasauri tajuya Ahmedyashigo aykuwa kyallen dake gefen kansa tajawotana dafa masa goshinsa , Ahmed yace sannu dakokari hjy, hjy tace yauwa Ahmed Allah yabasalfy ameen " dakin ta taje takira amina tace keayki zan saki akan mahaifinki, amina tace dadkuma dayake a kwance wani ayki za'a MarHjy tace inaso kisaka pillow ki ida mun shi,ma'ana ki karasa gawar, dasauri amina tajuyowhat? mamma anya zaki shiga aljanna kuwa?Wlh ko kiyashi bana iya kashe wa bare mutumkuma dad dina hava mama, hjy tace shikenanzancireki asahun yayana sann kisani babu nibanu ke " amina tafashe da kuka hava mamayazaki mun baki, ni nama fara zargin cewa kecekika hadda sa masa ciyonFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�5鈨�Hjy tace kwarai dagaske nice nan, amina tashigagirgiza mata kai tana kuka, hjy tabude wadroptajanyo mata wata doguwar riga tabata taceirinta joda tasaka kisaka irinta se dare idan kintabbatar da bata dakin sann kitabbatar waniyagan shigar ki kokuma fito warki adakin , umarnine ba shawara ba, amina taci kuka kamar rantazai fita daga gurin tafara nadamar kasancewayar hjyDare yayi su hafsa sunyi sallar isha itada joda,joda tawuce dakin Gwaggo hafsa ma tayi dakintadake gidan, amina dake labe tawuce harda hadajiki sukayi da hafsa, hafsa tace ke joda lfy wannsaurin haka , amina dataki juyowa tadaga matakai, sann tashige dakin,tadade tana kuka sann tace kayi hakuri dad wlhba laifi na bane hjy ce tasakani, tana kai nantadauko pillow ta aza masa aykuwa yafaraShure2 har dae yadena motsi tana ganin hakatafita aguje, ba'a Fi minti uku ba Sega jodatashigo dakin, pillow din datagani Akansa yabatamamaki hannun ta takai zata dauke Sega hafsatashigo , ido tazare sann tace joda mezan ganihakaJoda tace hafsa haka nasamesa wlh, hafsa tayoGunsa dasauri ta dafa girjinsa taji baya motsi,dasauri tajanyo joda tana dukanta joda tashigakwala ihu, macuciya azzalimi ki rasa dame zakisaka mana se wann " Ahmed yashigo dakindasauri , dakyar yasamu ya kwace joda a hannunhafsa, sann ya wanketa da mari, bakida hankaline zaki kasheta ne ma tayi miki, hafsa cikinmuryar kuka tace Ahmed! Ta kashe mana dad daidona nasameta tana danne sa da pillowAhmed yace what yajuyo gun joda yana jijjigatajoda tell me gaskiya ne abunda tace , joda kamkasa mgn tayi sema kukan datake yi, Ahmedyakwanketa da mari sann yayi ball da ita yajegun dad dinsu yaduba shi, ajiyar zuciya yayiganin akwai sauran rayuwa agunsa amma balallae bane ya tashi danko yayi nisa , Hjy daamina suka shigo dakin hjy tace lfy nake jinhayaniya, Ahmed yace bakomai, hafsa tace hjyjoda joda zata kashe mana dad , Ahmed yacedaga yau kar wanda yakara shigowa dakinsagwaggo itace zata cigaba da zama dashi harsatinsa uku su cika sa'annan muwuce EgyptdashiHjy tace gawar za'a zauna da ita, ? Ahmed yacebai mutuba daransa , hjy tace what? Ahmedkansa seda yajuyo yana kallonta sann ta basartace Alhmdllh bakar aniyarki ta biki, ana hakaSega Mahmud da abdallah sun shigo aykuwadasauri taje ta rungume abdallah tana son kaganjoda koh dayanxu ta kashe dad dinku , abdallahyace me, Mahmud kamar ya? nan ta zayyanemusu komai,abdallah yakalli joda yace joda yaushe kikacanza, Dan ya aura miki dansa bakyaso shinezakiyi kokarin kaisa lafira kin ban kunya,Mahmudyabanka mata harara yace butulu munafuka, jodataje dasauri tarike masa kafa hava ya Mahmudkafi kowa sanin waye ni wlh ahaka nasamesa,hafsa ta turata dakarfi tace karki sake taba munmiji tinda ke bakisan muhimmancin auren dayakekanki ba ........Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�6鈨�joda tace karku mun irin wann judge din wlhtallahi bani bace, abdallah yace kedai kika sani,ana haka Sega wani yadanna bell din parlorhafsa taje ta karbo sako envelop ne kamarhotuna ne aciki akace tabawa Ahmed, bata dubaba tabawa Ahmed yace menene joda tace cewaakayi nabaka, Ahmed yabude abunda yaganiyasaka shi shock dakyar yakai karshen hotunannoooo yafada acikin lion voice dinshi yacakumowuyan joda idonsa jajir ya dinga buga kantadabango dakyar Mahmud da abdallah suka kwachetaHotu nan suka dauko suna dubawa innalillahiwa'inna ilai'hir raji'un naji sun fada Mahmud yaceI hate you joda I hate you, abdallah yace I hateyou too, hafsa ma data gan hotunan tace hateyou again fasiqa kawai, dakyar tadaga hannuntatajanyo daya daga cikin hotunan, hotonta ne tanasanye da towel hannunta ajikin wani kato bakyangani, Ahmed yace me wann gardin yafini da shimiye amfanin......hawaye nagani suna kwarara aidon Ahmed abunda bantaba ganibaHafsa tace wlh wlh bazaki kara kwana agidannba ke koma abakin gate dinn kika sake lekowasena saka anmiki Dan banzan Duka, hafsa taceoya Ahmed kasaketa kuma uku, Ahmed ya girgizakanshi am sorry hafsa amma babu saki acikinaurenmu, sedai kuma kisani yanuna jodabanyarda da wann cikin ba kije kinemo ubansa,joda ko motsi batayi gata nan dae hakahafsa tajata tafita da ita har gate tamata korararKare amina abun duniya ya isheta, tasan wannma makircin uwarta da mansura ne " gwaggobakaramun tashin hankali tashiga ba tayi kukakamar me lokacin dataji lbrn hafsa tace gwaggokina nan amatsayin uwarmu kanwarmahaifiyarmu baxamu kikiba Dan yarki tamanalaifi gwaggo kam da bataga hotunan ba Sambaxata yarda ba,Daga ranar rayuwar joda ta lalace, haka zatayi tazuwa gidan hafsa kullum tin safe har mareceamma baza'a barta shiga ba tayi sintirin zuwagurin Mahmud shima ko kallonta bayayi khalthumma ta guje ta, gwaggo tace bata son ganinta "amina ce kawai yarinyar datake jin sanyi agurinta tana taimaka wa joda batareda sanin kowaba,dad yafara samun sauki saboda yanda gwaggoke kula dashi har yafara bude bakinsa dakanshi ,mansura tafito daga wanka Sega joda tafitoitama rike da cup ta tsiyayo vita milkmansura ta kwace ta zubar, sann tace baki isakici abun dadi ina agidann ba ana haka SegaAhmed yaxo, tsawa yadaka wa joda, ke Danubanki banga ya miki cewa idan nakara ganinki aparlor dinn sena karya kiba, joda tajuya cikedakwalla tashige dakinta tafada kan gado tanakuka, kwana take sallah yini take sallah tanakaiwa Allah kukanta akan wann ibtila'in dayasameta......Muje zuwaASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄9/29/16, 12:32 AM - Queen Safiyyert馃憫: FULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�7鈨�Kwanakin sunja , watanni sun tafi cikin jodayagirma wata takwas wanda yayi girma kamaryan hudu ne aciki dakyar take tashi, joda duktafita hayyacinta, gwaggo kuwa itake cigaba dakula da dad wanda sukayi 2month Egypt baijisauki ba dole suka hakura suka dawo gida , hjykam tafita har kasa se sha'aninta take , aminakuwa kullum adakin take wuni sekuka takegwaggo zatayi ta lallashinta har tayi shiruKhalthum nagani da abdallah sun fito supermarket sunyo siyayya, kai daganinsu kagamasoya, joda zaune a parlor tafito daure dazanise vest saboda duka rigunanta sunyi mata kadan,agwaluma take sha tana hawaye, Ahmed yayisallama amma Sam bata jiba, ido yabita dasu dukdamuwa datake ciki bata hanata yin kyau bacikin ya karbeta sosae, wani abu yaji lokacindaya kae dubansa ga boobs dinta wanda sukakara girma da tsayi , kamshin turarensa tajihakan yabata tabbacin shine tana juyowa yayisauri yakauda kansa , dakyar da cizon lips tadaga tana ta nishi daki ran wai waiGabansa taci sann tace zanje hospital anjima2dyz danka baya motsi, mari yawanke ta dashi,kana yace so nawa zangaya miki cewa kidenadan ganta danki da jinina , to bara kiji tin wuri kisake tunani kije kinemo ubansa Dan wlh baxanmasa suna ba, joda tadaga kafada tace it's of toyou, zamana agidann saboda nareni abundakecikina ne kasani bantaba son abunda ke cikinabakasancewar sa jininka, saboda bana sonka, inahaife shi zan bar maka shi sann inyi tafi yatabaxaku sake ganina baZakiyi nemana ko da a mafarki ne saboda kubanisedai lokaci yakure muku, tana kai nan ta juyatawuce har tabude dakinta sekuma tajuyo, taceAhmed! abunda bantaba jiba joda takira sunanAhmed, wlh wlh jininka ne danka ne ko yarka,ban yiwa dad din hafsa komai, hannu tadagasama tace ya rabbi kada ka karbi rayuwa ta bakanuna mun wanda yakulla mun wann sharrin ba,ya Allah kada ka karbi rayuwa ta baka nuna munnadamar wadann bayi na kaba wadanda kasa tarufe ma ido suka manta waye joda suka mantakyawawan halayenta suka manta dacewa bincikeshine gaba before a yanke hukunciJikin Ahmed yayi matukar sanyi, yarasa mawanne tunanin zaiyi, dakinsa yaje yakwanta kangado ya dubi sama, ya Allah ka dora ni akangaskiya nakasa yarda dakaina tin randa abun yafaru nakasa yarda 100% sedai kuma bazan iyamanta wann muna nan hotunan nata ba........FULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�8鈨�A asibity suka hadu da amina atare suka shigatayi matukar mamaki ganin doctor dinta yabatahakuri akan cewa yayi tafiya sann suka dawofada akan yaushe tayi aure har ta haihu, jodatace wann yanada tsawo gaskiya yanxun dae kaduba ni babyn baya motsi, doctor yace ammayanaga cikin kato kodai twins ne?Joda tace eh haka suka ce nima kuma cikinyanamun nauyi kuma suna wahaladda ni da yawanmotsi, haka dae yaduba ta yabata magani sannyace haihuwar ta nakusa fist month tazo asibityhaka suka dawo gida amina tawuce gidansu tunitacire wa rayuwar ta duk wata damuwa sedaiabunda ba'a rasaba sann tadena daukar raininmansura da Ahmed duk abunda suke matarawawa suke,amina ce ke kwantar mata da hankali sann taceinsha Allah tamata al qawarin cewa zata fallasaasirin wadanda suka mata sharrin dazaran tahaihu , shi isa tarage wa kanta tunani abunaranta , aranta kuwa tana mamakin yanda aminata sauya lokaci guda, kamar va itaba kullumsetayi wa joda kuka tana neman ta kafara, jodatace ay ko jiya kin roka kuma nace nayafe mikiBayan yan kwanaki, Ahmed yatara taron gidan daduk wani family na gidan , ciki harda gwaggo,Ahmed yayi gyaran murya yace dalilin tara kuanan shine, ina son sanin inda ake shiga da kudindad, abdallah yace yauwa bro nima abun nacimun tuwo a kwarya, hjy tabuga tsaki to mekukenufi sata akeyi kenan,Ahmed yace yes dole afito da kudinsa danko korabin dukiyar sa babu sann naga wasu takarduyasaka hannu da sunan hjy taya zai mallakamikiduk wann dukiyar bayan yanada yaya da yanuwa, hjy tace kai Ahmed bansan zancen banza 'abdallah kanaji ana gayamun magana baxaka yiwani abu baAbdallah yace mezanyi bayan gaskiya yake fada,hjy tace wlh kar ka sake mun wann zancentakardu dae yacika yabani kuma babu wanda yaisa yatada zancen, Ahmed yadaka mata tsawakarya ne wlh, I have free speech in diz house,dole kiyi bayani, abdallah kam yakasa mgn dukdayaji zafin tsawar da Ahmed yayi wa mahaifiyarsaMurya sukaji daga sama nacewa photo copy neoriginal na hannu na, kowa yazare ido hafsakam Dagudu tayi hanyar waje Ahmed yace dadar u? Dad yace yess kowa yaxauna nine nandaddinku, amma baxan zauna ba se ankira jodadamansura, hafsa tace no dad bakasan abunda tayibane, dad yadaga mata hannu kar wanda yasakemagana akira mun joda kawai dz my order .Ahmed yamike jiki a sanyaye yaje gidan, dakyaryashiga dakin joda, dukda tayi mamakin ganinsaamma seta basar tayi tamkar bata gansa baAhmed yace kishirya muje gida dad na songaninki joda tamasa banxa seda yakara maganasann tace wanda yamutu yana dawowa ne bayannakashesa, Ahmed yace kitashi nace kafun rankiyabaci, joda tace wlh ba inda zanje, Ahmedyafidda wayarshi yakira abdallah yace yabasadad, ya gayamasa tace bazata zoba , dad yaceabata wayar, Ahmed yace ungo gashi badantasoba ta karba , dad yace kiyi hakuri joda kimunda'a kizo, joda tace shikenan dad zanzo Allahyasa inji alkhairi ameen.........9/29/16, 12:34 AM - Queen Safiyyert馃憫: FULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�0鈨�9鈨�Mansura kam tace bazata jeba sekace waddatayi sata , Ahmed yace wlh zanci ubanki zaki fitokosae na karyaki, dole sae dataga dagaske yaketadauko mayafinta suka je, joda baya tashiga Danbata iya zama agaba , kwance tayi hancin taarufe bata san warin tiraren mansura, mansuratace tokuma ubanwa kike rufewa hanci ?Joda tabuga tsaki tsaki tace uban da yatanka ,mansura tace ni kike zagi, ? Joda tace Y notkifara nikuma naqi ramawa tinda ba tsoron ki nakeba, mansura tace dallah rufe mun baki, fasiqakawai, joda tace Alhmdllh ni dana tashifasiqancin da mijina nayi sann ba'a taba kamanida kato ba, mijina a budurwa ta yasame ni, bakutaba sanin ni fasiqa bace seda nadauki ciki,kuna bakin ciki dani saboda ke taki mahaifar tamutu saboda yagaji da daukar ciki ana zubarwaAhmed yataka burki dakarfi ya isheku yazakucikani da surutu , tsaki yabuga sann yaci gaba dadriving.suna isa kowa ta bude kofa tafita har cikin parlorsuka shiga joda taki kallon kowa tayiwa kantaguri daban nesa dakowa tazauna, amina taxotazauna a tareda da ita kowa yabita da kallobarinma da akaga ta kawo mata vita milk taceantynmu maman baby gashi joda tace tancuu, takarba tana sha , dad yayi gyaran murya sannyace Ahmed! Abdallah! Amina! Hafsa! Mahmud!Gwaggo!Duka ina hankalinku yaje lokacin dakukawulakanta joda agidann shin kun manta cewajoda itace silar shiruwar abdallah, shin kun mantakunya da kawai ci irin na joda, ko kuwa dacanjoda tana bibiyar gardi ne " waya gaya mukucewa tana iya kashe koda kiyashi bare mutum ayhankalin ku alkalinku , Ahmed yace wait dadbantari nun fashinka ba ya akai kasan wann? Dadyayi murmushi yace duk abunda kuke akan idonada hankalina ina jinku ina ganinku nadade dajinsauki amma na boye lafiyata ne domin in ganomasoya na agidan sann in gano wadanda sukayiwann aykinba joda bace taso kasheni ba, sedai bansankowace ce ba , alokacin, hjy kisani duk abunda kikekirika tuna wa da Allah b4 bisa wann baxan tonaas irinki ba agaban yayanki amma na sakekisakibiyu, naki yin uku ne saboda anyi hani da hakan ,amina tafashe da kuka ha kika ranar wanka ba'aboyon cibi , nan tazayyane musu duk yanda akayiharda makircin da uwarta ke hadawa , hjy damansura zufa tashiga karye musu,Wayar Ahmed tayi kara yaduba yaga ansakadoctor habib yana dagawa yace sir zancen matarka gaskiya bazata iya daukar cikiba sabodamahaifar ta mutu sann tana da ciyon sanyi daciyon daji wanda yake lalata al'aurar Dan Adam ,wann yaron dasuka zo inaga kamar agaresanetakwasa saboda yanda saka makon yanuna,wanigardi ne yashigo gidan aguje yana haki yafadi acapet yana Dan Allah ina joda kimun raikiyafemun tin randa , hotunan sukazo gidannnakasa barciSe mafarki nake zaki kasheni keda abunda yakecikin ki, abdallah yace kai shut up waya bakaizinin shigowa nan dakin, kuma miye hadin ka dajoda? Gardin yace nine wanda aka mana hoto daita lokacin tafito wanka sena sheka mata powdertayi bacci shine nadora hannunta a jikina akamana hoto , abdallah yace waya turoka kayihaka? Dasauri ya dubi mansura wadda jikinta kebari yace wann ce, Ahmed yayi tsalle yaka mosaya dinga dukansa kamar zai kashe sa, why ar uruning my mrrg , seda yafarfasa masa baki da jiki, babu wanda yayi kudurin rabasu yanda zuciyarAhmed yabaci hau kam kowa yana iya hallakawa,hannuwan sa biyu da kafarsa babu wanda baifasa ba haka ya dinga zubar masa da hakorasann yakoma kan mansura seda dad yamasarantsuwaA hankali Joda tamike tsaye tace toh hafsa se akiyaye gaba bincike shine gaba kafun hukunci, adena manta halin baya, Mahmud da abdallah Ihate u too kamar yanda kuka ce, sann ta juya gagwaggo, tace shikenan saboda wani yaki dananima sena manta tarbiyar dana basa, AhmedAlhmdllh da Allah ya bay yana komai banamurnar ku karbeni ko ku yarda dani fatana kawaikusan danku ne aciki na hakama ban iya kisa ba,tana kai nan ta juya zata fita hafsa tace havajoda ki tsaya mu fahimci Juna mana, joda tacealokacin dakuka watsar dani kun kasa tsayawaku fahimceni so babu wann damar aguna, hafsatace plss joda kiyi hakuriJoda tajuyo da karfi zatayi magana seta kasasakamakon murdawar da marar ta tayi, ihu tasakitafadi akasa........Muje zuwaASEEYAH BASHEER ALEEYULike 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�1鈨�0鈨�Ahmed yafito da gudu ya tallabi joda waddataketa bleeding kamar ruwan fampo, Ahmed dukyarude se kiran dana yake hafsa da amina sukakarbeta abdallah yafidda mota Mahmud yajasukayi asibity , kusan likita yakai biyar akantaciki harda Ahmed, firr yaki yarda Mahmudyashiga aciki saboda tsabar kishi, kusan awa ukuamma takasa haihuwa , Ahmed kam duk yazamawani iri dashi yazauce, doctor habib ya fito yacedoctor Ahmed yarinyar nan fah takasa haihuwasaboda batada wani sukuni dole anmata aykidasauri Ahmed yace ok bani file din nasakahannuKarfe 3 dae2 aka shiga da ita operation room,anhada komai za'a mata aykin Ahmed na gunkanta yarike hanunta yana topa mata addua,aykuwa segata tayi wani yunkuri danta yafado dasauri Ahmed yaje yatarbe Dan bai daga ba Segadaya yafado tareda komai da komai, Ahmed yayihamdala ga Allah yamika yayan gurin nurses dinsu gyara su, yakoma kan joda dinki aka mata akabata allurai da magani tasha tea sann aka hadamata ruwan wanka , amma kash dayan yaronyakoma dama baifi 20 minutes ba yamutu, doctorhabib yace bata samun kulawa lokacin datake daciki komai ci take gakuma damuwa tamata yawa,Su gwaggo da hafsa tareda abdallah da Mahmudsun shigo dakin joda na gaisawa da hafsa tanaganin su takauda kanta gefe hafsa da kwallayagama cika mata ido " tajanyo hannun jodazatayi mgn, dasauri joda tafizge hnnunta sanntace karki sake tabani, nasanki ne? Mahmud yacehava joda kaddara ce fa tariga fata, joda taceshhhhh badakai nake mgn ba gaba danku kufitabana son ganinku, amina tace joda hardagwaggon taki, cike da bacin rai tace ehh haritalokacin da aka wulakantani harda ita kufitanaceeeeeeDole kowa yafito yabata guri, abdallah yace plssjoda ki saurarenmu, joda tace ok ni zan fita inbaku gurin, Ahmed dake gefe yayi tagumi yarasamezai ce mata ga babyn se kuka yake amma kokallansa taki tayi, a hankali takoma kwancetamkar tayi bacci, Ahmed yace kowa yafito, ruwane kadai ake bawa yaron , joda kuwa tana Jinshiru ta mike zaune tacire drip din da aka sakamata duk ta yamutse dakin bataga metake nemaba, can idonta yasauka kan wani file da hanzaritaje tabude takuwa yi sa'a akwai biro aciki ataketafara rubutuFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�1鈨�1鈨� Gida suka koma aka bar abdallah da Mahmudkhalthum ma dole tayi gida saboda yanda jodatanuna tamkar bata santa ba, Ahmed yadawotareda amina tana rike da yaron bayan an basamadara, dakin ta yagani abude, yace wa abdallahwani doctor ne aciki? Abdallah yace bansanibamuna masallaci yanxu muka fito , Ahmed yaceok bara na duba, dakin yashiga yaga wayambakowa kuma duk an hargitse dakin, yadubatoilet bata nan, tuni hankalin sa yatashiIdonsa yafada kan guntuwar takarda dasauriyadauko yana karantawa, ga abunda yagani""""""Alhmdllh da Allah yabbayana mun gaskiyada raina, saboda haka zan tafi bazaku sakeganina ba, zama da mugun miji irinka hasara ne "yanda ka tsaneni haka nima na tsane ka banasonka ko kadan, ga yayanka nan Allah yaraya su" kasani bana bukatar koda yansu yanda kakekina haka nake kin yayanka " Sai watarana" hakakalmar tadinga masa yawo akai, ihu yabugatareda jodaaaaa , plss karki tafi kibarniI can't live without you, you are my soul, my lifeis in complete without you joda I love you I loveyou so so much beyond your imagine. abdallahyashigo dakin aguje yatallabo , Ahmed yacewhybruhh mekake yiwa kuka haka? Ahmed yamikamasa takardar, abdallah yace shittt, Ahmed yaceplss abdallah help kane momin joda, abdallahyace relax bruhh indae tana a duniyar nan ko inane wlh kamar mun sameta ne " amma aybaikamata soja kamarka ace kana yiwa macekuka ba tin bayan rasuwar umma bantaba ganinhawayenka ba se akan jodaAhmed yace baxaka gane bane joda meansa lotto me world can not express how I fell about her,Iove her with all my heart, abdallah yace kayikuskure daka maida so kiyayy, ana haka SegaMahmud shima bakaramun rudu yashiga ba,Ahmed kam yakasa tsayuwa , abdallah yacekaragayawa gwaggo abun zai mata yawa yanxun matana cikin damuwakawai asaka nemanta tin yanxu, kowannensuyafigi mota yabar asibityn Ahmed kuwa yazamakamar tababbe , Karfe 5 tayi yaga basu dawo ba,shima yafigi mota yabar asibityn har baima saninda yadosa ba baikuma tsaya tambayar kowa ba, yakai wani babban titi ne anan wata motatabigesa atake tasa motar ta gangara jama'asuka kaimasa dokin gaggawaWayarshi dake ring aka dauka abdallah ne yakirashi, wani mutum yadauka yayi masa bayani,abdallah yace ya salam ashe ma yana gurintaron daya taresa kenan dakyar ya kutsa acikinmutane ya samu wani yakama masa Ahmed sukasaka shi a mota akayi asibity dashi..........Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�1鈨�2鈨�Anyi sa'a bai samu wani rauni ba sedan ciyodayaji a hannun sa, yana farkawa yafara kiranjoda, dad ina joda na, Dan Allah kace tadawo dadkane momin joda in ne mata gafara, dad yadafakansa I'm sorry son joda zata dawo wasa takemaka, Ahmed yace hakane gwaggo?Gwaggo da hawaye yagama wanke mata fuskatace ehh ka santa dason wasa , ita kam ba bataryarta yada meta ba halin da Ahmed yashigasannga yaron ta tabarsa, Ahmed yaki cin komai yacedole se joda tadawo zasuci tare jifa jifa zakijiyace joda tadade sena mata duka idan tadawo ,abdallah da Mahmud suka shigo dakin duk sunyigumi sun wani iri dasuDa gudu hafsa taje ta rungume Mahmud tanakuka ya Mahmud ba'a ganta ba koh? Mahmudyace kiyi hakuri za'a ganta insha Allah, Ahmedyace ay wasa take yanxun zata dawo xua 10,seda kowa ya zubar masa da kwalla yandaAhmed yake da taurin zuciya bako wane abuyake daga masa hankali ba bare ma har yayikuka, babynsa yaduba yace you koh " kainekabawa matata wahala har tayi fushi tafita Allahidan tayi fushi dayawa zan baka punishmenttsallen kwado zakayi,Abdallah kam fita yayi Dan bazai iya kallon halinda Dan uwansa yake ciki ba, hafsa kam ancikuka kamar me, hakama khalthum abun dukyamaidata gata nan dae, Karfe goma na bugawaAhmed yace yeeee 馃槄 my cweet joda yanxuxata dawo aykuwa yayi tagumi yana kallon kofahar 10:30yana jin anbude ganbu yace oyoyo joda ta.amma me dad yagani tuni yabata fuska yafasheda kuka dad kace xata dawo kuma taki dawowakodae bazata dawo bane? Iye kuka yasaka musutamkar karamun yaro se lallashinsa ake ammakamar baya jinsu joda kadae yake kiraYau kusan kwana hudu ba inda ba'a saka nemanjoda ba, a ranar data bata seda Mahmud yasakaaka rufe kowace ta shar garin amma komaisunan joda basu samu ba , joda kam tana fita tanemi adaidaita tashiga se wata unguwa waddabatasan ko ina neba , tana zaune tana tunanininda zataje kamar a mafarki taga hansai na Janmota aykuwa aguje taje ta na kwala mata kira ,hansai tajuyo bazata taba manta wann muryarba, dasauri suka rungume Juna suna mamakibasu tsaya dogon zance ba, suka shiga mota segidan hansai, joda kam tace abata ruwan zafi tayiwanka tacanza kaya, sann tace hansai bani lbr ?Hansai tayi murmushi tace kamar yanda kuka bardaji muma haka muka bar gurin bayan mun fito agari se wani bawan Allah yakadeni da motaYakaimu asibity ana kula dani kasancewarnasamu kariya akafa seda muka kae kusan watadaya, daga nan muka je gidansa Allah sarkimatarsa da yayan sa masu kirki basu kyamacemu ba lokacin da sukaji waye mu, daga nanmuka cigaba da zama agidan muna tayasu ayki,yarda rufaida tanada kirki hakama dansa najibsannu sannu muka saba har yasakani islamiyyanafara shawa'ar boko dansa ne yasakaniin takai cemiki dae yanxu dansa najib nake aure,joda tace wow lbrn kamar nawa itama tabatanata lbrn ,hansai tace kamm amma joda kinga jarabawa wai yanxun kinada danyen jego ne lallaekuwa zan gasaki da ruwan zafi, joda tacekaniyarki hansai, hansai tace kullll kar in kara Jinwann sunan sedai kije deejerh kokuma Arabkamar yanda najib yake kirana da kanwarsa rufeemai kyau kema daga yau zainab kokuma zeebaby, babyn Ahmed, joda tace Allah sauwakemun dawani can.........Muje zuwaASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�1鈨�3鈨�Deejerh hansai tasaka mai mata ayki wato babarabi kula da joda komai itake mata wankan jegodasauran abunda yakamata mai haihuwa tayi,amma aranta tace dole na nemo su gwaggo kobakomai saboda danmu data bari ba mama alhalinuwarsa nada rai, gwaggo kanta boyewa takeamma damuwa ce fal aranta,Ahmed kuwa hauka hauka yaka mashi bayadaabun fada se joda anyi cigiya agidajen radiodaTV amma shiru, yau har anyi sunan yaro ansakamasa abbakar sadeeq, tareda auren gwaggo dadad wanda su abdallah da Ahmed suka rokigwaggo akan ta amunce ta auri dad dinsu , damakuwa naga suna kallon Lol.....Joda taci ko sosae tayi kiba boobs sun cikarigatam, gasu se tsiya ya su ke mata kamar me,yautafito parlor suna breakfast harda najeeb mijindeejerh, Sega breaking news anayi, ansaka hotonjoda akan 1 million akan duk Wanda yasamota,Ahmed aka nuno yana kuka yayi baki yarame duksuma tacika masa fuska acikin 10dyz kadai, cikeda nutsuwa yake zancen plss joda nasan nacuceki kiyafemun ki dawo agareni rayuwa babuke tamkar kifi ne aruwa,wlh nayi nadama zan bauta miki keda soyyr kimatukar xaki dawo agareni joda kin tafi kin bardanki gashi zai mutu baya shan madara, ananaka nuno yaron sekuka yake, hansai deejerhtacewoww najeeb kagan wani beau boi, Ahmed kukayake sosa please joda nasan kina jina dik indakike ki dawo gareni plss sekuma yafashe dakuka, tuni jikin ta yayi sanyi yanda taga yaron nakukaatake taji kaunarsa fiyeda tunanin masu tunaniarantaHansai deejerh tayi sauri tadauki number dinbatareda joda tagani ba , tana shiga daki takiranumber din Mahmud ne tamasa kwatancen indatake tace tanada information akan zancen batanjoda aykuwa dasauri Mahmud yace ya rubutaaddress din dankuwa tin randa tabata ko wandayaganta basu samu ba se yauAbdallah yakira sukaje har gidan, dama najib neyabada wann shawarar, har dakinsa suke sungaisa sann yakira hansai deejerh, Mahmud yacekamm hansai mai shinkafa ce ta goge haka,najibyace kuttt inkara jin hansai bare shinkafa,gabadai suka sa dariya. nan dae tabasu lbrnkomai,Abdallah yace wai yanxu joda tana agidann ne "deejerh tace sosae yanxu yanda za'ayi kuje kuzoda Ahmed da boi din karku da kowa, anan dakinzan ce taje ta dauko mun wani abu kaga daganan se yayi mata mgn Cox bana tunanin zatasaurareku bare shi, Mahmud yace right braindinki naja fahHaka kuwa akayi Ahmed nata kiran ina zakukainiamma suka masa banza seda aka kai gidansannsuka ce joda na ciki ka nutsu ka san yanda zakashawo kanta nasan kai smart guy ne " Ahmedyace ar u serious? Abdallah yace wlh bruhh aybaza mu maka karya ba, Ahmed yace shine kumabaku bari nayi wanka na shirya ba ahaka xan jegurin matata a hargitse, Mahmud yace yaragenaka inzaka je kaje inkuma epixy zaka yi tohyarage naka9/29/16, 12:40 AM - Queen Safiyyert馃憫: FULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�1鈨�4鈨�Dasauri Ahmed yabude ganbun motar zai rufe neyadatse kafarsa, seda yasaka kara Ahhhh.....abdallah yace kayi a hankali karka halaka fah ,Mahmud ya girgiza kanshi yace wann yarinyar taiya judging Sam banza ta xata iya haka ba,abdallah nima wlh mamaki nake yanda braindinta yabata wann abin amma fah gara datamasa haka koba komai yanxu xata karbi yancintaHar dakin suka kaisa sann suka fito yanarungume sa sadeeq dinshi, najib yazo suka gaisayace bara ya izo masa joda din. tana zaune tanashan kunun masu jego Sega deejerh tashigo tacejoda danxo plss dakin najib ungo wann key din kirufe mun kofar, joda tace naki xua ni kanwarki cedazaki ay keni , deejerh tace shikenan karki Jedin . joda tabuga tsaki bani key din kawai mutumnaxamansa dole se an tada shiDakin taje kanta ko Dan kwali babu zata rufekofar taji wani irin sanyi yafara ratsa ta sekumataji takasa tafiya kam shin Ahmed takeji ta koina a hankali ta tura ganbun ta leka bayansakawai taga ni se babyn su dayake rungumeakafadansa das das tashiga dakin tana son ganinko waye,Ahmed yaji sanyi nashigarsa hakan yatabbarmasa da joda na gurin a hankali yajuyo fuskarsafauke da hawaye, yace joda plss karki kara tafiyaki barni plss joda tace waya kawoka ananmekazo yi anan kazo ne kasake wulakanta nimekake da fasiqa jahila kazama kucaka yardaji,sekuma tafashe da kuka , Ahmed yace plss jodaki bani lokacinki koda na 15 mnt ne in mikibayani Dan soyy dake tsakanin ki da manzonrahma s w aJoda tace shikenan amma wlh Dan ka sokomunfiyayyen halitta ne " Ahmed yace nagode plss kizauna , joda tazauna Ahmed yashimfide sadeeqsaboda yayi bacci, dukawa yayi yarike kafafunta. yace joda Dan girman Allah kiyafemun dukkanabunda namiki, kewai da kin dauka kiyayyar kitasa hakan wlh so ne kurum , tin randa nadoraidona a kanki a daji kina busa sarewa bansakegane kaina batin a ranar nake jin inada felenz sosae akan kibankara tabbatar da hakan ba seda randa nadauko ki aruwa daga ranar komai yacanzanakasa gane so da kiyayya ne dalilin dayasakikaga ina miki wasu ababen amma plss on mykneel. Joda tayi tsaki tace dt x invalid excusebazaka mun zakin baki ba saboda matar da kaketinkaho da ita kaga no ko wacece, Ahmed yace Isure you not agree with me, buh believe me wlh Ilove you bantaba gayawa kowace mace haka bakece fist nd lastJoda tace I can't believe how much you love me,Ahmed yace why joda? Tace coz I never like you. Ahmed yace you layer, joda tace dakarfi tacekaikuma maudari ne Ahmed yace shikenan idanzuciyata karya take bakina seya kasance maikarya? Idan bakina yakasance mai karya idonabazasu miki karya ba joda luk into my eyes ,jodataki kallon saAhmed yadago fuskarta suna kallon Juna dasauritakauda idonta, Ahmed yace mekika gani aciki,joda tace plss n plss katafi Dan Allah , Ahmedyace it's alright am living amma kisani I loveyou. sann ni I have nothing more to say , all mywords end amma kisani danki yanada hakkiakanki bai miki laifin komai ba kika gujesa alokacin dayafi bukatar ki " Allah bazai barkiba.........Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�1鈨�6鈨�Yana kai nan yajuya zai yafita tareda daukarsadeeq, joda tace Ahmed! yatsaya cak bataredaya juyoba gabansa ta tsaya batace komai ba sekallonsa take a hankali taduka tarike masa kafainda taga jini na zuba, rigar dake jikinta ta yagota daure masa kafar sekuma tajuya tabar dakin,Ahmed yagirgixa kai yafita, dasauri suka taresaMahmud ya karbi sadeeq yasaka shi a motaabdallah yace yade? Zata fito ne "Ahmed yagirgixa kansa yace no shez waz besideher self with anger, abdallah yace muje nasanabunda zanyi , ciki yashiga deejerh tamasa isohar dakin da joda take kwance take se kukatake, abdallah yace kisani gwaggo batada lfysann ciyonta yayi tsanani batada abun ambatose jodaJoda ki kiyaye fushin mahaifiyarki da mijinkisannkiguji Hakkin danki .yana kai nan yafita, amotayasame su, Ahmed yace me kace mata ne?Abdallah yace kajira ta xua gobe zata xo, Ahmedyace to Allah yasa su kace ameen joda kamkasa komai tayi sekuka take taki cin kowaniabunci ,deejerh tasata agaba se nasiha take mata tacejoda tinda dae kinga yayi nadama yabaki hakuriyaduka miki yaka mata komai yawuce sann idanbakiyi hakuri ba wlh zakiga bakyau samun mijikamar Ahmed yanada wuya, yarigada yaganekuskuren sa yanxun atafin hannunki yake seyanda kikayi dashi, kihakura da yanda rayuwatazo miki ki gode AllahDakyar tasamu joda ta amunce akan zata komagida gobe shima din seda najib yasaka baki,tinsafe deejerh tagama hada musu komai, bayantayi wankan jego tasha kunun masu jego tashiryacikin wata atampa black and white se karamunhijab dinta , tareda najib sukaje har gidan, dakinGwaggo tawuce amma setaga wayam bakowadasauri tafito tayi parloranan tasame gwaggo kan kujera amina naajikinta tana mata tsifa, dasauri amina taxo tarungume joda, gwaggo tace wa zan gani kamarhansai? Deejerh tace nidin ce gwaggo ya bayanrabuwa, gwaggo tace Alhmdllh bismillah ku shigoanan take bata lbrn yanada akayi tasamu joda ,gwaggo tamata godiya sosae sann tace jodaangama fushi damu, joda tadukadda kanta kasabatace komai baHafsa ce tayi sallama dasauri joda tadaure fuska, hafsa tace baxamu gajiba da neman gafara,Dan Allah Dan Dan darajar fiyayyen halittakiyafemana kiyafewa ya yanxu ki dubi zumuncinmu, joda tabuga tsaki takalli gwaggo tacegwaggo yanaga kinkoma hjy dake haka, aminatace ay bakisan yanxun gwaggo itace matardadba, joda tazare ido ke bari wasa, amina tacewlhrana daya akayi da sunan sadeeq,Joda tayi murmushi aranta kuwa tace Alhmdllh,gwaggo tace joda ina neman wata alfarma dayaagurin ki, joda tace hava gwaggo ni har akwaiabunda zaki nema agurina ki kaddara harkinsamu ne " gwaggo tace yauwa yata Dan AllahDan Allah kiyi hakuri kidauki komai a matsayinkaddara ki yafewa kowa sann ki karbi danki kiyarda da mijinki, murya sukaji daga sama anasaukowa dad ne shima yace plss joda, joda kamhawaye yashiga sintiri a fuskarta dakyar ta iyafurta shikenan dad zan koma........Muje zuwaASEEYAH BASHEER ALEEYU 馃挄Like 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�1鈨�7鈨�Sadeeq hannun joda tagama basa nono yaronsewani like mata yake, tacewa amina ke karbidanku wlh ko nayi ball dashi, amina tace tavv wlhkuwa dana cire miki kafa yarinya ana haka SegaAhmed yashigo dakin amina tafita tabasu guri,joda kam yitayi tamkar bata gansa ba , agabansata kwabe kayan jikinta which menz kenan batama san dashi ba, Ahmed yayi matukar mamakiwadda koda vest bata bari yaganta amma yanxungata tana kwabe kaya agabansaToilet tashiga tafi kusan 40 mnt sann tafitowayyo Ahmed har yafara bacci sann tayisallah taci abinci duk yana a gurin, nightweartasaka ta kashe light din dakin tabi lafiyar gadofirgigit Ahmed yafarka daga bacci, mezai ganiwai har tayi shirin bacci, Ahmed yace joda jodatamasa banza gurinki fah nazo amma zakishareniWayarshi tayi ring yadauka tareda fadan hellobae yakk 2dyz wlh nayi missing dinki, kinko sanyanda nake sonki hava yazarce misali babu wataya mace aduniya danake so tamkar ki, jodatazaburo dakarfi takwace wayar ta dora akunneke tamba daddiya kwartuwa mai bin maza, to wlhI nagaya miki kinesantar dakanki daga alkaryarsoyy ta zuciyar mijina bakowa acikinta se nitunina rufe ta da babban kwado, sann najefashiacikin babban kogi bakida yanda zakiyi ki gansama bare ki dauko har ki bude ki shiga acikinharam tacciyar zuciyar saTsaki tabuga tajefa wayar agina, se huci take,Ahmed yace ashe bakiyi bacci ba, haka kikedakishi tabb gara kirage danni mijin mace hudu ne "joda tace wlh baka isaba wadda ma kake aurenyanxu sekayi waje road da ita zan zauna dakai ,Ahmed yace a iya sanina wanda kake so shikake kishi kina sona ne ? Joda tace tirrrr dainsoka wlh Ahmed karya kike sona kike kamarzaki mutu dubi sona danye akwayar idon kidasauri joda tadena kallon sa, wlh kayi karya nibana sonka, Ahmed yajuyo ta dakarfi bakin shikawai taji anata seda nunfashinta yakusadaukewa sann yasaketa yaturata agado takecare. yajuya yabarta agurinKwanci tashi yau joda har ancika arba'in hjybintada maman khalthum sun sata agaba se batakayan mata suke tasha gyara kam kamar me,Ahmed kam yaga wulakanci kala kala a gurintahar yayi alkawarin bazai kara koma wa a gurintaba, musamman data gaya masa bata sonsadoctor dinta take so " kwance take tana kallonkunshin da aka mata yayi matukar kyau itadakhalthum kasancewar za'ayi bikin khalthum daabdallah,tuni suka fara shiri hafsa, joda amina khalthum,Sallama akayi dasauri ta mike tsaye ganin doctora gabanta, joda tace mekazo yi anan randaabubuwa sukayi mun tsanani ina kashiga? Doctoryace karkice haka joda abbanmu ne bashida lfymunje outside gurin treatment dinshiJoda tace ok naji yanxun mekazo yine? Doctoryayi gyaran murya yace nazo ne in kashe mikiaure sann na aure ki!!!!!!! Joda tazaro ido whataurena kuma meyasa? Doctor yace saboda bkyasonsa nikike so kuma baxan bari kicutu ba nagajidaganinki a wahala, joda tace Allah sarki sedailokaci yakure mika wahala takare mun tindamijina nasona sann kuma nima ina sonsa fiyedazatoka.......FULANIN DAJI N@ B Aleeyu 馃挄 page1鈨�1鈨�8鈨�what kina sonsa? Joda tace yes, yace ammabaki taba gaya masa ba koh? Joda tace ehhinatunanin gaya masa ne idan nazauna dashi nagakomai normal . yace nikuma nawa son yazakiyidashi? Joda tace zanyi kokarin ganin na kaudashi in fuskanci na mijina, kafadunta yarike karyane joda sona yafi na Ahmed tasiri azuciyarki ,joda tace ko kadan naka daban nasa daban,nahada jini dashi sann kuma jinina ne tagefenzumunta, doctor yace na lie kokin manta jininjikina ke yawo a jikinki ne? Joda tace ban mantaba Allah zai baka wadda yafini insha Allah wishyou all the best, yace alright shikenan zan wuceamma kafun nan yau zan bude miki fuskata kiganni yanda ko a mafarki zaki iya she da niJuyawa yayi yacire face mark. joda kam duktakagu yajuyo barinma dataji sanyi na ratsa ta,yana juyowa joda tace you....ya....yanhaaffffsaaas dakyar tahada kalmar sekumatazube kan gado somammiya , toilet yashigayadebo ruwa ya watsa mata sann tafarkatakureshi da ido " abubuwan da dawo mata akaihawaye ne suka fara mata zubaAhmed yace menene abun kuka kuma? Joda tacenakasa yarda da abunda nagani ne " Meyasakaboye mun kanka kazo mun da fuska biyu?Ahmed yace nima bansaniba joda tace thenwhatdid you Ahmed yace birthday dinki skull dinkikula dake hospital suturarki da duk wani abudakikaji ance oga to by nine. dasauri jodatarungumesa tana kuka ilove you yayan hafsa,Ahmed no karki kara cemun yayan hafsa yayankidae,joda tace ok yayana, kanka meta yayi suka dadeahaka sann tace nifa wlh se amun bikin aurekamar yanda ake yiwa ko wace mace sann nimaakaini gidan mijina, Ahmed yace shikenan kikeso?Joda tace eh sekuma zancen karatu, Ahmedyace no bayanxu ba sekin gama bawa babynmuabinci tukun haka dae suka wuni a ranar makaleda Juna sewani nan nan yake da ita joda kamjinta take tamkar sarauniya yanda ake nuna matakauna zallar abin gwanin sha'awaKamu aka shirya naji da fada bakaramun kudi akazuba agurin ba , haka sukayi dinner itama abinbasauki aka dawo last walima dare aka kaikowace agidanta amarya khalthum da abdallahse amaryar 脳 joda 馃槄 hafsa kam ana gefe selaulayi ake joda se ramawa take tana mata tsiya,Joda tagama bawa sadeeq mama Ahmed yashigorikeda leda yakarbi Dan yakaishi dakinshi taredainnah mai renonshi yatofa masa addua sannyawuce, sallah sukayi suka gode Allah tamkarfist night, sukaci suka sha sann suka bi lafiyargado acan aka raya sunna bakaramun so yanunama joda ba itama hakaLike 路 Reply 路 Report 路 10 hours agoPharidah AhmadFULANIN DAJIN@ B Aleeyu 馃挄 page 1鈨�1鈨�9鈨�Dasafe bayan sunyi wanka suna breakfastAhmed yace wai ni in tambiki joda dama maceidan ta haihu dadi take karawa ne " joda takyalkyale da dariya tace nikam bansaniba, Ahmedyace tabbb kinji ki kuwa tamkar honey, joda tacekai kuma kazar ce honey din. Ahmed yace au harkinsan dadin abun dasauri tarufe fuskarta tanadariya no nikam wasa nake,Ahmed yace bawani nan kinata cewa wayyomijina, joda tace kai yayana bansan sharri nibance komai ba, dae2 nan seda innah tafitodasadeeq an shirya shi tsab Ahmed yakarbesyamasa kiss gud mrng son, Ahmed yace kinsanme , allah ya soni kadan inyi asarar mata yaraljanna kamarki, joda tace tabb nice dae nakusanayi asarar handsome like you daya tamkar dadubu,Ahmed yajata sukaje dakinshi yaciro mata wanidankwali yabata yace zaki iya tuna wann? Jodatace wow amma ka iya ajiya harda stones dinjigidana ina xua nima dakinta taje tadauko jacketdinshi tasaka tana xua tace bae nayi kyauAhmed yace how sweet tamiki kyau sosae anmameyasa kika aje, joda tace I dunno kawai idananbata mun itake sanya ni nishadi babu waniblanket dayake hana mun jin sanyi tamkar itaAhmed yayi murmushi yace Allah yabar mun kequeen of my heart Haka abun ketafiya komainormal tuni Ahmed yasaki mansura bayanangano tanada cutar HIV AIDS dakuma cancer tamai haifa, allah kara kiyayemu,Ahmed yashigo dauke da sadeeq wanda yazamatubarikallah dashi wata uku amma kamar yayi 7mnt bul bul dashi , joda nazauna tarasa yau kammeke damunta , Ahmed yace hello mamanunborn baby, joda tace wlcm lion bae, Ahmedyace wai meyasa kike cemun lion bae, joda tacesaboda komai naka tamkar nasa ne musammanvoice. Ahmed yayi murmushi yace toh mai ciki,Joda tace wani cikin kuma Ahmed yaceamatsayina na doctor na hango babyna a jikinki,joda ta bare baki impossible wlh wata ukuinsaka samun wani cikin Ahmed yace ay se kiyiamma akwai babe ajikin ki aykuwa tuni tafarabubbuga kafa tana shagwaba,Ahmed yace dama abunda nake so kenan kin yinkyau da wann yanayin , ayko dakyar yasamukanjoda da tace se ancire cikin seda taga Ahmedyafara masifa da ita sann ta hakura wani sabontattali yadawo sabo, magani mai kyau yake bawasadeeq ba abunda yasamesa, sema kyau dayakara , hafsa anjuye baby boi mai kyau dashiKhalthum ma an dauka, anyi bikin amina da Dancommissioner wato umar, inda sukaje dubaihoneymoon. Gwaggo nagani asibity wai anjuyetwins mace da namiji, joda tace gaskiya yaAhmed acirewa gwaggo mahaifar ta. Ahmedyace why? Joda tace abin kunya ni na haihuitata haihu, Ahmed yace bakida hankali kawai batagama haihuwar ba se acire lokuma ance miki mubama son kanne ne gashi ma koya wa bamuda,joda tagwaguda baki tawuce tabarsa,Bayan anyi sunan twin din gwaggo wato arifdaamra, gwaggo tanemi alfarmar yamaida hjyagidan, dad yace sedai kinemi wata alfarmaramma banda wann kusan sati uku tana biyarshidole yatara family meeting yanemi shawarar su,Ahmed yace idan kana sonta ka maida ita dad,abdallah yace dad hjy tayi nadama sosae DanAllah kamaida ita nidama kawai banda bakindazan nemi wann alfarmar ne "kowa dae yabada go ahead. dad yace shikenanbawani jimawa yaje yayi magana aka maidatazama suke nakauna da amana itada gwaggokoyaushe arif na gurinta gwaggo kuwa amra,wanda kamar sun raba yayan ne " dad namatukar farin cikin hakan yanda suka hade kansusosae sann baka gane Dan wane sun dauki suhafsa tamkar nasuBayan wata biyar cikin joda yagirma , sadeeqkuwa har an iya tafiya joda tamatsa akan setacire shi a mama Ahmed yace samm seya cikashekara daya dole ta hakura da hakan , wata taracib dasamun cikin joda tahaifo babynta macemai kyau tamkar balabara, Ahmed yarasa indazai sakata saboda dadi aka sakawa yarinyaraisha suna ce mata aysha, honeymoon sukajedaga can zasu wuce saudiyya, uhm...acan jodatakara kwaso wani cikin aysha na wata biyarcurrr Ahmed yaki gaya mata kar tasamasa rigimaHar suka dawo bata saniba , seda taga cikinta nagirma sann tafara korafi aykuwa dataji akwai cikikamar zata buga ihu, Ahmed yace shikam idantajuye takara daukar wani yaya yanxu akafara,****** BAYAN SHEKARA UKU*******JODA rungume da aysha tana gyara mata kantaSega sadeeq yashigo rikeda kaninsa ameer yanamasa wasa Ahmed yakarbesa yana basachocolate, Ahmed yace madam waike bakyatsufa ne haihuwa uku amma ko boobs dinki sunkijuyawa ma bare skin dinki ollwyz fresh kikekarawa, joda tace kaima ay nima wlh allah tsoronakeji kar wata tamun snach gaka tamkarsaurayi kullum, Ahmed au na manta ingaya mikifah commissioner yabani yarsa safina, joda tacewhat? tura aysha tayi ajikinta tawuce samaaguje, Ahmed yace yau nadebowa kaina rigima,dakyar tabude masa ganbun yajanyota sekukatake halshensa yasaka yashanye hawayentasanntace relax April fool ne " joda takai masa naushikaiko Allah bana so kadena " Ahmed yajanyotaajikinsa kece tafarko kece ta karshe agarenijodatace Allah koh? Ahmed yace nima Allah kararungumesa tayi I loves you so much mu husband,Ahmed yace loves you too my wife, Sega susadeeq sun shigo Ahmed yace kugyara zamudauki selfieTHEENDTAMMAT BI HAMDULLAH , ALHAMDULILLAH,Ina fatar adauki darasin dayake acikin wannnovel ba kyale2 cikinsa ba akwai sakon danakeson isarwa jama'a mai brain shiyake ganewa andthe last thing is Every Single Person On ThePlanet Has A Story Don't Judge People BeforeYou Truly Know Them The Truth Might SurpriseYouAll the best 馃憤馃徎Godiya ta musamman ga duk wadanda suka badalokacinsu gurin karanta novel dina Allah yabarzumunci da kauna, masoya a duk inda kuke.. Daga hausa NOVELS sokoto 07068808039 Document made by Admin ABDUL Za,a iya samu a website ABDULMKIBAB.HEXAT.COM