Copied By HAYATU BABA ZUBAIRU (YAYA HAYAT) (ADMIN OF ADMINS) (admin Hayat hausa novels Hausa novels and fashion Cool novel, makeup and kitchen1⃣ Cool novel, makeup and kitchen2⃣ AND Cool novel, makeup and kitchen3⃣) WHATSAPP NO: 09030159301 [28/04, 20:50] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar Gidan tsohuwa_😅) Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *AM BACK AGAIN BY THE GRECE OF ALLAH* _Alherin da ke ciki Allah yasadani dashi, shairin dake ciki Allah ya tsareni dashi_ _Muje zuwa masoya ana bugun tare🤝🏻_ *UMMU SAFWAN CE* *1* Cikin sand'a tashigo cikin zauren gidansu, tana wasar b'uya, ita da k'awayenta Lab'ewa tayi tasha jinin jinkinta kamar wacce tayi k'arya, tana tafiya a hankali yanda baxaka iyajin sautin takun k'afartaba." Gafda zata shiga cikin gidan ne Saiji tayi taci karo da wani abun,a gabanta." turus tayi, Taja ta tsaya gefe d'aya tana turo baki kasan cewar zauren gidan duhu ke gareshi, Ta d'auka *Kaka* ne, kaka Kwaishi da fitinar tsuha, Tashiga gunguni tana magana k'asa k'asa, " kai wannan tsohun kacika rigima yazaka taka min k'afa, idan kuma akace da kai ka kusan mutuwa, ka d'ora hannu a kai kace kai ba yanzun zaka mutuba." Shuru taji anyi Bataji antanka mata ba." Dogon tsaki taja harda d'an murgud'a baki taci gaba da tafiya zata shiga cikin gidan kenan taji ta kuma taka k'afar mutum a karo na biyu." Jikinta ya soma rawa fitsari ya fara d'iga a wandonta, saka makon marin da taji an kwad'a mata a fuska." Wata irin k'ara tasaki ta fad'i k'asa tana birgima, "Wayyo idona na shiga uku tsohuwa kizo ki ceceni." Mahmud dake tsaye cike da takaicinta, yace "Ke wace irin yarinya ce,wadda bata kallon gabanta, tunda kika shigo soron gidan nan naketa k'ok'arin naga na kauce mki amma duk da hakan saida kika taka min k'afa." Oh kin d'auka *kaka* ne da kike fad'awa magana yanda kikaga dama?" to bashi bane ni kika tak'ewa k'afa, wawuya kawai marar hankali wadda bata kallon gabanta bare bayanta, Ni maganin rashin kunyarki zanyi kafin na bar gidan nan." Tsohuwa dake sallah, Sallamewarta kenan taji sautin kukan Dije a zaure." Da sauri ta mik'e tsaye tafito daga d'akin tana fad'in "deejama wani mugunne ya dakeki?" Ai kuwa deejama najin muryar tsuhuwa ta kuma bud'e baki had'ida sanya hannu d'aya ta dafe b idonta d'aya, "wayyo idona nashiga uku tsuhuwa idona ya tsiyaye." Mahmud tsaye yayi ya tsura mata ido yana kallon ikon Allah, k'azafi takeso tayi mashi yanaji yana gani." Ta mik'e tsaye dafe da ido sai kuwa takeyi tana tsalle tana fad'uwa, sai da tazo dafdashi ta kuma taka masa k'afa da k'arfi ta xuba a guje tanufi wurin tsohuwa dake tsaye a k'ofar d'aki tana ruwan masifa." Tanufi wurin tsohuwa tana fad'in "wayyo idona tsohuwa ki taimakeni yaya muhmud ya tsiyayar min da ido d'aya." "Tsohuwa tace "burinka ya cika mamuda ka tsiyaye mata ido d'aya saika zuba ruwa k'asa kasha, Ni wlh bnsan irin k'iyayyar da kakeyiwa deejama ba, kwata kwata baka k'aunar ka bud"e ido ka ganta tana walwala a gida ko a waje." Tunda burinka ya cika ka makantar da ita, saikazo ka kwashe kayanka ka koma gidanku. Mungode da ziyarar Allah amfana." Muhmud da zaifita, jin k'azafinda dijana tayi masa yasashi dawowa ya fasa fitar. Yace "Allah tsohuwa ki daina biyewa wannan yarinya, kwata kwata batajin magana kuma batada kunya. Tun da nazo garin nan kullum sai ankawo maki k'arar dijama, amma kullum sai d'aure mata kikeyi bata laifi." "Saboda kana jin zafinta shiyasa ka tsiyayar mata da ido d'aya?" Tafad'i hakan had'ida kamo dijama dake gefenta tsaye kamar ta shige mata a ciki dafe da ido d'aya." Ta janye hannun deejama daga kan idon nata tana fad'in naga idon naki dije, idan ta kama mutafi asibity sai na kira ubanshi duk inda yake yazo ya d'aukemu ya kaimu asibitin." Ganin babu abunda idon nata yayi, tsohuwa ta kuma kallon muhmud dake tsaye gefe d'aya yana kallon ikon Allah. "To burinka bai cikaba baka makantar da itaba." tarik'a hannunta "mutafi deejamar tsohuwa kisha hura ki nemi wuri ki kwanta kirabu da wancan Azzalumin." Kallon mahmud deejama tayi ta fakaici idon tsohuwa tayi masa gwalo had'ida murgud'a mashi baki." Nuni yayi mata da hannu a lamar zanrik'eki." Bai d'aga daga inda yakeba. Sai sallama yaji anayi, wata mata ce tashigo da yaronta janye a hannunta wanda bai wuce shekara goma ba da bokitin markad'e a hannunta duk ya b'aci da k'asa alamar b'ari yayi." Tana fad'in "ina tsohuwa take?" Fito fito dan yau na rantse da Allah bazanyi asaraba. Kullum na aiki yarona wurin markad'e sai dijama ta tareshi a hanya tayi mashi dukan tsiya sannan daga k'arshe ta zubar min da markad'e to yau hak'urina ya k'are Dan bazanyi asaraba sai anbiyani ehe " Mahmud yadubi matar yace "d'aga murya kwarai yanda zasujiki suna ciki yanzun suka shiga." Tsohuwa tafito deejama ta biyo bayanta, Tsohuwa tace Abu mai waina mekike fad'i?" Me kuma deejama tayi?" Abu mai waina tarik'e k'ugu, ta maimaita mata b'arnar da deejama tayi mata." Tsuhuwa itama ta hau masifa tana fad'in Sam ba Deejama ta aikata hakan ba." "Na lura a garin nan babu wanda aka sanyawa ido irin deejama, yarinyar da na aika tasayomin sikari. Tayaya zatabi ta k'ofar gidanku?" to Wani irin sokon yaro ne gareki da har zai saki baki, Deejama tayi masa duka kuma har ta zubar mashi da markad'e." dan Allah Abu mai waina kifita a gidan nan tun cikin muna mu biyu, dan babu wani ranko da zan maki ehe." Ai kuwa Abu mai waina tashiga ruwan bala'i, "Ayi maka asara kuma baxa'a baka hak'uriba, to yau duk yanda za'ayi sai dai ayi amma sai anbiyani markad'ena." Mahmud da yaji fad'an ba mai k'arewa bane, ransa ya b'aci yaciro d'ari biyar ya mik'awa Abu mai waina had'ida bata hak'uri." Baki ta bud'e ta fara dariya takarb'i kud'in tana godiya, Sai ta koma yin magana cikin lalama da taushin murya, "aisu yaran ne basajin magana, amma ya kamata a k'ara jawa deejama kunne saboda kaf a cikin k'auyen nan ta hana yara walwala idan ta fito kowa tsoronta yakeji." Babu Wanda ya kuma tanka mata, sai Deejama da tace "kedai ki wuce kiba mutane wuri, tunda anbiyaki kud'in markad'anki, karki damemu da suruto." Ta dubi Sale yaron Abu mai waina, ta harareshi tace "kai kuma sale duk na rik'aka saina karye maka k'afa d'aya." Abu mai waina najin hakan kuma tasan halin dijama zata iya, zata fara wata sabuwar masifar mahmud ya bata hak'uri. SnnTa tafi, a hasale yanufi wurin dijama zai daketa tsohuwa ta turata d'aki tana fad'in wlh karka daketa. Meye ruwanka, to muddun ka daketa saina sab'a maka a gidan nan." Mahmud ya dawo baya, yana hararar dijama yana fad'in zan rik'akine saina d'ebi d'arina biyar a jikinki. Dan bazan biya mki kud'i a banzaba." Yanajin tsohuwa ta fara ruwan masifa ya fito ya baro masu gidan." Bayan sallar isha'i kamar yanda suka saba kowace yarinya zataci ado tanufi dandali, Haka dijama tayi kwalliya tasanya atamfa riga daban Zane da d'ankwali daban, tazane fuskarta da kwalliya kasan cewar dijama kyakkyawace kuma bafulatana ce, domin ba sosai hausarta ke fitowaba." An d'aure k'ugu da gyale." Da gudu tafito gidansu tana rera wak'a, k'awayenta najin sautin wak'arta kowa ya fito daga gidansu suka tareta Suna fad'in ga 'yar gidan tsohuwa nan ta fito, aikuwa da murna suka tareta suka jera suka nufi dandali." Dijama ce gaba k'awayenta suwaiba da lantana da ladidi, da luba a bayanta suntake mata baya domin itace boos duk Wanda yaja magana ita ke tare mashi." Gefe d'aya suka samu suka zauna a kusa da wani mai kifi, Mai kifin yana ganinsu , Sai da ya kuma dallara fitila ya duba da kyau ya tabbatar da sune, Ya sauke wani numfashi a ransa yace "Ashe yau zanyi kwantai bazan samu cinikiba. Saboda wad'an nan hatsibiban yaran." 'Dijama ta turo ido had'ida turo baki cikin tsiwa ta dubi mai kifi tace "lafiya meya faru kake haske mana ido da fitila?" Mai kifi da saida gabanshi ya fad'i dajin maganar dijama, dan ba k'aramin aikinta bane ta bad'e basa kifi da k'asa taja masa asara kuma ba yanda zaiyi. Ya k'ak'aro dariyar dole yace "yi hak'uri 'yar gidan tsohuwa ai bansan kece ba." Ya d'auko leda yasanya mata kifi. Yace 'yar gidan tsohuwa ga wannan kici, Ta dubeshi ta ya mutse fuska tace "ya'u kabar kifinka kawai yau bana ra'ayin cin kifin." Abokananta suna su, amma saboda tsoron da suke mata yasa ko wacce ta had'iya yawunta." Ya'u mai kifi yana ganin haka yatashi tsam ya d'auki tiren kifinshi ya bar wurin ya canza wurin zama yayi nesa da su sosai." Dijama bata lura dashiba, hankalinta yatafi wurin kallon wani saurayi da budurwa dasuke hira da alama saurayin bak'one zuwa yayi." Dariya tayi ta girgiza kai irin yanda ta hangosu saurayin sai wani kakkab'ar jiki yakeyi da hankicif, yana wani ya mutsa fuska wai shi d'an gaye." Gaba d'aya ta nunawa k'awayenta shi, suka tuntsire da dariya, Dijama tace "yawwa lantana jeki d'aukomin macijin robar nan naki Wanda yayanki yaje binni ya sawo maki." Lantana ta zuba da gudu taje gida ta d'auko ta kawowa dijama." Tace yawwa kuzo kuji abunda zamuyiwa wancan gayen." Suka had'a kai wuri d'aya abu na basu umurni suna girgiza kai alamar sun fahimta [28/04, 20:50] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_😅) Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *2* Dijama ta nuna masu inda zasuje su lab'e, Sai data tabbatar da sun b'oye, sannan A hankali ta lallab'a tanufi wurin saurayin da budurwar wad'anda suka samu wuri a gefen dakali suka zauna, suna hira suna dariya, basu lura da itaba sunyi nisa wurin hirarsu ta masoya, ta lallab'a taje bayansu ta d'ora masu macijin robar Wanda aka sanyawa batur sai wutsil wutsil yakeyi kamar macijin gaske, ta lallab'o ta baro wurin tayo wurin k'awayenta su lantana da suke lab'e wuri d'aya suna lekenta suna dariya." Itama b'oyewar tayi tashiga lek'awa domin ganin yanda d'an gaye zaiyi." Ganin basu lura da macijin a bayansu ba, yasata fitowa tanufi wurinsu tayi kamar wucewa zatayi, sai da tazo daf dasu ta kurma ihu tana nuna bayansu "wayyo Allah maciji a bayanku." Yahaya gaye yana waigawa yaci karo da maciji a bayanshi, ai baisan lokacin da ya b'urka tusaba ya kurma ihu ya zubar da talkamin k'afarshi Ya zuba a guje yana fad'in wayyo Allah maciji jama'a Ku kawo min agaji." Ladiyo dayake tasan halin dijama bataji tsoroba illah ta mik'e a hasale tanufesu, Suna ganinta tayo kansu suka zuba a guje suna dariya harda rik'e ciki, suna fad'in wasa mukeyi macijin roba ne." Yahaya gaye da saida yayi nisa sosai da wurin sannan ya tsaya yana zarar ido yana maida numfashi sama sama, a can yajiyo sautin dariyarsu dijama suna fad'in wasa mukeyi macijin roba ne." A hasale shima ya nufesu, cike dajin haushin muzantashi da sukayi a gaban budurwanshi, bugu da k'ari ga gudun da yayi harda tusa yasaki." Aikuwa ya tunkarosu gadan gadan, dijama na ganin haka ta d'aga murya da k'arfi tace "kowa yayi ta kansa." Suka zuba da gudu ko wannensu yanemi hanyar tsira." Juyawar da zatayi ta gudu, taji tayi karo da mutum a dai dai lokacin da yahaya gaye yanufota, aikuwa ta mak'alk'ale mutumin wanda batasan kowaye shiba, D'aga idon da zatayi sai taga Ashe yaya Mahmud ne." Mari ya kwad'a mata, ya rik'a hannunta ya mik'awa yahaya gaye yace "gata kaci ubanta, Domin ko mu kanmu mungaji da ita, mungaji da hali irin nata, kayi mata dukan tsiya ninace." Yahaya gaye babu abunda yakeyi sai ruwan masifa, Ladiyo ta matso kusa da ita ta xungure mata kai tace "kinci darajar yayanki da yau sai na lahira yafiki jin dad'i, Dijama da sai zarar ido takeyi tana kallon fuskar yahaya gaye tanaso tayi dariya amma ba hali." Mahmud yaja hannunta yana rankwashinta a kai yana mata fad'a, sai da sukazo k'ofar gida ta kwace hannunta da k'arfi tashige gida tana fad'in Allah ya isa mugu kawai." Da Sauri yabita cikin gidan yana Neman ya rik'ata, aikuwa ta fad'a d'akin tsohuwa da gudu, tsohuwa na ganinta tayi saurin tashi zaune tace "babu Wanda zaibiyoki sai mamuda domin nasan shi kad'ai ke k'ok'arin yaganki bakya motsi, hakan yayi dai dai da zuwanshi k'ofar d'akin yana huci, tsohuwa tace "karka kuskura ka shigo min d'aki kaji na fad'a maka." Yaja yayi tsaye a k'ofar d'aki yana huci, Saida dijama ta kalli fuskarshi ta tuntsire da dariya harda rik'e ciki, dariya takeyi sosai, sai ta kuma kallonshi ta kuma tuntsirewa da dariya, Ya kuma hasala, tana ganin ya hasala sosai tace "yaya kasan ko menakeyiwa dariya?" Ya wurga mata harara had'ida girgiza kai." Tace "ba komai yake bani dariya ba sai yahaya gaye, yanda yasaki tusa ya zuba a guje." Shima kanshi gudun da yaga yahaya gaye nayi sai da yabashi dariya kasan Cewar duk abunda sukeyi a kan idonshi, Dariya taso sub'uce mashi yayi saurin barin wurin, yanufi d'akinshi, yana fad'in idan kingama dariyar saiki kawo min abincina ina jiranki." Yitayi kamar bata jishiba, tashiga bawa tsohuwa labari suna dariya." Tsohuwa tace "tashi kije ki d'auki abincin yayanki ki kaimasa yana can yana jiranki." Ta turo baki tace "ni tsohuwa bazanjeba saboda duka na zaiyi." Tsohuwa tace "baxai dokeki ba aina riga nayi mashi magana, nace karya dakeki kuma kinsan mamuda yanada jin maganar mutane, Wurin nan yana burgeni." Sannan ta tashi tana turo bki tanufi kicin ta d'auki abincin shi tanufi d'akinshi, Kai tsaye tashiga d'akin batare da tayi sallama ba, ta tarar dashi zaune a kan katifarshi dagashi sai best da gajeran wando, jikinshi ko ta ina gashi gashine yayi kwance akan kyakkyawar fatar jikinkinshi fara fes. hankalinta ya tashi jikinta yasoma rawa aduniya bata tab'a ganin namiji a hakanba, Tsawa ya doka mata wadda tasanyata tadawo natsuwarta yace "ubnwaye yabaki izinin kishigo min d'aki batare da kinyi sallama ba?" Maxa kikoma kiyi sallama sannan ki kuma shigowa." Da Sauri ta juya ta koma jikinta na rawa." Yana ganin fitarta yayi saurin mik'ewa tsaye ya d'auko jallabiyarshi ya sanya." Sallama tayi sannan ya amsa mata had'ida bata umurnin shigowa, sannan ta shigo, Kallon yabita dashi yana harararta domin cike yake da jin haushinta, yanuna mata wni tebur yace "wuce ki ajiye a can." Kizo inaso zanyi magana dake, kuma kika kuskura kika gudu ko kika yimin ihu saina k'arye maki hannu d'aya idan na rik'aki." Sum sum ta wuce ta ajiye harda wani sunkuyar dakai kamar ta Allah, tazo kusa dashi ta durk'usa had'ida sunkuyar da kanta k'asa." Ya Matso daf da ita ya kama kunnenta ya murd'a sosai saida tasaki fitsari saboda azaba, Yace "maimaita abunda kikace d'azun. Ni kikeyiwa Allah ya isa baki yafeba?" Rantse rantse tashigayi ita batayi Allah ya isaba"don Allah kayi hakuri karka ciremin kunne, banyi maka Allah ya isaba." "Idan kika kuskura aka kuma sake kawo k'ararki a gidan nan saina farfasa maki baki kinyarda." Tayi saurin d'aga kanta alamar "eh." Idanta na zubar da hawaye." Ganin fitsarin dake d'iga a zanenta yasa yayi saurin sakinta yaja da baya da sauri ya d'auko bulala yanufota yace "koki goge fitsarin nan ko yanzun na lahira yafiki jin dad'i." Da Sauri ta mik'e tsaye, saiga takarda ta fad'o a zanenta, ya doka mata tsawa yace "ke zonan takardar meye?" zaro ido tayi waje takai durk'ushe tana matsar hawaye tana fad'in dan Allah yaya kayi hak"uri bazan sakeba." Tsawa ya Doka mata yace "ba kuka nace kiyi ba tambayarki nayi." Cikin rawar murya tace "Anty bushira ce antyn suwaiba k'awata tace nakawo maka." Ya wurga mata harara yace "bud'e karanta abunda ke ciki, Da sauri ta bud'e takardar tashiga karanta masa, jin kalaman soyayya ne alamar tana sonshi, yayi saurin doka mata tsawa yace "rufe min bakinki kiyi min shuru, Bari nafaracin k'aniyarki ke 'yar aiken kamun naje ga Wanda ta aikoki." Ke fitsararriya marar kunya ke ake aikowa da takarda kikawo min?" Tashi ki kama kunnanki." Tana hawaye tana fad'in "Dan Allah yaya kayi hak'uri bazan sakeba." Yasin sai kin kama kunnenki, yayo kanta da bulala a hannunshi, Tana ganin hakan tayi saurin mik'ewa tsaye takama kunnenta sai kuka takeyi tana bashi hak'uri." Abincinsa ya jawo ya fara ci, yana kammalawa ya haye katifarshi yajawo jarida ya Shiga karantawa, ganin ta wahala sosai ya dubeta yace "tashi kiwuce kiba mutane wuri." Tayi kuka idanunta sunyi jajir har sunfara kumbura, ya dubeta yace "ko gobe idan wata ta kuma aikoki da takarda da sunan kikawo min kika karb'a abunda zanyi mki sai yafi wannan, sannan idan kika kuma yimun Allah ya isa saina karye mki k'afa d'aya da hannu d'aya." Wuce kibani wuri kinyi tsaye kin kafeni da ido kina kallona saikace Aljanah." Sum sum tafita tana kuka, a bakin k'ofar d'akinshi ta tsaya tace anfad'a d'in "Allah ya isa ban yafeba, Lokacin da kake zuwa k'ofar gidansu zance na sani ne?" Dan kawai ta aikoni da takarda saika sanyani kamun kunne saboda mugunta, to banyafeba wuta balbal kuma sai dai idan Kaine Aljanin baniba." Ganinshi tayi ya nufota ta zuba a guje tayi cikin gida, karo taci da Kaka zaune a tsakar gida, yanajinta a zaure tana Allah ya isa, dama yana da takaicinta ya sanya sandar hannunshi yashiga zungurarta da ita, yana fad'in mamuda kikeyiwa Allah ya isa marar kunya.' Kuka takeyi sosai Wanda yasa tsohuwa tayi saurin fitowa daga d'aki ta ceceta Tana fad'in yanzun malam saboda Allah akan mamuda kake zungurar dijama da sanda, ai dole jidama tayi masa Allah ya isa saboda baya raga mata, baya tausayinta ko kad'an." Ta rik'a hannun dijama tace tashi mutafi ko gobe mamuda ya kuma zaluntarki kice masa baki yafeba." [28/04, 20:50] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_😅) Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *3* Shiri takeyi zataje makarantar boko. Kasan cewar Wannan shine zangonta na k'arshe da zata k'are pramary school." Ta kammala shirinta cikin riga da wando blue ta sanya hijabinta fari, ta d'auko jakarta ta goya a bayanta, ta dubi tsohuwa dake zaune gefe d'aya tana kallonta." tace "ni dai tsohuwa nagama shiryawa zantafi." Tsohuwa tace "to "dijamar tsohuwa Allah ya tsaremin ke kidawo lafiya, Karki tsaya ko ina, kuma karki kula kowa a kan hanya kiyi tafiyarki dan karkiyi latti." Tace "to tsohuwa, had'ida fitowa tasanya takalminta ta fita." Saida ta kai k'ofar gida, Sannan kuma ta juyo ta dawo a guje saka makon fitsarin da ya matseta, Da sauri ta sunkuya ta d'auki buta a guje ta fad'a ban d'aki." Wa zata gani yaya Mahmud ne, ya juya bayansa yana wanka, ihu ta kurma. Tana fad'in wayyo Allah k'ato ba wando, Tafito a guje cikin tashin hankali da tsoro, had'ida sakin butar hannunta tazuba aguje." Mahmud dajin ihunta yasanyashi Sanin shigowarta band'akin, ransa yayi matuk'ar b'aci Yashiga tunanin lallai wannan yarinyar bakad'an ta rainashiba tunda har take iya iskoshi band'aki." Tana kiranshi da k'ato ba wando." Gudu take falfalawa kamar filfilwa, bata zame a ko inaba sai makarantarsu, Da shigarta makarantar ta cikin, Taci karo da yara yan mkrtar tsugunne alamar latti sukayi, Da gudu ta wucesu Batabi ta kansuba tayi shigewarta Aji." Malam sani, mai hukunci yana ganinta ya rufa mata baya yana masifa, kai tsaye ajinsu ya nufa, ya tarar da ita zaune a kan kujerarta, Kujerar da ba Wanda ya isa ya zauna akanta sai ita, koda kuwa ranar da bataxo makaranta bane, idan taji lbrin wani Wanda tsotsayi yasa shi ya zauna a kanta to sai tayi mashi shegen dukan tsiya." Malam sani yashigo ajin a hasale, yadubeta yace "ke dijama fito nan waje, Wato kinyi latti saboda rashin kunya irin taki kika wani wuce mutane kika wuto aji, Sai kace kinfi kowa to kisani hukuncinki ya k'aru dana sauran d'alibai." Bata kulashiba sai ma tayi kamar bada ita yakeyiba, Tsawa ya doka mata "ke dijama wai bada ke nake maganaba,?" sai a lokacin ta dubeshi had'ida turo baki tana gunguni." Cike da jin haushinta ya nufeta da bulala a hannunshi, bai tsaya b'ata lokaciba yashiga zuga mata bulalar." Ihu ta kurma ta doka wani irin tsalle tashige mashi a babban Riga, kasan Cewar malam sani ma'abucin sanya babban rigane. Kokawa yashiga yi da ita yana k'ok'arin ya yakwace kansa daga gareta, amma ina, idan yayi nan gefen ta dawo masa nan gefen, sai ihu takeyi kamar Wanda ake cirewa ido." Malam sani ya jigata sosai zufa sai karye masa take, duk zufa ta wanke masa fuska, ga dijama cikin babban rigarshi yakasa cireta, sai jujuwashi takeyi kamar zai fad'i k'asa." Yashiga fad'in 'fito dijama nafasa dukan naki, kije kiyi zamanki, amma ina ta cimuimuyeshi tana ihu tana fad'in "wlh bazan fitoba." Suna hakan Allah yakawo malam mudi, Yashiga tmbyar mlm sani abun da kefaruwa?" ganin ya had'a zufa sai jujuwa shi akeyi, bai samu damar bud'e baki yayi maganaba illah yyi mashi da hannu zuwa cikin rigarshi." Aikuwa malan mudi yana lek'awa ya hango dijama ta cimuimuyeshi sai ihu takeyi, da kyar aka samu aka b'anb'ari dijama a jikin malam sani, sai nishi yakeyi kamar wanda yayi wasan tseren gudu." Ai kowa yana samu ancire mashi ita, bai kuma bi takan kowa ba yafita daga ajin da saurinshi, .dijama kuma na gefe d'aya tsugunne sai zarar ido takeyi tana turo bki cike da tsiwa, malam mudi yace "tashi kiwuce kitafi gida na koreki daga nakarantata sai kinzo da mahaifinki." Da sauri ta mik'e tsaye, Tana magana k'asa k'asa tana cewa "to sai me?" Kuma wlh duk nakama salihu sainayi mashi shegen dukan tsiya tunda har ka koreni makaranta." Salihu babban d'an malm mudi ne Wanda yake duk sa'a nine da dijama, tana kaiwa nan tafita waje tayi tafiyarta." Malm mudi dake tsaye yaji duk abunda tace yace "to idan kika kamashi karki barshi da rai kikashe kinji , kaji min hatsabibiyar yarinya." Tafiya takeyi akan titi duk inda taga mota ajiye saita lek'a kanta ta glass d'in motar ta hango abunda ke cikin motar sannan ta k'ara gaba." A can taci Karo da yan taxi su biyu suna rigimar fasinja a tsakaninsu, tsayawa tayi tana kallonsu, sai da ta fahimci a kan abunda suke yiwa fad'a, sannan ta k'arasa wurinsu ta rik'o rigar d'aya daga cikinsu wadda ya fahimci yafi fitina, Tace "yayana ina kwana, harda 'dan runsunawarta, kamar ta Allah, kallon rashin sani yayi mata cike da jin haushi yace "waye yayan naki?" Ke wai daga ina?" A ina kika sanni?" Tace "yi hak'uri dama turoni akayi daga gida akace idan naga mai taxi nakirashi domin, yayana ne zaiyi tafiya xuwa kano kuma bayason zuwa tasha shiga mota saboda baya son jira, gaba d'aya zai d'auki shatar mota domin ta kaishi har k'ofar gida, kud'ine gareshi sosai." Mai taxi yanajin hakan ya kyale abokin fad'an nashi ya maida hankalinshi a wurin dijama, yace 'a wace unguwa gidan naku yake?" Tanuna masa hanya tace "can gaba kad'an bama da nisa sosai." Yace "yawwa 'yar Albarka shiga mota mutafi, Girgiza kai tayi,tace "tsohuwa ta hanani shiga mutar mutane saboda kar'a saceni." Mai taxi da yake yaji maganar kud'i yace "to kishiga gaba kawai saiki dinga nuna min hanya." "To tace had'ida shigewa gaba, tana tafiya." Tana gaba d'an taxi na bayanya biye da ita, duk inda ya gifta mata matafiya sai tarenshi akeyi yana girgiza kai alamar ba aiki yakeyi ba dijama kawai yake biya." Sunzo kwanar da zata sadasu da gidansu, yara sunyi tsaye tsaye, a bakin hanya, tashiga kore yaran da hannu tana fad'in "kugafara nan ga mota nan zata shigo, kujanye daga nan." Tsofaffin unguwa da samari, kowa sai kallonta yakeyi yana mmki, yana kuma kallon mai taxi din dake biyeta da ita, yana k'ok'arin shigowa kwana." Tabb!!! su furta had'ida rik'e baki🤔 Suka ce, yau kuma wannan hatsabibiyar yarinya mai taxi ta janyo mana?" Ido kowa ya bita dashi saboda ba damar ayi mata magana cibi ya zama k'ari, Domin duk wanda yayi mgna da zarar d'ansa yafito waje, Idan ta rik'ashi sai tayi mashi shegen duka tsiya, tace "babanka ne janyo maka, idan ka koma gida kafad'a mashi ya daina sanya min ido." Wnn dalilin yasa kowane mutum sai dai yasanya mta ido."👀 Da kyar d'an taxi yasamu yashiga kwanar, saboda rashin kyawon hanyar, a ransa yana danasanin biyo ta da yyi, amma kuma idan ya tuna da shata 'a ka d'aukeshi sai ya d'anji sanyi yyi murmushi yaji dad'i." Suna zuwa daf da k'ofar gidansu ta hango yaya mahmud zaune a kan dakali, Gabanta ne yanke ya fad'i data tuna da shigarda tayi a b'and'a ta iskoshi." Taja dogon nishi, tace "to shi kuma wancan mugun ko zaman me yakeyi a waje?" Shima Mahmud d'in zaman da yayi, a nan zaman jiranta ne har zuwa lokacin da zata dawo daga makaranta, domin yau babu Wanda ya isa ya hana yaci ubnta." D'an taxi na zuwa sai ti k'ofar gidan tashiga d'aga masa hannu tana fad'in wait wait ya isa ga gidan nan." Dan taxi yaja burki ya tsaya had'ida sauke ajiyar zuciya wahalar da yasha wurin shigowa wannan hanyar." Mahmud na ganin hakan ya cika da mmki da Alajabi ya tashi tsam yashiga gida, yana mmkin dijama ko dai Aljanu sun shegeta ne?" Tsohuwa tashiga dokawa kira tun a waje, tsohuwa dake kishingid'e tana gyangyad'i, jin muryar dijama yasa tayi saurin bud'e idonta had'ida kai idonta ga dibon agogo, Mmki tashigayi ganin lokacin tashinsu daga mkranta baiyi ba." Kai tsaye ta fad'a kan jikin tsohuwa tana fad'in wash Allah tsohuwa nagaji." Tsohuwa tace "dijama meya dawo dake gida yanzun, bayan nadiba agogo na ga lokacin tashinku daga mkrsnta baiyi ba." Ta turo baki idonta ya cika da hawaye tace "wai malam Mudi ne yace ya koreni a mkrantar gaba d'aya, wai sainazo da mahaifina." Kuma na rantse da Allah tunda ya koreni, duk nakama d'ansa Salihu sainayi mashi dukan tsiya." Tsohuwa ta rabka sallalami, tace "ya koreki mekikayi mashi?" "Wai saboda kawai nayi latti ." Tsohuwa zata kuma yin magana taji ana rangad'a orda da mota a waje ba kafkaftawa, duk a rud'a mata kunne." Sai kuma ga yaro yashigo yana fad'in wai a waje wani mai mota yace yana kiran dijama." Tayi sauri ta fito da kayan sauri yakeyi." [28/04, 20:50] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_😅) Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *4* Tsohuwa ta juya ta dubi Deejama, itama Deejama tsohuwa take kallo." Tsohuwa tace dijama a ina kika samo mai mota kuma?" Sann Wad'anne kaya ne naji ance kiyi sauri kifito dasu?" Dijama ta turo baki cikin shagwab'a tace "yaya Mahmud ne nasamowa mota, domin ya kwashi kayansa yayi tafiyarshi garinsu, saboda nagaji da zaman da yakeyi a gidan nan kullum sai ya zalunceni, Ko kuma ya dokeni." Tsohuwa tayi tagumi🤔 tace "dijama waye yasanyaki ki taro motar mutane, shin kinada labarin cewa direbobi wasunsu basu da mutunci?" Ai kuwa bata rufe bakiba taji ankuma danna wata irin orda da k'arfi, had'ida dukan k'ofar gidan iya k'arfinsa, sai da tsohuwa da dijama suka razana." Da sauri tsohuwa ta mik'e tsaye ta janyo mayafinta had'ida Sanya talkaminta, ta dubi dijama tace "karki kuskura kifito, kibari nafara tafiya na bashi hak'uri, har musamu yayi tafiyarshi, amma dai yau dijama kin janyo mana fitina da bala'i 'yan taxi." Duk abunda akeyi mahmud yana d'akinshi yanaji bai fitoba, jira yakeyi a k'are da d'an taxi, ya rik'ata yaci ubnta, la'ada waje." Tsohuwa tafita waje ta tarar da mutane sunyi cincirindo manya da yara, kowa sai fad'in Albarkacin bakinsa yakeyi a kan dijama, suna fad'in indai dijama ce har abunda yafi wannan zata iya aikatawa." D'an taxi na ganin tsohuwa ta fito, yabita da kallo ya nufo wurinta, yana fad'in "tsohuwa fito min da yarinyar gidanki, yau na rantse da Allah tunda iskancinta ya kawo kaina, to ta kai k'arshen rashin kunya, domin ni a tasha nake kwana." yau zanyi mgnin rashin kunyar da takeyiwa mutanen garin." yanxun nan a bakin mutanen unguwa, nkejin labarinta tsaf, to tunda rashin kunyarki takawo gareni tazo k'ashe." Tsohuwa tashiga bashi hak'uri. Tana masifa da mutanen unguwa tana fad'in "dama tasani an dad'e da tsanar dijama a garin nan to ta Allah batasu ba, kuma bazasu iya komai da dijama ba." D'an taxi shima sai ruwan masifa yakeyi yana dukan mota yana fad'in bazai bar unguwar nan ba sai yayiwa dijama shegen dukan tsiya, ko kuma a biyashi kud'in mansa da ya k'one wurin shigowa wannan unguwar." Mahmud dake d'akinshi zaune yanajin duk abunda kefaruwa ganin fad'an ba mai k'arewa bane, yasashi fitowa, yanufi cikin gida kai tsaye d'akin tsohowa ya shiga ya tarar da dijama zaune a kan kujera abincinta kawai takeci, hnkalinta kwance." Ganin Mahmud da tayi yashigo ya sanyata sakin kwanon abincin had'ida zaro ido waje cike da tsoro, Tun kafin yakai wurinta tashiga matsar hawaye tana fad'in "dan Allah yaya kayi hak'uri bazan sakeba." Dank'ota yayi yashiga kwad'a mata mari yana dukanta, dama yana da takaicinta, Dukanta yakeyi ba girma ba arziki, sai ihu takeyi, tana neman tsira, sannan daga k'arshe ya rik'a hannunta yafito da ita, Yana jayen da ita yanufi k'ofar gida da ita, kai tsaye d'an taxi ya mik'awa ita yace "gata kaci ubnta, idan da hali dan Allah katafi da ita, domin ko mu kanmu ta addabemu ta zamar mana fitina." D'an taxi ya rik'e hannun dijama yana Neman ya turata a mota, Dijama ta kurma ihu tana fad'in nashiga uku tsohuwa kina gani d'an yankan kai zai tafi dani?' Tsohuwa tayo kansa tana masifa ta rik'e hannun dijama tace "na rantse da Allah ba inda zakaje min da yarinya." Nawane kud'in manka?" kafad'i ko nawa ne sai na biyaka." D'an taxi yayi murmushi yace "dubu biyu ne tsohuwa." Tsohuwa ta kama bakin zanenta ta kwanto dubu biyu ta mik'awa d'an taxi. Sannan ta janyo hannun dijama had'ida wurgawa mahmud harara." D'an taxi yace "kin fanshi jikanyarki tsohuwa, amma kija mata kunne Dan na rantse banda darajar wannan mutumin, ya nuna Mahmud dake tsaye da konawa kika biyani sai nayi mata dukan tsiya a wurin nan kafin na kyaleta." Dijama ta dubeshi cike da tsewa tace "mudai Dan Allah karka cika mana kunne da suruto tunda anbiyaka kud'inka sai kaja akwalar motarka kabar mana k'ofar gida." Ta d'aga kai ta dubi tsofafin da suka zagayesu suna kallonsu ko hak'uri bazasu iya bayarwa ba, Ta girgiza kai tace "duk wad'anda ke wurin nan babba da yaro duk na ganku, zamu had'e daku," Sunajin hakan kowa ya watse ya kama gabansa, saboda sanin halinta, d'iyansu da jikokinsu bazasu zauna lafiya ba, wurin dijama." D'an taxi yaja motarsa yayi tafiyarsa, Tsohuwa taja hannun dijama suka nufi cikin gida." Mahmud na ganin hakan ya fasa shiga cikin gidan saboda masifar tsohuwa shima ya kama gabansa." Tabarma tsohuwa ta d'auko ta shinfid'a mata a k'ofar d'aki, tana jera mata sannu had'ida yimata fifita inda Mahmud ya daketa wurin duk yayi kwancin bulala gashi Abu ga farin mutum." Tsohuwa ranta yakai k'ololuwa wurin b'aci sai masifa takeyi tana fad'in bari mamuda d'in ya shigo, yazo ya had'a kayanshi yayi yafiyarshi gidansu, ni banga amfanin tahowar nan tashiba, tunda yazo garin nan kullum cikin d'aga maki hankali yake." Dijama ta kuma marairaicewa sai nishi takeyi kamar Wanda zata mutuwa." Wasa wasa jikin dijama ya d'auki zafi alamar zazzab'i yakeson rufeta, Hankalin tsohuwa ya kuma tashi ta mik'e tsaye tashiga d'aki ta d'auko mata maganin zazzab'i ta k'ak'k'are mata tabata tasha, sannan barci mai nauyi ya d'auketa." Yinin ranar dijama ko k'ofar gida bata fitaba, jinya tajeyi." Sai bayan sallar isha'i Mahmud ya dawo, gidan Da sallama yashigo ya,Tarar da tsohuwa zauna, K'asa k'asa ta amsa mashi had'ida kauda idonta gefe d'aya hushi takeyi dashi." Murmushi yayi had'ida girgiza kai domin yasan za'ayi hakan tunda ya tab'a 'yar gidan tsohuwa." Ya kuma kallon tsohuwa yace " 'yar tsohuwa hushi kikeyi da namijin naki, to kwantar da hankalinki na kusan tattara kayana na barmaku garinku nayi tafiyata gidanmu" Yana kaiwa nan ya d'auki buta ya Shige ban d'aki." Fitowar da zaiyi sukayi ido biyu da dijama dake kwance a gefen tsohuwa, ta tsura mashi ido. Tanatana kallonshi Ajiye butarshi kenan yaji ta saki dariya harda rik'e ciki tana kallonshi tana kallon k'ofar b'an d'aki." Sai ta dubeshi ta dubi ban d'aki ta kuma b'arkewa da dariya.' Anan take ya fahimci abunda take yiwa dariya, wato d'azun da ta iskoshi yana wanka, kenan To metake yiwa dariya?" Duk haushi ya kamashi yaji kamar yaje yasameta yayi ta dukanta amma ba hali, tsohuwa bazata bariba." Amma kafin ya bar garin nan sai ya koya mata hankali, sannan yayi tafiyarshi." Washe gari dijama taji sauk'i, sosai Tafiya takeyi D'auke da allonta zataje makarantar islamiya ta d'ora allonta akai ta sha d'amara da gyalenta a k'ugunta, Tafiya takeyi tana rera wak'arta tana rawa a kan hnya." Karo taci da Salihu d'an mlam Mudi, Wanda ya koreta a makarantar boko, Ta ajiye allonta a gefe d'aya, tasha gabanshi yana d'auke da markad'en kayan miya a Kansa, ta ture markad'en ya zube, Tace "yawwa wana nakama?" Aidama nacewa babanka duk na kamaka sainayi maka duka, tunda har ya koreni a makaranta. Ai kuwa ta kamashi da kokawa, saida tayi mashi dukan tsiya, Sannan ya duk'a ya d'auki robar markad'ansa yanufi gida yana kuka." Dijama kenan, ita ba girma garetaba sai fitina, kwata kwata shekararta goma sha hud'u a duniya." Sai da taga yayi nisa yana tafiya yana kuka sann ta d'auki allonta tanufi mkranta." Gafda zata isa makarantarsu Ta kuma cin karo da Buba d'and'an mai gari tare da tawagarsa 'yan tauri." Buba d'an maigari kowa a cikin garin tsoronsa yakeyi, Domin ya kama mutum yayi masa duka saiya karkayashi ba wani abun bane gareshi." Allah ya d'ora mashi son dijama saboda hatsabibancinta da k'arfin hali irin nata, bugu da k'ari tafi duk 'yan matan garin kyawo." Gabanta ya Tara, yayiwa yaransa nuni da hannu da suyi tafiyarsu zaiyi magana da masoyiyarshi." Ita kuma dijama a duniya babu Wanda ta tsana kamar Buba, saboda shaye shayen da yakeyi, bata son ganin fuskarshi ko kad'an." Buba ya bud'e baki yana dariya bak'ak'en hak'oransa da sukayi bak'i suka dafe wurin shan sigari🤒 suka bayyana, Yace "dijama 'yar gidan tsohuwa matar buba duk Wanda ya tab'aki a garin nan zanci........ Murmushi tayi masa Wanda bata tab'a yimasa ba, Domin tasamu wata dama da zata sanya buba ya rama mata dukanta da yaya mahmud yayi mata jiya." [28/04, 20:50] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_😅) Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *5* Ganin murmushin da takeyi ne, a kan fuskarta ya kuma bawa Buba damar k'ara bud'e baki yana dariya, Yace "dijama ki amince dani naturo magabatana a d'aura mana aure." Dijama najin hakan ta had'e fuska had'ida ya tsine baki, Ta dubeshi da kyau tace "Buba kanaso nadinga kulaka?" Har na aureka?" Buba yace "abunda nake fata kenan dijamata." Ta karkace kai tace "kasan bak'on da yazo gidanmu?" Buba yace "mahmud kike nufi?" Tace "kwarai kuwa, to kasani yasanya mun ido, kullum sai ya dakeni bansan abunda na tare mashi ba. So nakeyi ka tsoratar dashi ya daina dukana, domin kuwa duk abunda yaga inayi sai ya sanya min ido, kuma ya dakeni." Buba ya d'aga hannu ya zunduma ashar yace "Alk'awari nayi duk Wanda ya tab'amun ke a garin nan sai nayi gunduwa gunduwa da namansa." Dijama tadinga tsallen tana jin dad'i tace "yawwa Buba, Amma karka dakeshi, karkayi mashi illah, kawai dai so nake ka tsoratar dashi saboda ya daina dukana." Buba ya kuma b'arkewa da dariya ya na kuwa ya fadin "saini na dije "yar gidan tsohuwa kowa yatab'aki agarin nan bazai kwana lafiya ba," Dijama najin hakan ta dinga dariya tana zugashi "Gaskiyar Buba sai kai na dije "yar gidan tsohuwa, nan fa tadinga zugashi yanajin dad'i saboda mahaucin son da yake mta." Sai kuwa yakeyi yana zage2 Ita kuma ta k'ara gaba tana cewa "sakarai wawa, waye zai auri d'an shaye2, tajuya ta hngeshi yayi nisa, taja dogon tsaki had'ida murgud'a baki." Wani gefen dad'i yacikata tana za a dakar mata yaya mahmud,haka dai har ta kai makarantar tasu", Tana zuwa tasamu wuri a gefe d'aya ta zauna batare da ta tsokani kowaba A Can ta dubi wani yaro ya hangame baki ya na bacci aiko tasanya hannun ta ta d'allamai baki sai da sauri ya bud'e idonshi yarik'e Baki yana kuka, Anan take bakin nashi yayi tudu, ya kunbura." Ta dubeshi tana dariya tace "yaro ubanka yajamaka tunda yana gani d'an taxi zai tafi dani amma ya kasa bada hak'uri sai dai yaja yayi tsaye yana kallonmu Dan haka nacire jin haushinsa a kanka." Ta kuma matsawa gefe d'aya ta zauna, ko wanne yaro yana zuwa afad'a masa karatu, amma ban da ita, domin acewar ta kotaje an fad'a mata ba ganewa zatayi ba garama tayi zamanta", Can itama sai tafara gyan gyad'i mlm dayaga tana bacci ya d'aga bulalar hannunshi ya doka mata a jiki, yana fad'in " aikin ki kenan bacci, baki gane komai mai kwanyar kifi keda jaki banga babban cin kuba, Ai kuwa d'alibai suka d'auki yimata dariya, ta hasala sosai taji haushi tashiga gun guni tana mgna k'asa k'asa, Ni dai ban daiji metake fad'aba Can ta nisa, tace mlm zanyi fitsari? Yace "tashi kitafi dama aikin kenan daga kashi sai fitsari, ko aci akwanta, amma kai kam wayam ba komai acikinsa sai rashin kunya, Da kuma majina, ya mere baki yace "ALLAH dai ya kyauta." Rab'awa tayi ta Wuce tagefen malam, ta dubeshi ta sakar masa murmushi, Mlm kuma harara ya kuma wurga mata, Hmm kun dai San dijama bata murmushin banza." bata zarce ko inaba sai cikin wani kango dake nesa da makarantar kad'an a hankali tashiga kangon tana waige waige, can ta hango leda fara, Ta duk'a ta d'auki ledar, Can nesa kad'an ta hango ramin cinnaka tashiga tsinta tana zubawa a cikin ledar, Tana tsinta tana fad'in Yau zaka ci ubanka mlm ni zaka zaga har kasa ayimun dariya,hmmmmm yau kaima za'ayi maka dariya." sai da ta tsinci mai isarta ta zuba a ledar, ta saki dariyar mugunta sannan ta mik'e tsaye. Ta fito, hannunta goyo a bayanta sai da tazo kusa da mlm Ya juya bayansa yana gayawa wad'ansu d'alibai karatu, ta faki idonsa ta lallab'a a hankali saiti rigarsa ta d'aga ledar cinnakan ta zuba mashi cikin riga d'alibai na ganinta amma ba halin yin magana." Dama sun san za'ayi hakan, tunda malam ya zageta, tayi shuru ta nuna alamar bata damuba, Kowa yashiga mamakin "dijama ce za a zaga bata tankaba hmmmm, akwai wata a k'asa Mlm da yaji anfara mintsinarshi, yafara sosawa, tun yana Sosawa a hankali harya ya zabura ya mik'e tsaye nan fa yakama susar jikinsa da sauri d'alibai me zasuyi inba dariyaba, kuwa takeyi tana tsalle tana tab'i da hannunta tana dariya, tasanya d'alibai najansa tana masu wak'a suna amsawa Itake fad'in cinnaka yaci jeshi Sunafad'in tashi kar ya k'arama 😅 [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_😅) Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *6* malm sai so she2_ yakeyi, yana hararar dijama had'ida da yimata dakuwa🖐🏿 har yakai sai da ya cire rigar sa, ganin cinnakun basu fita ba daga k'arshe ya tub'e wandon sa ya , yashiga kakkab'a ya koma daga shi sai gajeren wando." Can saiga cinnaku suna fad'owa d'aya bayan d'aya." tsaye yayi ya kasa magana yana sauke ajiyar zuciya,d'aya bayan d'aya Yakasa d'aga ido ya dubi d'alibansa saboda kunya domin ya fahimci cewa duk shairin dijama ne." Dijama tayi tsaye tana kallonshi tana dariya, ya dubeta da kyau cikin b'akin ciki da jin haushinta yace " dijama kitafi gida nakoreki karki k'ara zuwanmin mkrnta, Ta b'arkewa da dariya had'ida rik'e ciki tana nunanshi tace "toh saimi Dan ka Koreni, ainaga kai kafara zagina ni kuma narama, Harda yimin gorin ilimi, kuma ai naga shi ilimi Allah ke badashi nima ba Dan ya manta daniba, Kuma ai naga itama 'yartaka jakace bata San komiba sai jakanci,kuma doluwa ce, Idan ina da kwanyar kifi ita kuma kwanyar kwad'd'i ke gareta, Ta k'are maganar had'ida mur gud'a baki, tayi tafiyarta." Sai da tayi nisa da tafiya snn ta waigo a lokacin malma yana k'ok'arin maida kayan jikinsa tace "kuma sai naci uban Larai idan muka had'u rafi, Tunda ka koreni, daga makarantarka, sann ta juya rik'e da Allonta, tayi tafiyarta." Koda ta isa gida tana gunguni, Tsohuwa ke tmbayarta lfy? Meya dawo da ke gida ynzun?" Idonta ya cika da hawaye tashiga fad'awa tsohuwa abunda yafaru tun daga farko hark'arshe saboda dijama duk rashin jinta bata k'arya." Tsohuwa taja bakinta tayi shuru na minti goma, sannan tanisa tace "toh zauna kihuta, gaskiya dijama banji dad'in korarki da malam d'ahiru yayi ba." To yanzu yazanyi? An koroki a mktantar boko, gashi yanxun islamiyar ma ankoroki. gashi kuma ke ba k'ok'ariba, allonki sai yayi wata ukku bakiyi wankiba, haka boko baki ganewa, to ni yanzun miye mafita?" Dijama tayi shuru sai zarar ido takeyi Can taja dogon nishi tace "yauwa tsohuwa tunda kinga baganewa nakeyi ba shawara kawai ki sanyani makarantar koyon sak'e sak'e, watak'ila a can nafara ganewa kinga saina koyi sak'a dama nafison can." Mahmud dake tsaye yana jinsu tun shigowarta me zaiyi inba dariyaba, Yace kinko kawo shawara mai kyau, tunda da keda kwad'o bakuda wani banbanci, Bako mai a k'wak'walwarki sai rashin kunya da gidadanci, babu abunda kika iya, sai k'auyanci da jakanci takwalla me kan kifi me idanun mujiya." Idan har ba canxa hali kikayiba mki gama yawon makarantuba." Murgud'a baki tayi cike da jin haushin kala mansa tace "sai naga ai kamar gado nayi a wurinka tunda kamarmu d'aya da kai." Kuma k'wak'walwarmu d'aya, kaga kuwa gareka na gada, yayi saurin ja da baya yace wah?" Ni ?Allah ya tsaren Dake." Yana fad'ar hakan yayi waje abinsa domin ida yabiye mata zata hasalashi Dan yasan dijama badai bakiba." Ai kuwa tsohuwa ta hau masifa, tana fad'in "da kake ce mata kwanyar kifi gareta ai dai 'yar uwarka CE, kuma jininka CE, ni dai bansan irin tsanar da kake yiwa dijamaba." Mahmud baima San tsohuwa na masifaba yayi ficewarsa abunshi." tafiya yakeyi yana dariyar dijama saboda rashin kunya da tayi mata yawa akai ita da kanta tasan bata gane karatu, kai Allah dai ya kyauta." Yana shanye kwanan gidansu, bai ankaraba yaji ankwad'a masa sanda akai, waiga warda da zaiyi wa zaigani, Buba ne da yaransa sun zagayeshi suna shan taba." Cike da mmki Mahmud yake kallonsu, zai bud'a baki yayi masu mgna suka kuma yunkurin kuma buga masa sandar a karo na biyu, Hannunsa ya kara suka yashiga jujuwa yaron Buba ya yarb'ar dashi gefe d'aya, nanfa danbe yakaure tsakaninsu." Nanfa Mahmud ya shiga dukansu, baji ba gani ,duk suka zube warwas wasu kuma suka tsere a guje, Daga cikin masu gudun harda Buba😅 D'aya daga cikinsu daya daku ya kasa iya gudu, Mahmud ya shak'o wuyanshi ya mak'areshi, yashiga tmbyarsa, "waye yasanya Ku?" Menamaku kukeso kuga bayana?" Jinkinsa na rawa yace dijama ce tasanyamu." "what dijama?" Yace cike da mamaki, yanzu dijama bayan rashin kunya harda ta'addaci takeyi?" Ya wurgar dashi gefe d'aya yayi tafiyarshi, zuciyarsa cike da bak'in ciki d mmki." Haka ya koma gida Rigarsa rataye a kafad'arsa, Yana shiga cikin gidan, ya ta rar da dijama tsakar gida zaune, Tana ganinsa ta tashi da gudu ta tafad'a d'akin tsohuwa. Baibi ta kantaba yayi shige warsa d'akinsa, yashiga har had'a kayansa, cikin akwati. Saida ya d'auki komai nashi. Ya tallabo akwatinsa yafito." Lokaci da yafito janye da akwati, yayi dai dai da fitowar Tsohuwa daga band'aki ta dubeshi cike da mmki tace "Mamuda lafiya?" Ina zakaje da akwati?" Mahmud ya dubi tsohuwa yace "gida zantafi tunda naga har anfara turomin "yan iska su dakeni ,watara na maganin b'era za a sanya min a abinci domin naci na mutu, Dan haka tsohuwa kinga tafiyata sai wani lokacin." Ya kai dubansa ga dijama dake zatsaye a bakin k'ofar d'aki, ta marairaice fuska, duk bataji dad'in tafiyar da yace zaiyiba , yace " toh meye kuma na tsayawa kina kallona?" Zaki turosu ne su kuma tareni a hanya?", . Bata tanka masaba illah ta kuma sunkuyar da kanta k'asa, , tashiga tunanin kaddai ace Buba sanyawa yayi aka daki yaya Mahmud." Bai kuma bi takan kowaba ya Yakama hanya yayi tafiyarsa." Tsohuwa ta bishi da Addu'ar Allah ya tsareshi ya saukeshi lfy." bayan fitarsa tsohuwa ta dubi dijama da kyau, taga ba gaskiya a fuskarta tace dijama me ke faruwa da mahmud?" Bata b'oyewa tsohuwa ko maiba tashiga bata lbr abunda yafaru." Aikuwa tsohuwa tashiga yiwa dijama fad'a ta inda take shiga batanan take fitaba, fad'a takeyi sosai kamar ta daketa, dijama bata tankaba illah turo baki takeyi." ******************* *The following day* Tsohuwa takira dijama domin ta aiketa, Tafiya takeyi tana rawa a kan hannya tana d'an karkad'a k'ugunta, Ta k'ofar gidansu Buba tabi inda suke zama suna majalisa, ta hangosu ta d'aure fuska tayi kamar bata gansuba, Sai da tazo daf dasu abokanansa sukace Baba ga mutuniyar can, yana ganin takawo daf dasu ya wangame bakin sa da ya kunbura yayi suntum, yasha duka wurin mahmud." yayi saurin tashi ya shiga gabanta yana fad'in "dijama ta sai ina hakan?" Ta d'aga kai ta dubeshi taga yanda labbansa suka sundume kamar ganda, Bata San lkcin da ta tuntsire da dariya ba, tana nuna bakinsa da hannu, tana kuma dariya." Muzanta Buba yayi, Yashiga kallon kansa, yaga metake yiwa dariya?" Fahimta yayi da bakinshi take yiwa dariya ya, farajin haushi, amma kuma sai ya waske." Ta kuma karkace kai tana kallonshi had'ida ya motsa fuska, kamar ba ita bace ke dariya yanzun, Tace wai dama kai ragone?" Ina taurin naka yake wanda kake tsoratar da mutanen garin nan?" Shin wai meyasa harka bari yaya mahmud yaji maka ciwo, lallema amma dai buba kabani mmki, Ta kuma kallonshi ta tuntsire da dariya tace " toh Allah ya tsare gaba kaga tafiyata", ta barshi nan tsaye Ta rab'ashi ta wuce, me abokansa zasuyi inba dariyaba, da suka tuna da gudun dasukaga yayi jiya." Sukace gskya "oga munfaji kunya jiya wai ya akai hkan ta faru? Musamman kai oga duk kafimu gudu a nan take kashanye kwana, Nanfa yafara k'uluwa. Ya dubesu ya doka masu tsawa idonsa sunrik'e zuwa launin ja." Dijama nayin nisa snn tawaigo ta kallesa taga yana nan a inda ta barshi tsaye, ta kuma b'arkewa da dariya ta d'aga murya ynda zaijita tace "amma dai Buba Kai wawa ne wlh da mace zatasanya kaci duka hka, tunda ma Nagano kai ragone na rantse bazan aurekaba, tun wuri ka nemi matar aure amma ba dijamaba ehe, tana kaiwa nan ta zuba a guje ta b'ace masa." Aikuwa Buba ya k'ulu iya k'uluwa yashiga zage2, yana d'aga anda yana kirarinsu na 'yan tauri, Had'ida borin kunya." "Karya kike dijama na rantse da Allah Indai ina numfashi a garin nan bawani Wanda ya isa ya aureki saini, saini Buba na dijama yar gidan tsohuwa." *wacece dijama*?" Waye Mahmud?" Muje zuwa yanzun lbr yake ba'ayi komai ba." [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_😅) Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) 7⃣ Mahaifin Mahmud da mahaifin Dijama Hassan da Husaini ne, Hakan suka tashi a tare duk abunda zasuyi a tare sukeyinsa, har sha'awa suke bawa mutanen k'auyen Tofa dake cikin k'aramar hukumar Kano." Hassan da Husaini sun taso cikin so da k'auna da kulawa a wurin mahaifansu, Malam Adamu da Hadiza, Wanda a yanzun jikokinsu suka canxa masu suna suka mayar dasu tsohuwa da Kaka Babu wani Abu dake raba Hassan da Husaini, ako da yaushe suna tare da juna, a cewarsu a yanda suka fito tare sun d'aukarwa Kansu Alk'awarin baxasu tab'a rabewa ba." Tun haihuwar Hassan da Hussaini tsohohuwa bata kuma k'ara samun haihuwa ba, wannan dalilin yasa suka d'auki son duniyar nan suka d'orashi a Kansu." K'auyen Tofa k'auye ne mai tattare da Ni'ima da wadatuwa. Da kuma yalwar makarantun boka dana islama." Wannan dalilin yasa mlm Adamu ya tashi tsaye tsayen daka domin ganin Hassan da Husaini sun samu ilimi boko dana Islama, kasan cewar mlm Adamu manomi ne, akwaishi da wadatar zuci, da son yaga ya wadatar da iyalinshi batareda sun gani a wani gidan ba." Hakan kuwa akayi suntashi cikin hazak'a da k'ok'ari Wanda gaba d'aya k'auyen na Tofa, suna Alfahari dasu, suka zama abun sha'awa da kwatance." Akwana a tashi har suka kammala karatunsu na _secondary_ har suka tafi Jami'ar Bayaro _university_ dake cikin garin Kano." Shigarsu jami'a ra'ayinsu yarafa banbanta a wurin karatu domin Hassan _Business_ yakeson karanta, shi kuma husaini _mass_ _communication_ yake son ya karanta." Hakan suka Amincewa junansu amma kuma duk da hakan a cikin mkrantar a tare suke kwana a tare sukecin abinci, idan har ba saninsu kayiba bzaka tattace Waye hassan ba waye husainiba." Hakan sukayi karantunsu cikin Aminci da soyayyar juna tare da taimakon mahaifinsu har sukayi masters." Allah ya taimakeso suka fito da sakamako mai kyau, Nan take har rugogowar d'aukarsu aiki akeyi." Hassan aiki baya gabansa yafi ganewa kasuwanci domin tun kafin takardunsu su fito har ya bud'a d'an karamin shago a k'ofar gidansu yana sayarda atamfofi da shamdodi da takalma, wadda yin hakan harda taimakakon mahaifin nasu." Wani babban kamfani ne na sarrafa motoci, dake cikin garin Kano a can Hassan yasamu aiki inda ya samu matsayin manager campanin za'a dinga yimashi Albashi mai tsoka." murna a wurin mahaifan nasu da kuma d'an uwan nashi Husaini abun ba'a mgna Bayan kwana biyu da faruwar hakan, garin Lagos suka d'auki Husaini aiki a gidan TV na garin Lagos, inda shima suka bashi babban muk'ami." Hmmmm Hassan Husaina sunyi bak'in ciki sosai da rashin samun aikin da basuyiba a gari d'aya, inda suka buga Kansu da k'asa sukace sun fasa yin aikin indai ba gari d'aya suka samuba.". Tsohuwa da Kaka suka Shiga lallashinsu suna basu hak'uri a kan cewa rabuwar aikinsu ai bashine rabuwarsu ba, kuma ai ba'a can zasu dawwamaba." Da kyar a ka samu suka hak'ura had'ida yiwa junansu Addu'a." Ranar da zasu fara tafiya wurin aiki, ko wannensu ya shirya kayanshi a akwatinsa, sunja wuri d'aya sun zauna suka rungume junansu ko wanne idonshi ya cika da hawayen rabuwar da zasuyi." Tsohuwa da Kaka dake tsaye a tsakar gida suna jiran sufito surakasu, sukaji shuru basuda niyar fitowa, kai tsaye suka shiga d'akin, suka ta tarar dasu a zaune rungume da juna suna hawaye." Sukansu saida suka tausaya masu ganin cewa tunda aka haifesu basu tab'a rabuwaba, A yanxun shekara Ashirin da bakwai kenan sai yanzun da girmasu lokaci d'aya zasu rabu tabbas dole suyi kukan rabuwa." Hakan suka shiga lallashinsu da ban baki da komai sannan suka lallab'asu had'ida yi masu rakiya suna d'agawa junansu hannu sukatafi." Tsohuwa da Kaka sunyi kewar tafiyar tasu, sai dai daga k'arshe suka bisu da Addu'a Neman dacewa." Wata d'aya da tafiyarsu suka shiga aiki gadan gadan baji bagani, kuma sun tsare gskiyarsu da Amana, Kullu suna kiran junansu a waya ko kuma su hau charting suna fira cike da kewar junansu." albashinsu na farko suka shigo garin na Tofa suka shiga rarrabawa tsofafin garin da masara k'arfi." Sukayiwa tsohuwa gyaran gida aka mayar mata da ginin zamani, Kaka yacika da murna da farin ciki, suka wadata fahaifan nasu snn daga k'arshe suka koma wurin aikinsu." Bayan shekara d'aya da fara aikin Nasu, ba laifi kud'i sun zauna masu a rayuwa babu abunda suka nema suka rasa, Kaka ya tayar masu da fitina akan cewa zamansu a hakan ya isa, Ya kamata kowanne daga cikinsu ya nemi mata domin yayi aure, ko zasu ga jikokonsu tun suna da rayuwa." Suka amsa gaba d'ayansu da to." daman abunda suke jira kenan." Bayan wata biyu da yimasu maganar dukansu suka nemo matar aure a garin da suke aiki, Hassan ya nemo auren Hajara, Husaini kuma ya Nemo auren Bilkisu." Saida suka turawa junansu photo nan yan matansu dukansu sukayiwa juna sambarka da dacen da sukayi sannan suka isarwa da Kaka umurnin sa." Kaka da tsohuwa sunji dad'i sosai sunyi murna, cikin sati d'aya aka tsaida magana aka sanya ranar bikin nasu nan da wata d'aya masu zuwa." Akwana tashi lokacin bikinsu yayi aka shiga hidimar biki gadan gadan, in da Hassan ya k'era k'aton gida naji da gani a cikin garin kano, Shima Husaini hakan, gida iri d'aya sukayi duk abunda ke akwai gidan hassan akwaishi gidan Husaini gari kawai ya babbanta Hassan a kano husaini a lagos." Ansha shagalin biki anyi taron bikin da ba'a tab'ayin irinsaba a cikin k'auyen na Tofa." Ko wannansu Amaryarshi ta tare a gidansa." Hmmmmm." Bayan wata tara da aurensu matar Hassan ta haihu ta haifi d'anta namiji mai kama da Husaini sak👌🏻 mmki kowa yakeyi sai. Sai dai ba abun mmki bane kasancewa jini d'aya ne." Murna Husaini yashigayi dajin labari, tun kafin ya iso yasanyawa yaro suna *Mahmud* Hassan yaji dad'i sosai domin shi a kullum farin cikin husaini shine nashi. Kuma duk abunda yakeso shima shi yakeso." Shekarar Mahmud Uku aduniya aka Haifa mashi k'anwa aka Sanya mata suna Asma'u." Har a lokacin matar Husaini ko b'atan wata bata tab'ayiba." Ta d'auki damuwar duniyar nan ta d'orata a kanta, inda shi kuma Husaini sai dai ya dinga Addu"a, Allah yabashi mai Albarka idan lokaci yayi." Wanda a wannan lokacin Hassan kud'i sun zauna mashi ya daina aikin kamfani yashiga harkar siyasa gadan gadan." Shima Husaini hakan ta kasance a gareshi yazama babban d'an jarida a garin lagos wanda akeji dashi, kud'i sun zauna masu." Bayan matar Hassan ta yaye Asma'u ta kuma samun wani cikin ta haifi d'anta namiji aka sanya mashi suna Adamu wato sunan Kaka kenan suna kiranshi da Khalil." Wasa wasa sai da sukayi shekara goma sha uku da Aure sannan Allah yabawa matar Husaini ciki, Wanda yayi dai dai da kuma samun cikin matar hassan haihuwa ta hud'u." Samun cikin Bilkisu matar Husaini ba k'aramin murna sukayi ba gaba d'aya family musamman Hassan, da yakeji tamkar matarsa ce keda cikin." Haka sukaci gaba da renon cikinsu har ya kai watan haihuwa, ta haifi 'yarta macce sak Hassan, Masu karatu kusan dai Hassan da Husaini kamarsu d'aya idanba saninsu kayiba bazaka iya tattace d'ayansuba." Hassan yayi mata hud'uba yasanya mata suna Nana Khadija wato sunan tsohuwa kenan, inda tsohuwa taji dad'in wannan kara da akayi mata aka sanya sunanta, amma kuma ta shinfid'a sharad'in cewa baza'a canza mata sunaba akirata da ainahin sunanta Nana khadija." Hakan akayi domin bin umurnita, ba'a canxa mata sunaba da sunanta kowa ke kiranta, amma bnda mahaifan nata sai dai suka dinga kiranta da Ummie." Inda tsohuwa take kiranta da deejamah." Tunda akazo da Mahmud wurin bikin sunan Nana khadija, yaji yana sonta musamman da duk wanda ya gansu ake cewa kamarsu d'aya a lokacin mahmud yana da shekara goma sha d'aya." Idan zai kwanta barci dole sai a kusa da ita yake kwantawa. Wnn abun bak'aramin dad'i yayi wa mahaifan nasuba." Bayan haihuwar khadija da sati d'aya matar hassan ta kuma haihuwa ta haifi 'ya mace aka sanya mata suna Fateemah." Bilkisu tayi Arba'in d'in Nana Khadija cike da k'oshin lafiya, dijama tayi kyau harta gaji sak kamannunta suka dinga komawa na mahaifinta." Shiri sukeyi zasuzo Kano yawon Arba'in domin ya d'auk'i huto a wurin aikinsa." Sun shirya tsaf cikin Shiga ta Alfarma, anyiwa Deejamah kwanliya tayi kyau tana sab'e a kafad'ar mahaifiyarta, Husaini yana janye da a kwati yana k'ok'arin sanyashi a but, Bayan ya shirya komai suka shiga mota yajasu suka d'auki hnyar kano." Tafiya sukeyi suna yiwa 'yarsu wasa cike da so da k'auna, Suna kaf da kawowa Husaini yana yawa da Hassan kan cewa gasunan sun kusan kawowa, domin sai sunfara tsayawa cikin kano wurin hassan idan sukayi kwana biyu sai su wuce Tofa wurin tsohuwa idan suka gama kwanakin da zasuyi sai su dawo gida." Yana cikin waya da hassan saigani sukayi mai mota ya gifta masu ta gabansu ya daki motarsu, Tayar motar husaini ta fita ya yanki daji babu abunda sukeyi sai Addu'a domin kuwa yayita k'ok'arin ya tsayar da motar amma yakasa." Saida takai gindin wani k'aton icce, ta daki icce gaba d'aya motar takife, Wadda yyi ddai da zuwan mutanen da abun ya faru a gabansu suka biyo bayansu domin ceto rywarsu." K'ok'arin tsiratar da rayuwarsu aka shigayi, da kyar aka samu a ka fito dasu a k'ark'ashin motar wanda a lokacin ko wannensu baya motsi Allah ya karb'i rayuwar bayinsa." Cikin ikon Allah Nana khadija ko kwarzane batayiba, koda aka cirota a motar sai wasa takeyi da hannunta alamar tana cikin k'oshin lfy." [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Written By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *9* Gudu takeyi tana ihu, Buba na biye da ita. Samarin Antyn lantana ne, suka hangota tana tik'ar gudu suma suka dafo mata dama jiranta sukeyi sunada haushinta." Tana ganinsu suma sun biyota, ta kuma k'ara gudu tana fad'in wayyo jama'a kufito Ku taimakeni 'yan fashi da makami." Wani tsoho a kan kekensa yana tafiya yanajin hka yasaki keken ya xuba da gudu ya nemi ma b'oya." Matan Aure sai kama d'iyansu sukeyi suna rufewa a d'aki suna Addu'oi domin a tunaninsu 'yan fashin ne suka shigo cikin garin." Dantijawan garin da samaru suna ganin su Buba na gudu tareda dijama, sun d'auka 'yan fashin sukeyiwa gudu, ai kuwa har 'yan rigaggen gudu sukeyi suna shigewa gida had'ida rufo k'ofa da sanya sakata." Duk inda dijama ta gifta tana ihu su Buba na biye da ita suna Neman kamata, Jin ihunta tana fad'in wayyo 'yan fashi da makami, jama'a kufito Ku taimakeni Kowa ta Kansa yakeyi baya tsayawa saurarenta." Da kyar tasamu ta kawo gida, tana shiga gida ta mayar da k'ofa ta rufe ta sanya sakata, Ihun takeyi bakinta yak'i yayi shuru tana fad'in "wayyo tsohuwa 'yan fashi da makami." A razane Abba ya mik'e tsaye cike da tashin hankali da tsoro ya tallabi Kaka yashigar dashi d'aki, Tuni tsohuwa ta kai d'aki zaninta a hannu daga ita sai dogon siket, saura kad'an tayi tuntub'e ta fad'a wurin tashi." D'aki d'aya suka shige suka rufe ko wannensu sai zarar ido yakeyi." Can sukaji ana dukan k'ofar waje da k'arfi kamar za'a cire k'ofar.' Jikin tsohuwa ya soma rawa tana kallon Abba tana cewa "yanxun Hassan ya zamuyi?" Karfa su shigo su kashemu." Abba yace "kwantar da hankalinki tsohuwa baxasu kashemuba, jin haushina d'aya na baro bindigata a cikin mota." Kaka kuma ya sunkuyar da kai sai salati yakeyi yana addu'a jikinsa sai rawa yakeyi' Dukan k'ofa akeyi ba girma ba arziki, tsohuwa ta dinga rawar jiki zanenta a hannunta takasa d'aurawa sai addu'a takeyi idan tasaki wannan ta kwaso wannan." Dijama ta dubi tsohuwa ta dubi kaka ta rik'e ciki tashiga kwasar dariya, tana nunasu da hannu." Tsohuwa na ganin hakan ta fara tunanin ko dijamace ta janyo fitina a waje ba 'yan fashin bane." Tsohuwa tace Hassan ina ganin ba 'yan fashibane dijama ta janyo mana fitina." Abba yayi saurin waigawa ya dubi dijama da sai dariya takeyi idan ta dubi tsohuwa da kaka. "Yace dijama suwaye ne? Mekikayi masu?" Turo baki tayi tace Abba su Buba ne, bata k'arasa maganarba sukaji dukan k'ofar yayi yawa, kamar harda hayaniyar mutane a wajen, Sai a lokacin Kaka yayi magana yace "ai saikatashi kafita kaji abunda ke faruwa, Indai wann hatsabibiyar yarinyarce wata rana sai ta janyo mana mgnar da za'a cinnawa gidan nan wuta duk mu k'une gaba d'aya Yana gama mgnar ya wurgawa dijama harara ya d'aga sandarsa ya zungureta mata k'afa da ita." Abba ya mik'e da Sauri ya bud'e k'ofa yafita, Bbu abunda tsohuwa takeyi sai wurgawa dijama harara domin yau ta kaita bango." Abba yana fita yaga mutane jimjim a k'ofar gida, babba da yaro, tsofaffi da samari, kowa sai fad'in Albarkacin bakinsa yakeyi a kan dijama, a gefe d'aya tawagarsu Buba ce da makamai a hannunsu, d'aya gefen kuma samarin Antyn Lantanane suma rik'e da makamai, rik'e baki yayi yacika da mmki." Suna ganin fitowarshi sukayi saurin ajiye makamansu suka zube k'asa suna gaida shi." Bai tambayi abunda ke faruwaba Dan yaji duk abunda suke fad'i, illah yashiga basu hak'uri, tare da rarraba masu kud'i." Wani dantijo yagani zaune wuri d'aya ya rafka tagumi, kowa yana zuwa karb'ar Kud'i shi yana zaune wuri d'aya baya da niyar motsawa,daga inda yake, Abba ya isa kusa gareshi yace "Baba lfy meya faru?" Ko wanine bashi da lfy a cikin iyalinka." Dantijon ya dubi Abba yace "Alhaji dama ciwon ne ai da sauk'i." Abba yace "Baba meke faruwa?" Ina kan keke na ina tafiya yarinyar wurinka tadinga ihu tana fad'in 'yan fashi da makami, bansan lokacin da nasaki keken hannuna naba, wurin intsiratar da kaina, Kafin in ankara ansace mun keke, kuma wlh Alhaji shi kad'ai na mallaka shine kaddarata." Abba ya lallasheshi had'ida kirga kud'i masu yawa wad'anda sukafi na keken yabashi had'ida bashi hak'uri, Hakan Abba yayi bawa mutane hak'uri yana yimasu Alheri suna wucewa daga ciki kuwa harda Buba da yaranshi da saurayin Antyn lantana." Harda wani magidanci wurin gudun 'yan fashi bai saniba ya ture 'yarshi ta karye a hannu, bai ankaraba saida yaji ance ba yan fashin bane snn ya fahimci Ashe ya karye 'yarshi a hannu." Shima Abba yabashi hak'uri had'ida bashi kud'i masu yawa da zai nemarwa yarshi magani harta warke." Sann Abba ya juya yashiga gida yanata mmkin hatsabibanci irin na dijama, Dijama ta rakub'e wuri d'aya sai zarar ido takeyi tsohuwa sai faman fad'a take mata kamar ta daketa." Abba shima yashiga yimata fad'a kamar ya doketa abunda bai tab'a yi mataba tunda aka haifeta, Kaka dake zaune gefe d'aya yace "gwara da Allah yasa ka nan a gaban idonka hakan ta faru, Kullum a rana d'aya sai sama da mutum goma sunkawo k'ararta tsohuwa ke tare mata,bata son ganin b'acin ranta." Amma tunda ynxun ka ganewa idonka sai ka d'auki mataki, akai, Ga ganta nan Ko mkranta bata zuwa gaba d'aya makarantar biyu Arabic da boko duk ankorota, saboda hatsabibancinta gata bata gane komai sai fitina da rashin kunya. Yakai k'arshen maganarshi yana zungura mata sandar hannunshi." Tsohuwa bata tanka masuba saima taja bakinta tayi shuru, domin yau itama dijama ta kaita bango." Abba yayi kyaran murya ya dubi tsohuwa yace "inna kiyi hak'uri kibani dijama natafi da ita na nema mata ilimi Wanda zatayi dogaro da kanta tazama abar Alfahari a cikin Al'umma, yin hkan shi zai Sanya mana natsuwa a zuciyarmu ganin mun rik'e marainiyar Allah tsakani da Allah." Kaka yayi karaf yace "aikuwa wlh da ka taimakemu ka taimaki mutanen garin nan mundun katafi da dijama kabar garin nan da ita, ni wlh wani lkcin idan na tsaya ina tunanin inda dijama ta gado wnn halin nata sai inkasa tunano kowa a cikin zuri'armu, ina ganin wata k'ila a can cikin dangin mahaifiyarta tayi gadon wnn halin." Tsohuwa tace "nidai ya isa haka malam kamata yayi kadinga yiwa dijama Addu'a ba aibatataba." Kaka yace "ni Sam bana aibata dijama a kullum Addu'a ta d'aya Allah ya shirya mana ita, yabamu ikon rik'e amarta da Allah ya d'ora mana a kai." Abba ya katse zancan da yace "to Ummie tashi kishiga ciki ki had'o kayanki mutafi marece yafara." Tana murna tana tsalle zataje birni. Ta tashi tashiga d'aki ta fara had'a kayanta." Tsohuwa bata son tafiyar dijama dan dai ba yanda zatayi ne, dole ta hak'ura tabari za'a tafi da ita." Sai da ta shirya kayanta tsaf a jaka ta tallabo jakar tana dariya tana jin dad'i, ta fito." Abba har ya kammala shirinsa ya fito had'ida yiwa su tsohuwa sallama dijama na gabansa Jakarta a hannunta suka nufi hanyar waje, Tsohuwa dai Addu'a take masu Wanda takejin kanta duk ba dad'i an d'auke Mata dijamarta." Kaka kuma saboda dad'i kamar ya zuba ruwa a k'asa yashi, domin yasan yau idan ya kwanta barci ba bak'ocin da zai tayar dashi domin kawo shedun dijama." Har mota suka rakasu, suna yimasu add'o'i." Mutanene cimjim gaban motar k'awayen dijama suna bangwana, Abba ya bud'a mota yashiga dijama itama tashiga gidan gaba sai wasar baki takeyi tana dariya tana d'agawa su suwaiba hannu." Murmushi Abba yayi ya kunna mota ya fara tafiya, Dijama ta lek'o ta k'ofar marfin mota tace "suwaiba idan kukaje gonar Audu wurin satar gwaiba, idan kukaga Buba kuce masa natafi birni amma zandawo don saina rama abunda yayi mun." Abba yace Ummie na wai meye hkan? Ki zauna dai dai mana karda kiji ciwo." Snn tayi saurin gyara zamanta Abba yaja mota Yatafi yana dariyarta, suka d'auki hnyar kano." _dijama a birni ikon Allah🤔_ [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_😅) Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) 8⃣ Hassan dake waya da Husaini yanajinsa yana kalmar shahada a waya, gaba d'aya hankalinsa ya tashi ya fito da saurin shi baibi ta kan kowaba ya shiga motarshi yajata da k'arfi ya mik'i hanya, ya nufi wurin da yaji Husaini yace masa ya kawo." Cikin minti talatin ya isa wurin ya d'aga wayarsa ya shiga kiran wayar husaini, d'aya daga cikin wad'anda suka kawo masu taimakon gaggawa, ya d'aga wayar yashiga yiwa Hassan bayanin abunda ya faru, ya shaida mashi da cewa gasunan Asibity, Had'ida yimashi kwatancen asibity dasuke." Cikin tashin hankali Hassan yanufi Asibity idonsa yana zubar da hawaye kamar macce." A Gaban gawarsu yake dur'kushe yana kuka yana jijjiga Husaini yana fad'in "Husaini katashi don Allah karka mutu kabarni rayuwata idan babu kai bnga amfaninta ba, kai kad'ai ne d'an uwana jinina Wanda nake shawara dashi husaini katashi." Kuka yakeyi sosai kamar ya d'auke numfashi yana jijjigar gawar Husaini." Mutanen wurin suka tallabeshi suka bar wurin dashi ana bashi hkr, Snn dga k'arshe yakira mahaifan Bilkisu da sauri suka zo, snn ya kira Kaka da tsohuwa, a tare sukazo asibity aka d'auki gawarsu aka nufi Kano da su gidan Hassan akayi masu wanka da sutura aka kaisu gidansu na gskiya." A nan gidan Hassan akayi amsar gaisuwa, Inda Dijama tana rungume a hannun tsohuwa tana bata madara." Hassan yayita lallashin tsohuwa akan ta amince tabari Hajara taci gaba da shayar dasu tareda fateema, Amma tsohuwa ta kafe tace "sam bazai yiwoba, kuma da anyi sadakar bakwai zatayi tafiyarta gida, tare da dijama tazata tafi Dan bazata bartaba." Hankalin Hassan ya kuma tashi, ya shiga rok'on tsohuwa akan ta amince ta bar masa dijama zai kula da ita ya had'ata da 'ya'yanshi yanda bazata tab'ayin maraiciba." Tsohuwa tace "Sam bazai yiwoba, itama ita zata dinga gani a gabanta tana jin sanyi tana d'ebe mata kewar Husaini da tarasa." Hakan akayi bayan sadakar bakwai ta harhad'a kayanta ta goya Dijama zata tafi, direba yana jiranta." Hassan da iyanlansa suka yomata rakiya, ko wannensu idonshi cike da hawaye domin ji sukeyi mutuwar Husaini ta kuma dawo masu sabuwa." Mahmud kuka yakeyi sosai yana birgima yarik'e tsohuwa yana fad'in bazataje masa da dijamarsaba." Kuka yakeyi sosai kowa ya tausaya masa, tsohuwa tace a had'o masa kayanshi sutafi tare idan hutunsu na mkranta ya k'are sai aje a d'aukoshi, tun da daman hutun makaranta sukeyi." Haka kuwa akayi, aka had'awa Mahmud kayansa yana murna yana dariya, sukayi masu rakiya zuwa mota direba yazasu suka d'auki hanyar Tofa." Wnn shine dalilin zaman dijama a wurin tsohuwa a cikin k'auyen tofa." Tsohuwa bata son jin kukan dijama bata son ganin b'acin ranta, Haka mahmud da zarar akayi masu hutun mkranta zai tsira fita a kan dole sai ankawoshi wurin tsohuwa yaga dijamarsa." Itama dijama tun tana k'arama da zarar Mahmud yazo hutu, bata kuma yarda da kowa sai mahmud a tare sukecin abinci a tare suke kwana, idan tayi kashi shike wanke mata, shike mata wanka, zarar hutunsu ya k'are Idan direba yazo d'aukarshi, da kuka da komai suke rabuwa, Tsohuwa tana jijjinawa wannan shak'uwa tasu, haka shima Abbah wato Hassan kenan shima yana jijjinawa wann soyayyar tasu." Wnn dalilin ne yasa mahmud duk lokacin da suka samu hutu baya iya zama garin kano sai dai yatahowarsa Tofa yayi zamansa saboda dijama, har zuwa yanzun da girma yazo masa ya mallaki hnkalin kansa yashiga jami'a a yanzun yana zangonshi na k'arshe a dgree d'insa." Tun tashin dijama a rayuwa babu abunda ta nema ta rasa, domin tsohuwa da Kaka da muhmud basu da wani buri da yawuce a koda yaushe su farantawa marainiya, basa son ganin kukanta." Abba shike d'auke da karatunda da duk wani Abu da yashafi rayuwata, tunda tsohuwa ta kafe a kan cewa baxata bashi itaba, amma shi har ga Allah yaso ya d'auki dijama ya had'ata da yaranshi yabata gata Wanda yin hkan shi zai sanyashi ako da yaushe zai dinga ganin kamar Hussainin shi yana nan bai mutuba." Tun tashin Mahmud shi mutum ne mai son a girmama shi, baya d'aukar raini a gida ko a waje, K'annansa su fateema da zarar yashigo a gida kowa yake kama Kansa, idan ba hakan ba da zarar sunyi abunda ba dai dai ba a nan take zai hukuntasu. Ya azzabtar dasu yayi tafiyarsa." Wnn dalilin ne yasa yaji ya tsani dijama saboda rashin jinta, gata bata gane karatu, Kuma bata ganin girmanshi kwata kwata ta rainashi raininda ba Wanda ya tab'a yi mashi irinshi." Tsohuwa bata ganin laifinta duk rashin kunyar da zatayi jan maganar da zatayi a waje tsohuwa bata ganin laifinta, Wann dalilin yasa a rayuwarshi yaji ya tsaneta basa shiri kwata kwata.wani lokaci Sai ya d'auki niyar cewa bazai k'ara zuwa Tofa hutuba saboda rashin kunyar dijama, Amma da zarar anyi masu hutun ko na kwana biyu ne baya iyawa sai yazo Tofa yayi hutunsa snn ya koma." Kamar ynzun da Hutu yazo yayi, bai iyar da kammala hutun nashiba, ta had'ashi dasu Buba, ya tattara kayansa ya koma warsa gida Wanda tsohuwa tacika da mmki." *Wnn kenan mudawo labari* *************** Mahmud na komawa gida, kowa ya cika da mmki dan ganin hutunsu bai k'areba ya dawo." Abba ne yakirashi a falonsa yana tare da momy mahaifiyarsu yashiga tmbayar sa, lafiya me yadawo dashi bayan ba hakan ya sababa hutunsu bai k'areba?" Murmushi yayi ya sunkuyar da kansa yace " Ba komai Abba hakan nan kawai nadawo babu abunda ya faru." Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "ina fatan kowa yana lafiya?" Ya 'yata Ummie ina fatan tana cikin k'oshin lfy?" Murmushi mahmud ya k'ak'aro yace kowa lfy Abba. Kaka ne kawai yake fama da ciwon k'afa, amma kuma yaji sauk'i sosai." Abba yace subahanallahi!!! Ai kuwa zanje cikin _weekend_ d'in nan nadiboshi, Momy tace "Allah yabashi lafiya." Suka amsa da "Amin gaba d'ayansu." Snn Abba yayi kyaran murya yadubi mahmud da kyau yace "dama ko baka dawoba zankira ka, a waya nace kadawo, domin Alhaji Atiku commonden d'in sojoji wnn abokin nawa yayo mun waya a kan cewa anfitarda form na sojoji ya d'aukar maka d'aya, Saika had'a takardunka katafi Abuja cikin satin nan zakuyi jarabawa Allah yabada sa'a yasa a dace." Suka Amsa da Amin." Sannan Mahmud yayi masu sallama ya fito yanufi d'akinshi yana kuma jin haushin dijama a ranshi." ************** Dijama zaune a kusa da tsohuwa tana turo baki, tsohuwa nayi mata fad'a akan ta fara gajiya da halinta kullum saita janyo mata fad'a da fitina a mak'ota." Ta mik'a mata kud'i tace "gashi kitafi gidan jummai ki kai mata kud'in zubi, dan Allah dijama karki tsaya kuma karki kula kowa a hnya kiyi tafiyarki." Mik'ewa tsaye tayi had'ida turo baki tana gun guni, sannan ta karb'i kud'in ta fita." Tana tafiyarta cikin natsuwa abunda bata tab'a yiba, k'awayenta su lantana tagani sunfito daga rafi, suka had'a baki suna mata magana suna cewa "dijama 'yar gidan tsohuwa sai ina?" Bata tsaya ta kulasuba sai dai ta nuna masu da hannu tana tafiya tace "Tsohuwa ta aikeni gidan jummai nakai kud'in zubi, batajira taji amsarsu ba, tayi tafiyarta, sab'anin da, da sai ta tsaya sunyi jan magana snn kowa ya kama gabansa." Mmki suka shiga yi ko meyasamu dijama?" Lantana tace ko dai batada lafiya ne?" Suka had'a baki sukace lafiyarta k'alau akwai dai abunda ke damunta." Sukace "Allah ya kyauta gaba d'ayansu sannan sukayi tafiyarsu." Dijama anfara jin mgnar tsohuwa kenan, hnmmm Bari dai mugani." Tana gafda da zata shiga gidan jummai mai adashi, taci karo da Antyn lantana wadda tabata takarda ta kaiwa yaya Mahmud, ta sha gabanta tana fad'in "yawwa dijama shine nabaki sak'o ki kaiwa yayanki d'an birni shine baki bashiba kika yaga." Bata tanka mata ba, sai ma k'ok'ari takeyi tabi ta gefenta ta wuce, ta kuma tarar gabanta, tana d'auke da k'waryar da tayo nik'an dawa a kanta, Tacewa dijama "wani sabon iskanci kika samo wadda idan ana yimaki mgna kidinga kyale mutane, taciyo kwalar rigar dijama." A rayuwar dijama babu abunda ta tsana irin a rik'e mata kwalar riga, cike dajin haushi ta dubeta tace "lallai ma Antynnan harda wani rigemun riga, bakisan ina ragamaki bane a k'auyen nan saboda lantana amma yau zakisan kowacece dijama." Ta duk'a kamar wadda wani abun nata ya fad'i a k'asa zata d'auka, Tasanya hannunta ta yaye k'afar Antyn lantana, sai gata tafad'i k'asa dab'as kwaryar nik'an dawa ta rabe biyu, nik'an ya zube k'asa Ta rik'e k'ungunta tana fad'in "wayyo Allah nashiga uku K'uguna dijama kin lahantani." Me dijama zatayi idan ba dariya ba, tace "dankinga ina ragamaki, lallai ma Antyn nan to ba tsoronki nkejiba, ni bana tsoron kowa a garin nan ki kiyaye ehe." Babu abunda antyn lantana takeyi sai kuka da murje2 sboda masifar rad'ad'in da k'ugunta yake mata." Dijama nayi mata dariya, ta rab'ata zata wuce, saiga samarin Antyn lantana sunbiyo ta wurin, zasu wuce Ganinta sukayi zaune a k'asa warwas dafe da k'ugu tana kuka tana fad'in wayyo dijama kin lahantani wayyo k'uguna." Dijama na ganinsu taja da baya ta koma hanyar gida, ta arce da gudu, basu ankaraba sai ganinta sukayi tana gudu kamar filfilwa ta kusan shanye kwanar gidansu." Dijama ba dai guduba kamar mai Aljanun gudu." Saurayin Antyn lantana yace "nayi Alk'awarin tunda dijama tashigo gonata saina saita mata hankali A garin nan." Yashiga taimakon budurwanshi ya mik'ar da ita tsaye ya rakata yarakata har k'ofar gida sannan ya juya ya tafi." Dijama na shanye kwana gidansu sai hango motar Abban kano tayi a jiye a k'ofar gidansu, murna tashigayi tun daga nesa ta dinga stalle Tana "Abba oyoyo." Kai tsaye taje kan jikinshi ta fad'a tana dariya tana murna ganinshi domin Abban kano yana sonta sosai, Murna yayi da ganinta yashiga shafar bayanta yana fad'in "Iye Ummie na ta girma, kina nan kina karatu kuwa?" Taji gabanta ya fad'i domin Abba baya wasa idan akazo fagen karatu." Tayi saurin kauda maganar da cewa "Abba ina su fateemah?" Yayi dariya yace sunanan lfyrsu glau, suna gaisheku." Anan suka shiga shirya Kaka domin a d'aukeshi a tafi dashi asibity dake cikin garin domin a kuma diba mashi lfyar k'afarshi." Alhmdulillah anyi mashi aune aune angano ciwon k'afar da sauk'i, aka rubuta mashi magani Abba yasawo mashi sann suka dawo gida." Anan Abba yace zai kwana sai gobe idan yaga ynda jikin Kaka ya kwana snn sai yatafi gida ko da marecene yatashi safiyar _Monday_ a garin kano." Tun zuwansa garin bai hutaba, mutane ne cingim a k'ofar gidan tsofaffi da samari, Abba sai rarraba masu kud'i yakeyi suna godiya tare da sanya mashi Albarka." Abba mutum ne mai taimako da tausayi, wannan dalilin ne yasa mutanen cikin garin tofa suke mutuntashi da darajashi." Washe garin ranar lahadi da safe, misalin k'arfe goma na safe, Abba yana stakar gida zaune, tsohuwa na gefensa d'aya gefensa Kaka ne zaune da sandarsa gefensa a jiye, Abba yana b'are mashi ayaba yana bashi yanaci had'ida sanya mashi Albarka." Dijama na cikin d'aki zaune ta fito daga wanka tana tsara kwanliya." Fuskarta tasha kwalli da jambaki da hoda." Tsohuwa tashiga kiran sunanta tana fad'in "dijama kiyi Sauri Ki shirya kizo na aikeki gidan kuluwa ki kaimata tsarabarda bbnki yazo da ita." To dijama tace had'ida mik'ewa tsaye ta d'auki kayanta tasanya Snn ta fito." Tsohuwa ta mik'a mata Leda cike da ayaba da lemu tace "ungo ki kai mata kuma Dan Allah karki tsaya a kan hanya." Tace "to." Ta karb'a had'ida fita, Abba ya dubita yayi murmushi yace "Ummie ba dai wayoba." Tsohuwa tayi dariya, Kaka kuma yace "hmmm yaja bakinshi yayi shuru." Bayan ta dawo aiken datsohuwa tsohuwa tayi mata tana tafiyarta a hanya tana wak'a tana rawa, tana d'an karkad'a k'ugunta." Wazata gani Buba tagani a gabanta yana wasar Baki yana fad'in dijamata kinyi kyau wnn kwanliya hkan." Bakin buba ta kalla inda har ynzun bai iyar da warkewa ba daga kumburin da yayi." Batasan lokacin da dariya ta sub'uce mata ba, Ta dubeshi tana dariya tace "Wai amma dai Yaya mahmud ya iya duka." Wai kai Buba kana aikin me harya kumbura baka Baki, ta kuma shek'ewa da dariya, ta dubeshi Tace a hkan kake cewa zaka aureni. Allah ya tsaran da auren ragon mutum kamarka, Ni nafison na aure jarumin namiji mai firgita 'yan maxa, amma kai ai macce ne." Ta rab'ashi ta wuce tana dariya, Buba yaji haushi ya k'ulu iya k'uluwa, idonsa ya canza launi zuwa ja, ya zunduma ashar, Wanda yasa dijama saurin juyowa da sauri tana kallonsa." Yace "duk son da nake maki dijama yau bazai hana naci ...... Ya zunduba wani kalar shar ya dafawa dijama da saurinshi cikin hushi." Dijama na ganin hakan ta zuba da gudu ai kuwa buba ya dafa mata, da yaranshi." Gudu takeyi tana kuwa tana fad'in "wayyo Allah jama'a kutaimakeni 'yan fashi wayyo Allah 'yan fashi.da makami" [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Written By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *10* Gafda da sallar magariba suka isa gida, Horn Abba yakeyi baba maigadi yafito da saurinshi ya bud'e mashi get yashigar da motar sa." Dijama sai waige waige takeyi tana kallon yanayin tsarin ginin gida." Abba da kansa ya bud'e mata murfin mota tafito, ya zagaya but ya d'auko jakar kayanta ya rik'e mata suka jera a tare suka shiga ciki." Gaba d'aya family gidan suna kan dinner table suna cin abinci cike da burgewa, Abba yayi sallama da gudu Fatima ta rugo ta rungumeshi tana oyoyo Abba." Ba Wanda ya lura da dijama a gefensa, yaya muhmud daya kai lomar tuwon shinkafa miyar a gushi a bakinsa ya d'aga kansa sama yana murmushi zaiyiwa Abba sannu da zuwa karaf yayi da dijama a tsaye a gefen Abba." Kasa iyar da had'iye tuwon yayi, ya rik'e baki yana nuna dijama batare da yayi maganaba." Sai a lokacin hankalin kowa ya tafi wurin dijama dake tsaye sai zarar ido takeyi, Khalil na ganin hakan yatashi yaje wurin Abba yayi mashi sannu da zuwa, had'ida kallon dijama ya mere baki☹ Ya ranb'a ta gefensu yayi tafiyar shi." Khalil dama hakan yake ko oho gareshi, a rayuwarshi bbu abunda ya tsana sama da mutumin k'auye bagidaje, ko kuma yayi ido biyu da mummunar mace, Wnn dalili. Yasa baya zuwa Tofa gurin Tsohuwa, Ya kuma yiwa kansa Alk'awarin bazai tab'a auren macce mummunaba, ko bagidajiya, sai Wanda ta amsa sunanta macce ta ko ina." Fateema tayi saurin sakin Abba taje ta rungume dijama tana fad'in oyoyo dijamar tsohuwa kai amma. Naji dad'in zuwanki." Hakan itama momy tazo ta kama hannun dijama gaba d'aya suka zauna a kan kujera har da Abba." Mahmud dake zaune a kan dinner table ya kasa motsawa kamar wani mattance saboda ankawo masu fita a gida." Muryar Abba ta ankarar dashi dayaji yana cewa "mahmud lfy kake kuwa ka k'ame wuri d'aya kamar Wanda baya motsi, Bakaga 'yar gidan taka bace Ummie?" Bayan nan tukuna tashi mutafi masallaci mu farayin sallah sann mudawo muyi magana." Mik'ewa sukayi suka nufi masallaci domin gabatar da sallar magariba." Da fitarsu momy ta kama hannun dijama cike da kulawa tace "ummie ya hanya?" Ya kuka baro Kaka da tsohuwa?" Dijama tace "lafiya glau sunce a gaisheku." Murmushi momy tayi, ta kai dibonta ga fateema tace "fateema d'auki kayan 'yar uwarki ki kaimata d'akinki, kibata ruwa tayi Arwala kuyi sallah ki kuma taimaka mata ta cire kayan jikinta kibata d'aya daga cikin kayanki ta sanya sannan kufito taci abinci." Cikin ladabi da biyayya fateema ta "amsa da to mmy, sann ta d'auki jakar kayan dijama had'ida rik'a hannunta suka nufi d'akin fateema. Ita dai dijama biye take sai zarar ido takeyi tana kale kale." Suna tafiya momy itama ta tashi tayi Arwala tayi sallah, tana kammalawa yayi dai dai da shigowar Abba da mahmud." Abba ya dubi Mahmud yace "kaje kafad'awa khalil da zarar munyi sallar isha'i kuzo gaba d'ayanku inaso zanyi mgna daku." Mahmud ya d'an runsuna yace "to Abba." Yana so ya tambayeshi dalilin da yasa yazo da dijama masifa amma baiga fuskaba a wurin Abba hakan yanufi d'akinshi da yana sak'awa yana kwancewa a ransa." Bayan Abba yayi wanka yaci abinci yayi sallah isha'i yana gincire a tsakar falonshi momy na gefenshi tana yanka mashi kankana tana bashi yana sha suna firarsu cike da kulawa da sha'awa." Mahmud da khalil sukayi sallama saka shigo, sannan fateema tareda dijama suma suka shigo, suka zauna a gefen momy." Babu abunda khalili yakeyi da yayi ido biyu da dijama sai ya mutsa fuska kamar Wanda yaga kashi." Dijama na lura dashi, ta wurga mashi harara had'ida murgud'a mashi baki, Karaf sai a kan idonshi, zaro ido yayi yana kallonta cike da mmki." Abba ya katse masa tunani da yafara magana [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Written By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *11* "Abunda yasa na taraku a nan sai Dan in gabatar maku da 'yar uwarku, Ummie ya nuna dijama dake zaune a gefen mmy." Yanuna khalil "Musamman kai khalil da bakowa kasani ba a cikin dangi, saboda baud'and'en ra'ayinka, Amma kasan ko wacece dijama, kasan matsayinta a gidan nan, Baka buk'atar na kuma yi maka wani dogon bayani a kanta." Ya kuma maida hankalinshi a kan Mahmoud, yace "Mahmoud ga k'anwarka nan nasan kafi kowa farin cikin dawowarta gidan nan baki d'aya." "Abunda nakeso daku Ku d'auketa kamar yanda kuka d'auki fateema a wurinku, kubata kulawa kamar yanda kuke bawa fateema, kai inma son samune Kubata kulawa fiye da ynda kuke bawa fateema saboda Ummie marainiyace." Sai a lokacin mahmoud yayi mgna yace "Abba meyasa ka d'auko mana dijama?" Abba dijamar da kasani a da ayanxun ta canza hali, Na rantse da Allah dijama tana iya tayarda gidan nan da unguwar nan gaba d'aya saboda hatsabiban cinta." Nidai Abba dazakaji sha'warata da anmayar da dijama can Tofa Dan tafi ganewa can, kowa ma sai yahuta." Dijama tayi saurin d'ago kai ta dubi yaya Mahmoud ta murgud'e mashi maki cike da tsiwa, ta karkace kai tace "lallai ma yaya nan wai a mayardani tofa to sannu." Khalil yayi saurin nufarta ya sanya hannu ya buge mata baki, dama yana ganin take takenta saitayi rashin kunya." Dijama tayi saurin rik'e baki, tana fad'in wayyo Allah na ya fasa mun baki" "Yace k'azama 'yar k'auye, yaya muhmoud d'in kike yiwa rashin kunya?" Abba ya doka masu tsawa cike da b'acin rai yace "kar in kuma ganin d'aya daga cikinku ya kuma dukanta, bana son hkan, Na rantse akan Ummie zan iya sab'awa da kowa a cikinku, domin ganin farin cikinta, na kuma rik'e Amanar d'an uwana." Ya maida kallonsa zuwa wurin mahmuod yace "Kai Mahmoud yaushe kuka fara 'yar hakan da kaida Ummien taka?" "To koma dai me takeyi a can k'auye ba ruwanku, Domin yanxun ta baro k'auye ta shigo birni." Rayuwarta zata canza, kuma banason tsangwama da hantara a tsakaninku." "Idan Allah ya kaimu gobe kaje makarantar su fateema, Kasan yanda za'ayi ayo mata takardun shedan ta kammala primary sannan, sai a sanyata a jss1 sai suci gaba da karatunsu tare da fateema." Kai kuma khalil kaje islamiyarsu fateema ka yanko mata form a d'unka mata uniform sai ta tafara zuwa." Batare da sun musaba suka amsa da "to Abba." Ya dubesu yace "Allah yayi maku Albarka." Suka amsa da Amin." Sannan ya dawo wurin fateema yace "fateema ga 'yar uwarki nan Ku had'a kanku, kiko ya mata wasu abubuwa wad'anda batasaniba, Kuma ina so ki d'auketa tamkar 'yar uwarki Asma'u da kika rasa, Allah ya jikan Asma'u da rahama suka amsa da amin gaba d'ayansu." Sannan ya basu umurnin kowa ya tashi, Bayan sunfita ne ya kuma kiran Mahmoud ya dawo ya tsuguna, Yace "ya kukayi da baban naka Alhaji Atiku?" Mahmoud ya sunkuyar da kai, yace "zuwan danayi Abuja wurinsa ya karramani sosai, sannan ya turani mukayi jaraba." Yace kuma "nafad'a maka musanya ido daga nan zuwa wata biyu za'a lik'a sunayen mutanen da sukaci, sannan zai kirani mutafi wurin trening Abba yayi murnushi yace "karka damu indai Alhaji Atiku ne kasanyawa rayuwarka har kazama soja." Momy tace "Allah ya taimaka ya tayaka rik'o da gaskya." Suka "Amsa da Amin." Sannan yayi masu sallama yatashi ya fita." Abba ya dubi momy da sai murmushi takeyi d'auke a kan fuskarta, Yace momyn yara babu abunda zance maki a rayuwa sai dai Addu'a domin kinsamarmun farin ciki a cikin zuri'ata Allah ya barmu tare dake, babban burina shine na faranta maki har k'arshen rayuwarta." Ya Matso daf da ita, yarik'a hannunta ya shiga murzawa yana kallonta had'ida kashe mata ido d'aya." Yace "kinsan wani Abu kuwa?" A kasalance ta dubeshi ta girgiza kai alamar A'a." "A kullum idan ina tare dake jinakeyi tamkar ina tare da yarinya yar shekara 17, saboda komai naki na dabanne a koda yaushe yarinya kike komawa." Ya kuma shege mata a jiki yana shishinar daddad'an k'amshin jikinta, had'ida sab'ule mata d'ankwalin kanta yana shafa gashin kanta dayasha gyara da mayunka masu Sanya laushin gashi da santsi uwa uba kuma k'amshi." _Ina ganin hakan nayi saurin fitowa cike da mmkin su Abba da momy ba'a tsofa🤔_ Mahmoud yaje makarantarsu fateema yayi duk abunda Abba ya umurceshi, ya k'arb'o mata uniform d'inta da littafanta yataho mata dasu, Ranar Monday zata fara zuwa makaranta." Da sallamarshi ya shigo cikin babban falon gidan, ba kowa a cikinsa, sai tausin k'arar TV kawai yakeji yana tashi, gefe d'aya yaji sai dariya akeyi harda buga k'afa.' Koba'a fad'a masaba yasan dijama ce." Mmki yashigayi yanufi wurin TV yayi saurin kashewa, Ya juya ya kalleta, sukayi ido biyu da ita, ta turo baki tana hararsa k'asa k'asa." Cikin fushi yace "lallai d'an k'auye yashigo birni yafara wayewa, Tomu a nan gidan ba'a mana kallo a k'urema volume, anan gidan karatu akeyi a koda yaushe ba zaman shashnciba da rashin kunya, takwala kawai Wanda bata gane karatu." Ya jefa mata ledar kayan makarantarta yace "gasu nan ki kwana da shiri gobe Monday zaki fara zuwa makaranta, kuma nizan kaiki da kaina, zan shaida masu cewa baki gane komai kwakwalwar kifi ce dake, kuma da zarar kinyi masu irin rashin kunyar da kikeyi a k'auye, zance suyi fata fata da naman jikinki su jefar dake a bula." Dama tsohuwa ke tare maki yanxunfa?" Kallonshi tayi idonta cike da hawaye domin a rayuwarta bbu abunda ta tsana irin yaya Mahmoud ya kirata da takkwala mai kwanyar kifi." Shima yayi mmkin ganin zubar hawaye a idon dijama anan take lokaci d'aya." Zata bud'a Baki tayi magana kenan ya matso daf da ita, yace "muddun kika bud'a baki kikayimun rashin kunya saina tattakaki." Ta fasayin maganar ta sunkuyar da kanta k'asa tana aika mashi da Allah ya isa a zuciyarta.' Mik'ewa tayi tsaye ta d'auki ledar uniform d'inta, saida ta kwatanci saiti wurin k'afarshi ta sakar mashi remote d'in TV a babban d'an yatsan k'afa, sai da yayi sarin runtse idonshi yace "washh." Saboda zafin dayaji wurin namasa." Ta zuba da gudu ta haiye sama tanufi d'akinsu, taja tayi tsaya a bakin k'ofar d'aki, tana kallonshi tana burgud'a baki tace "kuma bani bace takwala sai dai inkaine." Kuma tunda kakeyimun gorin karatu saina baka mamaki mugu kawai, dan kana ganin nazo gidanku, to kasani duk abunda kakeyimun a rubuce yake a kaina saina fad'awa tsohuwa." Ganin ya nufota tayi saurin shigewa d'akin had'ida sanyawa k'ofar key." Tsaye yayi yakasa tafiya yana kallon babban d'an ya tsanshi da ya somayin ja, Yana tunanin dijama wato bata daina halintaba kenan lallai akwai aiki a nan gaba." Yana nan tsaye wuri d'aya saiji yayi andafashi a bayanshi, Khalil yagani yace "brother lfy kayi tsaye a nan?" Su momyn basu dawobane?" Mahmoud yace "fita sukayi ne? "Khalil yace "sunje gidan gaisuwa tare da Abba." Ya mik'awa Mahmoud wani takarda Mahmoud ya karb'a yana dubawa yana cewa "takardar meye?" Khalil ya yamutsa fuska yace form d'in islamiyar wnn bagidajiyar nan ne, wadda Abba yasanyani karb'owa, nagama cika komai sunanta ne kawai bansaniba, Wlh bnsan abunda yasa Abba ya dawo da ita gidan nan ba, da zarar munyi ido biyu da ita jinakeyi kamar zanyi amai." Mahmoud ya dubeshi yace "khalil 'yar uwarka face, gakya ya kamata ka canza hali Kuma ka canza rayuwa, kadaina ganin 'yan matan Jami"a kyawawa wayayi suna rud'arka har kake kyamatar jininka. To kasani asalinka k'auye a can Abbamu ya tashi a can ya girma har gobe mahaifansa suna k'auye." Wani saurin ja da baya yayi yana duba bayansa, ganin baiga kowa a wurinba yace "haba brother bazaka gane bane, nagodewa Allah da bakowa a kusa dani lokacinda kake fad'in hakan daka sanyani naji kunya." Ido Mahmoud ya tsora mashi yana mmkinsa domin yanda ya d'aukeshi sai yaga ya wuce nan." Takarda ya mik'a mashi yace "ynda bakasan sunantaba nima bnsan sunantaba, kabari idan Abba ya dawo shida ya sanyaka saika tmbayeshi sunanta kagani sai ya fad'a maka." Yana kawowa nan yayi tafiyarshi ya barshi nan tsaye zuciyarshi cike da mmkin khalil." Khalil yabi mahmoud da kallo yace "ya za'ayi na tambayi Abba sunanta, nasan yanda yakejinta a gidan nan yana iya kafsamin a gabanta Zan dai jira har lokacin da fateema dawo daga mkranta saina tambayeta." Yajuya yanufi d'akinshi yana mamakin mohmuod ganin yanda shima yakeji da wann bagidajiyar a gidan nan☹ [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Written By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *13* Da sauri shugaban mkranta ya nufo ajin har da tuntub'e. Yakeyi domin lbrin da ya isar mashi anjiwa 'yar ciyaman da 'yar kassila ciwo." Ganin saurin da yakeyi yasa sauran malamai suka fahimci a akwai abunda ke faruwa, suka rufo mashi baya." Ganin jinin dake zuba a bakukansu ya d'agawa malamai hankali. Anan take aka Shiga basu taimakon gaggawa." Shugaban makaranta ya d'aga waya ya kira ciyaman da kassila yake shaida masu abunda ke faruwa." Ko wannensu cikin tashin hankali suka bugawa jami'an tsaro waya, anan take mota biyu ta 'yan sanda kamar had'in baki, motar ciyaman da motar kassila." Suka shigo cikin mkrantar sai jiniya kukeji kamar za'a tashi makarantar, 'yan sandan kowanensu da zungureriyar bindigarshi a hannunshi." Sai tambaya sukeyi ina yarinyar da taji masu ciwo, a wuce da ita atafi da ita a hukuntata." Dijama dake tsugune gefe d'aya sai Zarar ido takeyi ta karkace kai duk Wanda ke magana tana binshi da kallon tana kallon bakinshi." Turanci kawai takeji yana tashi Wanda bata san abunda suke cewaba kallonsu kawai takeyi." Can taga shugaban makaranta ya nunata da yatsa yana fad'i da Hausa yana cewa "kunganta can itace, yau yau d'in nan da zuwanta makarantar nan amma har ta fara dazamun bala'i." Shekarata goma sha d'aya da bud'a makarantar nan hakan bata tab'a faruwa daniba sai zuwan wann fiti nan niyar yarinya." Tsawa aka dokawa dijama Wanda yasa tayi saurin mik'ewa tsaye saboda ganin zungureriyar bindigar dake hannun d'an sandar." Tashiga ja da baya tana "fad'in Dan Allah kuyi hak'uri karku harbeni sune suka fara tsokanata." Fateema kuma babu abunda takeyi sai aikin kuka, Wanda a cikin mutanen wurin bbu Wanda ya lura da ita tana gefe d'aya a tsaye." Kuma doka mata tsawa d'an sandar yayi, yace "ba kasheki zamuyiba tafiya zamuyi dake sai munji ko waye ubanki a garin nan snn mu d'aukar mki hukunci." Haka aka sanya k'eyar dijama a gaba tare da shugaban mkranta aka sanyasu a mota aka tafi dasu." Dijama sai Zarar ido takeyi wuk'i wuk'i a bayan mota, shugaban makaranta da juya ya kalleta sunyi ido biyu da ita sai ya wurga mata harara." A zuciyarshi yana da yasani karb'arta da yayi a matsayin d'aliba." Fateema na ganin antafi da dijama, ta kuma fashewa da kuka, tayiwa wani malami magani tace "dan Allah uncle kabani Aron wayarka zankira Abba na na fad'a mashi abunda ke faruwa." Zaro ido yyi cike da mmki yace "dama kinsanta ne?" Ta d'aga kai alamar "eh tace yayata ce uwarmu d'aya ubanmu d'aya." Uncle ya xaro ido waje yace "kina nufin 'yar Alhaji Hassan Adam CE?" To ya akayi bansanta ba a cikin gidanku?" Cike dajin haushin tambayarshi fateema ta turo baki tace "bazaka Santaba saboda ba'a garin nan takeba, dan Allah uncle kabani aron wayar mana." Yace "Ayyah fateema kiyi hak'uri banada waya a hannuna, amma nasan za'aje da ita ta nuna gidansu." _kuyi hk'uri d wnn pls yau sai a hnkli_ [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Written By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *12* 7:30am. Shiri sukeyi domin zuwa makaranta, tasanya uniform dinta, wad'anda sukayi mata kyau sunfito mata da fuskarta sak 'yar fillo." Fuskar nan tata tasha hoda da jambaki, fateema dake gefenta zaune, ta dubeta tace "dijama ki goge wnn kwanliyar ta fuskarki tayi yawa sosai idan mukaje Anty tana iya sanya hijabinki fari ta goge mki ita." Ta murgud'a baki tace "bazan gogeba, a hakan zanje kuma bata isa ta gogemun kwanliya taba." Fateema zata kuma yin magana tajiyo sautin muryar yaya Mahmoud yana fad'in "wai bazaku fitoba lokaci fa na tafiya, Allah duk kuka kuskura kuka bari na hawo saman nan sai jikinku ya gaya maku." Da sauri fateema ta d'auki school bag d'inta ta goya. Bata kuma bi takan dijamaba don tasan halin yaya Mahmoud ba sauk'i ne dashi ba." Dijama da ke k'ok'arin sanya sendel a k'afarta tana turo baki cikin magana k'asa k'asa tace "to idan ka hawo karka barmu da rai ka kashemu." Ido fateema ta zaro waje tace "yayan kike cewa hakan lallai dijama bakisan halin yaya Mahmoud bane, tana fad'in hakan tayi saurin bud'e k'ofa ta fita, tabar dijama na sanya takalmi." Tana gama sanyawa itama ta biyo bayanta, ta fito tana tafiya harda wani rangwad'a takeyi wai ita 'yar boko." Gaba d'anyansu Suna babban falo zaune suna Brest fast, Abba da shirinsa na zuwa Office khalil shima da shirinsa zuwa makaranta BUK." Mahmuod a tsaye da key d'in mota a hannunshi yana jiran fitowarsu ya kaisu, yadawo yana da inda zaije, har sun b'ata mashi time." Fateema ta fara fitowa sann dijama ta biyo bayanta, Abba na ganinsu cikin uniform yaji dad'i sosai sai murmushi yakeyi a fuskarshi, Momy itama murmushin takeyi tana fad'in "iye 'yan matana lallai kunyi kyau musamman 'yata ummie." Mahmoud dake tsaye gefe d'aya yanayi yana kallon agogon gwal dake d'aure a hannunshi." Khalil ya d'aga kansa yana ya mutsa fuska yana kallon dijama. Da take k'ok'arin k'arb'ar flast d'in break d'insu. Wanda momy ke mik'a masu, Ido biyu yayi da fuskar dijama datasha kwalliya, mai zaiyi idan ba dariya ba, Dariya yakeyi yana nuna fuskarta yana fad'in tab "mutumin k'auye baiyi ba wlh ke wai kwanliyace kikayi hakan ko meye?" Brother wlh karka bari wnn abar ta shigar maka mota, ai sai kuzama abunda kwatance duk inda kuka gifta." Cikin zafin rai Abba ya doka mashi tsawa da k'arfi yace "khalil tashi kafita karna na sab'a maka wlh." Momy Itama tabishi da harara tana fad'in "ni bansan irin rayuwar khalil ba a cikin gidan nan." Ta jawo hannun dijama dake tsaye wuri d'aya tana cije baki had'ida girgiza kai, ranta ya b'aci matuk'a." Mahmoud dake tsaye a inda yake, ya had'e fuska, yayi saurin waigawa ya wurgawa khalil harara cike da jin haushinsa." Mmy ta rik'o hannuta tace "zo nan 'yata na gyara maki fuskarki karki damu da abunda khalili yayi mki hka halinshi yake." Momy tashiga gyara mata fuskarta, ta goge mata janbakin da 'yar gira, ta kuma rage mata hudar fuskarta, Sauran kwallin da tashafa a idonta ne yak'i goguwa. Gudun karsuyi latti momy ta barta haka suka tafi." Bayan sunfita ne Abba ya maida kallonsa ga momy yace "nafara ganin take taken khalil a gidan nan a kan ummie zan d'aukar mashi mummunan mataki idan hakan ta kuma faruwa a kan idona." Inason Allah yabani iko da nisan kwana nacika Alk'awarin da nayiwa d'an uwana kafin ya mutu, na aurawa muhmud Ummie idan ba hakan ba a yanda naga khalil na kyamatarta a gidan nan da bbu abunda zai hana na aura mashi ita, domin kawai naga iya karshi." Hak'uri momy kawai take bashi domin ganin ranshi ya b'aci sosai." A bayan mota suka shiga mahmud bai kulasuba, fuskarshi a had'e, ya tayar da motarsa yaja yanufi makarantarsu." Suna shiga cikin makarantar yayi parking d'in motar shi a cikin harabar makarantar, , tun kafin ya fito dijama ta rigashi fitowa harwani sauri takeyi k'asa na tashi, Da sauri ya doka mata tsawa yace "ke 'yar k'auye da Allah malama ki dawo ki tsaya." Kina wata tafiya k'ura na tashi sallan ki b'atawa mutane jiki da k'asa, 'yar k'auye kawai Takkwala mai kwanyar kifi, kamar da gske sai kace ganewa kikeyi. To bari na fad'a mki nan ba k'auye bane mudun kikayiwa malamai rashin kunyar da kikeyi a k'auye tsinanen dukan tsiya zakici kuma ba Wanda zai rama maki." Juyowa tayi tana kallonshi ta sunkuyar da kanta k'asa, a rayuwar ta bbu abunda ta tsana irin yaya Mahmud ya kirata da mai kwanyar kifi, ta d'aukarwa kanta Alk'awarin cewa zata maida hankali tayi karatu Wanda yaya Mahmud sai yayi mmkinta, a lokacin zata bud'e baki ta mayar masa da raddin takkwalar da yake kiranta da ita." A fusace ya juya wurin fateema da mmkinsa bai gantaba sai ma hangota da yayi ta kusan shigewa class." Gaba ya shige dijama na biye dashi, office d'in shugaban mkranta ya shiga ya gabatar da dijama, sann daga k'arshe gaban idonsa aka kaita class, Aji d'aya aka ajiyesu da fateema kamar yanda ya buk'ata, saboda fateema ta dinga koya mata wasu abubuwa wad'anda bata saniba." Sai da yaga shigarta aji sann ya shiga motarsa ya dawo gida." Da shigarta ajin d'alibai sai kallonta sukeyi ganin yanda ta tsurawa silin roba ido sai kallo takeyi, gaba d'aya sai k'arewa ajin kallo takeyi da kujerun dake ajiye a cikin class d'in." Fateema ta hango a can zaune tayi saurin bud'e baki tare da d'aga murya tace "lah fati Ashe aji d'aya aka ajiyemu ai kuwa naji dad'i." Gaba d'aya ajin suka tuntsere mata da dariya, wata 'd'iyar chiyaman d'in garin, Wanda suke mak'otaka da Abba, tace "amma dai ke 'yar k'auyece wlh." Suka kuma shek'e mata da dariya, wata d'aliba daga cikinsu tace "dubi yanda ta shafa kwanli a idonta, ta fad'i hakan had'ida nuna idon dijama suka kuma shek'ewa da dariya." Dijama taji haushi sosai, fateema ta mik'e tsaye ta kama hannun dijama da tayi tsaye takasa zama saboda jin haushi, ta zaunar da ita a kan kujera kusa da ita." Dijama taja wuri d'aya ta zauna tana sake sake a ranta, Malam mai English ya shigo ya fara yi masu karatu ta kashe kunne ta kwantar da hankalinta tana saurare kuma tana fahimta." K'araurawa taji an buga alamar antashi break fast, hakan yayi dai dai da fitar malma mai English, d'alibai suka fara fita waje domin cin abinci." Da sauri dijama ta duro a kan kujera ta shagaban 'yar gidan chiyaman karon farko mari ta fara kai mata, ta cire hijabin jikinta tasha d'amara cikin d'aga murya tace "ubnwa kike cewa 'yar k'auye?" Tashiga nusarta, baji bagani, saida bakinta ya fashe da jini, gaba d'aya ta b'ata gaban hijabinta, D'aya yarinya wanda harda ita wurin yi mata dariya, ta matso wurin dijama ta cimuimuye mata riga a bayanta, Dijama tasanya k'afa ta bayanta ta shure mata baki, aikuwa yarinya ta kwatsa ihu ta duk'e ta rik'e bakinta da jini yaketa zuba." Ihu 'yan aji keyi da gudu suka fita suka kira shugaban makarantar." Babu abunda fateema keyi sai aikin kuka, Dama kuka baya mata wuya, saboda kwata kwata fateema bata da fad'a batason tashin hankali, sanyin hali ke gareta." [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Written By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *14* 12:30pm Abba ne zaune a Palo ya dawo daga office Mahmud zaune a gefensa yana shaida masa cewa Alhaji Atiku ya kirashi a waya akan cewa ya xama cikin shiri satin nan ya shirya kayansa ya sameshi Abuja domin sunansa ya fito zasu wuce wurin trening." "Alhmdulillahi Abba yace, Yana murmushi cike da jin dad'i da farin ciki, ya dubi Mahmud yace "Alhaji Atiku mutumin k'irkine abokina ne tare muka tashi mukayi makaranta d'aya dashi, A rayuwata ta duniya bbu abunda Alhaji Atiku zai nema gareni banyi mashiba indai baifi k'arfinaba, saboda yanda yake nunamun k'aramci da k'auna." Mahmud inaso idan kaje ka kula da kanka, Kabishi sau da k'afa kayi mashi biyayya kamar yanda kasan kanayi mun Allah yayi mka Albarka." Bai rufe bakinsaba fateema tashigo ko sallama bbu idonta yayi ja alamar taci kuka,har ta gaji." Mahmud ya dubeta cike da kulawa yace "fateema meyasameki?" Abba yace "ina Ummie take?" Kafin tabasu amsa sukajiyo jiniyar motar 'yan sanda a k'ofar gida, Saiga Baba maigadi yashigo da saurinsa ya zube k'asa gaban Abba yace "ranka ya dad'e 'yan sanda na sallama da kai a waje." Abba ya zaro ido cike da mmki yace "yan sanda?" Meyafaru?" Mahmud shima hakan, Fateema ta kuma fashewa da kuka tace "wlh sune, Momy ta taso tashiga girgixata tana tambayarta "sune suwa?" Meya faru?" "Sune wad'anda suka kama dijama suka tafi da ita, Mahmud yayi saurin juyowa ya kalleta, ya kuma kallon Abba da momy, yace "dijama tayi halinta kenan tajanyo mana fitina." Suka d'unguma gaba d'ayansu suka fita, Mahmud ke gaba sai Sauri yakeyi Abba na biye dashi snn momy da fateema." Yana tukarar motar ya hango dijama zaune a bayan mota sai zarar ido takeyi" 'Yan sandan na ganin Abba sukayi saurin fitowa suna gaisuwa gareshi kasan cewar Abba ta fito takarar d'an majalisa na jahar kano, A garin na kano, kowa yasanshi babba da yaro, kuma Abba mutum ne mai yawan Alheri ga jama'a." Tambaya yashigayi meke faruwa?" Anan sukashiga yi mashi bayani cike da girmamawa." Hak'uri Abba yashiga basu, snn dga k'arshe ya d'aga waya kira ciyaman da kassila yashiga bsu hkri ya kuma shaida masu da cewa 'yarsace ta aikata hakan a bisa kuskure." Ko wannensu mmki ykeyi, Gnin basu san dijamaba." Anan sukayi sallma da cewa ko mai yawuce Allah ya tsare gaba." Snn aka fito da dijama daga cikin motar, Abba ya d'auki kud'i masu yawa ya mik'awa 'yan sandar suka amsa suna godiya snn sukaja motarsu sukayi tafiyarsu." Mahmud yayi kanta da sauri, ya rik'o hannunta yashige da ita d'akinsa ya sanya key yashiga jifgarta yana dukanta ba girma ba arxik'i, Ihu takeyi tana fad'in wayyo tsohuwa kizo ki ceceni, Abba da momy sai dukan k'ofa sukeyi amma yak'i bud'ewa, rai b'ace Abba ya nufi d'akinsa ya d'auko extra key ya nufi d'akin mahmud ya bud'e ya shiga." Ya daina dukanta ya sanyata kamun kunne yana zaune gefe d'aya yana kallonta hannunshi rik'e da bulala." Yana ganin Abba ya shigo yayi saurin tashi tsaye yashiga ja da baya, Abba ya rik'a dijama ya mik'ar da ita tsaye, Tana ganin Abba ta fad'a jikinsa ta fashe da wani sabon kuka, tana fad'in "Dan Allah Abba ka taimakeni ka bayar dani wurin tsohuwa idan naci gaba da zama gidan nan yaya Mahmud kasheni zainyi." Abba ya rik'a hannunta yana bata hak'uri had'ida juyawa ya wurgawa Mahmud harara snn suka fita." Da fitarsu mahmud ya sauke ajiyar zuciya, ya fad'a kan gadonsa ya kwanta rufda ciki, Ya shiga tunanin dijama, Sam bayajin dad'in rashin jin maganar da takeyi, babban abunda yafi b'ata masa rayuwa shine akan karatu dijama batason karatu ko kad'an rashin kunya da tujara yayimata yawa a kai." Yashiga tunanin yanZun meye mafita wani mataki ya kamata ya d'aukar mata wadda yin hakan zai sanyata dole ta tsaya ta natsu tayi karatu, Wanda a ynxun ilimi shine gishirin zaman duniya." Idan bakada shi babban cinka da jaki kad'an ne." Makarantar barci boarding school ta fad'o masa a rai, Wani murmushi yayi ya kuma juya kwanciya yace "tabbas makarantar barci zan kaita inda bata ganin kowa da zarar tayi rashin ji abata kashi kuma dole ta tsaya tayi karatu ba Dan tasoba." Hakan dai ya yanke shawarar kaita boarding school kafin ya bar garin hankalin kowa ya kwanta." Mik'ewa yayi yashiga toilet yayi wanka ya fito ya canza kayanshi ya d'auki key d'in motarshi yajata yanufi gidan wani abokinshi Ahmad wadda shima k'anwarshi a makarantar barci take karatu. domin ya tambaye shi abubuwan da yakamata a shiryawa dijama." Abba na rik'e da hannun dijama suka nufi babban Palon gidan, inda momy take zaune, momy na ganinta ta mik'a mata hannu alamar ta taxo gareta, Cikin sauri taje jikin momy ta fad'a tana kuka." Momy sai bubbugar bayanta takeyi tafad'in yi shuru Ummie daina kuka, barni da Mahmud duk yashigo falon nan saina rama mki dukanki da yayi mki." Suna hakan sai ga Khalil ya shigo da littafai a hannunshi, yana fad'in " Momy meya faru yau a gidan nan ina shigowa unguwar nan ake fad'amun 'yan sanda sunzo gidan nan harda wnn ya nuna dijama da hannu don har ynzun baisan sunantaba, suka gani a bayan motarsu." Momy tace "bkmai akwai abunda ya kawosu wurin Abbanku." Ya mere bki da dayaga ynda dijama ta wani shigewa momy ajiki ta lafe." Haushi tabashi ya doka mata tsawa yace "Dan Allah malama ki d'aga mata k'afa karki gajiyar mana da ita." Momy ta wurga mashi harara tace "ina ruwanka?" Meye nka aciki ina ganin dai k'afatace ba takaba." "Momy to karta gajiyar da ke tasanya ciwon k'afarki ya tashi." "Kaga Khalil ni banason tsangwama, kawuce kayi tafiyarka kayi abunda ke gabanka." Momy taja hannu dijama suka tafi d'akinta cikin dabara da hikima tashiga yiwa dijama nasiha, "Ummie na ya kamata a ce kin natsu kin fara sanin ciwon kanki, ki tsaya kiyi karatu domin ki hau wani mataki da mu kanmu zamu yi Alfahari dake." Ki zubarda duk wasu halayanki na k'auye, ki tsaya kiyi karatu ki zama 'yar birni, maiji da kanta." Ki daina tsokanar fad'a, Tace "momy banice na tsokanesu ba, sune suka fara tsokanata suja cemun 'yar k'auye, kuma ni ynxun bnaso ana kirana da 'yar k'auye." Momy tayi murmushi tace "tunda bakiso a dinga kiranki da yar k'auye sai kin tsaya kinyi karatu Arabic da boko, kindaina tsokanar fad'a, kizama kamar 'yar uwarki fateema." Dijama tace inaso nima nazama yar birnin kamar fateema, ko Dan yaya mahmud ya daina kirana da mai kwanyar kifi yar k'auye, sai idonta ya kuma cika da hawaye." Momy tadinga share mata,hawaye tare da yimata nasihohi cikin hikima da dabara taja hannunta tasanya ta toilet ta taimaka mata tayi wanka momy ta gyara mata gashin kanta, had'ida gyara mata jikinta man shafi kawai ta shafa mata da hoda, da kuma man Baki." Ta d'auko mata wata dogowar riga ta atamfa tabata ta sanya had'ida d'aura mata d'an kwali ta zubo mata gashinta a bayan ta." Dijama tayi kyau sosai tafara fitowa 'yar birni, dama kuma dijama kyakkyawace." Momy tace "eyeh Ummie na kinga ynda kikayi kyau kuwa?" Dijama taji dad'i tayi dariya." "Maza kitafi wurin yar uwarki fateema k'arfe uku Khalil zaizo ya kaiku makarantar islamiya." A guje tafita tana dariya tana jin dad'i." Momy na ganin yanda tafita da gudu tayi murmushi ta girgiza kai "mai hali baya fasa halinshi." Momy tafitoTanufi d'akin Abba, ta Tarar dashi yayi zaune a kan kujera yayi shuru alamar akwai abunda yake tunani." Sallama tayi ta zauna kusa dashi, ta rik'o hannunshi tace "Abban yara lafiya?" Meke faruwa?" Wani dogon nishi yaja ya dubeta yace "wato lamarin ummie ne narasa ynda zanyi da ita, akan ta natsu ta tsaya tayi karatu, hankalina ya kwanta domin ganin narik'e amanar da d'an uwana ya barmun." Momy tace "ka kwantar da hankalinka, Ummie tayi mun Alk'awarin cewa ta daina duk abunda takeyi zata tsaya tayi karatu, domin kawai a daina ce mata 'yar k'auye." Abba yayi murmushi yace "inko hakan ne danafi kowa murna da jin dad'i." Momy tashiga kwantar mashi da hankali da kalamai masu dad'i, harya fara sakin jikinshi yana dariya, Hajiya Bilkisu kenan mace ta tagari A wurin Alhaji Hassan Adamu Tofa. Uwa a wurinsu Mahmud da Khalil da fateema." Da kuma _dijama 'yar gidan tsohuwa😃_ Dijama na shiga d'akin su ta tarar da Fateema a kwance tayi wanka tayi kwalliya ta kwanta barci ya d'auketa." A hankali ta fito ta janyo mata k'ofar ta rufe dan kar ta tasheta daga barci." Ta sauko falo tanufi kicin tazobo abinci a plate ta tanufi wurin TV ta kwanna tashar MBC 3 suna shirinsu na kartom tanacin abinci tana kallo tana dariya." Abba dake tare da momy suna hira, ya duba agogo hannunshi yaga k'arfe 3:15 lokacin zuwa makaranta islamiya yayi, da sauri yakira wayar Khalil domin yazo ya d'aukesu ya kaisu, saboda yau ne dijama zata fara zuwa mkranta." Khalil dake d'akin wani abokinshi suna hutawa da 'yan matansu wayayyi yan boko masuji da Kansu suna zaune a gefensu suna hutawa, ko wannesu yayi matashin filo da Brest d'in budurwanshi ana kallo ana hutawa." Khalil kansa a kan Brest d'in budurwarshi mai sona Yasmin 'yar wani hamshak'in mai kud'ice a anan cikin garin kano, Hannunshi d'aya yana sanya cikin pant d'inta yana wasa dashi, ita kuma tashiga shafashi tana wani nishi." Wayar Abba ta katse masu jin dad'i, Yayi saurin d'agawa yaji Abba yana cewa "Khalil kana ina ne? To duk inda kake duk abunda kakeyi kamaza kazo ka kaimun su fateema makaranta yanzun nan jiranka nkeyi." Da sauri khalil ya sauka a kan Yasmin yace "bbyna Abbana kekirana bara naje nadawo, Kishirya zanbiyo ta nan na d'aukeki na ajiyeki gida tunda bada mota kikazoba. Ya juya ya dubi abokinsa Auwal da yayi nisa tareda budurwanshi yayi murmushi yace "Auwal baka da sauk'i wlh." Auwal ya d'ago rinannun idonshi, ya d'aga mashi gira yacika bakinshi da Brest d'in budurwanshi yana sha." Dariya khalil yayi yaja hannun Yasmin ya canxa mata d'aki yace kijarani a nan tafi nadawo, Ta dubeshi had'ida kashe ido tace "OK saika dawo my." Yafito ya ja motarshi yanufi gida." Kai tsaye cikin falo ya nufa. Da sallamarshi d'auke a bakinshi." Wata kyakkyawar bby ya hango kwance a kan kujera da alama kallo takeyi barci ya d'auketa TV kawai ke aiki." Kasa hak'ura yayi sai da yanufi wurinta, gashin ganta yayi tozali dashi Wanda d'ankwalin kanta ya zame, gashin kanta ya bayya ya rufe maya fuska." "Wow khalil ya furta ya tsinci kanshi da durk'usawa saiti fuskarta yasanya hannunshi yashiga gyara mata gashin da ya rufe mata fuska." Karan hancinta yagani har baka, Wanda yayiwa kyakkyawar fuskarta kyau yashiga k'are mata kallo yana fad'i a zuciyarshi "gata k'aramar yarinya gata da masifar kyau, kuma daga ganinta idan ta girma saitayi mnyan kayan aiki." Murya Abba ya tsinkayo tareda momy suna saukowa daga sama, yayi saurin mik'ewa tsaye ya daidaita kanshi, ido biyu sukayi da Abba ya sunkuyar da kai alamar girmamawa yace "Abba sannu da fitowa." Abba yayi murmushi yace "yawwa khalil harka iso?" Abba ya kuma maida kallonshi wurin momy yace momyn yara, kiyiwa yaranki mgna su shirya sufito sutafi mkranta." Momy tayi murmushi ta Amsa da "to." Snn ta tashi tanufi d'akinsu fateema." Tafara tafiya kenan khalil ya dubeta yace "momy bak'uwa kikayi ne?" Momy ta waigo ta kalleshi cike da mmki tace "bak'uwa kuma a ina?" Ya juya yana kallon wurin da yaga kyakkyawar yarinyar kwance." Momy ta bi wurin da yake kallo da ido, kasan cewar babban falo ne set d'in kujeru uku ke cikin falon." Hango dijama tayi tayi ale ale sai barcinta takeyi hankalinta a kwance." [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Written By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *ina Sarah yau ranarkice kuma snnu a hankali duk zanzo kanku masu tsarguwar Sarah*😅😅 *15* Bata kuma tanka mashiba illah ta nufi wurin dijama, Wanda tayi d'ai d'ai sai barcinta takeyi, Momy tashiga ta yarda da ita, a Hankali ta bud'e idonta, sukayi ido biyu da momy ta sakar mata murmushi, Wnda ya kuma yasanya khalil rud'ewa ya k'ura mata ido yana kallonta harda d'an murmushi yake fitarwa a fuskarshi, domin ba k'aramin kyau tayi mashi ba." Momy taci gaba da cewa "ummie kitashi mana lokaci na tafiya." Mik'ewa tsaye tayi, ta turo baki alamar su�L/���4��3t�/] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar Gidan tsohuwa_😅) Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *AM BACK AGAIN BY THE GRECE OF ALLAH* _Alherin da ke ciki Allah yasadani dashi, shairin dake ciki Allah ya tsareni dashi_ _Muje zuwa masoya ana bugun tare🤝🏻_ *UMMU SAFWAN CE* *1* Cikin sand'a tashigo cikin zauren gidansu, tana wasar b'uya, ita da k'awayenta Lab'ewa tayi tasha jinin jinkinta kamar wacce tayi k'arya, tana tafiya a hankali yanda baxaka iyajin sautin takun k'afartaba." Gafda zata shiga cikin gidan ne Saiji tayi taci karo da wani abun,a gabanta." turus tayi, Taja ta tsaya gefe d'aya tana turo baki kasan cewar zauren gidan duhu ke gareshi, Ta d'auka *Kaka* ne, kaka Kwaishi da fitinar tsuha, Tashiga gunguni tana magana k'asa k'asa, " kai wannan tsohun kacika rigima yazaka taka min k'afa, idan kuma akace da kai ka kusan mutuwa, ka d'ora hannu a kai kace kai ba yanzun zaka mutuba." Shuru taji anyi Bataji antanka mata ba." Dogon tsaki taja harda d'an murgud'a baki taci gaba da tafiya zata shiga cikin gidan kenan taji ta kuma taka k'afar mutum a karo na biyu." Jikinta ya soma rawa fitsari ya fara d'iga a wandonta, saka makon marin da taji an kwad'a mata a fuska." Wata irin k'ara tasaki ta fad'i k'asa tana birgima, "Wayyo idona na shiga uku tsohuwa kizo ki ceceni." Mahmud dake tsaye cike da takaicinta, yace "Ke wace irin yarinya ce,wadda bata kallon gabanta, tunda kika shigo soron gidan nan naketa k'ok'arin naga na kauce mki amma duk da hakan saida kika taka min k'afa." Oh kin d'auka *kaka* ne da kike fad'awa magana yanda kikaga dama?" to bashi bane ni kika tak'ewa k'afa, wawuya kawai marar hankali wadda bata kallon gabanta bare bayanta, Ni maganin rashin kunyarki zanyi kafin na bar gidan nan." Tsohuwa dake sallah, Sallamewarta kenan taji sautin kukan Dije a zaure." Da sauri ta mik'e tsaye tafito daga d'akin tana fad'in "deejama wani mugunne ya dakeki?" Ai kuwa deejama najin muryar tsuhuwa ta kuma bud'e baki had'ida sanya hannu d'aya ta dafe b idonta d'aya, "wayyo idona nashiga uku tsuhuwa idona ya tsiyaye." Mahmud tsaye yayi ya tsura mata ido yana kallon ikon Allah, k'azafi takeso tayi mashi yanaji yana gani." Ta mik'e tsaye dafe da ido sai kuwa takeyi tana tsalle tana fad'uwa, sai da tazo dafdashi ta kuma taka masa k'afa da k'arfi ta xuba a guje tanufi wurin tsohuwa dake tsaye a k'ofar d'aki tana ruwan masifa." Tanufi wurin tsohuwa tana fad'in "wayyo idona tsohuwa ki taimakeni yaya muhmud ya tsiyayar min da ido d'aya." "Tsohuwa tace "burinka ya cika mamuda ka tsiyaye mata ido d'aya saika zuba ruwa k'asa kasha, Ni wlh bnsan irin k'iyayyar da kakeyiwa deejama ba, kwata kwata baka k'aunar ka bud"e ido ka ganta tana walwala a gida ko a waje." Tunda burinka ya cika ka makantar da ita, saikazo ka kwashe kayanka ka koma gidanku. Mungode da ziyarar Allah amfana." Muhmud da zaifita, jin k'azafinda dijana tayi masa yasashi dawowa ya fasa fitar. Yace "Allah tsohuwa ki daina biyewa wannan yarinya, kwata kwata batajin magana kuma batada kunya. Tun da nazo garin nan kullum sai ankawo maki k'arar dijama, amma kullum sai d'aure mata kikeyi bata laifi." "Saboda kana jin zafinta shiyasa ka tsiyayar mata da ido d'aya?" Tafad'i hakan had'ida kamo dijama dake gefenta tsaye kamar ta shige mata a ciki dafe da ido d'aya." Ta janye hannun deejama daga kan idon nata tana fad'in naga idon naki dije, idan ta kama mutafi asibity sai na kira ubanshi duk inda yake yazo ya d'aukemu ya kaimu asibitin." Ganin babu abunda idon nata yayi, tsohuwa ta kuma kallon muhmud dake tsaye gefe d'aya yana kallon ikon Allah. "To burinka bai cikaba baka makantar da itaba." tarik'a hannunta "mutafi deejamar tsohuwa kisha hura ki nemi wuri ki kwanta kirabu da wancan Azzalumin." Kallon mahmud deejama tayi ta fakaici idon tsohuwa tayi masa gwalo had'ida murgud'a mashi baki." Nuni yayi mata da hannu a lamar zanrik'eki." Bai d'aga daga inda yakeba. Sai sallama yaji anayi, wata mata ce tashigo da yaronta janye a hannunta wanda bai wuce shekara goma ba da bokitin markad'e a hannunta duk ya b'aci da k'asa alamar b'ari yayi." Tana fad'in "ina tsohuwa take?" Fito fito dan yau na rantse da Allah bazanyi asaraba. Kullum na aiki yarona wurin markad'e sai dijama ta tareshi a hanya tayi mashi dukan tsiya sannan daga k'arshe ta zubar min da markad'e to yau hak'urina ya k'are Dan bazanyi asaraba sai anbiyani ehe " Mahmud yadubi matar yace "d'aga murya kwarai yanda zasujiki suna ciki yanzun suka shiga." Tsohuwa tafito deejama ta biyo bayanta, Tsohuwa tace Abu mai waina mekike fad'i?" Me kuma deejama tayi?" Abu mai waina tarik'e k'ugu, ta maimaita mata b'arnar da deejama tayi mata." Tsuhuwa itama ta hau masifa tana fad'in Sam ba Deejama ta aikata hakan ba." "Na lura a garin nan babu wanda aka sanyawa ido irin deejama, yarinyar da na aika tasayomin sikari. Tayaya zatabi ta k'ofar gidanku?" to Wani irin sokon yaro ne gareki da har zai saki baki, Deejama tayi masa duka kuma har ta zubar mashi da markad'e." dan Allah Abu mai waina kifita a gidan nan tun cikin muna mu biyu, dan babu wani ranko da zan maki ehe." Ai kuwa Abu mai waina tashiga ruwan bala'i, "Ayi maka asara kuma baxa'a baka hak'uriba, to yau duk yanda za'ayi sai dai ayi amma sai anbiyani markad'ena." Mahmud da yaji fad'an ba mai k'arewa bane, ransa ya b'aci yaciro d'ari biyar ya mik'awa Abu mai waina had'ida bata hak'uri." Baki ta bud'e ta fara dariya takarb'i kud'in tana godiya, Sai ta koma yin magana cikin lalama da taushin murya, "aisu yaran ne basajin magana, amma ya kamata a k'ara jawa deejama kunne saboda kaf a cikin k'auyen nan ta hana yara walwala idan ta fito kowa tsoronta yakeji." Babu Wanda ya kuma tanka mata, sai Deejama da tace "kedai ki wuce kiba mutane wuri, tunda anbiyaki kud'in markad'anki, karki damemu da suruto." Ta dubi Sale yaron Abu mai waina, ta harareshi tace "kai kuma sale duk na rik'aka saina karye maka k'afa d'aya." Abu mai waina najin hakan kuma tasan halin dijama zata iya, zata fara wata sabuwar masifar mahmud ya bata hak'uri. SnnTa tafi, a hasale yanufi wurin dijama zai daketa tsohuwa ta turata d'aki tana fad'in wlh karka daketa. Meye ruwanka, to muddun ka daketa saina sab'a maka a gidan nan." Mahmud ya dawo baya, yana hararar dijama yana fad'in zan rik'akine saina d'ebi d'arina biyar a jikinki. Dan bazan biya mki kud'i a banzaba." Yanajin tsohuwa ta fara ruwan masifa ya fito ya baro masu gidan." Bayan sallar isha'i kamar yanda suka saba kowace yarinya zataci ado tanufi dandali, Haka dijama tayi kwalliya tasanya atamfa riga daban Zane da d'ankwali daban, tazane fuskarta da kwalliya kasan cewar dijama kyakkyawace kuma bafulatana ce, domin ba sosai hausarta ke fitowaba." An d'aure k'ugu da gyale." Da gudu tafito gidansu tana rera wak'a, k'awayenta najin sautin wak'arta kowa ya fito daga gidansu suka tareta Suna fad'in ga 'yar gidan tsohuwa nan ta fito, aikuwa da murna suka tareta suka jera suka nufi dandali." Dijama ce gaba k'awayenta suwaiba da lantana da ladidi, da luba a bayanta suntake mata baya domin itace boos duk Wanda yaja magana ita ke tare mashi." Gefe d'aya suka samu suka zauna a kusa da wani mai kifi, Mai kifin yana ganinsu , Sai da ya kuma dallara fitila ya duba da kyau ya tabbatar da sune, Ya sauke wani numfashi a ransa yace "Ashe yau zanyi kwantai bazan samu cinikiba. Saboda wad'an nan hatsibiban yaran." 'Dijama ta turo ido had'ida turo baki cikin tsiwa ta dubi mai kifi tace "lafiya meya faru kake haske mana ido da fitila?" Mai kifi da saida gabanshi ya fad'i dajin maganar dijama, dan ba k'aramin aikinta bane ta bad'e basa kifi da k'asa taja masa asara kuma ba yanda zaiyi. Ya k'ak'aro dariyar dole yace "yi hak'uri 'yar gidan tsohuwa ai bansan kece ba." Ya d'auko leda yasanya mata kifi. Yace 'yar gidan tsohuwa ga wannan kici, Ta dubeshi ta ya mutse fuska tace "ya'u kabar kifinka kawai yau bana ra'ayin cin kifin." Abokananta suna su, amma saboda tsoron da suke mata yasa ko wacce ta had'iya yawunta." Ya'u mai kifi yana ganin haka yatashi tsam ya d'auki tiren kifinshi ya bar wurin ya canza wurin zama yayi nesa da su sosai." Dijama bata lura dashiba, hankalinta yatafi wurin kallon wani saurayi da budurwa dasuke hira da alama saurayin bak'one zuwa yayi." Dariya tayi ta girgiza kai irin yanda ta hangosu saurayin sai wani kakkab'ar jiki yakeyi da hankicif, yana wani ya mutsa fuska wai shi d'an gaye." Gaba d'aya ta nunawa k'awayenta shi, suka tuntsire da dariya, Dijama tace "yawwa lantana jeki d'aukomin macijin robar nan naki Wanda yayanki yaje binni ya sawo maki." Lantana ta zuba da gudu taje gida ta d'auko ta kawowa dijama." Tace yawwa kuzo kuji abunda zamuyiwa wancan gayen." Suka had'a kai wuri d'aya abu na basu umurni suna girgiza kai alamar sun fahimta [28/04, 20:50] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_😅) Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *2* Dijama ta nuna masu inda zasuje su lab'e, Sai data tabbatar da sun b'oye, sannan A hankali ta lallab'a tanufi wurin saurayin da budurwar wad'anda suka samu wuri a gefen dakali suka zauna, suna hira suna dariya, basu lura da itaba sunyi nisa wurin hirarsu ta masoya, ta lallab'a taje bayansu ta d'ora masu macijin robar Wanda aka sanyawa batur sai wutsil wutsil yakeyi kamar macijin gaske, ta lallab'o ta baro wurin tayo wurin k'awayenta su lantana da suke lab'e wuri d'aya suna lekenta suna dariya." Itama b'oyewar tayi tashiga lek'awa domin ganin yanda d'an gaye zaiyi." Ganin basu lura da macijin a bayansu ba, yasata fitowa tanufi wurinsu tayi kamar wucewa zatayi, sai da tazo daf dasu ta kurma ihu tana nuna bayansu "wayyo Allah maciji a bayanku." Yahaya gaye yana waigawa yaci karo da maciji a bayanshi, ai baisan lokacin da ya b'urka tusaba ya kurma ihu ya zubar da talkamin k'afarshi Ya zuba a guje yana fad'in wayyo Allah maciji jama'a Ku kawo min agaji." Ladiyo dayake tasan halin dijama bataji tsoroba illah ta mik'e a hasale tanufesu, Suna ganinta tayo kansu suka zuba a guje suna dariya harda rik'e ciki, suna fad'in wasa mukeyi macijin roba ne." Yahaya gaye da saida yayi nisa sosai da wurin sannan ya tsaya yana zarar ido yana maida numfashi sama sama, a can yajiyo sautin dariyarsu dijama suna fad'in wasa mukeyi macijin roba ne." A hasale shima ya nufesu, cike dajin haushin muzantashi da sukayi a gaban budurwanshi, bugu da k'ari ga gudun da yayi harda tusa yasaki." Aikuwa ya tunkarosu gadan gadan, dijama na ganin haka ta d'aga murya da k'arfi tace "kowa yayi ta kansa." Suka zuba da gudu ko wannensu yanemi hanyar tsira." Juyawar da zatayi ta gudu, taji tayi karo da mutum a dai dai lokacin da yahaya gaye yanufota, aikuwa ta mak'alk'ale mutumin wanda batasan kowaye shiba, D'aga idon da zatayi sai taga Ashe yaya Mahmud ne." Mari ya kwad'a mata, ya rik'a hannunta ya mik'awa yahaya gaye yace "gata kaci ubanta, Domin ko mu kanmu mungaji da ita, mungaji da hali irin nata, kayi mata dukan tsiya ninace." Yahaya gaye babu abunda yakeyi sai ruwan masifa, Ladiyo ta matso kusa da ita ta xungure mata kai tace "kinci darajar yayanki da yau sai na lahira yafiki jin dad'i, Dijama da sai zarar ido takeyi tana kallon fuskar yahaya gaye tanaso tayi dariya amma ba hali." Mahmud yaja hannunta yana rankwashinta a kai yana mata fad'a, sai da sukazo k'ofar gida ta kwace hannunta da k'arfi tashige gida tana fad'in Allah ya isa mugu kawai." Da Sauri yabita cikin gidan yana Neman ya rik'ata, aikuwa ta fad'a d'akin tsohuwa da gudu, tsohuwa na ganinta tayi saurin tashi zaune tace "babu Wanda zaibiyoki sai mamuda domin nasan shi kad'ai ke k'ok'arin yaganki bakya motsi, hakan yayi dai dai da zuwanshi k'ofar d'akin yana huci, tsohuwa tace "karka kuskura ka shigo min d'aki kaji na fad'a maka." Yaja yayi tsaye a k'ofar d'aki yana huci, Saida dijama ta kalli fuskarshi ta tuntsire da dariya harda rik'e ciki, dariya takeyi sosai, sai ta kuma kallonshi ta kuma tuntsirewa da dariya, Ya kuma hasala, tana ganin ya hasala sosai tace "yaya kasan ko menakeyiwa dariya?" Ya wurga mata harara had'ida girgiza kai." Tace "ba komai yake bani dariya ba sai yahaya gaye, yanda yasaki tusa ya zuba a guje." Shima kanshi gudun da yaga yahaya gaye nayi sai da yabashi dariya kasan Cewar duk abunda sukeyi a kan idonshi, Dariya taso sub'uce mashi yayi saurin barin wurin, yanufi d'akinshi, yana fad'in idan kingama dariyar saiki kawo min abincina ina jiranki." Yitayi kamar bata jishiba, tashiga bawa tsohuwa labari suna dariya." Tsohuwa tace "tashi kije ki d'auki abincin yayanki ki kaimasa yana can yana jiranki." Ta turo baki tace "ni tsohuwa bazanjeba saboda duka na zaiyi." Tsohuwa tace "baxai dokeki ba aina riga nayi mashi magana, nace karya dakeki kuma kinsan mamuda yanada jin maganar mutane, Wurin nan yana burgeni." Sannan ta tashi tana turo bki tanufi kicin ta d'auki abincin shi tanufi d'akinshi, Kai tsaye tashiga d'akin batare da tayi sallama ba, ta tarar dashi zaune a kan katifarshi dagashi sai best da gajeran wando, jikinshi ko ta ina gashi gashine yayi kwance akan kyakkyawar fatar jikinkinshi fara fes. hankalinta ya tashi jikinta yasoma rawa aduniya bata tab'a ganin namiji a hakanba, Tsawa ya doka mata wadda tasanyata tadawo natsuwarta yace "ubnwaye yabaki izinin kishigo min d'aki batare da kinyi sallama ba?" Maxa kikoma kiyi sallama sannan ki kuma shigowa." Da Sauri ta juya ta koma jikinta na rawa." Yana ganin fitarta yayi saurin mik'ewa tsaye ya d'auko jallabiyarshi ya sanya." Sallama tayi sannan ya amsa mata had'ida bata umurnin shigowa, sannan ta shigo, Kallon yabita dashi yana harararta domin cike yake da jin haushinta, yanuna mata wni tebur yace "wuce ki ajiye a can." Kizo inaso zanyi magana dake, kuma kika kuskura kika gudu ko kika yimin ihu saina k'arye maki hannu d'aya idan na rik'aki." Sum sum ta wuce ta ajiye harda wani sunkuyar dakai kamar ta Allah, tazo kusa dashi ta durk'usa had'ida sunkuyar da kanta k'asa." Ya Matso daf da ita ya kama kunnenta ya murd'a sosai saida tasaki fitsari saboda azaba, Yace "maimaita abunda kikace d'azun. Ni kikeyiwa Allah ya isa baki yafeba?" Rantse rantse tashigayi ita batayi Allah ya isaba"don Allah kayi hakuri karka ciremin kunne, banyi maka Allah ya isaba." "Idan kika kuskura aka kuma sake kawo k'ararki a gidan nan saina farfasa maki baki kinyarda." Tayi saurin d'aga kanta alamar "eh." Idanta na zubar da hawaye." Ganin fitsarin dake d'iga a zanenta yasa yayi saurin sakinta yaja da baya da sauri ya d'auko bulala yanufota yace "koki goge fitsarin nan ko yanzun na lahira yafiki jin dad'i." Da Sauri ta mik'e tsaye, saiga takarda ta fad'o a zanenta, ya doka mata tsawa yace "ke zonan takardar meye?" zaro ido tayi waje takai durk'ushe tana matsar hawaye tana fad'in dan Allah yaya kayi hak"uri bazan sakeba." Tsawa ya Doka mata yace "ba kuka nace kiyi ba tambayarki nayi." Cikin rawar murya tace "Anty bushira ce antyn suwaiba k'awata tace nakawo maka." Ya wurga mata harara yace "bud'e karanta abunda ke ciki, Da sauri ta bud'e takardar tashiga karanta masa, jin kalaman soyayya ne alamar tana sonshi, yayi saurin doka mata tsawa yace "rufe min bakinki kiyi min shuru, Bari nafaracin k'aniyarki ke 'yar aiken kamun naje ga Wanda ta aikoki." Ke fitsararriya marar kunya ke ake aikowa da takarda kikawo min?" Tashi ki kama kunnanki." Tana hawaye tana fad'in "Dan Allah yaya kayi hak'uri bazan sakeba." Yasin sai kin kama kunnenki, yayo kanta da bulala a hannunshi, Tana ganin hakan tayi saurin mik'ewa tsaye takama kunnenta sai kuka takeyi tana bashi hak'uri." Abincinsa ya jawo ya fara ci, yana kammalawa ya haye katifarshi yajawo jarida ya Shiga karantawa, ganin ta wahala sosai ya dubeta yace "tashi kiwuce kiba mutane wuri." Tayi kuka idanunta sunyi jajir har sunfara kumbura, ya dubeta yace "ko gobe idan wata ta kuma aikoki da takarda da sunan kikawo min kika karb'a abunda zanyi mki sai yafi wannan, sannan idan kika kuma yimun Allah ya isa saina karye mki k'afa d'aya da hannu d'aya." Wuce kibani wuri kinyi tsaye kin kafeni da ido kina kallona saikace Aljanah." Sum sum tafita tana kuka, a bakin k'ofar d'akinshi ta tsaya tace anfad'a d'in "Allah ya isa ban yafeba, Lokacin da kake zuwa k'ofar gidansu zance na sani ne?" Dan kawai ta aikoni da takarda saika sanyani kamun kunne saboda mugunta, to banyafeba wuta balbal kuma sai dai idan Kaine Aljanin baniba." Ganinshi tayi ya nufota ta zuba a guje tayi cikin gida, karo taci da Kaka zaune a tsakar gida, yanajinta a zaure tana Allah ya isa, dama yana da takaicinta ya sanya sandar hannunshi yashiga zungurarta da ita, yana fad'in mamuda kikeyiwa Allah ya isa marar kunya.' Kuka takeyi sosai Wanda yasa tsohuwa tayi saurin fitowa daga d'aki ta ceceta Tana fad'in yanzun malam saboda Allah akan mamuda kake zungurar dijama da sanda, ai dole jidama tayi masa Allah ya isa saboda baya raga mata, baya tausayinta ko kad'an." Ta rik'a hannun dijama tace tashi mutafi ko gobe mamuda ya kuma zaluntarki kice masa baki yafeba." [28/04, 20:50] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_😅) Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *3* Shiri takeyi zataje makarantar boko. Kasan cewar Wannan shine zangonta na k'arshe da zata k'are pramary school." Ta kammala shirinta cikin riga da wando blue ta sanya hijabinta fari, ta d'auko jakarta ta goya a bayanta, ta dubi tsohuwa dake zaune gefe d'aya tana kallonta." tace "ni dai tsohuwa nagama shiryawa zantafi." Tsohuwa tace "to "dijamar tsohuwa Allah ya tsaremin ke kidawo lafiya, Karki tsaya ko ina, kuma karki kula kowa a kan hanya kiyi tafiyarki dan karkiyi latti." Tace "to tsohuwa, had'ida fitowa tasanya takalminta ta fita." Saida ta kai k'ofar gida, Sannan kuma ta juyo ta dawo a guje saka makon fitsarin da ya matseta, Da sauri ta sunkuya ta d'auki buta a guje ta fad'a ban d'aki." Wa zata gani yaya Mahmud ne, ya juya bayansa yana wanka, ihu ta kurma. Tana fad'in wayyo Allah k'ato ba wando, Tafito a guje cikin tashin hankali da tsoro, had'ida sakin butar hannunta tazuba aguje." Mahmud dajin ihunta yasanyashi Sanin shigowarta band'akin, ransa yayi matuk'ar b'aci Yashiga tunanin lallai wannan yarinyar bakad'an ta rainashiba tunda har take iya iskoshi band'aki." Tana kiranshi da k'ato ba wando." Gudu take falfalawa kamar filfilwa, bata zame a ko inaba sai makarantarsu, Da shigarta makarantar ta cikin, Taci karo da yara yan mkrtar tsugunne alamar latti sukayi, Da gudu ta wucesu Batabi ta kansuba tayi shigewarta Aji." Malam sani, mai hukunci yana ganinta ya rufa mata baya yana masifa, kai tsaye ajinsu ya nufa, ya tarar da ita zaune a kan kujerarta, Kujerar da ba Wanda ya isa ya zauna akanta sai ita, koda kuwa ranar da bataxo makaranta bane, idan taji lbrin wani Wanda tsotsayi yasa shi ya zauna a kanta to sai tayi mashi shegen dukan tsiya." Malam sani yashigo ajin a hasale, yadubeta yace "ke dijama fito nan waje, Wato kinyi latti saboda rashin kunya irin taki kika wani wuce mutane kika wuto aji, Sai kace kinfi kowa to kisani hukuncinki ya k'aru dana sauran d'alibai." Bata kulashiba sai ma tayi kamar bada ita yakeyiba, Tsawa ya doka mata "ke dijama wai bada ke nake maganaba,?" sai a lokacin ta dubeshi had'ida turo baki tana gunguni." Cike da jin haushinta ya nufeta da bulala a hannunshi, bai tsaya b'ata lokaciba yashiga zuga mata bulalar." Ihu ta kurma ta doka wani irin tsalle tashige mashi a babban Riga, kasan Cewar malam sani ma'abucin sanya babban rigane. Kokawa yashiga yi da ita yana k'ok'arin ya yakwace kansa daga gareta, amma ina, idan yayi nan gefen ta dawo masa nan gefen, sai ihu takeyi kamar Wanda ake cirewa ido." Malam sani ya jigata sosai zufa sai karye masa take, duk zufa ta wanke masa fuska, ga dijama cikin babban rigarshi yakasa cireta, sai jujuwashi takeyi kamar zai fad'i k'asa." Yashiga fad'in 'fito dijama nafasa dukan naki, kije kiyi zamanki, amma ina ta cimuimuyeshi tana ihu tana fad'in "wlh bazan fitoba." Suna hakan Allah yakawo malam mudi, Yashiga tmbyar mlm sani abun da kefaruwa?" ganin ya had'a zufa sai jujuwa shi akeyi, bai samu damar bud'e baki yayi maganaba illah yyi mashi da hannu zuwa cikin rigarshi." Aikuwa malan mudi yana lek'awa ya hango dijama ta cimuimuyeshi sai ihu takeyi, da kyar aka samu aka b'anb'ari dijama a jikin malam sani, sai nishi yakeyi kamar wanda yayi wasan tseren gudu." Ai kowa yana samu ancire mashi ita, bai kuma bi takan kowa ba yafita daga ajin da saurinshi, .dijama kuma na gefe d'aya tsugunne sai zarar ido takeyi tana turo bki cike da tsiwa, malam mudi yace "tashi kiwuce kitafi gida na koreki daga nakarantata sai kinzo da mahaifinki." Da sauri ta mik'e tsaye, Tana magana k'asa k'asa tana cewa "to sai me?" Kuma wlh duk nakama salihu sainayi mashi shegen dukan tsiya tunda har ka koreni makaranta." Salihu babban d'an malm mudi ne Wanda yake duk sa'a nine da dijama, tana kaiwa nan tafita waje tayi tafiyarta." Malm mudi dake tsaye yaji duk abunda tace yace "to idan kika kamashi karki barshi da rai kikashe kinji , kaji min hatsabibiyar yarinya." Tafiya takeyi akan titi duk inda taga mota ajiye saita lek'a kanta ta glass d'in motar ta hango abunda ke cikin motar sannan ta k'ara gaba." A can taci Karo da yan taxi su biyu suna rigimar fasinja a tsakaninsu, tsayawa tayi tana kallonsu, sai da ta fahimci a kan abunda suke yiwa fad'a, sannan ta k'arasa wurinsu ta rik'o rigar d'aya daga cikinsu wadda ya fahimci yafi fitina, Tace "yayana ina kwana, harda 'dan runsunawarta, kamar ta Allah, kallon rashin sani yayi mata cike da jin haushi yace "waye yayan naki?" Ke wai daga ina?" A ina kika sanni?" Tace "yi hak'uri dama turoni akayi daga gida akace idan naga mai taxi nakirashi domin, yayana ne zaiyi tafiya xuwa kano kuma bayason zuwa tasha shiga mota saboda baya son jira, gaba d'aya zai d'auki shatar mota domin ta kaishi har k'ofar gida, kud'ine gareshi sosai." Mai taxi yanajin hakan ya kyale abokin fad'an nashi ya maida hankalinshi a wurin dijama, yace 'a wace unguwa gidan naku yake?" Tanuna masa hanya tace "can gaba kad'an bama da nisa sosai." Yace "yawwa 'yar Albarka shiga mota mutafi, Girgiza kai tayi,tace "tsohuwa ta hanani shiga mutar mutane saboda kar'a saceni." Mai taxi da yake yaji maganar kud'i yace "to kishiga gaba kawai saiki dinga nuna min hanya." "To tace had'ida shigewa gaba, tana tafiya." Tana gaba d'an taxi na bayanya biye da ita, duk inda ya gifta mata matafiya sai tarenshi akeyi yana girgiza kai alamar ba aiki yakeyi ba dijama kawai yake biya." Sunzo kwanar da zata sadasu da gidansu, yara sunyi tsaye tsaye, a bakin hanya, tashiga kore yaran da hannu tana fad'in "kugafara nan ga mota nan zata shigo, kujanye daga nan." Tsofaffin unguwa da samari, kowa sai kallonta yakeyi yana mmki, yana kuma kallon mai taxi din dake biyeta da ita, yana k'ok'arin shigowa kwana." Tabb!!! su furta had'ida rik'e baki🤔 Suka ce, yau kuma wannan hatsabibiyar yarinya mai taxi ta janyo mana?" Ido kowa ya bita dashi saboda ba damar ayi mata magana cibi ya zama k'ari, Domin duk wanda yayi mgna da zarar d'ansa yafito waje, Idan ta rik'ashi sai tayi mashi shegen duka tsiya, tace "babanka ne janyo maka, idan ka koma gida kafad'a mashi ya daina sanya min ido." Wnn dalilin yasa kowane mutum sai dai yasanya mta ido."👀 Da kyar d'an taxi yasamu yashiga kwanar, saboda rashin kyawon hanyar, a ransa yana danasanin biyo ta da yyi, amma kuma idan ya tuna da shata 'a ka d'aukeshi sai ya d'anji sanyi yyi murmushi yaji dad'i." Suna zuwa daf da k'ofar gidansu ta hango yaya mahmud zaune a kan dakali, Gabanta ne yanke ya fad'i data tuna da shigarda tayi a b'and'a ta iskoshi." Taja dogon nishi, tace "to shi kuma wancan mugun ko zaman me yakeyi a waje?" Shima Mahmud d'in zaman da yayi, a nan zaman jiranta ne har zuwa lokacin da zata dawo daga makaranta, domin yau babu Wanda ya isa ya hana yaci ubnta." D'an taxi na zuwa sai ti k'ofar gidan tashiga d'aga masa hannu tana fad'in wait wait ya isa ga gidan nan." Dan taxi yaja burki ya tsaya had'ida sauke ajiyar zuciya wahalar da yasha wurin shigowa wannan hanyar." Mahmud na ganin hakan ya cika da mmki da Alajabi ya tashi tsam yashiga gida, yana mmkin dijama ko dai Aljanu sun shegeta ne?" Tsohuwa tashiga dokawa kira tun a waje, tsohuwa dake kishingid'e tana gyangyad'i, jin muryar dijama yasa tayi saurin bud'e idonta had'ida kai idonta ga dibon agogo, Mmki tashigayi ganin lokacin tashinsu daga mkranta baiyi ba." Kai tsaye ta fad'a kan jikin tsohuwa tana fad'in wash Allah tsohuwa nagaji." Tsohuwa tace "dijama meya dawo dake gida yanzun, bayan nadiba agogo na ga lokacin tashinku daga mkrsnta baiyi ba." Ta turo baki idonta ya cika da hawaye tace "wai malam Mudi ne yace ya koreni a mkrantar gaba d'aya, wai sainazo da mahaifina." Kuma na rantse da Allah tunda ya koreni, duk nakama d'ansa Salihu sainayi mashi dukan tsiya." Tsohuwa ta rabka sallalami, tace "ya koreki mekikayi mashi?" "Wai saboda kawai nayi latti ." Tsohuwa zata kuma yin magana taji ana rangad'a orda da mota a waje ba kafkaftawa, duk a rud'a mata kunne." Sai kuma ga yaro yashigo yana fad'in wai a waje wani mai mota yace yana kiran dijama." Tayi sauri ta fito da kayan sauri yakeyi." [28/04, 20:50] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_😅) Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *4* Tsohuwa ta juya ta dubi Deejama, itama Deejama tsohuwa take kallo." Tsohuwa tace dijama a ina kika samo mai mota kuma?" Sann Wad'anne kaya ne naji ance kiyi sauri kifito dasu?" Dijama ta turo baki cikin shagwab'a tace "yaya Mahmud ne nasamowa mota, domin ya kwashi kayansa yayi tafiyarshi garinsu, saboda nagaji da zaman da yakeyi a gidan nan kullum sai ya zalunceni, Ko kuma ya dokeni." Tsohuwa tayi tagumi🤔 tace "dijama waye yasanyaki ki taro motar mutane, shin kinada labarin cewa direbobi wasunsu basu da mutunci?" Ai kuwa bata rufe bakiba taji ankuma danna wata irin orda da k'arfi, had'ida dukan k'ofar gidan iya k'arfinsa, sai da tsohuwa da dijama suka razana." Da sauri tsohuwa ta mik'e tsaye ta janyo mayafinta had'ida Sanya talkaminta, ta dubi dijama tace "karki kuskura kifito, kibari nafara tafiya na bashi hak'uri, har musamu yayi tafiyarshi, amma dai yau dijama kin janyo mana fitina da bala'i 'yan taxi." Duk abunda akeyi mahmud yana d'akinshi yanaji bai fitoba, jira yakeyi a k'are da d'an taxi, ya rik'ata yaci ubnta, la'ada waje." Tsohuwa tafita waje ta tarar da mutane sunyi cincirindo manya da yara, kowa sai fad'in Albarkacin bakinsa yakeyi a kan dijama, suna fad'in indai dijama ce har abunda yafi wannan zata iya aikatawa." D'an taxi na ganin tsohuwa ta fito, yabita da kallo ya nufo wurinta, yana fad'in "tsohuwa fito min da yarinyar gidanki, yau na rantse da Allah tunda iskancinta ya kawo kaina, to ta kai k'arshen rashin kunya, domin ni a tasha nake kwana." yau zanyi mgnin rashin kunyar da takeyiwa mutanen garin." yanxun nan a bakin mutanen unguwa, nkejin labarinta tsaf, to tunda rashin kunyarki takawo gareni tazo k'ashe." Tsohuwa tashiga bashi hak'uri. Tana masifa da mutanen unguwa tana fad'in "dama tasani an dad'e da tsanar dijama a garin nan to ta Allah batasu ba, kuma bazasu iya komai da dijama ba." D'an taxi shima sai ruwan masifa yakeyi yana dukan mota yana fad'in bazai bar unguwar nan ba sai yayiwa dijama shegen dukan tsiya, ko kuma a biyashi kud'in mansa da ya k'one wurin shigowa wannan unguwar." Mahmud dake d'akinshi zaune yanajin duk abunda kefaruwa ganin fad'an ba mai k'arewa bane, yasashi fitowa, yanufi cikin gida kai tsaye d'akin tsohowa ya shiga ya tarar da dijama zaune a kan kujera abincinta kawai takeci, hnkalinta kwance." Ganin Mahmud da tayi yashigo ya sanyata sakin kwanon abincin had'ida zaro ido waje cike da tsoro, Tun kafin yakai wurinta tashiga matsar hawaye tana fad'in "dan Allah yaya kayi hak'uri bazan sakeba." Dank'ota yayi yashiga kwad'a mata mari yana dukanta, dama yana da takaicinta, Dukanta yakeyi ba girma ba arziki, sai ihu takeyi, tana neman tsira, sannan daga k'arshe ya rik'a hannunta yafito da ita, Yana jayen da ita yanufi k'ofar gida da ita, kai tsaye d'an taxi ya mik'awa ita yace "gata kaci ubnta, idan da hali dan Allah katafi da ita, domin ko mu kanmu ta addabemu ta zamar mana fitina." D'an taxi ya rik'e hannun dijama yana Neman ya turata a mota, Dijama ta kurma ihu tana fad'in nashiga uku tsohuwa kina gani d'an yankan kai zai tafi dani?' Tsohuwa tayo kansa tana masifa ta rik'e hannun dijama tace "na rantse da Allah ba inda zakaje min da yarinya." Nawane kud'in manka?" kafad'i ko nawa ne sai na biyaka." D'an taxi yayi murmushi yace "dubu biyu ne tsohuwa." Tsohuwa ta kama bakin zanenta ta kwanto dubu biyu ta mik'awa d'an taxi. Sannan ta janyo hannun dijama had'ida wurgawa mahmud harara." D'an taxi yace "kin fanshi jikanyarki tsohuwa, amma kija mata kunne Dan na rantse banda darajar wannan mutumin, ya nuna Mahmud dake tsaye da konawa kika biyani sai nayi mata dukan tsiya a wurin nan kafin na kyaleta." Dijama ta dubeshi cike da tsewa tace "mudai Dan Allah karka cika mana kunne da suruto tunda anbiyaka kud'inka sai kaja akwalar motarka kabar mana k'ofar gida." Ta d'aga kai ta dubi tsofafin da suka zagayesu suna kallonsu ko hak'uri bazasu iya bayarwa ba, Ta girgiza kai tace "duk wad'anda ke wurin nan babba da yaro duk na ganku, zamu had'e daku," Sunajin hakan kowa ya watse ya kama gabansa, saboda sanin halinta, d'iyansu da jikokinsu bazasu zauna lafiya ba, wurin dijama." D'an taxi yaja motarsa yayi tafiyarsa, Tsohuwa taja hannun dijama suka nufi cikin gida." Mahmud na ganin hakan ya fasa shiga cikin gidan saboda masifar tsohuwa shima ya kama gabansa." Tabarma tsohuwa ta d'auko ta shinfid'a mata a k'ofar d'aki, tana jera mata sannu had'ida yimata fifita inda Mahmud ya daketa wurin duk yayi kwancin bulala gashi Abu ga farin mutum." Tsohuwa ranta yakai k'ololuwa wurin b'aci sai masifa takeyi tana fad'in bari mamuda d'in ya shigo, yazo ya had'a kayanshi yayi yafiyarshi gidansu, ni banga amfanin tahowar nan tashiba, tunda yazo garin nan kullum cikin d'aga maki hankali yake." Dijama ta kuma marairaicewa sai nishi takeyi kamar Wanda zata mutuwa." Wasa wasa jikin dijama ya d'auki zafi alamar zazzab'i yakeson rufeta, Hankalin tsohuwa ya kuma tashi ta mik'e tsaye tashiga d'aki ta d'auko mata maganin zazzab'i ta k'ak'k'are mata tabata tasha, sannan barci mai nauyi ya d'auketa." Yinin ranar dijama ko k'ofar gida bata fitaba, jinya tajeyi." Sai bayan sallar isha'i Mahmud ya dawo, gidan Da sallama yashigo ya,Tarar da tsohuwa zauna, K'asa k'asa ta amsa mashi had'ida kauda idonta gefe d'aya hushi takeyi dashi." Murmushi yayi had'ida girgiza kai domin yasan za'ayi hakan tunda ya tab'a 'yar gidan tsohuwa." Ya kuma kallon tsohuwa yace " 'yar tsohuwa hushi kikeyi da namijin naki, to kwantar da hankalinki na kusan tattara kayana na barmaku garinku nayi tafiyata gidanmu" Yana kaiwa nan ya d'auki buta ya Shige ban d'aki." Fitowar da zaiyi sukayi ido biyu da dijama dake kwance a gefen tsohuwa, ta tsura mashi ido. Tanatana kallonshi Ajiye butarshi kenan yaji ta saki dariya harda rik'e ciki tana kallonshi tana kallon k'ofar b'an d'aki." Sai ta dubeshi ta dubi ban d'aki ta kuma b'arkewa da dariya.' Anan take ya fahimci abunda take yiwa dariya, wato d'azun da ta iskoshi yana wanka, kenan To metake yiwa dariya?" Duk haushi ya kamashi yaji kamar yaje yasameta yayi ta dukanta amma ba hali, tsohuwa bazata bariba." Amma kafin ya bar garin nan sai ya koya mata hankali, sannan yayi tafiyarshi." Washe gari dijama taji sauk'i, sosai Tafiya takeyi D'auke da allonta zataje makarantar islamiya ta d'ora allonta akai ta sha d'amara da gyalenta a k'ugunta, Tafiya takeyi tana rera wak'arta tana rawa a kan hnya." Karo taci da Salihu d'an mlam Mudi, Wanda ya koreta a makarantar boko, Ta ajiye allonta a gefe d'aya, tasha gabanshi yana d'auke da markad'en kayan miya a Kansa, ta ture markad'en ya zube, Tace "yawwa wana nakama?" Aidama nacewa babanka duk na kamaka sainayi maka duka, tunda har ya koreni a makaranta. Ai kuwa ta kamashi da kokawa, saida tayi mashi dukan tsiya, Sannan ya duk'a ya d'auki robar markad'ansa yanufi gida yana kuka." Dijama kenan, ita ba girma garetaba sai fitina, kwata kwata shekararta goma sha hud'u a duniya." Sai da taga yayi nisa yana tafiya yana kuka sann ta d'auki allonta tanufi mkranta." Gafda zata isa makarantarsu Ta kuma cin karo da Buba d'and'an mai gari tare da tawagarsa 'yan tauri." Buba d'an maigari kowa a cikin garin tsoronsa yakeyi, Domin ya kama mutum yayi masa duka saiya karkayashi ba wani abun bane gareshi." Allah ya d'ora mashi son dijama saboda hatsabibancinta da k'arfin hali irin nata, bugu da k'ari tafi duk 'yan matan garin kyawo." Gabanta ya Tara, yayiwa yaransa nuni da hannu da suyi tafiyarsu zaiyi magana da masoyiyarshi." Ita kuma dijama a duniya babu Wanda ta tsana kamar Buba, saboda shaye shayen da yakeyi, bata son ganin fuskarshi ko kad'an." Buba ya bud'e baki yana dariya bak'ak'en hak'oransa da sukayi bak'i suka dafe wurin shan sigari🤒 suka bayyana, Yace "dijama 'yar gidan tsohuwa matar buba duk Wanda ya tab'aki a garin nan zanci........ Murmushi tayi masa Wanda bata tab'a yimasa ba, Domin tasamu wata dama da zata sanya buba ya rama mata dukanta da yaya mahmud yayi mata jiya." [28/04, 20:50] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_😅) Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *5* Ganin murmushin da takeyi ne, a kan fuskarta ya kuma bawa Buba damar k'ara bud'e baki yana dariya, Yace "dijama ki amince dani naturo magabatana a d'aura mana aure." Dijama najin hakan ta had'e fuska had'ida ya tsine baki, Ta dubeshi da kyau tace "Buba kanaso nadinga kulaka?" Har na aureka?" Buba yace "abunda nake fata kenan dijamata." Ta karkace kai tace "kasan bak'on da yazo gidanmu?" Buba yace "mahmud kike nufi?" Tace "kwarai kuwa, to kasani yasanya mun ido, kullum sai ya dakeni bansan abunda na tare mashi ba. So nakeyi ka tsoratar dashi ya daina dukana, domin kuwa duk abunda yaga inayi sai ya sanya min ido, kuma ya dakeni." Buba ya d'aga hannu ya zunduma ashar yace "Alk'awari nayi duk Wanda ya tab'amun ke a garin nan sai nayi gunduwa gunduwa da namansa." Dijama tadinga tsallen tana jin dad'i tace "yawwa Buba, Amma karka dakeshi, karkayi mashi illah, kawai dai so nake ka tsoratar dashi saboda ya daina dukana." Buba ya kuma b'arkewa da dariya ya na kuwa ya fadin "saini na dije "yar gidan tsohuwa kowa yatab'aki agarin nan bazai kwana lafiya ba," Dijama najin hakan ta dinga dariya tana zugashi "Gaskiyar Buba sai kai na dije "yar gidan tsohuwa, nan fa tadinga zugashi yanajin dad'i saboda mahaucin son da yake mta." Sai kuwa yakeyi yana zage2 Ita kuma ta k'ara gaba tana cewa "sakarai wawa, waye zai auri d'an shaye2, tajuya ta hngeshi yayi nisa, taja dogon tsaki had'ida murgud'a baki." Wani gefen dad'i yacikata tana za a dakar mata yaya mahmud,haka dai har ta kai makarantar tasu", Tana zuwa tasamu wuri a gefe d'aya ta zauna batare da ta tsokani kowaba A Can ta dubi wani yaro ya hangame baki ya na bacci aiko tasanya hannun ta ta d'allamai baki sai da sauri ya bud'e idonshi yarik'e Baki yana kuka, Anan take bakin nashi yayi tudu, ya kunbura." Ta dubeshi tana dariya tace "yaro ubanka yajamaka tunda yana gani d'an taxi zai tafi dani amma ya kasa bada hak'uri sai dai yaja yayi tsaye yana kallonmu Dan haka nacire jin haushinsa a kanka." Ta kuma matsawa gefe d'aya ta zauna, ko wanne yaro yana zuwa afad'a masa karatu, amma ban da ita, domin acewar ta kotaje an fad'a mata ba ganewa zatayi ba garama tayi zamanta", Can itama sai tafara gyan gyad'i mlm dayaga tana bacci ya d'aga bulalar hannunshi ya doka mata a jiki, yana fad'in " aikin ki kenan bacci, baki gane komai mai kwanyar kifi keda jaki banga babban cin kuba, Ai kuwa d'alibai suka d'auki yimata dariya, ta hasala sosai taji haushi tashiga gun guni tana mgna k'asa k'asa, Ni dai ban daiji metake fad'aba Can ta nisa, tace mlm zanyi fitsari? Yace "tashi kitafi dama aikin kenan daga kashi sai fitsari, ko aci akwanta, amma kai kam wayam ba komai acikinsa sai rashin kunya, Da kuma majina, ya mere baki yace "ALLAH dai ya kyauta." Rab'awa tayi ta Wuce tagefen malam, ta dubeshi ta sakar masa murmushi, Mlm kuma harara ya kuma wurga mata, Hmm kun dai San dijama bata murmushin banza." bata zarce ko inaba sai cikin wani kango dake nesa da makarantar kad'an a hankali tashiga kangon tana waige waige, can ta hango leda fara, Ta duk'a ta d'auki ledar, Can nesa kad'an ta hango ramin cinnaka tashiga tsinta tana zubawa a cikin ledar, Tana tsinta tana fad'in Yau zaka ci ubanka mlm ni zaka zaga har kasa ayimun dariya,hmmmmm yau kaima za'ayi maka dariya." sai da ta tsinci mai isarta ta zuba a ledar, ta saki dariyar mugunta sannan ta mik'e tsaye. Ta fito, hannunta goyo a bayanta sai da tazo kusa da mlm Ya juya bayansa yana gayawa wad'ansu d'alibai karatu, ta faki idonsa ta lallab'a a hankali saiti rigarsa ta d'aga ledar cinnakan ta zuba mashi cikin riga d'alibai na ganinta amma ba halin yin magana." Dama sun san za'ayi hakan, tunda malam ya zageta, tayi shuru ta nuna alamar bata damuba, Kowa yashiga mamakin "dijama ce za a zaga bata tankaba hmmmm, akwai wata a k'asa Mlm da yaji anfara mintsinarshi, yafara sosawa, tun yana Sosawa a hankali harya ya zabura ya mik'e tsaye nan fa yakama susar jikinsa da sauri d'alibai me zasuyi inba dariyaba, kuwa takeyi tana tsalle tana tab'i da hannunta tana dariya, tasanya d'alibai najansa tana masu wak'a suna amsawa Itake fad'in cinnaka yaci jeshi Sunafad'in tashi kar ya k'arama 😅 [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_😅) Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *6* malm sai so she2_ yakeyi, yana hararar dijama had'ida da yimata dakuwa🖐🏿 har yakai sai da ya cire rigar sa, ganin cinnakun basu fita ba daga k'arshe ya tub'e wandon sa ya , yashiga kakkab'a ya koma daga shi sai gajeren wando." Can saiga cinnaku suna fad'owa d'aya bayan d'aya." tsaye yayi ya kasa magana yana sauke ajiyar zuciya,d'aya bayan d'aya Yakasa d'aga ido ya dubi d'alibansa saboda kunya domin ya fahimci cewa duk shairin dijama ne." Dijama tayi tsaye tana kallonshi tana dariya, ya dubeta da kyau cikin b'akin ciki da jin haushinta yace " dijama kitafi gida nakoreki karki k'ara zuwanmin mkrnta, Ta b'arkewa da dariya had'ida rik'e ciki tana nunanshi tace "toh saimi Dan ka Koreni, ainaga kai kafara zagina ni kuma narama, Harda yimin gorin ilimi, kuma ai naga shi ilimi Allah ke badashi nima ba Dan ya manta daniba, Kuma ai naga itama 'yartaka jakace bata San komiba sai jakanci,kuma doluwa ce, Idan ina da kwanyar kifi ita kuma kwanyar kwad'd'i ke gareta, Ta k'are maganar had'ida mur gud'a baki, tayi tafiyarta." Sai da tayi nisa da tafiya snn ta waigo a lokacin malma yana k'ok'arin maida kayan jikinsa tace "kuma sai naci uban Larai idan muka had'u rafi, Tunda ka koreni, daga makarantarka, sann ta juya rik'e da Allonta, tayi tafiyarta." Koda ta isa gida tana gunguni, Tsohuwa ke tmbayarta lfy? Meya dawo da ke gida ynzun?" Idonta ya cika da hawaye tashiga fad'awa tsohuwa abunda yafaru tun daga farko hark'arshe saboda dijama duk rashin jinta bata k'arya." Tsohuwa taja bakinta tayi shuru na minti goma, sannan tanisa tace "toh zauna kihuta, gaskiya dijama banji dad'in korarki da malam d'ahiru yayi ba." To yanzu yazanyi? An koroki a mktantar boko, gashi yanxun islamiyar ma ankoroki. gashi kuma ke ba k'ok'ariba, allonki sai yayi wata ukku bakiyi wankiba, haka boko baki ganewa, to ni yanzun miye mafita?" Dijama tayi shuru sai zarar ido takeyi Can taja dogon nishi tace "yauwa tsohuwa tunda kinga baganewa nakeyi ba shawara kawai ki sanyani makarantar koyon sak'e sak'e, watak'ila a can nafara ganewa kinga saina koyi sak'a dama nafison can." Mahmud dake tsaye yana jinsu tun shigowarta me zaiyi inba dariyaba, Yace kinko kawo shawara mai kyau, tunda da keda kwad'o bakuda wani banbanci, Bako mai a k'wak'walwarki sai rashin kunya da gidadanci, babu abunda kika iya, sai k'auyanci da jakanci takwalla me kan kifi me idanun mujiya." Idan har ba canxa hali kikayiba mki gama yawon makarantuba." Murgud'a baki tayi cike da jin haushin kala mansa tace "sai naga ai kamar gado nayi a wurinka tunda kamarmu d'aya da kai." Kuma k'wak'walwarmu d'aya, kaga kuwa gareka na gada, yayi saurin ja da baya yace wah?" Ni ?Allah ya tsaren Dake." Yana fad'ar hakan yayi waje abinsa domin ida yabiye mata zata hasalashi Dan yasan dijama badai bakiba." Ai kuwa tsohuwa ta hau masifa, tana fad'in "da kake ce mata kwanyar kifi gareta ai dai 'yar uwarka CE, kuma jininka CE, ni dai bansan irin tsanar da kake yiwa dijamaba." Mahmud baima San tsohuwa na masifaba yayi ficewarsa abunshi." tafiya yakeyi yana dariyar dijama saboda rashin kunya da tayi mata yawa akai ita da kanta tasan bata gane karatu, kai Allah dai ya kyauta." Yana shanye kwanan gidansu, bai ankaraba yaji ankwad'a masa sanda akai, waiga warda da zaiyi wa zaigani, Buba ne da yaransa sun zagayeshi suna shan taba." Cike da mmki Mahmud yake kallonsu, zai bud'a baki yayi masu mgna suka kuma yunkurin kuma buga masa sandar a karo na biyu, Hannunsa ya kara suka yashiga jujuwa yaron Buba ya yarb'ar dashi gefe d'aya, nanfa danbe yakaure tsakaninsu." Nanfa Mahmud ya shiga dukansu, baji ba gani ,duk suka zube warwas wasu kuma suka tsere a guje, Daga cikin masu gudun harda Buba😅 D'aya daga cikinsu daya daku ya kasa iya gudu, Mahmud ya shak'o wuyanshi ya mak'areshi, yashiga tmbyarsa, "waye yasanya Ku?" Menamaku kukeso kuga bayana?" Jinkinsa na rawa yace dijama ce tasanyamu." "what dijama?" Yace cike da mamaki, yanzu dijama bayan rashin kunya harda ta'addaci takeyi?" Ya wurgar dashi gefe d'aya yayi tafiyarshi, zuciyarsa cike da bak'in ciki d mmki." Haka ya koma gida Rigarsa rataye a kafad'arsa, Yana shiga cikin gidan, ya ta rar da dijama tsakar gida zaune, Tana ganinsa ta tashi da gudu ta tafad'a d'akin tsohuwa. Baibi ta kantaba yayi shige warsa d'akinsa, yashiga har had'a kayansa, cikin akwati. Saida ya d'auki komai nashi. Ya tallabo akwatinsa yafito." Lokaci da yafito janye da akwati, yayi dai dai da fitowar Tsohuwa daga band'aki ta dubeshi cike da mmki tace "Mamuda lafiya?" Ina zakaje da akwati?" Mahmud ya dubi tsohuwa yace "gida zantafi tunda naga har anfara turomin "yan iska su dakeni ,watara na maganin b'era za a sanya min a abinci domin naci na mutu, Dan haka tsohuwa kinga tafiyata sai wani lokacin." Ya kai dubansa ga dijama dake zatsaye a bakin k'ofar d'aki, ta marairaice fuska, duk bataji dad'in tafiyar da yace zaiyiba , yace " toh meye kuma na tsayawa kina kallona?" Zaki turosu ne su kuma tareni a hanya?", . Bata tanka masaba illah ta kuma sunkuyar da kanta k'asa, , tashiga tunanin kaddai ace Buba sanyawa yayi aka daki yaya Mahmud." Bai kuma bi takan kowaba ya Yakama hanya yayi tafiyarsa." Tsohuwa ta bishi da Addu'ar Allah ya tsareshi ya saukeshi lfy." bayan fitarsa tsohuwa ta dubi dijama da kyau, taga ba gaskiya a fuskarta tace dijama me ke faruwa da mahmud?" Bata b'oyewa tsohuwa ko maiba tashiga bata lbr abunda yafaru." Aikuwa tsohuwa tashiga yiwa dijama fad'a ta inda take shiga batanan take fitaba, fad'a takeyi sosai kamar ta daketa, dijama bata tankaba illah turo baki takeyi." ******************* *The following day* Tsohuwa takira dijama domin ta aiketa, Tafiya takeyi tana rawa a kan hannya tana d'an karkad'a k'ugunta, Ta k'ofar gidansu Buba tabi inda suke zama suna majalisa, ta hangosu ta d'aure fuska tayi kamar bata gansuba, Sai da tazo daf dasu abokanansa sukace Baba ga mutuniyar can, yana ganin takawo daf dasu ya wangame bakin sa da ya kunbura yayi suntum, yasha duka wurin mahmud." yayi saurin tashi ya shiga gabanta yana fad'in "dijama ta sai ina hakan?" Ta d'aga kai ta dubeshi taga yanda labbansa suka sundume kamar ganda, Bata San lkcin da ta tuntsire da dariya ba, tana nuna bakinsa da hannu, tana kuma dariya." Muzanta Buba yayi, Yashiga kallon kansa, yaga metake yiwa dariya?" Fahimta yayi da bakinshi take yiwa dariya ya, farajin haushi, amma kuma sai ya waske." Ta kuma karkace kai tana kallonshi had'ida ya motsa fuska, kamar ba ita bace ke dariya yanzun, Tace wai dama kai ragone?" Ina taurin naka yake wanda kake tsoratar da mutanen garin nan?" Shin wai meyasa harka bari yaya mahmud yaji maka ciwo, lallema amma dai buba kabani mmki, Ta kuma kallonshi ta tuntsire da dariya tace " toh Allah ya tsare gaba kaga tafiyata", ta barshi nan tsaye Ta rab'ashi ta wuce, me abokansa zasuyi inba dariyaba, da suka tuna da gudun dasukaga yayi jiya." Sukace gskya "oga munfaji kunya jiya wai ya akai hkan ta faru? Musamman kai oga duk kafimu gudu a nan take kashanye kwana, Nanfa yafara k'uluwa. Ya dubesu ya doka masu tsawa idonsa sunrik'e zuwa launin ja." Dijama nayin nisa snn tawaigo ta kallesa taga yana nan a inda ta barshi tsaye, ta kuma b'arkewa da dariya ta d'aga murya ynda zaijita tace "amma dai Buba Kai wawa ne wlh da mace zatasanya kaci duka hka, tunda ma Nagano kai ragone na rantse bazan aurekaba, tun wuri ka nemi matar aure amma ba dijamaba ehe, tana kaiwa nan ta zuba a guje ta b'ace masa." Aikuwa Buba ya k'ulu iya k'uluwa yashiga zage2, yana d'aga anda yana kirarinsu na 'yan tauri, Had'ida borin kunya." "Karya kike dijama na rantse da Allah Indai ina numfashi a garin nan bawani Wanda ya isa ya aureki saini, saini Buba na dijama yar gidan tsohuwa." *wacece dijama*?" Waye Mahmud?" Muje zuwa yanzun lbr yake ba'ayi komai ba." [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_😅) Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) 7⃣ Mahaifin Mahmud da mahaifin Dijama Hassan da Husaini ne, Hakan suka tashi a tare duk abunda zasuyi a tare sukeyinsa, har sha'awa suke bawa mutanen k'auyen Tofa dake cikin k'aramar hukumar Kano." Hassan da Husaini sun taso cikin so da k'auna da kulawa a wurin mahaifansu, Malam Adamu da Hadiza, Wanda a yanzun jikokinsu suka canxa masu suna suka mayar dasu tsohuwa da Kaka Babu wani Abu dake raba Hassan da Husaini, ako da yaushe suna tare da juna, a cewarsu a yanda suka fito tare sun d'aukarwa Kansu Alk'awarin baxasu tab'a rabewa ba." Tun haihuwar Hassan da Hussaini tsohohuwa bata kuma k'ara samun haihuwa ba, wannan dalilin yasa suka d'auki son duniyar nan suka d'orashi a Kansu." K'auyen Tofa k'auye ne mai tattare da Ni'ima da wadatuwa. Da kuma yalwar makarantun boka dana islama." Wannan dalilin yasa mlm Adamu ya tashi tsaye tsayen daka domin ganin Hassan da Husaini sun samu ilimi boko dana Islama, kasan cewar mlm Adamu manomi ne, akwaishi da wadatar zuci, da son yaga ya wadatar da iyalinshi batareda sun gani a wani gidan ba." Hakan kuwa akayi suntashi cikin hazak'a da k'ok'ari Wanda gaba d'aya k'auyen na Tofa, suna Alfahari dasu, suka zama abun sha'awa da kwatance." Akwana a tashi har suka kammala karatunsu na _secondary_ har suka tafi Jami'ar Bayaro _university_ dake cikin garin Kano." Shigarsu jami'a ra'ayinsu yarafa banbanta a wurin karatu domin Hassan _Business_ yakeson karanta, shi kuma husaini _mass_ _communication_ yake son ya karanta." Hakan suka Amincewa junansu amma kuma duk da hakan a cikin mkrantar a tare suke kwana a tare sukecin abinci, idan har ba saninsu kayiba bzaka tattace Waye hassan ba waye husainiba." Hakan sukayi karantunsu cikin Aminci da soyayyar juna tare da taimakon mahaifinsu har sukayi masters." Allah ya taimakeso suka fito da sakamako mai kyau, Nan take har rugogowar d'aukarsu aiki akeyi." Hassan aiki baya gabansa yafi ganewa kasuwanci domin tun kafin takardunsu su fito har ya bud'a d'an karamin shago a k'ofar gidansu yana sayarda atamfofi da shamdodi da takalma, wadda yin hakan harda taimakakon mahaifin nasu." Wani babban kamfani ne na sarrafa motoci, dake cikin garin Kano a can Hassan yasamu aiki inda ya samu matsayin manager campanin za'a dinga yimashi Albashi mai tsoka." murna a wurin mahaifan nasu da kuma d'an uwan nashi Husaini abun ba'a mgna Bayan kwana biyu da faruwar hakan, garin Lagos suka d'auki Husaini aiki a gidan TV na garin Lagos, inda shima suka bashi babban muk'ami." Hmmmm Hassan Husaina sunyi bak'in ciki sosai da rashin samun aikin da basuyiba a gari d'aya, inda suka buga Kansu da k'asa sukace sun fasa yin aikin indai ba gari d'aya suka samuba.". Tsohuwa da Kaka suka Shiga lallashinsu suna basu hak'uri a kan cewa rabuwar aikinsu ai bashine rabuwarsu ba, kuma ai ba'a can zasu dawwamaba." Da kyar a ka samu suka hak'ura had'ida yiwa junansu Addu'a." Ranar da zasu fara tafiya wurin aiki, ko wannensu ya shirya kayanshi a akwatinsa, sunja wuri d'aya sun zauna suka rungume junansu ko wanne idonshi ya cika da hawayen rabuwar da zasuyi." Tsohuwa da Kaka dake tsaye a tsakar gida suna jiran sufito surakasu, sukaji shuru basuda niyar fitowa, kai tsaye suka shiga d'akin, suka ta tarar dasu a zaune rungume da juna suna hawaye." Sukansu saida suka tausaya masu ganin cewa tunda aka haifesu basu tab'a rabuwaba, A yanxun shekara Ashirin da bakwai kenan sai yanzun da girmasu lokaci d'aya zasu rabu tabbas dole suyi kukan rabuwa." Hakan suka shiga lallashinsu da ban baki da komai sannan suka lallab'asu had'ida yi masu rakiya suna d'agawa junansu hannu sukatafi." Tsohuwa da Kaka sunyi kewar tafiyar tasu, sai dai daga k'arshe suka bisu da Addu'a Neman dacewa." Wata d'aya da tafiyarsu suka shiga aiki gadan gadan baji bagani, kuma sun tsare gskiyarsu da Amana, Kullu suna kiran junansu a waya ko kuma su hau charting suna fira cike da kewar junansu." albashinsu na farko suka shigo garin na Tofa suka shiga rarrabawa tsofafin garin da masara k'arfi." Sukayiwa tsohuwa gyaran gida aka mayar mata da ginin zamani, Kaka yacika da murna da farin ciki, suka wadata fahaifan nasu snn daga k'arshe suka koma wurin aikinsu." Bayan shekara d'aya da fara aikin Nasu, ba laifi kud'i sun zauna masu a rayuwa babu abunda suka nema suka rasa, Kaka ya tayar masu da fitina akan cewa zamansu a hakan ya isa, Ya kamata kowanne daga cikinsu ya nemi mata domin yayi aure, ko zasu ga jikokonsu tun suna da rayuwa." Suka amsa gaba d'ayansu da to." daman abunda suke jira kenan." Bayan wata biyu da yimasu maganar dukansu suka nemo matar aure a garin da suke aiki, Hassan ya nemo auren Hajara, Husaini kuma ya Nemo auren Bilkisu." Saida suka turawa junansu photo nan yan matansu dukansu sukayiwa juna sambarka da dacen da sukayi sannan suka isarwa da Kaka umurnin sa." Kaka da tsohuwa sunji dad'i sosai sunyi murna, cikin sati d'aya aka tsaida magana aka sanya ranar bikin nasu nan da wata d'aya masu zuwa." Akwana tashi lokacin bikinsu yayi aka shiga hidimar biki gadan gadan, in da Hassan ya k'era k'aton gida naji da gani a cikin garin kano, Shima Husaini hakan, gida iri d'aya sukayi duk abunda ke akwai gidan hassan akwaishi gidan Husaini gari kawai ya babbanta Hassan a kano husaini a lagos." Ansha shagalin biki anyi taron bikin da ba'a tab'ayin irinsaba a cikin k'auyen na Tofa." Ko wannansu Amaryarshi ta tare a gidansa." Hmmmmm." Bayan wata tara da aurensu matar Hassan ta haihu ta haifi d'anta namiji mai kama da Husaini sak👌🏻 mmki kowa yakeyi sai. Sai dai ba abun mmki bane kasancewa jini d'aya ne." Murna Husaini yashigayi dajin labari, tun kafin ya iso yasanyawa yaro suna *Mahmud* Hassan yaji dad'i sosai domin shi a kullum farin cikin husaini shine nashi. Kuma duk abunda yakeso shima shi yakeso." Shekarar Mahmud Uku aduniya aka Haifa mashi k'anwa aka Sanya mata suna Asma'u." Har a lokacin matar Husaini ko b'atan wata bata tab'ayiba." Ta d'auki damuwar duniyar nan ta d'orata a kanta, inda shi kuma Husaini sai dai ya dinga Addu"a, Allah yabashi mai Albarka idan lokaci yayi." Wanda a wannan lokacin Hassan kud'i sun zauna mashi ya daina aikin kamfani yashiga harkar siyasa gadan gadan." Shima Husaini hakan ta kasance a gareshi yazama babban d'an jarida a garin lagos wanda akeji dashi, kud'i sun zauna masu." Bayan matar Hassan ta yaye Asma'u ta kuma samun wani cikin ta haifi d'anta namiji aka sanya mashi suna Adamu wato sunan Kaka kenan suna kiranshi da Khalil." Wasa wasa sai da sukayi shekara goma sha uku da Aure sannan Allah yabawa matar Husaini ciki, Wanda yayi dai dai da kuma samun cikin matar hassan haihuwa ta hud'u." Samun cikin Bilkisu matar Husaini ba k'aramin murna sukayi ba gaba d'aya family musamman Hassan, da yakeji tamkar matarsa ce keda cikin." Haka sukaci gaba da renon cikinsu har ya kai watan haihuwa, ta haifi 'yarta macce sak Hassan, Masu karatu kusan dai Hassan da Husaini kamarsu d'aya idanba saninsu kayiba bazaka iya tattace d'ayansuba." Hassan yayi mata hud'uba yasanya mata suna Nana Khadija wato sunan tsohuwa kenan, inda tsohuwa taji dad'in wannan kara da akayi mata aka sanya sunanta, amma kuma ta shinfid'a sharad'in cewa baza'a canza mata sunaba akirata da ainahin sunanta Nana khadija." Hakan akayi domin bin umurnita, ba'a canxa mata sunaba da sunanta kowa ke kiranta, amma bnda mahaifan nata sai dai suka dinga kiranta da Ummie." Inda tsohuwa take kiranta da deejamah." Tunda akazo da Mahmud wurin bikin sunan Nana khadija, yaji yana sonta musamman da duk wanda ya gansu ake cewa kamarsu d'aya a lokacin mahmud yana da shekara goma sha d'aya." Idan zai kwanta barci dole sai a kusa da ita yake kwantawa. Wnn abun bak'aramin dad'i yayi wa mahaifan nasuba." Bayan haihuwar khadija da sati d'aya matar hassan ta kuma haihuwa ta haifi 'ya mace aka sanya mata suna Fateemah." Bilkisu tayi Arba'in d'in Nana Khadija cike da k'oshin lafiya, dijama tayi kyau harta gaji sak kamannunta suka dinga komawa na mahaifinta." Shiri sukeyi zasuzo Kano yawon Arba'in domin ya d'auk'i huto a wurin aikinsa." Sun shirya tsaf cikin Shiga ta Alfarma, anyiwa Deejamah kwanliya tayi kyau tana sab'e a kafad'ar mahaifiyarta, Husaini yana janye da a kwati yana k'ok'arin sanyashi a but, Bayan ya shirya komai suka shiga mota yajasu suka d'auki hnyar kano." Tafiya sukeyi suna yiwa 'yarsu wasa cike da so da k'auna, Suna kaf da kawowa Husaini yana yawa da Hassan kan cewa gasunan sun kusan kawowa, domin sai sunfara tsayawa cikin kano wurin hassan idan sukayi kwana biyu sai su wuce Tofa wurin tsohuwa idan suka gama kwanakin da zasuyi sai su dawo gida." Yana cikin waya da hassan saigani sukayi mai mota ya gifta masu ta gabansu ya daki motarsu, Tayar motar husaini ta fita ya yanki daji babu abunda sukeyi sai Addu'a domin kuwa yayita k'ok'arin ya tsayar da motar amma yakasa." Saida takai gindin wani k'aton icce, ta daki icce gaba d'aya motar takife, Wadda yyi ddai da zuwan mutanen da abun ya faru a gabansu suka biyo bayansu domin ceto rywarsu." K'ok'arin tsiratar da rayuwarsu aka shigayi, da kyar aka samu a ka fito dasu a k'ark'ashin motar wanda a lokacin ko wannensu baya motsi Allah ya karb'i rayuwar bayinsa." Cikin ikon Allah Nana khadija ko kwarzane batayiba, koda aka cirota a motar sai wasa takeyi da hannunta alamar tana cikin k'oshin lfy." [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Written By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *9* Gudu takeyi tana ihu, Buba na biye da ita. Samarin Antyn lantana ne, suka hangota tana tik'ar gudu suma suka dafo mata dama jiranta sukeyi sunada haushinta." Tana ganinsu suma sun biyota, ta kuma k'ara gudu tana fad'in wayyo jama'a kufito Ku taimakeni 'yan fashi da makami." Wani tsoho a kan kekensa yana tafiya yanajin hka yasaki keken ya xuba da gudu ya nemi ma b'oya." Matan Aure sai kama d'iyansu sukeyi suna rufewa a d'aki suna Addu'oi domin a tunaninsu 'yan fashin ne suka shigo cikin garin." Dantijawan garin da samaru suna ganin su Buba na gudu tareda dijama, sun d'auka 'yan fashin sukeyiwa gudu, ai kuwa har 'yan rigaggen gudu sukeyi suna shigewa gida had'ida rufo k'ofa da sanya sakata." Duk inda dijama ta gifta tana ihu su Buba na biye da ita suna Neman kamata, Jin ihunta tana fad'in wayyo 'yan fashi da makami, jama'a kufito Ku taimakeni Kowa ta Kansa yakeyi baya tsayawa saurarenta." Da kyar tasamu ta kawo gida, tana shiga gida ta mayar da k'ofa ta rufe ta sanya sakata, Ihun takeyi bakinta yak'i yayi shuru tana fad'in "wayyo tsohuwa 'yan fashi da makami." A razane Abba ya mik'e tsaye cike da tashin hankali da tsoro ya tallabi Kaka yashigar dashi d'aki, Tuni tsohuwa ta kai d'aki zaninta a hannu daga ita sai dogon siket, saura kad'an tayi tuntub'e ta fad'a wurin tashi." D'aki d'aya suka shige suka rufe ko wannensu sai zarar ido yakeyi." Can sukaji ana dukan k'ofar waje da k'arfi kamar za'a cire k'ofar.' Jikin tsohuwa ya soma rawa tana kallon Abba tana cewa "yanxun Hassan ya zamuyi?" Karfa su shigo su kashemu." Abba yace "kwantar da hankalinki tsohuwa baxasu kashemuba, jin haushina d'aya na baro bindigata a cikin mota." Kaka kuma ya sunkuyar da kai sai salati yakeyi yana addu'a jikinsa sai rawa yakeyi' Dukan k'ofa akeyi ba girma ba arziki, tsohuwa ta dinga rawar jiki zanenta a hannunta takasa d'aurawa sai addu'a takeyi idan tasaki wannan ta kwaso wannan." Dijama ta dubi tsohuwa ta dubi kaka ta rik'e ciki tashiga kwasar dariya, tana nunasu da hannu." Tsohuwa na ganin hakan ta fara tunanin ko dijamace ta janyo fitina a waje ba 'yan fashin bane." Tsohuwa tace Hassan ina ganin ba 'yan fashibane dijama ta janyo mana fitina." Abba yayi saurin waigawa ya dubi dijama da sai dariya takeyi idan ta dubi tsohuwa da kaka. "Yace dijama suwaye ne? Mekikayi masu?" Turo baki tayi tace Abba su Buba ne, bata k'arasa maganarba sukaji dukan k'ofar yayi yawa, kamar harda hayaniyar mutane a wajen, Sai a lokacin Kaka yayi magana yace "ai saikatashi kafita kaji abunda ke faruwa, Indai wann hatsabibiyar yarinyarce wata rana sai ta janyo mana mgnar da za'a cinnawa gidan nan wuta duk mu k'une gaba d'aya Yana gama mgnar ya wurgawa dijama harara ya d'aga sandarsa ya zungureta mata k'afa da ita." Abba ya mik'e da Sauri ya bud'e k'ofa yafita, Bbu abunda tsohuwa takeyi sai wurgawa dijama harara domin yau ta kaita bango." Abba yana fita yaga mutane jimjim a k'ofar gida, babba da yaro, tsofaffi da samari, kowa sai fad'in Albarkacin bakinsa yakeyi a kan dijama, a gefe d'aya tawagarsu Buba ce da makamai a hannunsu, d'aya gefen kuma samarin Antyn Lantanane suma rik'e da makamai, rik'e baki yayi yacika da mmki." Suna ganin fitowarshi sukayi saurin ajiye makamansu suka zube k'asa suna gaida shi." Bai tambayi abunda ke faruwaba Dan yaji duk abunda suke fad'i, illah yashiga basu hak'uri, tare da rarraba masu kud'i." Wani dantijo yagani zaune wuri d'aya ya rafka tagumi, kowa yana zuwa karb'ar Kud'i shi yana zaune wuri d'aya baya da niyar motsawa,daga inda yake, Abba ya isa kusa gareshi yace "Baba lfy meya faru?" Ko wanine bashi da lfy a cikin iyalinka." Dantijon ya dubi Abba yace "Alhaji dama ciwon ne ai da sauk'i." Abba yace "Baba meke faruwa?" Ina kan keke na ina tafiya yarinyar wurinka tadinga ihu tana fad'in 'yan fashi da makami, bansan lokacin da nasaki keken hannuna naba, wurin intsiratar da kaina, Kafin in ankara ansace mun keke, kuma wlh Alhaji shi kad'ai na mallaka shine kaddarata." Abba ya lallasheshi had'ida kirga kud'i masu yawa wad'anda sukafi na keken yabashi had'ida bashi hak'uri, Hakan Abba yayi bawa mutane hak'uri yana yimasu Alheri suna wucewa daga ciki kuwa harda Buba da yaranshi da saurayin Antyn lantana." Harda wani magidanci wurin gudun 'yan fashi bai saniba ya ture 'yarshi ta karye a hannu, bai ankaraba saida yaji ance ba yan fashin bane snn ya fahimci Ashe ya karye 'yarshi a hannu." Shima Abba yabashi hak'uri had'ida bashi kud'i masu yawa da zai nemarwa yarshi magani harta warke." Sann Abba ya juya yashiga gida yanata mmkin hatsabibanci irin na dijama, Dijama ta rakub'e wuri d'aya sai zarar ido takeyi tsohuwa sai faman fad'a take mata kamar ta daketa." Abba shima yashiga yimata fad'a kamar ya doketa abunda bai tab'a yi mataba tunda aka haifeta, Kaka dake zaune gefe d'aya yace "gwara da Allah yasa ka nan a gaban idonka hakan ta faru, Kullum a rana d'aya sai sama da mutum goma sunkawo k'ararta tsohuwa ke tare mata,bata son ganin b'acin ranta." Amma tunda ynxun ka ganewa idonka sai ka d'auki mataki, akai, Ga ganta nan Ko mkranta bata zuwa gaba d'aya makarantar biyu Arabic da boko duk ankorota, saboda hatsabibancinta gata bata gane komai sai fitina da rashin kunya. Yakai k'arshen maganarshi yana zungura mata sandar hannunshi." Tsohuwa bata tanka masuba saima taja bakinta tayi shuru, domin yau itama dijama ta kaita bango." Abba yayi kyaran murya ya dubi tsohuwa yace "inna kiyi hak'uri kibani dijama natafi da ita na nema mata ilimi Wanda zatayi dogaro da kanta tazama abar Alfahari a cikin Al'umma, yin hkan shi zai Sanya mana natsuwa a zuciyarmu ganin mun rik'e marainiyar Allah tsakani da Allah." Kaka yayi karaf yace "aikuwa wlh da ka taimakemu ka taimaki mutanen garin nan mundun katafi da dijama kabar garin nan da ita, ni wlh wani lkcin idan na tsaya ina tunanin inda dijama ta gado wnn halin nata sai inkasa tunano kowa a cikin zuri'armu, ina ganin wata k'ila a can cikin dangin mahaifiyarta tayi gadon wnn halin." Tsohuwa tace "nidai ya isa haka malam kamata yayi kadinga yiwa dijama Addu'a ba aibatataba." Kaka yace "ni Sam bana aibata dijama a kullum Addu'a ta d'aya Allah ya shirya mana ita, yabamu ikon rik'e amarta da Allah ya d'ora mana a kai." Abba ya katse zancan da yace "to Ummie tashi kishiga ciki ki had'o kayanki mutafi marece yafara." Tana murna tana tsalle zataje birni. Ta tashi tashiga d'aki ta fara had'a kayanta." Tsohuwa bata son tafiyar dijama dan dai ba yanda zatayi ne, dole ta hak'ura tabari za'a tafi da ita." Sai da ta shirya kayanta tsaf a jaka ta tallabo jakar tana dariya tana jin dad'i, ta fito." Abba har ya kammala shirinsa ya fito had'ida yiwa su tsohuwa sallama dijama na gabansa Jakarta a hannunta suka nufi hanyar waje, Tsohuwa dai Addu'a take masu Wanda takejin kanta duk ba dad'i an d'auke Mata dijamarta." Kaka kuma saboda dad'i kamar ya zuba ruwa a k'asa yashi, domin yasan yau idan ya kwanta barci ba bak'ocin da zai tayar dashi domin kawo shedun dijama." Har mota suka rakasu, suna yimasu add'o'i." Mutanene cimjim gaban motar k'awayen dijama suna bangwana, Abba ya bud'a mota yashiga dijama itama tashiga gidan gaba sai wasar baki takeyi tana dariya tana d'agawa su suwaiba hannu." Murmushi Abba yayi ya kunna mota ya fara tafiya, Dijama ta lek'o ta k'ofar marfin mota tace "suwaiba idan kukaje gonar Audu wurin satar gwaiba, idan kukaga Buba kuce masa natafi birni amma zandawo don saina rama abunda yayi mun." Abba yace Ummie na wai meye hkan? Ki zauna dai dai mana karda kiji ciwo." Snn tayi saurin gyara zamanta Abba yaja mota Yatafi yana dariyarta, suka d'auki hnyar kano." _dijama a birni ikon Allah🤔_ [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMA*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_😅) Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) 8⃣ Hassan dake waya da Husaini yanajinsa yana kalmar shahada a waya, gaba d'aya hankalinsa ya tashi ya fito da saurin shi baibi ta kan kowaba ya shiga motarshi yajata da k'arfi ya mik'i hanya, ya nufi wurin da yaji Husaini yace masa ya kawo." Cikin minti talatin ya isa wurin ya d'aga wayarsa ya shiga kiran wayar husaini, d'aya daga cikin wad'anda suka kawo masu taimakon gaggawa, ya d'aga wayar yashiga yiwa Hassan bayanin abunda ya faru, ya shaida mashi da cewa gasunan Asibity, Had'ida yimashi kwatancen asibity dasuke." Cikin tashin hankali Hassan yanufi Asibity idonsa yana zubar da hawaye kamar macce." A Gaban gawarsu yake dur'kushe yana kuka yana jijjiga Husaini yana fad'in "Husaini katashi don Allah karka mutu kabarni rayuwata idan babu kai bnga amfaninta ba, kai kad'ai ne d'an uwana jinina Wanda nake shawara dashi husaini katashi." Kuka yakeyi sosai kamar ya d'auke numfashi yana jijjigar gawar Husaini." Mutanen wurin suka tallabeshi suka bar wurin dashi ana bashi hkr, Snn dga k'arshe yakira mahaifan Bilkisu da sauri suka zo, snn ya kira Kaka da tsohuwa, a tare sukazo asibity aka d'auki gawarsu aka nufi Kano da su gidan Hassan akayi masu wanka da sutura aka kaisu gidansu na gskiya." A nan gidan Hassan akayi amsar gaisuwa, Inda Dijama tana rungume a hannun tsohuwa tana bata madara." Hassan yayita lallashin tsohuwa akan ta amince tabari Hajara taci gaba da shayar dasu tareda fateema, Amma tsohuwa ta kafe tace "sam bazai yiwoba, kuma da anyi sadakar bakwai zatayi tafiyarta gida, tare da dijama tazata tafi Dan bazata bartaba." Hankalin Hassan ya kuma tashi, ya shiga rok'on tsohuwa akan ta amince ta bar masa dijama zai kula da ita ya had'ata da 'ya'yanshi yanda bazata tab'ayin maraiciba." Tsohuwa tace "Sam bazai yiwoba, itama ita zata dinga gani a gabanta tana jin sanyi tana d'ebe mata kewar Husaini da tarasa." Hakan akayi bayan sadakar bakwai ta harhad'a kayanta ta goya Dijama zata tafi, direba yana jiranta." Hassan da iyanlansa suka yomata rakiya, ko wannensu idonshi cike da hawaye domin ji sukeyi mutuwar Husaini ta kuma dawo masu sabuwa." Mahmud kuka yakeyi sosai yana birgima yarik'e tsohuwa yana fad'in bazataje masa da dijamarsaba." Kuka yakeyi sosai kowa ya tausaya masa, tsohuwa tace a had'o masa kayanshi sutafi tare idan hutunsu na mkranta ya k'are sai aje a d'aukoshi, tun da daman hutun makaranta sukeyi." Haka kuwa akayi, aka had'awa Mahmud kayansa yana murna yana dariya, sukayi masu rakiya zuwa mota direba yazasu suka d'auki hanyar Tofa." Wnn shine dalilin zaman dijama a wurin tsohuwa a cikin k'auyen tofa." Tsohuwa bata son jin kukan dijama bata son ganin b'acin ranta, Haka mahmud da zarar akayi masu hutun mkranta zai tsira fita a kan dole sai ankawoshi wurin tsohuwa yaga dijamarsa." Itama dijama tun tana k'arama da zarar Mahmud yazo hutu, bata kuma yarda da kowa sai mahmud a tare sukecin abinci a tare suke kwana, idan tayi kashi shike wanke mata, shike mata wanka, zarar hutunsu ya k'are Idan direba yazo d'aukarshi, da kuka da komai suke rabuwa, Tsohuwa tana jijjinawa wannan shak'uwa tasu, haka shima Abbah wato Hassan kenan shima yana jijjinawa wann soyayyar tasu." Wnn dalilin ne yasa mahmud duk lokacin da suka samu hutu baya iya zama garin kano sai dai yatahowarsa Tofa yayi zamansa saboda dijama, har zuwa yanzun da girma yazo masa ya mallaki hnkalin kansa yashiga jami'a a yanzun yana zangonshi na k'arshe a dgree d'insa." Tun tashin dijama a rayuwa babu abunda ta nema ta rasa, domin tsohuwa da Kaka da muhmud basu da wani buri da yawuce a koda yaushe su farantawa marainiya, basa son ganin kukanta." Abba shike d'auke da karatunda da duk wani Abu da yashafi rayuwata, tunda tsohuwa ta kafe a kan cewa baxata bashi itaba, amma shi har ga Allah yaso ya d'auki dijama ya had'ata da yaranshi yabata gata Wanda yin hkan shi zai sanyashi ako da yaushe zai dinga ganin kamar Hussainin shi yana nan bai mutuba." Tun tashin Mahmud shi mutum ne mai son a girmama shi, baya d'aukar raini a gida ko a waje, K'annansa su fateema da zarar yashigo a gida kowa yake kama Kansa, idan ba hakan ba da zarar sunyi abunda ba dai dai ba a nan take zai hukuntasu. Ya azzabtar dasu yayi tafiyarsa." Wnn dalilin ne yasa yaji ya tsani dijama saboda rashin jinta, gata bata gane karatu, Kuma bata ganin girmanshi kwata kwata ta rainashi raininda ba Wanda ya tab'a yi mashi irinshi." Tsohuwa bata ganin laifinta duk rashin kunyar da zatayi jan maganar da zatayi a waje tsohuwa bata ganin laifinta, Wann dalilin yasa a rayuwarshi yaji ya tsaneta basa shiri kwata kwata.wani lokaci Sai ya d'auki niyar cewa bazai k'ara zuwa Tofa hutuba saboda rashin kunyar dijama, Amma da zarar anyi masu hutun ko na kwana biyu ne baya iyawa sai yazo Tofa yayi hutunsa snn ya koma." Kamar ynzun da Hutu yazo yayi, bai iyar da kammala hutun nashiba, ta had'ashi dasu Buba, ya tattara kayansa ya koma warsa gida Wanda tsohuwa tacika da mmki." *Wnn kenan mudawo labari* *************** Mahmud na komawa gida, kowa ya cika da mmki dan ganin hutunsu bai k'areba ya dawo." Abba ne yakirashi a falonsa yana tare da momy mahaifiyarsu yashiga tmbayar sa, lafiya me yadawo dashi bayan ba hakan ya sababa hutunsu bai k'areba?" Murmushi yayi ya sunkuyar da kansa yace " Ba komai Abba hakan nan kawai nadawo babu abunda ya faru." Abba ya sauke ajiyar zuciya yace "ina fatan kowa yana lafiya?" Ya 'yata Ummie ina fatan tana cikin k'oshin lfy?" Murmushi mahmud ya k'ak'aro yace kowa lfy Abba. Kaka ne kawai yake fama da ciwon k'afa, amma kuma yaji sauk'i sosai." Abba yace subahanallahi!!! Ai kuwa zanje cikin _weekend_ d'in nan nadiboshi, Momy tace "Allah yabashi lafiya." Suka amsa da "Amin gaba d'ayansu." Snn Abba yayi kyaran murya yadubi mahmud da kyau yace "dama ko baka dawoba zankira ka, a waya nace kadawo, domin Alhaji Atiku commonden d'in sojoji wnn abokin nawa yayo mun waya a kan cewa anfitarda form na sojoji ya d'aukar maka d'aya, Saika had'a takardunka katafi Abuja cikin satin nan zakuyi jarabawa Allah yabada sa'a yasa a dace." Suka Amsa da Amin." Sannan Mahmud yayi masu sallama ya fito yanufi d'akinshi yana kuma jin haushin dijama a ranshi." ************** Dijama zaune a kusa da tsohuwa tana turo baki, tsohuwa nayi mata fad'a akan ta fara gajiya da halinta kullum saita janyo mata fad'a da fitina a mak'ota." Ta mik'a mata kud'i tace "gashi kitafi gidan jummai ki kai mata kud'in zubi, dan Allah dijama karki tsaya kuma karki kula kowa a hnya kiyi tafiyarki." Mik'ewa tsaye tayi had'ida turo baki tana gun guni, sannan ta karb'i kud'in ta fita." Tana tafiyarta cikin natsuwa abunda bata tab'a yiba, k'awayenta su lantana tagani sunfito daga rafi, suka had'a baki suna mata magana suna cewa "dijama 'yar gidan tsohuwa sai ina?" Bata tsaya ta kulasuba sai dai ta nuna masu da hannu tana tafiya tace "Tsohuwa ta aikeni gidan jummai nakai kud'in zubi, batajira taji amsarsu ba, tayi tafiyarta, sab'anin da, da sai ta tsaya sunyi jan magana snn kowa ya kama gabansa." Mmki suka shiga yi ko meyasamu dijama?" Lantana tace ko dai batada lafiya ne?" Suka had'a baki sukace lafiyarta k'alau akwai dai abunda ke damunta." Sukace "Allah ya kyauta gaba d'ayansu sannan sukayi tafiyarsu." Dijama anfara jin mgnar tsohuwa kenan, hnmmm Bari dai mugani." Tana gafda da zata shiga gidan jummai mai adashi, taci karo da Antyn lantana wadda tabata takarda ta kaiwa yaya Mahmud, ta sha gabanta tana fad'in "yawwa dijama shine nabaki sak'o ki kaiwa yayanki d'an birni shine baki bashiba kika yaga." Bata tanka mata ba, sai ma k'ok'ari takeyi tabi ta gefenta ta wuce, ta kuma tarar gabanta, tana d'auke da k'waryar da tayo nik'an dawa a kanta, Tacewa dijama "wani sabon iskanci kika samo wadda idan ana yimaki mgna kidinga kyale mutane, taciyo kwalar rigar dijama." A rayuwar dijama babu abunda ta tsana irin a rik'e mata kwalar riga, cike dajin haushi ta dubeta tace "lallai ma Antynnan harda wani rigemun riga, bakisan ina ragamaki bane a k'auyen nan saboda lantana amma yau zakisan kowacece dijama." Ta duk'a kamar wadda wani abun nata ya fad'i a k'asa zata d'auka, Tasanya hannunta ta yaye k'afar Antyn lantana, sai gata tafad'i k'asa dab'as kwaryar nik'an dawa ta rabe biyu, nik'an ya zube k'asa Ta rik'e k'ungunta tana fad'in "wayyo Allah nashiga uku K'uguna dijama kin lahantani." Me dijama zatayi idan ba dariya ba, tace "dankinga ina ragamaki, lallai ma Antyn nan to ba tsoronki nkejiba, ni bana tsoron kowa a garin nan ki kiyaye ehe." Babu abunda antyn lantana takeyi sai kuka da murje2 sboda masifar rad'ad'in da k'ugunta yake mata." Dijama nayi mata dariya, ta rab'ata zata wuce, saiga samarin Antyn lantana sunbiyo ta wurin, zasu wuce Ganinta sukayi zaune a k'asa warwas dafe da k'ugu tana kuka tana fad'in wayyo dijama kin lahantani wayyo k'uguna." Dijama na ganinsu taja da baya ta koma hanyar gida, ta arce da gudu, basu ankaraba sai ganinta sukayi tana gudu kamar filfilwa ta kusan shanye kwanar gidansu." Dijama ba dai guduba kamar mai Aljanun gudu." Saurayin Antyn lantana yace "nayi Alk'awarin tunda dijama tashigo gonata saina saita mata hankali A garin nan." Yashiga taimakon budurwanshi ya mik'ar da ita tsaye ya rakata yarakata har k'ofar gida sannan ya juya ya tafi." Dijama na shanye kwana gidansu sai hango motar Abban kano tayi a jiye a k'ofar gidansu, murna tashigayi tun daga nesa ta dinga stalle Tana "Abba oyoyo." Kai tsaye taje kan jikinshi ta fad'a tana dariya tana murna ganinshi domin Abban kano yana sonta sosai, Murna yayi da ganinta yashiga shafar bayanta yana fad'in "Iye Ummie na ta girma, kina nan kina karatu kuwa?" Taji gabanta ya fad'i domin Abba baya wasa idan akazo fagen karatu." Tayi saurin kauda maganar da cewa "Abba ina su fateemah?" Yayi dariya yace sunanan lfyrsu glau, suna gaisheku." Anan suka shiga shirya Kaka domin a d'aukeshi a tafi dashi asibity dake cikin garin domin a kuma diba mashi lfyar k'afarshi." Alhmdulillah anyi mashi aune aune angano ciwon k'afar da sauk'i, aka rubuta mashi magani Abba yasawo mashi sann suka dawo gida." Anan Abba yace zai kwana sai gobe idan yaga ynda jikin Kaka ya kwana snn sai yatafi gida ko da marecene yatashi safiyar _Monday_ a garin kano." Tun zuwansa garin bai hutaba, mutane ne cingim a k'ofar gidan tsofaffi da samari, Abba sai rarraba masu kud'i yakeyi suna godiya tare da sanya mashi Albarka." Abba mutum ne mai taimako da tausayi, wannan dalilin ne yasa mutanen cikin garin tofa suke mutuntashi da darajashi." Washe garin ranar lahadi da safe, misalin k'arfe goma na safe, Abba yana stakar gida zaune, tsohuwa na gefensa d'aya gefensa Kaka ne zaune da sandarsa gefensa a jiye, Abba yana b'are mashi ayaba yana bashi yanaci had'ida sanya mashi Albarka." Dijama na cikin d'aki zaune ta fito daga wanka tana tsara kwanliya." Fuskarta tasha kwalli da jambaki da hoda." Tsohuwa tashiga kiran sunanta tana fad'in "dijama kiyi Sauri Ki shirya kizo na aikeki gidan kuluwa ki kaimata tsarabarda bbnki yazo da ita." To dijama tace had'ida mik'ewa tsaye ta d'auki kayanta tasanya Snn ta fito." Tsohuwa ta mik'a mata Leda cike da ayaba da lemu tace "ungo ki kai mata kuma Dan Allah karki tsaya a kan hanya." Tace "to." Ta karb'a had'ida fita, Abba ya dubita yayi murmushi yace "Ummie ba dai wayoba." Tsohuwa tayi dariya, Kaka kuma yace "hmmm yaja bakinshi yayi shuru." Bayan ta dawo aiken datsohuwa tsohuwa tayi mata tana tafiyarta a hanya tana wak'a tana rawa, tana d'an karkad'a k'ugunta." Wazata gani Buba tagani a gabanta yana wasar Baki yana fad'in dijamata kinyi kyau wnn kwanliya hkan." Bakin buba ta kalla inda har ynzun bai iyar da warkewa ba daga kumburin da yayi." Batasan lokacin da dariya ta sub'uce mata ba, Ta dubeshi tana dariya tace "Wai amma dai Yaya mahmud ya iya duka." Wai kai Buba kana aikin me harya kumbura baka Baki, ta kuma shek'ewa da dariya, ta dubeshi Tace a hkan kake cewa zaka aureni. Allah ya tsaran da auren ragon mutum kamarka, Ni nafison na aure jarumin namiji mai firgita 'yan maxa, amma kai ai macce ne." Ta rab'ashi ta wuce tana dariya, Buba yaji haushi ya k'ulu iya k'uluwa, idonsa ya canza launi zuwa ja, ya zunduma ashar, Wanda yasa dijama saurin juyowa da sauri tana kallonsa." Yace "duk son da nake maki dijama yau bazai hana naci ...... Ya zunduba wani kalar shar ya dafawa dijama da saurinshi cikin hushi." Dijama na ganin hakan ta zuba da gudu ai kuwa buba ya dafa mata, da yaranshi." Gudu takeyi tana kuwa tana fad'in "wayyo Allah jama'a kutaimakeni 'yan fashi wayyo Allah 'yan fashi.da makami" [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Written By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *10* Gafda da sallar magariba suka isa gida, Horn Abba yakeyi baba maigadi yafito da saurinshi ya bud'e mashi get yashigar da motar sa." Dijama sai waige waige takeyi tana kallon yanayin tsarin ginin gida." Abba da kansa ya bud'e mata murfin mota tafito, ya zagaya but ya d'auko jakar kayanta ya rik'e mata suka jera a tare suka shiga ciki." Gaba d'aya family gidan suna kan dinner table suna cin abinci cike da burgewa, Abba yayi sallama da gudu Fatima ta rugo ta rungumeshi tana oyoyo Abba." Ba Wanda ya lura da dijama a gefensa, yaya muhmud daya kai lomar tuwon shinkafa miyar a gushi a bakinsa ya d'aga kansa sama yana murmushi zaiyiwa Abba sannu da zuwa karaf yayi da dijama a tsaye a gefen Abba." Kasa iyar da had'iye tuwon yayi, ya rik'e baki yana nuna dijama batare da yayi maganaba." Sai a lokacin hankalin kowa ya tafi wurin dijama dake tsaye sai zarar ido takeyi, Khalil na ganin hakan yatashi yaje wurin Abba yayi mashi sannu da zuwa, had'ida kallon dijama ya mere baki☹ Ya ranb'a ta gefensu yayi tafiyar shi." Khalil dama hakan yake ko oho gareshi, a rayuwarshi bbu abunda ya tsana sama da mutumin k'auye bagidaje, ko kuma yayi ido biyu da mummunar mace, Wnn dalili. Yasa baya zuwa Tofa gurin Tsohuwa, Ya kuma yiwa kansa Alk'awarin bazai tab'a auren macce mummunaba, ko bagidajiya, sai Wanda ta amsa sunanta macce ta ko ina." Fateema tayi saurin sakin Abba taje ta rungume dijama tana fad'in oyoyo dijamar tsohuwa kai amma. Naji dad'in zuwanki." Hakan itama momy tazo ta kama hannun dijama gaba d'aya suka zauna a kan kujera har da Abba." Mahmud dake zaune a kan dinner table ya kasa motsawa kamar wani mattance saboda ankawo masu fita a gida." Muryar Abba ta ankarar dashi dayaji yana cewa "mahmud lfy kake kuwa ka k'ame wuri d'aya kamar Wanda baya motsi, Bakaga 'yar gidan taka bace Ummie?" Bayan nan tukuna tashi mutafi masallaci mu farayin sallah sann mudawo muyi magana." Mik'ewa sukayi suka nufi masallaci domin gabatar da sallar magariba." Da fitarsu momy ta kama hannun dijama cike da kulawa tace "ummie ya hanya?" Ya kuka baro Kaka da tsohuwa?" Dijama tace "lafiya glau sunce a gaisheku." Murmushi momy tayi, ta kai dibonta ga fateema tace "fateema d'auki kayan 'yar uwarki ki kaimata d'akinki, kibata ruwa tayi Arwala kuyi sallah ki kuma taimaka mata ta cire kayan jikinta kibata d'aya daga cikin kayanki ta sanya sannan kufito taci abinci." Cikin ladabi da biyayya fateema ta "amsa da to mmy, sann ta d'auki jakar kayan dijama had'ida rik'a hannunta suka nufi d'akin fateema. Ita dai dijama biye take sai zarar ido takeyi tana kale kale." Suna tafiya momy itama ta tashi tayi Arwala tayi sallah, tana kammalawa yayi dai dai da shigowar Abba da mahmud." Abba ya dubi Mahmud yace "kaje kafad'awa khalil da zarar munyi sallar isha'i kuzo gaba d'ayanku inaso zanyi mgna daku." Mahmud ya d'an runsuna yace "to Abba." Yana so ya tambayeshi dalilin da yasa yazo da dijama masifa amma baiga fuskaba a wurin Abba hakan yanufi d'akinshi da yana sak'awa yana kwancewa a ransa." Bayan Abba yayi wanka yaci abinci yayi sallah isha'i yana gincire a tsakar falonshi momy na gefenshi tana yanka mashi kankana tana bashi yana sha suna firarsu cike da kulawa da sha'awa." Mahmud da khalil sukayi sallama saka shigo, sannan fateema tareda dijama suma suka shigo, suka zauna a gefen momy." Babu abunda khalili yakeyi da yayi ido biyu da dijama sai ya mutsa fuska kamar Wanda yaga kashi." Dijama na lura dashi, ta wurga mashi harara had'ida murgud'a mashi baki, Karaf sai a kan idonshi, zaro ido yayi yana kallonta cike da mmki." Abba ya katse masa tunani da yafara magana [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Written By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *11* "Abunda yasa na taraku a nan sai Dan in gabatar maku da 'yar uwarku, Ummie ya nuna dijama dake zaune a gefen mmy." Yanuna khalil "Musamman kai khalil da bakowa kasani ba a cikin dangi, saboda baud'and'en ra'ayinka, Amma kasan ko wacece dijama, kasan matsayinta a gidan nan, Baka buk'atar na kuma yi maka wani dogon bayani a kanta." Ya kuma maida hankalinshi a kan Mahmoud, yace "Mahmoud ga k'anwarka nan nasan kafi kowa farin cikin dawowarta gidan nan baki d'aya." "Abunda nakeso daku Ku d'auketa kamar yanda kuka d'auki fateema a wurinku, kubata kulawa kamar yanda kuke bawa fateema, kai inma son samune Kubata kulawa fiye da ynda kuke bawa fateema saboda Ummie marainiyace." Sai a lokacin mahmoud yayi mgna yace "Abba meyasa ka d'auko mana dijama?" Abba dijamar da kasani a da ayanxun ta canza hali, Na rantse da Allah dijama tana iya tayarda gidan nan da unguwar nan gaba d'aya saboda hatsabiban cinta." Nidai Abba dazakaji sha'warata da anmayar da dijama can Tofa Dan tafi ganewa can, kowa ma sai yahuta." Dijama tayi saurin d'ago kai ta dubi yaya Mahmoud ta murgud'e mashi maki cike da tsiwa, ta karkace kai tace "lallai ma yaya nan wai a mayardani tofa to sannu." Khalil yayi saurin nufarta ya sanya hannu ya buge mata baki, dama yana ganin take takenta saitayi rashin kunya." Dijama tayi saurin rik'e baki, tana fad'in wayyo Allah na ya fasa mun baki" "Yace k'azama 'yar k'auye, yaya muhmoud d'in kike yiwa rashin kunya?" Abba ya doka masu tsawa cike da b'acin rai yace "kar in kuma ganin d'aya daga cikinku ya kuma dukanta, bana son hkan, Na rantse akan Ummie zan iya sab'awa da kowa a cikinku, domin ganin farin cikinta, na kuma rik'e Amanar d'an uwana." Ya maida kallonsa zuwa wurin mahmuod yace "Kai Mahmoud yaushe kuka fara 'yar hakan da kaida Ummien taka?" "To koma dai me takeyi a can k'auye ba ruwanku, Domin yanxun ta baro k'auye ta shigo birni." Rayuwarta zata canza, kuma banason tsangwama da hantara a tsakaninku." "Idan Allah ya kaimu gobe kaje makarantar su fateema, Kasan yanda za'ayi ayo mata takardun shedan ta kammala primary sannan, sai a sanyata a jss1 sai suci gaba da karatunsu tare da fateema." Kai kuma khalil kaje islamiyarsu fateema ka yanko mata form a d'unka mata uniform sai ta tafara zuwa." Batare da sun musaba suka amsa da "to Abba." Ya dubesu yace "Allah yayi maku Albarka." Suka amsa da Amin." Sannan ya dawo wurin fateema yace "fateema ga 'yar uwarki nan Ku had'a kanku, kiko ya mata wasu abubuwa wad'anda batasaniba, Kuma ina so ki d'auketa tamkar 'yar uwarki Asma'u da kika rasa, Allah ya jikan Asma'u da rahama suka amsa da amin gaba d'ayansu." Sannan ya basu umurnin kowa ya tashi, Bayan sunfita ne ya kuma kiran Mahmoud ya dawo ya tsuguna, Yace "ya kukayi da baban naka Alhaji Atiku?" Mahmoud ya sunkuyar da kai, yace "zuwan danayi Abuja wurinsa ya karramani sosai, sannan ya turani mukayi jaraba." Yace kuma "nafad'a maka musanya ido daga nan zuwa wata biyu za'a lik'a sunayen mutanen da sukaci, sannan zai kirani mutafi wurin trening Abba yayi murnushi yace "karka damu indai Alhaji Atiku ne kasanyawa rayuwarka har kazama soja." Momy tace "Allah ya taimaka ya tayaka rik'o da gaskya." Suka "Amsa da Amin." Sannan yayi masu sallama yatashi ya fita." Abba ya dubi momy da sai murmushi takeyi d'auke a kan fuskarta, Yace momyn yara babu abunda zance maki a rayuwa sai dai Addu'a domin kinsamarmun farin ciki a cikin zuri'ata Allah ya barmu tare dake, babban burina shine na faranta maki har k'arshen rayuwarta." Ya Matso daf da ita, yarik'a hannunta ya shiga murzawa yana kallonta had'ida kashe mata ido d'aya." Yace "kinsan wani Abu kuwa?" A kasalance ta dubeshi ta girgiza kai alamar A'a." "A kullum idan ina tare dake jinakeyi tamkar ina tare da yarinya yar shekara 17, saboda komai naki na dabanne a koda yaushe yarinya kike komawa." Ya kuma shege mata a jiki yana shishinar daddad'an k'amshin jikinta, had'ida sab'ule mata d'ankwalin kanta yana shafa gashin kanta dayasha gyara da mayunka masu Sanya laushin gashi da santsi uwa uba kuma k'amshi." _Ina ganin hakan nayi saurin fitowa cike da mmkin su Abba da momy ba'a tsofa🤔_ Mahmoud yaje makarantarsu fateema yayi duk abunda Abba ya umurceshi, ya k'arb'o mata uniform d'inta da littafanta yataho mata dasu, Ranar Monday zata fara zuwa makaranta." Da sallamarshi ya shigo cikin babban falon gidan, ba kowa a cikinsa, sai tausin k'arar TV kawai yakeji yana tashi, gefe d'aya yaji sai dariya akeyi harda buga k'afa.' Koba'a fad'a masaba yasan dijama ce." Mmki yashigayi yanufi wurin TV yayi saurin kashewa, Ya juya ya kalleta, sukayi ido biyu da ita, ta turo baki tana hararsa k'asa k'asa." Cikin fushi yace "lallai d'an k'auye yashigo birni yafara wayewa, Tomu a nan gidan ba'a mana kallo a k'urema volume, anan gidan karatu akeyi a koda yaushe ba zaman shashnciba da rashin kunya, takwala kawai Wanda bata gane karatu." Ya jefa mata ledar kayan makarantarta yace "gasu nan ki kwana da shiri gobe Monday zaki fara zuwa makaranta, kuma nizan kaiki da kaina, zan shaida masu cewa baki gane komai kwakwalwar kifi ce dake, kuma da zarar kinyi masu irin rashin kunyar da kikeyi a k'auye, zance suyi fata fata da naman jikinki su jefar dake a bula." Dama tsohuwa ke tare maki yanxunfa?" Kallonshi tayi idonta cike da hawaye domin a rayuwarta bbu abunda ta tsana irin yaya Mahmoud ya kirata da takkwala mai kwanyar kifi." Shima yayi mmkin ganin zubar hawaye a idon dijama anan take lokaci d'aya." Zata bud'a Baki tayi magana kenan ya matso daf da ita, yace "muddun kika bud'a baki kikayimun rashin kunya saina tattakaki." Ta fasayin maganar ta sunkuyar da kanta k'asa tana aika mashi da Allah ya isa a zuciyarta.' Mik'ewa tayi tsaye ta d'auki ledar uniform d'inta, saida ta kwatanci saiti wurin k'afarshi ta sakar mashi remote d'in TV a babban d'an yatsan k'afa, sai da yayi sarin runtse idonshi yace "washh." Saboda zafin dayaji wurin namasa." Ta zuba da gudu ta haiye sama tanufi d'akinsu, taja tayi tsaya a bakin k'ofar d'aki, tana kallonshi tana burgud'a baki tace "kuma bani bace takwala sai dai inkaine." Kuma tunda kakeyimun gorin karatu saina baka mamaki mugu kawai, dan kana ganin nazo gidanku, to kasani duk abunda kakeyimun a rubuce yake a kaina saina fad'awa tsohuwa." Ganin ya nufota tayi saurin shigewa d'akin had'ida sanyawa k'ofar key." Tsaye yayi yakasa tafiya yana kallon babban d'an ya tsanshi da ya somayin ja, Yana tunanin dijama wato bata daina halintaba kenan lallai akwai aiki a nan gaba." Yana nan tsaye wuri d'aya saiji yayi andafashi a bayanshi, Khalil yagani yace "brother lfy kayi tsaye a nan?" Su momyn basu dawobane?" Mahmoud yace "fita sukayi ne? "Khalil yace "sunje gidan gaisuwa tare da Abba." Ya mik'awa Mahmoud wani takarda Mahmoud ya karb'a yana dubawa yana cewa "takardar meye?" Khalil ya yamutsa fuska yace form d'in islamiyar wnn bagidajiyar nan ne, wadda Abba yasanyani karb'owa, nagama cika komai sunanta ne kawai bansaniba, Wlh bnsan abunda yasa Abba ya dawo da ita gidan nan ba, da zarar munyi ido biyu da ita jinakeyi kamar zanyi amai." Mahmoud ya dubeshi yace "khalil 'yar uwarka face, gakya ya kamata ka canza hali Kuma ka canza rayuwa, kadaina ganin 'yan matan Jami"a kyawawa wayayi suna rud'arka har kake kyamatar jininka. To kasani asalinka k'auye a can Abbamu ya tashi a can ya girma har gobe mahaifansa suna k'auye." Wani saurin ja da baya yayi yana duba bayansa, ganin baiga kowa a wurinba yace "haba brother bazaka gane bane, nagodewa Allah da bakowa a kusa dani lokacinda kake fad'in hakan daka sanyani naji kunya." Ido Mahmoud ya tsora mashi yana mmkinsa domin yanda ya d'aukeshi sai yaga ya wuce nan." Takarda ya mik'a mashi yace "ynda bakasan sunantaba nima bnsan sunantaba, kabari idan Abba ya dawo shida ya sanyaka saika tmbayeshi sunanta kagani sai ya fad'a maka." Yana kawowa nan yayi tafiyarshi ya barshi nan tsaye zuciyarshi cike da mmkin khalil." Khalil yabi mahmoud da kallo yace "ya za'ayi na tambayi Abba sunanta, nasan yanda yakejinta a gidan nan yana iya kafsamin a gabanta Zan dai jira har lokacin da fateema dawo daga mkranta saina tambayeta." Yajuya yanufi d'akinshi yana mamakin mohmuod ganin yanda shima yakeji da wann bagidajiyar a gidan nan☹ [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Written By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *13* Da sauri shugaban mkranta ya nufo ajin har da tuntub'e. Yakeyi domin lbrin da ya isar mashi anjiwa 'yar ciyaman da 'yar kassila ciwo." Ganin saurin da yakeyi yasa sauran malamai suka fahimci a akwai abunda ke faruwa, suka rufo mashi baya." Ganin jinin dake zuba a bakukansu ya d'agawa malamai hankali. Anan take aka Shiga basu taimakon gaggawa." Shugaban makaranta ya d'aga waya ya kira ciyaman da kassila yake shaida masu abunda ke faruwa." Ko wannensu cikin tashin hankali suka bugawa jami'an tsaro waya, anan take mota biyu ta 'yan sanda kamar had'in baki, motar ciyaman da motar kassila." Suka shigo cikin mkrantar sai jiniya kukeji kamar za'a tashi makarantar, 'yan sandan kowanensu da zungureriyar bindigarshi a hannunshi." Sai tambaya sukeyi ina yarinyar da taji masu ciwo, a wuce da ita atafi da ita a hukuntata." Dijama dake tsugune gefe d'aya sai Zarar ido takeyi ta karkace kai duk Wanda ke magana tana binshi da kallon tana kallon bakinshi." Turanci kawai takeji yana tashi Wanda bata san abunda suke cewaba kallonsu kawai takeyi." Can taga shugaban makaranta ya nunata da yatsa yana fad'i da Hausa yana cewa "kunganta can itace, yau yau d'in nan da zuwanta makarantar nan amma har ta fara dazamun bala'i." Shekarata goma sha d'aya da bud'a makarantar nan hakan bata tab'a faruwa daniba sai zuwan wann fiti nan niyar yarinya." Tsawa aka dokawa dijama Wanda yasa tayi saurin mik'ewa tsaye saboda ganin zungureriyar bindigar dake hannun d'an sandar." Tashiga ja da baya tana "fad'in Dan Allah kuyi hak'uri karku harbeni sune suka fara tsokanata." Fateema kuma babu abunda takeyi sai aikin kuka, Wanda a cikin mutanen wurin bbu Wanda ya lura da ita tana gefe d'aya a tsaye." Kuma doka mata tsawa d'an sandar yayi, yace "ba kasheki zamuyiba tafiya zamuyi dake sai munji ko waye ubanki a garin nan snn mu d'aukar mki hukunci." Haka aka sanya k'eyar dijama a gaba tare da shugaban mkranta aka sanyasu a mota aka tafi dasu." Dijama sai Zarar ido takeyi wuk'i wuk'i a bayan mota, shugaban makaranta da juya ya kalleta sunyi ido biyu da ita sai ya wurga mata harara." A zuciyarshi yana da yasani karb'arta da yayi a matsayin d'aliba." Fateema na ganin antafi da dijama, ta kuma fashewa da kuka, tayiwa wani malami magani tace "dan Allah uncle kabani Aron wayarka zankira Abba na na fad'a mashi abunda ke faruwa." Zaro ido yyi cike da mmki yace "dama kinsanta ne?" Ta d'aga kai alamar "eh tace yayata ce uwarmu d'aya ubanmu d'aya." Uncle ya xaro ido waje yace "kina nufin 'yar Alhaji Hassan Adam CE?" To ya akayi bansanta ba a cikin gidanku?" Cike dajin haushin tambayarshi fateema ta turo baki tace "bazaka Santaba saboda ba'a garin nan takeba, dan Allah uncle kabani aron wayar mana." Yace "Ayyah fateema kiyi hak'uri banada waya a hannuna, amma nasan za'aje da ita ta nuna gidansu." _kuyi hk'uri d wnn pls yau sai a hnkli_ [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Written By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *12* 7:30am. Shiri sukeyi domin zuwa makaranta, tasanya uniform dinta, wad'anda sukayi mata kyau sunfito mata da fuskarta sak 'yar fillo." Fuskar nan tata tasha hoda da jambaki, fateema dake gefenta zaune, ta dubeta tace "dijama ki goge wnn kwanliyar ta fuskarki tayi yawa sosai idan mukaje Anty tana iya sanya hijabinki fari ta goge mki ita." Ta murgud'a baki tace "bazan gogeba, a hakan zanje kuma bata isa ta gogemun kwanliya taba." Fateema zata kuma yin magana tajiyo sautin muryar yaya Mahmoud yana fad'in "wai bazaku fitoba lokaci fa na tafiya, Allah duk kuka kuskura kuka bari na hawo saman nan sai jikinku ya gaya maku." Da sauri fateema ta d'auki school bag d'inta ta goya. Bata kuma bi takan dijamaba don tasan halin yaya Mahmoud ba sauk'i ne dashi ba." Dijama da ke k'ok'arin sanya sendel a k'afarta tana turo baki cikin magana k'asa k'asa tace "to idan ka hawo karka barmu da rai ka kashemu." Ido fateema ta zaro waje tace "yayan kike cewa hakan lallai dijama bakisan halin yaya Mahmoud bane, tana fad'in hakan tayi saurin bud'e k'ofa ta fita, tabar dijama na sanya takalmi." Tana gama sanyawa itama ta biyo bayanta, ta fito tana tafiya harda wani rangwad'a takeyi wai ita 'yar boko." Gaba d'anyansu Suna babban falo zaune suna Brest fast, Abba da shirinsa na zuwa Office khalil shima da shirinsa zuwa makaranta BUK." Mahmuod a tsaye da key d'in mota a hannunshi yana jiran fitowarsu ya kaisu, yadawo yana da inda zaije, har sun b'ata mashi time." Fateema ta fara fitowa sann dijama ta biyo bayanta, Abba na ganinsu cikin uniform yaji dad'i sosai sai murmushi yakeyi a fuskarshi, Momy itama murmushin takeyi tana fad'in "iye 'yan matana lallai kunyi kyau musamman 'yata ummie." Mahmoud dake tsaye gefe d'aya yanayi yana kallon agogon gwal dake d'aure a hannunshi." Khalil ya d'aga kansa yana ya mutsa fuska yana kallon dijama. Da take k'ok'arin k'arb'ar flast d'in break d'insu. Wanda momy ke mik'a masu, Ido biyu yayi da fuskar dijama datasha kwalliya, mai zaiyi idan ba dariya ba, Dariya yakeyi yana nuna fuskarta yana fad'in tab "mutumin k'auye baiyi ba wlh ke wai kwanliyace kikayi hakan ko meye?" Brother wlh karka bari wnn abar ta shigar maka mota, ai sai kuzama abunda kwatance duk inda kuka gifta." Cikin zafin rai Abba ya doka mashi tsawa da k'arfi yace "khalil tashi kafita karna na sab'a maka wlh." Momy Itama tabishi da harara tana fad'in "ni bansan irin rayuwar khalil ba a cikin gidan nan." Ta jawo hannun dijama dake tsaye wuri d'aya tana cije baki had'ida girgiza kai, ranta ya b'aci matuk'a." Mahmoud dake tsaye a inda yake, ya had'e fuska, yayi saurin waigawa ya wurgawa khalil harara cike da jin haushinsa." Mmy ta rik'o hannuta tace "zo nan 'yata na gyara maki fuskarki karki damu da abunda khalili yayi mki hka halinshi yake." Momy tashiga gyara mata fuskarta, ta goge mata janbakin da 'yar gira, ta kuma rage mata hudar fuskarta, Sauran kwallin da tashafa a idonta ne yak'i goguwa. Gudun karsuyi latti momy ta barta haka suka tafi." Bayan sunfita ne Abba ya maida kallonsa ga momy yace "nafara ganin take taken khalil a gidan nan a kan ummie zan d'aukar mashi mummunan mataki idan hakan ta kuma faruwa a kan idona." Inason Allah yabani iko da nisan kwana nacika Alk'awarin da nayiwa d'an uwana kafin ya mutu, na aurawa muhmud Ummie idan ba hakan ba a yanda naga khalil na kyamatarta a gidan nan da bbu abunda zai hana na aura mashi ita, domin kawai naga iya karshi." Hak'uri momy kawai take bashi domin ganin ranshi ya b'aci sosai." A bayan mota suka shiga mahmud bai kulasuba, fuskarshi a had'e, ya tayar da motarsa yaja yanufi makarantarsu." Suna shiga cikin makarantar yayi parking d'in motar shi a cikin harabar makarantar, , tun kafin ya fito dijama ta rigashi fitowa harwani sauri takeyi k'asa na tashi, Da sauri ya doka mata tsawa yace "ke 'yar k'auye da Allah malama ki dawo ki tsaya." Kina wata tafiya k'ura na tashi sallan ki b'atawa mutane jiki da k'asa, 'yar k'auye kawai Takkwala mai kwanyar kifi, kamar da gske sai kace ganewa kikeyi. To bari na fad'a mki nan ba k'auye bane mudun kikayiwa malamai rashin kunyar da kikeyi a k'auye tsinanen dukan tsiya zakici kuma ba Wanda zai rama maki." Juyowa tayi tana kallonshi ta sunkuyar da kanta k'asa, a rayuwar ta bbu abunda ta tsana irin yaya Mahmud ya kirata da mai kwanyar kifi, ta d'aukarwa kanta Alk'awarin cewa zata maida hankali tayi karatu Wanda yaya Mahmud sai yayi mmkinta, a lokacin zata bud'e baki ta mayar masa da raddin takkwalar da yake kiranta da ita." A fusace ya juya wurin fateema da mmkinsa bai gantaba sai ma hangota da yayi ta kusan shigewa class." Gaba ya shige dijama na biye dashi, office d'in shugaban mkranta ya shiga ya gabatar da dijama, sann daga k'arshe gaban idonsa aka kaita class, Aji d'aya aka ajiyesu da fateema kamar yanda ya buk'ata, saboda fateema ta dinga koya mata wasu abubuwa wad'anda bata saniba." Sai da yaga shigarta aji sann ya shiga motarsa ya dawo gida." Da shigarta ajin d'alibai sai kallonta sukeyi ganin yanda ta tsurawa silin roba ido sai kallo takeyi, gaba d'aya sai k'arewa ajin kallo takeyi da kujerun dake ajiye a cikin class d'in." Fateema ta hango a can zaune tayi saurin bud'e baki tare da d'aga murya tace "lah fati Ashe aji d'aya aka ajiyemu ai kuwa naji dad'i." Gaba d'aya ajin suka tuntsere mata da dariya, wata 'd'iyar chiyaman d'in garin, Wanda suke mak'otaka da Abba, tace "amma dai ke 'yar k'auyece wlh." Suka kuma shek'e mata da dariya, wata d'aliba daga cikinsu tace "dubi yanda ta shafa kwanli a idonta, ta fad'i hakan had'ida nuna idon dijama suka kuma shek'ewa da dariya." Dijama taji haushi sosai, fateema ta mik'e tsaye ta kama hannun dijama da tayi tsaye takasa zama saboda jin haushi, ta zaunar da ita a kan kujera kusa da ita." Dijama taja wuri d'aya ta zauna tana sake sake a ranta, Malam mai English ya shigo ya fara yi masu karatu ta kashe kunne ta kwantar da hankalinta tana saurare kuma tana fahimta." K'araurawa taji an buga alamar antashi break fast, hakan yayi dai dai da fitar malma mai English, d'alibai suka fara fita waje domin cin abinci." Da sauri dijama ta duro a kan kujera ta shagaban 'yar gidan chiyaman karon farko mari ta fara kai mata, ta cire hijabin jikinta tasha d'amara cikin d'aga murya tace "ubnwa kike cewa 'yar k'auye?" Tashiga nusarta, baji bagani, saida bakinta ya fashe da jini, gaba d'aya ta b'ata gaban hijabinta, D'aya yarinya wanda harda ita wurin yi mata dariya, ta matso wurin dijama ta cimuimuye mata riga a bayanta, Dijama tasanya k'afa ta bayanta ta shure mata baki, aikuwa yarinya ta kwatsa ihu ta duk'e ta rik'e bakinta da jini yaketa zuba." Ihu 'yan aji keyi da gudu suka fita suka kira shugaban makarantar." Babu abunda fateema keyi sai aikin kuka, Dama kuka baya mata wuya, saboda kwata kwata fateema bata da fad'a batason tashin hankali, sanyin hali ke gareta." [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Written By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *14* 12:30pm Abba ne zaune a Palo ya dawo daga office Mahmud zaune a gefensa yana shaida masa cewa Alhaji Atiku ya kirashi a waya akan cewa ya xama cikin shiri satin nan ya shirya kayansa ya sameshi Abuja domin sunansa ya fito zasu wuce wurin trening." "Alhmdulillahi Abba yace, Yana murmushi cike da jin dad'i da farin ciki, ya dubi Mahmud yace "Alhaji Atiku mutumin k'irkine abokina ne tare muka tashi mukayi makaranta d'aya dashi, A rayuwata ta duniya bbu abunda Alhaji Atiku zai nema gareni banyi mashiba indai baifi k'arfinaba, saboda yanda yake nunamun k'aramci da k'auna." Mahmud inaso idan kaje ka kula da kanka, Kabishi sau da k'afa kayi mashi biyayya kamar yanda kasan kanayi mun Allah yayi mka Albarka." Bai rufe bakinsaba fateema tashigo ko sallama bbu idonta yayi ja alamar taci kuka,har ta gaji." Mahmud ya dubeta cike da kulawa yace "fateema meyasameki?" Abba yace "ina Ummie take?" Kafin tabasu amsa sukajiyo jiniyar motar 'yan sanda a k'ofar gida, Saiga Baba maigadi yashigo da saurinsa ya zube k'asa gaban Abba yace "ranka ya dad'e 'yan sanda na sallama da kai a waje." Abba ya zaro ido cike da mmki yace "yan sanda?" Meyafaru?" Mahmud shima hakan, Fateema ta kuma fashewa da kuka tace "wlh sune, Momy ta taso tashiga girgixata tana tambayarta "sune suwa?" Meya faru?" "Sune wad'anda suka kama dijama suka tafi da ita, Mahmud yayi saurin juyowa ya kalleta, ya kuma kallon Abba da momy, yace "dijama tayi halinta kenan tajanyo mana fitina." Suka d'unguma gaba d'ayansu suka fita, Mahmud ke gaba sai Sauri yakeyi Abba na biye dashi snn momy da fateema." Yana tukarar motar ya hango dijama zaune a bayan mota sai zarar ido takeyi" 'Yan sandan na ganin Abba sukayi saurin fitowa suna gaisuwa gareshi kasan cewar Abba ta fito takarar d'an majalisa na jahar kano, A garin na kano, kowa yasanshi babba da yaro, kuma Abba mutum ne mai yawan Alheri ga jama'a." Tambaya yashigayi meke faruwa?" Anan sukashiga yi mashi bayani cike da girmamawa." Hak'uri Abba yashiga basu, snn dga k'arshe ya d'aga waya kira ciyaman da kassila yashiga bsu hkri ya kuma shaida masu da cewa 'yarsace ta aikata hakan a bisa kuskure." Ko wannensu mmki ykeyi, Gnin basu san dijamaba." Anan sukayi sallma da cewa ko mai yawuce Allah ya tsare gaba." Snn aka fito da dijama daga cikin motar, Abba ya d'auki kud'i masu yawa ya mik'awa 'yan sandar suka amsa suna godiya snn sukaja motarsu sukayi tafiyarsu." Mahmud yayi kanta da sauri, ya rik'o hannunta yashige da ita d'akinsa ya sanya key yashiga jifgarta yana dukanta ba girma ba arxik'i, Ihu takeyi tana fad'in wayyo tsohuwa kizo ki ceceni, Abba da momy sai dukan k'ofa sukeyi amma yak'i bud'ewa, rai b'ace Abba ya nufi d'akinsa ya d'auko extra key ya nufi d'akin mahmud ya bud'e ya shiga." Ya daina dukanta ya sanyata kamun kunne yana zaune gefe d'aya yana kallonta hannunshi rik'e da bulala." Yana ganin Abba ya shigo yayi saurin tashi tsaye yashiga ja da baya, Abba ya rik'a dijama ya mik'ar da ita tsaye, Tana ganin Abba ta fad'a jikinsa ta fashe da wani sabon kuka, tana fad'in "Dan Allah Abba ka taimakeni ka bayar dani wurin tsohuwa idan naci gaba da zama gidan nan yaya Mahmud kasheni zainyi." Abba ya rik'a hannunta yana bata hak'uri had'ida juyawa ya wurgawa Mahmud harara snn suka fita." Da fitarsu mahmud ya sauke ajiyar zuciya, ya fad'a kan gadonsa ya kwanta rufda ciki, Ya shiga tunanin dijama, Sam bayajin dad'in rashin jin maganar da takeyi, babban abunda yafi b'ata masa rayuwa shine akan karatu dijama batason karatu ko kad'an rashin kunya da tujara yayimata yawa a kai." Yashiga tunanin yanZun meye mafita wani mataki ya kamata ya d'aukar mata wadda yin hakan zai sanyata dole ta tsaya ta natsu tayi karatu, Wanda a ynxun ilimi shine gishirin zaman duniya." Idan bakada shi babban cinka da jaki kad'an ne." Makarantar barci boarding school ta fad'o masa a rai, Wani murmushi yayi ya kuma juya kwanciya yace "tabbas makarantar barci zan kaita inda bata ganin kowa da zarar tayi rashin ji abata kashi kuma dole ta tsaya tayi karatu ba Dan tasoba." Hakan dai ya yanke shawarar kaita boarding school kafin ya bar garin hankalin kowa ya kwanta." Mik'ewa yayi yashiga toilet yayi wanka ya fito ya canza kayanshi ya d'auki key d'in motarshi yajata yanufi gidan wani abokinshi Ahmad wadda shima k'anwarshi a makarantar barci take karatu. domin ya tambaye shi abubuwan da yakamata a shiryawa dijama." Abba na rik'e da hannun dijama suka nufi babban Palon gidan, inda momy take zaune, momy na ganinta ta mik'a mata hannu alamar ta taxo gareta, Cikin sauri taje jikin momy ta fad'a tana kuka." Momy sai bubbugar bayanta takeyi tafad'in yi shuru Ummie daina kuka, barni da Mahmud duk yashigo falon nan saina rama mki dukanki da yayi mki." Suna hakan sai ga Khalil ya shigo da littafai a hannunshi, yana fad'in " Momy meya faru yau a gidan nan ina shigowa unguwar nan ake fad'amun 'yan sanda sunzo gidan nan harda wnn ya nuna dijama da hannu don har ynzun baisan sunantaba, suka gani a bayan motarsu." Momy tace "bkmai akwai abunda ya kawosu wurin Abbanku." Ya mere bki da dayaga ynda dijama ta wani shigewa momy ajiki ta lafe." Haushi tabashi ya doka mata tsawa yace "Dan Allah malama ki d'aga mata k'afa karki gajiyar mana da ita." Momy ta wurga mashi harara tace "ina ruwanka?" Meye nka aciki ina ganin dai k'afatace ba takaba." "Momy to karta gajiyar da ke tasanya ciwon k'afarki ya tashi." "Kaga Khalil ni banason tsangwama, kawuce kayi tafiyarka kayi abunda ke gabanka." Momy taja hannu dijama suka tafi d'akinta cikin dabara da hikima tashiga yiwa dijama nasiha, "Ummie na ya kamata a ce kin natsu kin fara sanin ciwon kanki, ki tsaya kiyi karatu domin ki hau wani mataki da mu kanmu zamu yi Alfahari dake." Ki zubarda duk wasu halayanki na k'auye, ki tsaya kiyi karatu ki zama 'yar birni, maiji da kanta." Ki daina tsokanar fad'a, Tace "momy banice na tsokanesu ba, sune suka fara tsokanata suja cemun 'yar k'auye, kuma ni ynxun bnaso ana kirana da 'yar k'auye." Momy tayi murmushi tace "tunda bakiso a dinga kiranki da yar k'auye sai kin tsaya kinyi karatu Arabic da boko, kindaina tsokanar fad'a, kizama kamar 'yar uwarki fateema." Dijama tace inaso nima nazama yar birnin kamar fateema, ko Dan yaya mahmud ya daina kirana da mai kwanyar kifi yar k'auye, sai idonta ya kuma cika da hawaye." Momy tadinga share mata,hawaye tare da yimata nasihohi cikin hikima da dabara taja hannunta tasanya ta toilet ta taimaka mata tayi wanka momy ta gyara mata gashin kanta, had'ida gyara mata jikinta man shafi kawai ta shafa mata da hoda, da kuma man Baki." Ta d'auko mata wata dogowar riga ta atamfa tabata ta sanya had'ida d'aura mata d'an kwali ta zubo mata gashinta a bayan ta." Dijama tayi kyau sosai tafara fitowa 'yar birni, dama kuma dijama kyakkyawace." Momy tace "eyeh Ummie na kinga ynda kikayi kyau kuwa?" Dijama taji dad'i tayi dariya." "Maza kitafi wurin yar uwarki fateema k'arfe uku Khalil zaizo ya kaiku makarantar islamiya." A guje tafita tana dariya tana jin dad'i." Momy na ganin yanda tafita da gudu tayi murmushi ta girgiza kai "mai hali baya fasa halinshi." Momy tafitoTanufi d'akin Abba, ta Tarar dashi yayi zaune a kan kujera yayi shuru alamar akwai abunda yake tunani." Sallama tayi ta zauna kusa dashi, ta rik'o hannunshi tace "Abban yara lafiya?" Meke faruwa?" Wani dogon nishi yaja ya dubeta yace "wato lamarin ummie ne narasa ynda zanyi da ita, akan ta natsu ta tsaya tayi karatu, hankalina ya kwanta domin ganin narik'e amanar da d'an uwana ya barmun." Momy tace "ka kwantar da hankalinka, Ummie tayi mun Alk'awarin cewa ta daina duk abunda takeyi zata tsaya tayi karatu, domin kawai a daina ce mata 'yar k'auye." Abba yayi murmushi yace "inko hakan ne danafi kowa murna da jin dad'i." Momy tashiga kwantar mashi da hankali da kalamai masu dad'i, harya fara sakin jikinshi yana dariya, Hajiya Bilkisu kenan mace ta tagari A wurin Alhaji Hassan Adamu Tofa. Uwa a wurinsu Mahmud da Khalil da fateema." Da kuma _dijama 'yar gidan tsohuwa😃_ Dijama na shiga d'akin su ta tarar da Fateema a kwance tayi wanka tayi kwalliya ta kwanta barci ya d'auketa." A hankali ta fito ta janyo mata k'ofar ta rufe dan kar ta tasheta daga barci." Ta sauko falo tanufi kicin tazobo abinci a plate ta tanufi wurin TV ta kwanna tashar MBC 3 suna shirinsu na kartom tanacin abinci tana kallo tana dariya." Abba dake tare da momy suna hira, ya duba agogo hannunshi yaga k'arfe 3:15 lokacin zuwa makaranta islamiya yayi, da sauri yakira wayar Khalil domin yazo ya d'aukesu ya kaisu, saboda yau ne dijama zata fara zuwa mkranta." Khalil dake d'akin wani abokinshi suna hutawa da 'yan matansu wayayyi yan boko masuji da Kansu suna zaune a gefensu suna hutawa, ko wannesu yayi matashin filo da Brest d'in budurwanshi ana kallo ana hutawa." Khalil kansa a kan Brest d'in budurwarshi mai sona Yasmin 'yar wani hamshak'in mai kud'ice a anan cikin garin kano, Hannunshi d'aya yana sanya cikin pant d'inta yana wasa dashi, ita kuma tashiga shafashi tana wani nishi." Wayar Abba ta katse masu jin dad'i, Yayi saurin d'agawa yaji Abba yana cewa "Khalil kana ina ne? To duk inda kake duk abunda kakeyi kamaza kazo ka kaimun su fateema makaranta yanzun nan jiranka nkeyi." Da sauri khalil ya sauka a kan Yasmin yace "bbyna Abbana kekirana bara naje nadawo, Kishirya zanbiyo ta nan na d'aukeki na ajiyeki gida tunda bada mota kikazoba. Ya juya ya dubi abokinsa Auwal da yayi nisa tareda budurwanshi yayi murmushi yace "Auwal baka da sauk'i wlh." Auwal ya d'ago rinannun idonshi, ya d'aga mashi gira yacika bakinshi da Brest d'in budurwanshi yana sha." Dariya khalil yayi yaja hannun Yasmin ya canxa mata d'aki yace kijarani a nan tafi nadawo, Ta dubeshi had'ida kashe ido tace "OK saika dawo my." Yafito ya ja motarshi yanufi gida." Kai tsaye cikin falo ya nufa. Da sallamarshi d'auke a bakinshi." Wata kyakkyawar bby ya hango kwance a kan kujera da alama kallo takeyi barci ya d'auketa TV kawai ke aiki." Kasa hak'ura yayi sai da yanufi wurinta, gashin ganta yayi tozali dashi Wanda d'ankwalin kanta ya zame, gashin kanta ya bayya ya rufe maya fuska." "Wow khalil ya furta ya tsinci kanshi da durk'usawa saiti fuskarta yasanya hannunshi yashiga gyara mata gashin da ya rufe mata fuska." Karan hancinta yagani har baka, Wanda yayiwa kyakkyawar fuskarta kyau yashiga k'are mata kallo yana fad'i a zuciyarshi "gata k'aramar yarinya gata da masifar kyau, kuma daga ganinta idan ta girma saitayi mnyan kayan aiki." Murya Abba ya tsinkayo tareda momy suna saukowa daga sama, yayi saurin mik'ewa tsaye ya daidaita kanshi, ido biyu sukayi da Abba ya sunkuyar da kai alamar girmamawa yace "Abba sannu da fitowa." Abba yayi murmushi yace "yawwa khalil harka iso?" Abba ya kuma maida kallonshi wurin momy yace momyn yara, kiyiwa yaranki mgna su shirya sufito sutafi mkranta." Momy tayi murmushi ta Amsa da "to." Snn ta tashi tanufi d'akinsu fateema." Tafara tafiya kenan khalil ya dubeta yace "momy bak'uwa kikayi ne?" Momy ta waigo ta kalleshi cike da mmki tace "bak'uwa kuma a ina?" Ya juya yana kallon wurin da yaga kyakkyawar yarinyar kwance." Momy ta bi wurin da yake kallo da ido, kasan cewar babban falo ne set d'in kujeru uku ke cikin falon." Hango dijama tayi tayi ale ale sai barcinta takeyi hankalinta a kwance." [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Written By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *ina Sarah yau ranarkice kuma snnu a hankali duk zanzo kanku masu tsarguwar Sarah*😅😅 *15* Bata kuma tanka mashiba illah ta nufi wurin dijama, Wanda tayi d'ai d'ai sai barcinta takeyi, Momy tashiga ta yarda da ita, a Hankali ta bud'e idonta, sukayi ido biyu da momy ta sakar mata murmushi, Wnda ya kuma yasanya khalil rud'ewa ya k'ura mata ido yana kallonta harda d'an murmushi yake fitarwa a fuskarshi, domin ba k'aramin kyau tayi mashi ba." Momy taci gaba da cewa "ummie kitashi mana lokaci na tafiya." Mik'ewa tsaye tayi, ta turo baki alamar shagwab'a tayi mik'a tana salati, Khalil sai da yayi saurin kaiwa zaune, a inda yake, Ya runtsi idonshi domin mik'ar da yaga dijama nayi ta kuma fito mata da kyanta da yarintarta sak 'yar fillo kyakyawa." Abba ya dubeshi cike da kulawa yace "khalil lfy" ko baka da lafiya ne?" Dafe da kai ya girgiza Kansa "Eh "Abba kaina keyimun ciwo." Cikin tausayi yace "subahanallah idan KA ajiyesu ka tabbatar da kaje asibiti kaga likita domin ya baka magani." D'aga kai yayi alamar "to." Ashagwab'e dijama ta nufi d'akinsu tana turo bki momy ta katse mata barcinta,mai dad'i da takeyi tana mafarkin tsohuwa, karo taci da FATEEMA sanye da uniform har ta shirya tafito. FATEEMA tace dijama kiyi Sauri ki shirya kifito mutafi kinsan yaya khalil bayason jira." "To kawai tace "a tak'aice ta wuce tashiga d'akin domin shiryawa." Khalil yanaji FATEEMA ta ambaci dijama yayi saurin joyawa ya kuma kallonta, yana mamaki kar dai ace bagidajiyar yarinyar nan ce tafara wayewa." Anan ya fara jin haushin Kansa, Meyema yagani a jikin 'yar k'auye wanda har ya yasanyashi jin kasala a nan take lokaci d'aya." Haushin Kansa ya faraji yaja dogon tsaki ya mik'e tsaye had'ida kallon d'akin nasu cike da masifa da jin haushi ya d'aga murya yace "na rantse da zarar kuka k'ara minti biyu tafiyata zanyi." Bai rufe bakinsaba dijama tafito cikin shigar uniform d'inta ruwan k'asa wad'anda sunyi masifar yimata kyau." Kallo d'aya yayi mata ya had'e fuska had'ida jan dogon tsaki, yayi gaba suna biye dashi a baya." Momy da Abba suka bisu da Addu'a suka tafi." FATEEMA tayi saurin shigewa gidan baya dijama ta bud'e gidan gaba zata Shiga, ya doka mata tsawa Wanda yasa tayi saurin firgita taja da baya da sauri." Yace "ke bagidajiya 'yar k'auye karki kuskura ki shigarmun gaban mota salan kisanya duk ta inda na gifta a dinga kallona ana nunani nazama abun kwatance." Harara ta wurga mashi k'asa k'asa had'ida murgud'a baki, Bbu abunda ta tsana sama da Khalil a rayuwarta." Gidan bayan tabud'e ta shiga, batare da ta kuma kallonshiba." Ma zauninshi ya shiga ya tayar da motar suka fara tafiya. Kai tsaye gidan abokinshi ya nufa yyi parking a k'ofar gidan yafito batare da ya dubi inda sukeba yace "kujirani ina zuwa." Dijama ta dubeshe ta wurga mashi harara ta ya tsine fuska, Ta kalli FATEEMA tace "nan ne mkrantar?" FATEEMA tace "ba nan bane munkusan kaiwa, wata k'ila akwai abunda zaiyi a ciki." Dijama bata tanka mataba, illah ta kauda kanta gefe d'aya ta shiga kallon motocin dake wucewa." kai tsaye Ya shiga cikin gidan, d'akin da ya ajiye budurwanshi ya nufa, sautin nishinta kawai yakeji yana tashi harda 'yar kuwarta." Da sauri ya murd'a k'ofar d'akin ya shiga, tarar da ita yayi tsirara ta bud'e k'afarta tana biyawa kanta buk'ata da ya tsun hannunta." Tana ganinshi tayi saurin cire hannunta daga gabanta, taja bargo ta rufe jikinta, idonta ya cika da hawaye, Tashiga magana tana girgiza kai "karkaga laifina Khalil kaine sanadin sanyani yin hakan, saida ka jagwalgwalani ka katayar mun da sha'awa, snn ka tashi kayi tafiyarka, Khalil kafi kowa yasanin ina da yawan buk'ata sosai kamar yanda kake." hasalima kaine ka sabamun da hakan akai akai, KA saurara kaji sautin me kakeji a kunnenka a d'akin Ahmad?" Khalil da yayi tsaye kamar gunki mmki da Al'ajabi sunyi mashi yawa, Ashe dama macce tana iya biyawa kanta buk'ata da kanta, lallai idan baka mutuba a gidan bariki komai kana iya gani." Sautin nishin abokinsa yakeji Wanda ya saba da jin irinsa idan yana tare da macce yanajin dad'i." Tsikar jikinshi tashiga tashi ya runtse idonshi, bai kuma bi takantaba ya fito had'ida rufe mata k'ofa da k'arfi." Mik'ewa tayi da sauri ta Sanya kayanta ta d'auko Jakarta tabiyoshi tana kiran sunanshi, amma ko waigota baiyiba ya fita daga get d'in gida." Motarshi ya fad'a ya shiga yafigeta da k'arfi ya bar wurin, dijama ta dubi yasmin da tabiyo motar da gudu tana kiran khalil, Mere baki tayi cike da mamaki tace FATEEMA wancan fa?" Mai kama da lakwani?" Shuru FATEEMA tayi tashiga da d'ewa dijama baki gudun karda khalil yaji abunda take fad'i tunda tasan ba shiri sukeyiba." Khalil yanajinta kyaleta kawai yyi saboda ba itace a gabansaba." Tuk'i yakeyi yana Tunani, duk a cikin 'yan matan da yake ma'amala dasu bbu macce da yaji yana so yana kuma samun natsuwa da ita sama da yasmin." Ya shaida cewa shine ya bud'e yasmin a ledarta ya fasa budurcinta, wnn dalilin yasa yaji yana Sonta yana son kad'aicewa da ita duk a cikin bbys d'insa." Yasmin irin Matan nan ce da samun irinta a cikin mata sai an tona, domin a kullum idan zaishigeta sai yayi da kyar yake shigarta sabda matsewarta, sab'anin wasu yan matan nashi da yana shigarsu zaijishi ya shige batare da yasha wata wahalaba." Wata budurwa da yayi mai sona Salma, da zarar yashigeta jinta yakeyi kamar an bud'e k'ofar text😊 wnn dalilin yasa ya rabu da ita." Hakan kuma yayi wata budurwar mai suna mariam itama hakan take, kamar Salma😊 Khalil mutum ne mai yawan sha'awa sosai baya iya zaman awa biyu batare da Mace na kusa gareshiba ko ba komai yajishi kwance a kanta yana wasa da ita musamman Brest d'inta." Amma daga yau yyi alk'awarin yabar yasmin kenan tunda har tana iya biyawa kanta buk'ata da kanta." Shi ya hak'ura A cikin harabar makarantarsu ya shiga yayi parking FATEEMA ta fito ya juya ta madubi ya kalli dijama ta jingine da kujera sai sharar barcinta kawai takeyi." Fuskarta ya kalla sai da gabanshi ya fad'i, yarasa dalili yin hkan, Ya doka mata tsawa, "ke bagidajiya tashi kifito mun a mota 'yar k'auye ba sabanba sanyi Ac ya dokeki kinsaki bki kina barci." Fitowa tayi batareda ta kulashiba, tana fitowa ya d'auki turare yashiga fesawa a motar." Yana gamawa bai kallesuba ya wucesu yayi gaba ya nufi wurin shugaban makatantar, FATEEMA na ganin hakan tayi sauri tashige aji tana cewa dijama Allah yasa a jiyeki a jinmu." Murmushi Dijama tayi bata tankawa fateema, tana ganin inda Khalil, yashiga ta lallab'a takoma bayan motarshi ta tsinci k'usa a k'asa, Ta duk'a inda ba Wanda ke iya hangota tashiga caccakar mashi Tayar mota, gaba d'aya tayarshi ta baya guda biyu sai da ta sokesu tayi mashi faci snn ta lallab'a ta nufi inda taga ya nufa." Bayani taji yana yiwa shugaban makarantar yana fad'in "daga k'auye tafito batasan komaiba akanta, Dan haka taimaka akaita ajin k'arshe.' Saboda inajin lbri a bakin brother d'ina Wanda yafi kusanci da ita cewa kwanyar kifi ne gareta bata gane karatu." Sannan batada kunya, Allah gafarta malam kasan renon k'auye yanda Yake, Dan Allah malam karka nuna sananya ko wani abu da zarar tayi ba dai daiba ko tak'i karatu a bata kashi sosai har sai ta daina motsi." Ya juya ya kalleta ya wurga mata harara, ya d'ebo kud'i a Aljihunsa ya mik'awa malam had'ida yi mashi sallama." [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Written By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *16* Khalil Yana wucewa shugaban mkranta ya d'aga kai ya dubi dijama yace "a gaban idonki kuma kinajin duk abunda Yayanki yake fad'a a kanki," To Idan har kinaso mu shirya dake ki maida hankali a karatu, idan ba hakanba jikinkin ne zai fad'a mki snn dga k'arshe na d'aura maki mari a k'afa, kamar yanda kikaga nayiwa wad'an can yaran." Ya nuna mata wasu yara 'yan maza da ya d'aurawa mari a k'afa har da kwad'o yasanya masu." Zaro ido tayi waje cike da tsoro da tashin hankali tace "Dan Allah malam kayi hak'uri zanyi karatun basai kasanya mun mari a k'afaba." Murmushi malam yayi yace "kinyi Alk'awari?" Ta d'aga kai alamar "Eh." Sann yayi mata tambayoyi game da karatunta anan ya fahimci cewa tana da k'ok'ari sosai rashinjin magana ne kawai yayi mata yawa." Aji uku ya ajiyeta suka shiga karatu gadan gadan, dijama ta maida hankali sai karatu takeyi." Khalil yashiga motarsa da Sauri ya tayar da ita, amma abun mmki tak'i yin tafiya." Dogon tsaki yaja ya kuma kunnata amma taki tayi tafiya, da Sauri ya fito yanufi bayan motar wurin tayoyin motar domin ya fahimci matsalar a nan take." Abun mamaki mai zai gani gaba d'aya tayoyinshi na baya guda biyu asokesu har sun fara soncewa." Wani gumi yaji ya fara zubo mashi. Cike da ta kaici, ya rasa ynda zaiyi, gashi babu abunda ya tsana irin ya hau motar haya, Ganinshi Ajinsa zubewa zaiyi idan a ka Ganshi a cikin motar haya." Wani dogon tsaki ya kumaja ya sanya hankicif ya shiga goge zufar dake zubo mashi a kan fuskarshi Ya zagaya ya shiga cikin motar ya zauna ya had'a kanshi da sitiyarin motar yana tunanin mafita, Yana kuma tunanin Wanda yayi mashi wnn aika aika." Mahmud tare da abokinshi Auwal sunfito daga wurin yiwa dijama siyayyar kayan makaranta domin ya shirya mata komai har uniform ya d'unka mata batare da Abba ya saniba." Labarin dijama mahmud yakebawa Auwal, Auwal sai dariya yakeyi, Mahmud yace "wnn ai ba abun dariya bane illah kawai ataimaka mana da Addu'a domin ina ganin kamar Aljanune suka shigeta, Auwal ya kuma shek'ewa da dariya yace "Mahmud nida kabani dijamar nan na aureta inasonta a hakan." Mahmud yanajin hakan yaja bakinshi yyi shuru bai kuma yin mgna." Karya kwanar da zasuyi Mahmud ya hango motar khalil a bakin makarantarsu fateema ya kuma kallon motar da kyau, ya hango shi cikin motar ya had'a kai da sitiyari ko motsi bayayi da alamar akwai abunda ke damunshi." Muhmud yayi saurin nufa wurinshi yayi parking a gefen hanya ya fito ya nufi wurinshi tare da abokin nashi." Khalil da bai lura dashiba sai ji yayi ana kwankwasa mashi glass din mota, Idonshi ya d'aga da suka soma komawa launin ja saboda b'acin rai da takaici, ido biyu yyi da Mahmud murmushi ya sakar mashi had'ida sauke ajiyar zuciya ya Bud'e motar ya yafito , mahmud ya tsura mashi ido yana kallonshi had'ida tambayarshi meke faruwa?" Meyasa yayi parking wuri d'aya kuma ya had'a kanshi da sitiyarin mota yana tunani meke damunshi?" Khalil ya nisa yace "tayar motata CE narasa Wanda yayi mun hakan kuma lfy k'alau na d'auko FATEEMA da wnn yarinyar Wanda tazo daga k'auye na kawosu makaranta, abunda mmki daga shigata mkrantar na fito, na tarar gaba d'aya an farfasa mun tayar mota ta baya, Ni Abun yana bani mmki." Murmushi Mahmud yayi ya dubi khalil yace " muguntar me kayiwa dijama kafin kuzo nan?" Khalil ya ya mutsa fuska yace "Niko meye had'ina da ita da har zanyi mta wani abun? Kawai dai muna cikin tafiya tasaki baki tana barci na tayar da ita, had'ida zubawa mota ta turare saka makon jin da nayi motata ta canza wani wari naji yana fitowa a ciki kamar tayi mun tusa a ciki, kasan mutumin k'auye yanda yake da k'azanta, kawai shine." Mahmud yasan za'ayi hakan domin yasan dijama bata barin bashi." Ya dubi khalil ya yace "mundun baka daina shiga harkar dijama ba saita daza maka fitinar da bazaka mnta da itaba a rayuwarka, domin kuwa dijama bata barin bashi kuma bata yafiya da zarar kayi mata abu komai girmanka saitabi ta wata hanya ta rama abunda kayi mata, Dan haka KA daina tunanin Wanda ya aikata maka hakan bakowa bane face dijama ce." Khalil ya zaro ido waje yana mmki a fusace ya juya zai shiga cikin mkrantar Dan yaci ubanta." Mahmud yayi saurin rik'oshi ya dawo dashi yace "yi hkri KA kyaleta ai nasamo maganinta gobe gobe nan makarantar barci zan turata kowama ya huta." Khalil ya kuma har zuk'a yace brother Dan Allah KA barni natafi naci ubnta Dan wlh nafita iya rashin kunya da tujara." Nafita iya k'auyanci wlh zan kakkarya mata hannu idan na rik'ata." Mahmud ya kuma rik'eshi yana fad'in " KA natso mana kayi hak'uri dibeka 'yar k'auye duk ta da kula maka lissafi." Auwal shima ya shiga bashi hak'uri snn ya hk'ura ya bisu suka shiga motar Mahmud suka nufi gida da cewar zasu turo mai gyaran mota tare da direba idan ya gyara sai a dawo mashi da motarshi gida." Sai da suka fara ajiye Auwal gida snn Mahmud yaja motar suka nufi gida." Kai tsaye wurin ajiye motocin gida mahmud yayi parking da sauri khalil ya bud"e murfin mota ya fito ranshi a dagule, kai tsaye d'akinshi ya nufa batare da ya bi takan kowa ba." Ido Mahmud yabishi dashi snn yyi murmushi a ransa yace "indai dijama ce kad'an ma kagani." Ya duk'a ya d'auki takardun makarantarta da siyayyar da yayi mata ta makaranta yanufi ciki da ita." Da sallama ya shiga palon gidan ya tarar da Abba da mmy zaune akan kujera suna kallon film d'in marigayi d'an ibro mai suna hajiya babba, suna dariya." Gefen Abba ya nufa ya gaida shi tare da momy suka amsa mashi cike da kulawa." Jim kad'an yayi shuru Dan baisan yanda Abba zai d'auki maganar da yazo da ita ba, ta mayar da dijama boarding school." Ya nisa ya sunkuyar da kai yace "bansan ynda zka d'auki maganataba, Abba Kayi hakuri Abba, rashin jin magnar dijama yana d'aga mun hnkali, musamman rashin karatun da batason yi" Abba idan muka nuna muna tausayawa dijama muk'ak'i tilassa mata akan tayi karatu to anan gaba abun saiyafi damun rayuwarmu akan yanzun." Abba wnn dalilin yasa na yanke shawarar gobe idan Allah ya kaimu zan mayarda dijama makarantar barci. Domin nagama shirya ko mai har uniform na d'unko mata da siyayyarta da komai yanuna wa Abba." Abba yayi shuru nawani d'an lokaci yana tunani sann ya d'an nisa, yace "Allah yayi maka Albarka Mahmud hakan dakayi dai daine domin kuwa dijama takace duk hukuncin da kayanke a kanta dai daine." Mahmud yayi saurin d'aga kanshi da sauri ya kalli Abba da yaji yace dijama tashishi, to meyake nufi da cewa hakan?" Hakan dai ya barwa cikinsa maganar ya tashi yayiwa Abba sallama ya nufi d'akinshi." Lokacin tashinsu dijama nayi, Abba ya kira wayar khalil yajita a kashe, bai kuma bi takanshiba yayi wa direba waya cewa yaje ya d'aukosu makaranta." Dijama anci karatu muryar harta dusashe a kan d'aga murya wurin karatu." Direba na ajiyesu ta fito da karatun da akayi masu a bakinta tanayi tundaga waje take karatun har tashigo gida." Sautin karatunta ya tayar da mahmud daga barci, yaja dogon tsaki ya tashi zaune a kan gadonshi ya rik'e kanshi da yaji yana Sara mashi." Wato ita wnn yarinyar rashin karatunta baka hutaba yin karatun ma baka hutaba." Yaja dogon tsaki ya Tashi ya fad'a toilet domin yayi wanka ya fita." Da karatu tashiga babban falon gidan, karatun shine sallamarta Abba da momy sukayi dariya, Abba yace Alhmdulillah Ashe ummie na mahaddaciya ce😊 kai Allah na gode maka [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Written By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *17* _pls dan Allah readers na rok'eku da Allah duk Wanda ke karatun littafin nan idan yazo indabayaso ya k'etare kawai🙅‍♀__ Dariya tasaki ta kai zaune kusa da mmy had'ida fad'in wash mmy nagaji yau munsha karatu." Momy tayi dariya tace "ai naga alama Ummie nah Allah yasa ki d'ore da hakan, da munfi kowa jin dad'i." Murmushi kawai Abba keyi ya mik'e yanufi massalaci domin yin sallar magariba, Momy ta kallesu tace "to 'yan matana kutashi kuje kuyi sallah kuyimun addu'a snn kufito muci abinci." Da gudu suka tashi suka nufi d'akinsu domin yin sallah." Khalil yana kwance rufda ciki sai juyi yakeyi saboda matsananciyar sha'awa dake damunsa, gashi yanxun budurwanshi d'aya ce Yasmin kuma ya d'auki Alk'awari yabarta, ba zai kuma wai waiyartaba." Juyi kawai yakeyi yana sauke nishi sama sama, Khalil mutum ne mai yawan sha'awa wnn dalilin yasa da momy taga take takensa, tasha kamashi yana kallon fina finan BF, ta fad'awa Abba duk abunda tagani, don hka shawararta d'ayace, ya fitar da wacce yakeso ayi mashi aure gudun karya fad'a ga aikata zina." Anan take ran Abba ya b'aci yashiga yin fad'a yana fad'in khalil mai zaiyi da macce kwata kwata shekararsa Ashirin da biyar a duniya, ko Dan ta ganshi da jikin girma za'a kira mashi zancen aure yanxun." Mahmud ma yayansa ba yanzun zaiyi aureba bare khalil jariri, da yanxun yake karatu mataki na uku, Dan haka kar a kuma yimun irin wnn zancen a kiyaye." Momy tabashi hak'uri taja bakinta tayi shuru, amma sai dai tana sanya ido game da shiga da ficenshi." ko da dai khalil d'in yana kiyaye duk wata hanya da zata sanya a fahimci yana neman wasu matan a waje." Juyi kawai yakeyi a kan gado, Jiyayi baya iya hak'ura, kuma gashi ba mota a hannunshi, tashi yayi ya fad'a toilet ya sakarwa kanshi ruwan sanyi, Sanyin ruwan na ratsashi ta ko ina ajikinsa yana sauke ajiyar xuciya sannu a hankali." Bayan ya k'are wankan ne yayi arwala yafito ya shinfid'a abar sallah yayi sallarshi a d'aki, wasu k'ananan kaya ya d'auko ya sanya wad'anda suka amshi jikinshi suka fito mashi da mazantakar shi, idan ka ganshi sai kace ya shekara talatin a duniya.' Fitowa yayi daga d'akinshi kai tsaye d'akin mahmud yanufa domin ya ara mashi key d'in motarshi, yana murd'a k'ofar d'akin yajita a rufe ya tabbatarwa kanshi da baya nan." Palon cikin gidan ya nufa da sallamarshi, a can ya hangosu gaba d'ayansu harda mahmud zaune a tsakar falo suna cin abinci." A hankali yake tafiya ya nufi wurinsu, Abba ya kalleshi cike da kulawa yace "dama kana ciki ne baka fito mukaci abinciba, ko ciwon kanne ke damunka?" Runsunawa yayi ya rage tsawonshi yace "eh Abba Amma naji sauki sosai." Ya Kalli mahmud yace brother aro mun key d'in motarka zanje gidan abokina zan amso littafaina ynzun zan dawo." Momy tace "amma ya kamata ka tsaya kaci abinci ko kad'an ne." Ya ya mutsa fuska domin matsanan ciyar sha'awar da yakeji komai na iya faruwa dashi." Ya danne ya k'ak'aro murmushi yace "yanxun zandawo mmy ba dad'ewa zanyiba." Bai rufe bakin saba dijama dake zaune gefe d'aya kusa da momy tayi ale ale tana cin tuwon shinkafa,da miyar agushi ta d'auko lemon kwakwa Wanda momy ta had'a ta d'aga kofin sama ta kai bakinta, saida tasha ta k'oshi sann ta ajiye k'ofin k'asa, Snn tasaki baki tasaki wani irin kyatsa jikakeyi kyrrrrrr." Da sauri khalil ya waigo cike da jin haushi da takaici, dama yanada haushinta, Yanufeta gadan gadan ya kwad'a mata mari, yace "banza 'yar k'auye kinzo kinsaki baki kina yiwa mutane k'auyanci." Rik'e baki tayi ta kurma ihu tana fad'in "wayyo Allah Abba bakina, ya fasamun baki." Mahmud ya doka mata tsawa yace "Dan Allah malama ki rufe mana baki duk kin rud'a mana kunne." Kafin Abba da momy suyi magana tuni khalil ya bar falon domin yasan za'ayi hakan." Abba ya juya wurin mahmud yace "wai meyasa kukeyiwa yarinyar nan hkn ne? To tashi kafita, karna sab'a mka." Mahmud yana murmushi ya tashi,ya fita." Khalil yana shiga mota ya figeta da gudu bai zame ko inaba sai ciki makarantarsu a lokacin ana kiran sallar isha'i." Inda yasaba ajiye motarsa a nan yayi parking yafito, ya haye kan matar yana kallon 'yan mata wayayu masu aji suna wucewa, duk Wanda tayi tozali dashi saita canxa tafiya domin kawai ya ganta yaji ta burgeshi." Kowace macce mai wucewa k'ok'arin takeyi taga ta burgeshi ya tayata, kasancewar khalil kyskkyawane bafulatani d'an gaye mai ji da kansa." Wasu 'yan mata ne su biyu 'yan gaye suna sanye da riga da wando wad'anda suka kama jikinsu idan kika gansu saiki rantse da Allah kice ba 'ya'yan musulmaiba ne." K'irjinsu ya cika da Brest har rawa yakeyi haka bayansu mazaune sun zauna masu Masha Allah, Tun daga nesa da khalil ya hangosu sai da yaji tsikar jikinshi ta tashi. Wata matsananciyar sha'awa ta tasoma shi." Kafesu da ido yayi yana kallonsu, saida sukazo daf dashi wani k'amshin turarensu yaji ya daki hncinsa, da hannu yayi masu nuni da alamar yanason mgna dasu." Dama abunda suke nema kenan khalil ya tayasu, Batare da b'ata lokaciba suka nufi wurinsa." Durowa yayi daga kan motar ya bud'e murfin motarshi ya shiga yayi masu nuni da su shigo." D'aya ta shiga gidan gaba d'aya tashiga gidan baya." Yaja motar sukabar makarantar, kai tsaye gidan abokinshi Ahmad ya nufa inda suke shek'e ayarsu." Babu abunda kakeji yana tashi a gidan sai kid'e kid'e 'yan matan Ahmad ne cike a gidan ko wacce tana nuna mashi tata bajinta." Kasan cewar Ahmad d'an wani hamshak'in mai kud'ine a nan cikin garin kano yana taka Wanda yaga dama kuma a zauna lafiya, a Tare suke karatu da khalil halinsu ya zo d'aya, dan haka suke shek'e a yarsu a gidan hutawar Ahmad Wanda Abbanshi ya Gina mashi." Khalil yana shiga da 'yan matanshi kai tsaye d'akin Ahmad yashiga ya tarar dashi kwance tsirara, 'yan mata uku a kusa dashi ko wacce da abunda take yimashi najin dad'i."" Hannu khalil ya d'aga mashi alamar jinjinawa, snn yayi mashi nuni akan yabashi key d'in d'aya d'akin." Ahmad da baya iya magana saboda jin dad'i sai dai yayiwa khalil nuni da hannu a Inda yake." Da sauri khalil yanufi wurin, ya d'auki key d'in ya fita, domin jinshi yakeyi ya tsuma, wata matsananciyar sha'awa yakeji tana fisgarshi, 🍌 tamik'e mashi kamar ta fito cikin wandonshi, So yakai kawai yajishi ya fara aiki." Da sauri ya fita ya bud'e d'akin suka shiga Wanda d'akin yasha kayan more rayuwa." Suna shiga ya mayar da k'ofa yarufe ya sanya key, Bai tsaya b'ata lokaciba yashiga wasa dasu, Anan take ya fahimci cewa suma 'yan hannu ne, domin wani sabon salo da yaji sunayi mashi kasa d'auka yayi sai nishi yakeyi yana wani irin sabbatu." Gaba d'ayansu suna kanshi kowa ce da irin nata salon Jan hankali." Duk yanda khalil yake buk'ace da macce sai ya fara sanya hannunshi a gabanta da zarar yajita a bud'e to ba zai kusance taba." Hakan yaci gaba da wasa da 'yan matan nan yana kashesu da zazzafar soyayyarshi, sannu a hankali cikin wani salo, yafara sanya hannu a gaban d'ayan mai suna billy, Jinshi yayi kamar yajefa hannunshi a rame, saboda zurfi da fad'i,da take dashi." cikin wani salo yashiga wasa da hannunshi cikin HQ d'inta snn daga k'arshe ya fitar dashi ynda bzata fahimci komai ba." Wurin d'ayan ya nufa mai sona sa'ade, hakan itama yasanya hannunshi ya shiga wasa dashi a gabanta, amma har k'ara Billy a kan sa'ade."😊 Cikin dubara ya kai kwance suka haye kanshi suna faranta mashi har sai da yabiya buk'atarshi batare da ya kusancesuba." Safiyar Monday dijama shiri akeyi domin zuwa karanta, murna kawai takeyi za'a kaita makarantar kwana, Duk wata siyayyar kayan makaranta Mahmud yayi mata." Momy da Abba nasiha suke mata akan ta tsaya tayi karatu, Abba yyi mta Alk'awarin cewa da zarar ta d'auko na d'aya zai saya mata handset wanda take mutuwar so ta ganta tana dannawa." Ihu ta kurma tana tsalle tana fad'in "nagode Abba indai zaka sayamun waya to ni kuma nayi mka Alk'awarin nice xanyi ta d'aya." Mahmud ya fito cikin dakakkiyar shadda mai kyau mai tsada fara fes👌🏻 wanda ta amshi shi yyi kyau sosai, da key d'in mota a hannunshi." Ya tsugunna ya gaida momy da Abba, snn ya juya ya kalli dijama Wanda ta tsura mashi ido tana kallonshi, ganin tayi yayi mata kyau." Tsawa ya daka mata had'ida zare mata ido yace "baki iya gaisuwa bane, kika kafeni da ido kamar baki sanniba." Turo maki tayi tace "dan kasamu na kalleka, gani nayi kayi kyau shiyasa nke kallonka." Kuma zaro ido yayi waje ya yunkura zai kaimata duka, tayi saurin zuwa wurin momy ta b'uya. "Rashin kunya zakimun, to k'ulelanki karki cinyemun kyau da wnn bakin naki na rashin kunya." Ya mik'e tsaye yace idan kingadama kifito mutafi kayanki na mota." Momy ta rik'a hannunta tareda Abba suka yimata rakiya har mota, zata shiga gidan baya mahmud ya Daka mata tsawa yace "keni direbanki ne." Ta marairaice fuska tace momy Abba Dan Allah kuyi mashi magana karya dakeni." Abba yace "Mahmud karka kuskura ka dakarmun ummie kaji na fad'a mka." Murmushi mahmud yyi yace "to Abba." Snn tadawo gidan gaba ta zauna, ya tayar da mota suka tafi. Tana d'agawa Abba da momy hannu." Sai da sukaga fitarsu gidan snn Abba yyi murmushi yace ummie na case ce, narasa a inda tagado rashin jin nan." Momy itama dariya tayi tace "ai mahmud yafita zama case meye a ciki Dan mata ta kalli mijinta tace yyi kyau." Abba ya kuma yin dariya yace "ai basu San da wnn mgnarba." Tafiya sukeyi ba Wanda ya kula d'an uwansa sautin karatun qur'ani kawai yake tashi a mota k'ira'ar sudes, Tafiya mai nisa sukayi snn suka kawo makarantar mahmud yayi parking a harabar mkrantar yafito dijama na biye dashi a bayanshi." ofishin shugaban makaranta ya nufa ya gabatar da komai." Shugaban makaranta ya kira wata prefet ya had'ata da dijama, ta kaita class snn idan aka tashi ta nuna mata d'akin barcinsu." Mahmud yace "kayanta na mota, suka d'unguma har prefet d'in suka nufi motar mahmud ya shiga fitowa da dijama kayanta harda 'yar katifarta ta kwana." Bayan ya gama fito mata da kayan ne ya dubeta yace "to dijama nakawoki inda dole ki tsaya kiyi karatu arabic da boko ko jikinki ya fad'a maki. Bakida wnda zai ceceki ba tsohuwa ba Abba ba momy dagake sai halinki." Ya juya zai shiga mota tayi saurin binshi da gudu ta rik'e mashi riga, idonta ya cika da hawaye tace "tafiya zakayi kabarni yaya?" Dan Allah kayi hak'uri karka tafi kabarni bnsan kowaba a nan, nayi maka Alk'awarin duk halina Wanda bakaso zan daina." Tabashi tausayi sosai domin dijama jininshi ce k'anwarshice Wanda yakeji da ita a cikin k'annanshi rashin jin maganarta ne yake had'ashi da ita." Yyi k'ok'arin saita kanshi, ya ciro hankacif a Aljihunshi mai cike da k'amshin turare ya mik'a mata yace "goge hawayenki, ta amsa ta goge." Yace "idan kika tsaya kikayi karatu da zarar nazo yimaki visting k'arshen watan nan zancire ki natafi dake gida, Idan kuma baki tsaya kikayi karatuba kikaci gaba da rashin kunyar da kika saba, to anan zaki tabbata har sai ranar da kika fara ganewa." Yaciro kud'i ya mik'a mata bai kuma bi ta kantaba domin tana iya karya mashi zuciya." Yayi shigewarshi motarshi yayi tafiyarshi yana kallonta a madubi tana kuka tana share hawaye da hankacif d'inda ya bata." Prefet d'in ta taimaka mata ta kaimata kayanta d'akinsu snn ta nuna mata class d'insu jss1A dijama tashiga jikinta duk a mace sai sharar hawaye kawai takeyi." [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Written By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *19* "Inason yusra tare danida mahaifiyarta saboda batada k'ane ko k'anna, burin a kullum shine muga Yusra cikin farin ciki da walwala." Babba burinmu a rayuwa shine muga ranar auren yusra." Manyan mutane shuwa gabanni da Alhazai, samari da magidanta, sunta fitowa Neman auren yusra amma sai dai tanuna gaba d'ayansu bbu wnda takeso." Munshiga damuwa mai tsanani da nida mahaifiyarta, Amma ba yarda zamuyi sai dai muka tashi tsaye da yimata addu'a, Allah ya fito mata da Wanda takeso ya aureta, Abun mmki sai gashi abun yazo gidan sauk'i kaine Wanda yusra tagani taji tana so. Alhaji Atiku ya taso daga Inda yake zaune yaxo daf da mahmud ya zauna, Wanda yayi mutuwar tsaye, saboda mmki, da Al'ajabi, ko a shirin film bai tab'a ganin rayuwa irin ta wnn gidan ba mai shinfid"e da rashin tarbiya. Ya dafa kafad'arshi yce "mahmud bazan yi maka doleba, amma nasan bazakak'i 'yataba domin nasan 'yata Yusra ta tara duk wani Abu da d'a namiji yakeso ya samu a jikin macce, Yusra cikakkiyar macce lafiyayya Wanda bata illah ko ta ina." Kaje kayi shawara kuma Ku fahimci junanku Allah yayi maka Albarka, tashi kaje ka huta ka kwana da shirin gobe fitar asuba zakuyi." Mahmud bai samu bakin yin maganaba saboda gaskiyar tayi mashi yawa, hakan ya tashi jiki ba kwari ya fito, ya nufi masaukinshi." Jiki ba kwari ya shiga d'akinsa Wanda aka ware mashi, shi kad'ai Wanda yake d'auke da katafaren gado da duk wani abun more rayuwa." Ajiyar zuciya yasaki ya'ajiye akwatin kayanshi gefe d'aya, ya fad'i zaune a kan gadon yana tunanin, "Alhaji Atiku dake fad'a mashi wai 'yarshi a duniya babu abunda ta rasa." Kuma ta cika macce ta ko ina, to ya akayi yasan da hakan?" Babu abunda ta nema ta rasa Wato harda shi kenan yana nufin harta sameshi, Hmmm lallai kuwa zai nunawa Alhaji Atiku ba komai ake nema a gidan duniyar nan a sameshi ba." Zai nunawa yusra cewa ba komai take iya samuba a duniya, musamman ni kaina da kwatata bata cikin tsarin matan da nakeso, Asalima koda nayi ido biyu da ita bntab'ajin na tsani wani mutum ba kamar yanda naji na tsaneta." Mik'ewa yayi jiki ba kwari ya cire kayan jikinshi yafad'a toilet domin yayi wanka yayi sallah la'asar ko zaiji dad'in jikinshi." Fitowa yayi sanye da jallabiya ya shinfid'a abar sallah ya yatayar sallah." Bayan ya kammala sallar ne yaji yana da buk'atar Hutu, yatashi daga kan abar sallar ya haye kan gado ya kwanta. Yashiga tunani Dijama ta fad'o mashi a rai, murmushi yayi ya kuma mirginawa da ya tuna da rashin jin da takeyi a gida." Koya zata kasance a boarding school? yasan dai muddun tayi ba dai dai ba a can dukan tsiya zata sha domin bakarantar kwana ba uwa ba uba dole kayi biyayya ga senior dinka." Yana kwance ruf da ciki. Sai mutum yaji a gefenshi a kwance yana shafa kyawawan k'afafuwanshi da suka lullub'e da gashin jikinshi, a kan farar fatarshi mai cike da santsi da laushi." A razane ya mik'e zaune cike da fargaba da b'acin rai ya kai dubonshi wurin wazai gani *Yusra* ce cikin shiga ta wasu k'ana nun kaya riga da siket Wanda iya kacinsu a kan cinyarta rigar kuma mai kamar best duk gaba d'aya Rabin k'irjinta a waje yake." Kanta ba d'an kwali ta zubo gashinta a kafad'a Kallo d'aya yayi mata ya runtse idonshi had'ida kauda kanshi gefe d'aya, yayi saurin durowa daga kan gadon cike da b'acin rai." Ya doka mata tsawa yanuna mata hanyar waje yace "xoki fita d'akin nan shed'aniya kawai." Zaro ido tayi waje tana mmkin kalamanshi gashi kyakkyawa ajin farko tana tunanin ya waye Ashe kansa a cikin kwali yake." To meye a ciki Dan tazo d'akinshi ta tab'a jikinshi?" Cikin rausaya da jan hankali ta nufeshi da nufin kai mashi runguma, yayi saurin zaro ido waje had'ida ja da baya, da sauri Ya d'aga hannu ya kai mata mata mari a fuska har sau biyu, Yana huci yana fad'in karki kuskura kice zaki had'a jiki na da naki Domin ni ko a mafarki bana Fatan Allah ya nuna mun wnn nakasanshin jikin naki mai d'auke da najasa." Kifita a d'akin nan nace karna tattakaki." Murmushi tasaki mai cike da takaici tana shafar gefen fuskarta a inda ya mareta duk ga shatin ya tsun hannunshi Nan ya kwanta a gefen fuskarta Tunda Allah yasa a ka haifeta har ta girma babu wnda ya tab'a yimata fad'a bare tsawa bare har a xo ga dukanta, Amma gashi abun mmki yau itace wani d'a namiji ke d'aga hannu ya mareta har sau biyu." A maimakon taji zafin Marin, saima jitayi sonshi da k'aunarshi ya kuma lumkuwa a cikin zuciyarta." Still idonta a kanshi tana mashi kallon sha'awa. Tana shafar kunci, murmushi tasaki tace "ina sonka Mahmud, kuma kasani zan iya jure komai akanka." Ya kuma kallonta a hasale yace " ni kuma banasonki, ke barima kiji bantab'a jin na tsane wani Abu a rayuwata ba kamar yanda nakiji natsaneki." Kalamanshi sunyi mata zafi sosai, tasaki dariya mai Sauti tace "kasanyawa zuciyarka sai na aureka domin bantab'a Neman Abu na rasaba a rayuwata, dan haka dole ka soni kuma ka aureni tunda kana k'ark'ashin mahaifina, Kama d'auka daga yau na zama matarka." Tana kaiwa nan ta fito idonta yana xubar da hawaye." Kai tsaye palon daddynta ta nufa, tana zuwa kai tsaye ta fad'a kan jikinshi ta fashe da kuka mai sauti, Abunda daddy bai tab'a ganiba a idon 'yatshi, tace daddy ina sonshi, katai makamun ka aura munshi." Wlh Mundun narasa Mahmud xan iya rasa rayuwata." Cikin razana ya janyota ya rungumeta yace daina kuka shalele bazaki mutuba a kan wani, "indai INA da rai da lafiya INA numfinshi a doron k'asa baxaki tab'a Neman wani abun kirasaba, shalele daina kuka ki d'auka har kin aure mahmud, Har Mahmud ya zama mallakinki." Dariya tasaki tace "Ngd daddy nah." [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Written By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *18* Mahmud yana komawa gida dama ya shirya kayanshi yau zai wuce Abuja zasu fara trening." A kwati kayanshi ya d'auka tare da duk wani Abun da yake buk'ata yafito, Abba yayi mashi rakiya tareda Sanya mashi Albarka yana kuma jaddamashi akan yayiwa Alhaji Atiku biyayya ya d'aukeshi tambakar mahaifinshi." Mahmud yayi murmushi yace "insha Allah Abba bazaka samu wata Matsala daga gareniba." Suka had'a baki tare da momy sukace Allah yayi maka Albarka yabaka sa'a aduk abunda kasanyawa gaba." Yaji dad'in Addu'ar tasu, ya runsuna k'asa yace "Amin Abba da Momy ngd, Allah ya barmun ku, naci gaba da kyautata maku har k'arshen rayuwata, idan khalil ya dawo mmy kice masa na wuce." Yana fad'in haka yabud'e mota yashiga yatayar suna d'aga mashi hannu har ya yafita get d'in gidan ya d'auki hanyar Abuja." **************** Bayan antashi break fast Kowa ya fito daga aji yanufi wurin cin abinci dijama kuma taja wuri d'aya gefe d'aya ta rakub'e babu abunda takeyi sai ruwan hawaye." Tana tunanin tsohuwa, tana nan zaune tana tunani tana hawaye batasan kowa ya watseba ya ba kowa a wajen duk ankoma class." Bata ankaraba sai saukar bulala taji a bayanta a firgice ta zabura ta mik'e tsaye cike da tashin hankali da tsoro tana kallon wanda ya daketa." prefet ce tsaye a gabanta tana fad'in ubanme kikeyi a nan kowa ya koma aji ya barki, sai magana ake maki kin kyale mutane." Zuciyar dijama takawo mata a wuya, dame zataji da kad'aici ko da mugunta, Prefet taga dijama bata da niyar motsawa daga inda take ta kuma d'aga bulala cike da jin haushi ta kuma doka mata a tsakiyar baya." Sai da dijama ta gantsare saboda axabar zafi, tunda Allah yasa aka haifeta ba'a tab'a yimata irin wnn dukanba." Tana zaune a inda take bata da alamar motsawa bare ta tashi daga wurin." Prefet d'in ta kuma harzuk'a cike da takaici ta d'aga balala zata kuma kai mata a karo na uku, tana wani huci." Dijama tayi saurin mik'ewa tsaye cikin zafin nama ta rik'e bulalar, ta duk'a ta d'auki prefet d'in saida ta d'agata sama snn tabugata a k'asa, ta karb'e bulalar hannunta tashiga zuga mata ita." Ganin duka da bulala b'ata lokacine tayi jifa da bulalar ta haye ruwan cikinta tashiga nusarta." Ihunda prefet d'in keyi shi yaja hankalin sauran d'alibai da malamai suka firfito. Cikin hanzari suna kallon ikon Allah, D'alibai sun zagayesu suna kallo, Duk a tunaninsu Aljanun dijama ne suka tashi, dibo da yanda suka dijama ta haye kanta, nesa ba kusaba prefet tafi dijama girma tsawo da k'iba da komai, duk cikin makarantar bbu wanda d'alibai ke tsoro sai ita saboda girman jikinta gashi kuma muguwa ce bata ragawa nak'asa da ita, malamai su kansu sunsan da hakan, Amma yanzun abun mmki gata a k'asa k'aramar yarinya 'yar shekara 14 'yar jss1 ta d'agata Sama ta kayar k'asa ta danne tana duka sai ihu takeyi." Wnn yarinyar Aljanune suka hau kanta bayin kanta bane, inji malaman dake tsaitsaye sunkasa isa wurin su taimaki prefet. D'in." Dijama tanajin malamai na fad'in Aljanune ai kuwa ta kuma birkicewa taci gaba da jifgarta, ta mak'e murya kamar ba muryar taba tana fad'in "Dan kinga mun kyaleki, kina dukanta, bakisan ko mu suwaye bane?" Can wata malama tayi k'arfin halin tunkararsu da kyar tasamu ta fincike dijama a kan prefet d'in." Dijama na huci tana harararta tana fad'in "idan kika kuskura kika kuma kulamu sai munyi maki illah a makarantar nan." Ai kuwa malamai sukayo kan dijama aka shiga bata hak'uri had'ida yi mata Addu'oi." Shugaban makaranta yana office yana aiki labari ya sameshi, cikin hanzari a ka had'a Assambully kowa ya hallara, A ka d'ora dijama a kan Assambully, sai zarar ido takeyi tana turo bki." shugaban makaranta yashiga bayani a kanta, yashiga nunata yana fad'in "kuyi taka tsantsan da ita kadda Wanda ya kuma kulata a cikinku, idan tayiwa wani daga cikinku wani abun ya hanzarta zuwa wurina ya kawo mun k'ararta ninasan yanda zanyi mata." Idan kuka lura da abunda tayiwa 'yar uwarku, ya nuna prefet d'in dake rakub'e wuri d'aya sai zare ido takeyi tana sauke numfashi da sauri, alamar ta daku." Ya isa kubawa kanku amsar cewa Nana khadija Hassan ba ita kad'ai takeba tana tare da Aljanu, ko Aljanun manyan Aljanu." Dan haka abunda nkeso daku shine ku kiyaye abunda na fad'a maku a kanta, Suka amsa da "to malam." Snn ya umurci kowa ya watse ya koma aji, Dijama na shiga aji kowa ya kama kanshi da ita, Hakan malamin English yashigo suka fara karatu gadan gadan." Bayan antashi daga makaranta kowa yanufi d'akin barci domin cin abinci suyi wanka ayi sallah, snn akoma karatun marece wasu kuma sutafi islamiya." Dijama taja tayi tsaye a wuri d'aya domin batasan inda zatajeba." Anan idonta ya fara cika da hawaye." Prefet d'in da tafara gani farkon zuwanta Senior Rukayyah ita tagani a gabanta tana mata murmushi ta rik'a hannunta suka nufi d'akinsu inda ta ajiye mata kayanta." Senior Rukayyah tun lokacinda taga dijama taji tashiga ranta, Hakan kuma a nan take taji ta kamu da son Mahmud lokaci d'aya, wnn dalilin yasa tad'auki d'amarar taimakawa dijama. A kan karatunta domin ta fahimci burin yayanta kenan tayi karatu." ***************** Mahmud ya sauka Abuja lfy, Inda yaga karramawa wurin Alhaji Atiku. Yana zaune cikin katafaren palon gidan Alhaji Atiku commondent anzagayeshi da kayan ciye ciye da abinci kala kala." Alhaji Atiku a gefenshi nesa dashi yana mashi bayanin yanda zasu fara trening d'in gobe." Sai jiyaniya sukeji tana tashi a harabar gidan, mahmud baiyi mmkiba dibon da yayi tundaga farkon layin gidan har zuwa cikin gidan sojojine birjik aka Zuba a wurin." Yashiga tunanin wata k'ila bak'ine Alhaji Atiku, yayi Bai gama tunaninsaba aka bud'o k'ofa aka shigo batareda anyi sallama ba." Ganin murmushi yayi d'auke a kan fuskar Alhaji Atiku, waigawa yayi domin ganin mai yake kallo yake yiwa murmushi." Wata tsaleliyar budurwa yagani fara fes da ita wanda bazata wuce shekara 23 ba a duniya. tana da kyaunta ba laifi, ta sanya riga da wando wad'anda suka bayyanar mata da duk ilahirin surar jikinta, ta d'ora wani figigin gyale a kanta Wanda dashi da babu duk d'aya. Fuksarta sanye da bak'in glass hannunta d'aya d'auke da katuwar waya. D'ayan kuma d'auke da jaka. Gefen hannunta dama da hagu, sojojine ke take mata baya." Hannu ta d'aga masu tare da ya tsine fuska a kan suyi tafiyarsu, Saida suka Sare mata snn suka juya suka tafi." ganinta yayi taje cikin shagwab'a ta haye a kan cinyar Alhaji Atiku." Mutuwar tsaye Mahmud yayi ya tsura masu ido yana kallon ikon Allah." Cikin shagwab'a take cewa daddy na gaji dayawa." Hannu ya sa yana shafa bayanta yana "fad'in Ayyah sannu shalele kitashi kitafi kiyi wanka ki huta momynki na ciki, tayi maki tausa." Turo bki tayi tace "ni kai nakeso kayimun." Dariya yasaki mai sauti yace "nida kaina shalele?" To tashi kitafi gani nan zuwa yanzun nan Yace baki gaida yayankiba gashi nan zaune, ya Nuna mata Mahmud da yasaki baki yana kallonsu." Taya tsine fuska ta kai dubanta ga mahmud, dan bata lura da akwai wata halitta a wurinba, Ido biyu sukayi da Mahmud ta tsayar da idonta gareshi ta kasa d'auke idonta a kanshi gaba d'aya kyanshi da haibarshi ya tafi da imaninta." Mahmud kuma lokaci d'aya yaji ya tsaneta, saboda daga ganinta bata da tarbiya da kamun kai a tare da ita." Wow ta furta had'ida mik'ewa tsaye tanufi wurin mahmud tasanya hannu zata shafi gefen fuskarshi yayi saurin rik'e mata hannu had'ida had'e fuska yayi jifa da hannunta gefe d'aya saura kad'an ta fad'i k'asa" Bata damu da abunda yyi mataba, illah tazo gabanshi daf da shi ta zauna yanda suna iya jin saukar numfashin junansu tace "kana da kyau wanda baya misaltuwa, ina sonka." Ta juya ta dubi Alhaji Atiku tace "daddy wnn yana da kyau ina son shi zan aureshi." Alhaji Atiku yasaki dariya, yace shalele ai yayankine Abu yazo gida kenan, ki sanyawa rayuwarki kinsameshi, harma kin aureshi." Mahmud yayi saurin d'aga kai sama ya dube Alhaji Atiku cike da mmki." Shalele tasaki dariyar jin dad'i, tace "nagode daddy na dan haka nake sonka fiye da momy, tana kaiwa nan tafita cike da jin ddi Tana fita Alhaji Atiku ya maida kallonshi a kan mahmud da murmushi a kan fuskarshi yakira sunanshi. "Mahmud wnn itace 'yata kwaya d'aya tilo a duniya sunanta *YUSRA* A duniya babu abunda yusra ta nema ta rasa." [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_)😅 Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *20* Tafe take d'auke da robar abnci, a hannunta, tuwon masara da miyar karkashi, tafito daga danie tafe take tana 'yar wak'arta wadda taji d'alibai nayi." . A gefen wasu manyan 'yan mata ta wuce da alama prefet ne Taji suna fad'in "sai munyi mgnin wann shigiyar yarinyar badai ance Aljanu garetaba, Idan dare yayi musameta a. D'akin da take, ai a d'akin senior Rukayyah take, musameta a can idan tayi barci muci ubnta." Suka sanya dariya harda tab'awa." Dijama na gefensu basu lura da itaba, amma ta fahimci da ita suke, Ta girgiza kai, ta kuma shan jinin jikinta saida taga wuce warsu tabisu a baya Sai da taga inda suka shiga snn ta juya ta nufi d'akinsu." Duk d'alibai kowa yanacin abincinsa amma bnda dijama, senior rukayya ta tambayeta meyasa batacin abinci?" Murmushi ta kakaro tace batajin yunwa ba ynzun zataciba." Misalin k'arfe 9pm kowanne d'alibi ya kwanta indai Junior ne." Itama dijama ta kwanta barci yak'i d'aukarta gudun kartayi barci prefet d'in d'azun sushigo suyi mata illah duk a tsorace take." Ai kuwa a can bayan d'akinsu taji tahowarsu suna fad'in ga d'akinsu nan mushiga muci uwarta." Ai kuwa tanajinsu tayi saurin durowa daga kan gadon ta d'auki robar miyar tuwonta tanufi bakin k'ofar d'akin, Kasan cewa k'ofar d'akin shafe yake da siminti, Robar miyar ta d'aga gaba d'aya ta wanke k'ofar d'akin da miyar karkashi, ta juya takoma kan gadonta ta kwanta." Su biyar ne ko wannesu da zangareriyar bulalarshi, a hannunshi suka tunkaro d'akin gadan gad'an suna zage zage, Suna kawo wa kan dangaramar bakin k'ofar d'akin, dukansu suka darje k'afa suka fad'i, had'a baki sukayi gaba d'ayansu suka saki ihu suna fad'in "wayyo Allah jama'a kukawo mana d'auki, Wnn tace k'afarta wnn tace wyyo hannunta wata kuma tace k'ugunta." Dijama na kan gado ta lafe kamar barci, takeyi Dariya ce kunshe a cikinta." Anan d'alibai suka kawo masu taimako aka tallabesu aka d'aukesu daga wurin zuwa d'akinsu." Kowa sai mmki yakeyi meyasa suka fad'i kuma a lokaci d'aya?" Washe gari ko waccensu tayi targad'e a hannu wasu kuma a k'afa, suka jera suna tafiya zasu nufi class d'insu." Dijama itama cikin shirinta na makaranta, sanye take da uniform, ta gabansu ta gifta ta wuce suka bita da kallo basuyi mata maganaba, d'aya daga ciknsu ta wurga mata harara," Suna ganin hakan suka had'a baki sukace daina harararta karki kuma janyo mana wani sabon bala'i, Ina ganin Aljanun wancan yarinyar manyan Aljanune ko furtawa kayi zaka daketa, sunajinka zasu rama mata." D'aya daga cikinsu tace nidai daga yau ko kallon inda take bazan kuma yiba wlh ba yarda za'ayi akasheni a banza ni kad'ai ce iyaye na suka Haifa." Dukansu suka had'a baki sukace muma ai mun kyaleta, ,wurin da takema baxamu kuma bi ta wurinba." Duk abunda suke fad'i shugaban makaranta yana bayansu basu saniba, ya kuma fahimci ko a kan waye suke magana." Mmki ya shigayi da tunanin kalaman yayanta Mahmud a lokacin da ya kawota, saida yayi ta bashi hak'uri akan duk abunda dijama zata aikata na rashin jin magana yayi hak'uri dan Allah karya kureta, amma kuma ya hukuntata, Daga k'arshe Yayi mashi kyautar kud'i mai tsoka yatafi." Dama yasan batajin magana kenan." Kai tsaye class d'insu dijama ya nufa, tana zaune a kan kujera ta d'auko littafinta tana dubawa ko da dai ba komai tasani a cikin littafinba tana karanta wqni wuri wani wurin kuma bata ganewa." Kiran sunanta shugaban karanta yayi yace tabiyoshi." Yana tafe tana bayanshi saida ya shiga office dinshi ya zauna snn ita kuma ta duk'a Ya dubeta da kyau yace khadija bakyajin magana, dama yayanki ya fad'a mun halinki, Ynzun muka k'are waya dashi yace zaizo ya d'aukeki ya bar garin nan dake yakaiki wata k'asa kiyi karatu a inda bakisan kowaba, kuma ba wnda zaije wurinki." Ido ta zaro waje ta turo baki idonta ya fara zubar da hawaye. Tana fad'in "Dan Allah malam kayi hak'uri kakirashi a waya kabashi hak'uri na tuba bazan sakeba." Kuka takeyi Sosai snn malam yace tayi shuru, Zai kirashi yabashi hak'uri. Amma da sharad'in bazata kuma rashin jiba, Da Sauri ta d'aga kai tace "eh tayi mashi Alk'awari." Anan shiga yimata nasihohi a kan ta tsaya tayi karatu da amfanin ilimi ga rayuwar d'an Adam. Jikinta duk ya mutu Tayi mashi Alk'awarin daga yau zatayi karatu, amma kuma ya kuma jawa prefet kunne karsu daketa." Murmurshi kawai ya d'aga kai yace xanfad'a masu, snn yabata umurnin ta tashi tawuce aji." Tun daga ranar Dijamah tashiga karatu baji ba gani tare da taimakon senior rukayyah." Hankinta ya kwanta karatunta kawai takeyi sai dai wani lokacin idan ta tuna da gida, Taji kewar tsohuwa, zataja wuri d'iya inda ba mai ganinta taci kukanta har tagaji snn ta share hawayenta ta koma cikin mutane ta zauna." Duk wani rashin jin magana ko tsiwa duk ta zubar dasu babu abunda ta Sanya agaba sai karatu, Musamman idan ta tuna da kalaman da yaya Mahmud yake furta mata " takwala mai kwanyar kifi, bata gane karatu, A kullum idan ta tuna da wad'an nan kalaman nashi sai ta kuma maida hankali a kan karatu domin so takeyi ta nuna mashi ba kwanyar kifin ke garetaba." Burin ta d'aya ne a yanxun ta ganta tafarajin turanci domin wani lokacin yaya mahmud harda turanci yake zaginta amma bata sanin abunda yake cewa." Yanzun ba laifi ta fara ganewa, Dama dijama tana da k'ok'ari da saurin gane karatu, rashin jine yayi mata yawa, bata Samun lokacin zama tayi karatun." D'aliban makarantar kuma tun daga lokacin da suka ganta tayiwa prefet dukan tsiya kamar mai Aljanu kowannensu ya shiga tsoronta, yana taka tsantsan da ita, ko aikin house akeyi bnda dijama domin kuwa gaba d'aya makarantar shakkarta sukeyi." A cewarsu Aljanu ke gareta masuyiwa mutum shegen duka." Wnn dalilin yasa tasamu sauki takeyin abunda takeso ba wanda zai hanata." Hatta da shugaban makaranta lallab'ata yakeyi baya son ganin b'acin ranta. duk abunda take buk'ata zaiyi mata, domin kawai a zauna lafiya." *************** 5:30 Mahmud ya tashi yyi sallah yayi wanka snn ya sanya k'ananun kayanshi wad'anda suka kuma fito mashi da mazan takarshi ta d'a namiji." Yana cikin shirinsa saiga wayar Alhaji Atiku yakirashi a kan yayi sauri yafito shi kad'ai ake jira, zasu wuce ibadan wurin trening, yana kashe wayar mahmud ya kira number Abba ya shaida mashi yanzun zasu wuce, Abba da momy suka yimashi Addu'a sosai snn ya kashe wayar cike da jin dad'i yafito janye da akwatin kayanshi ya nufi harabar gidan inda yakejin hayaniyar mutane da alamar abokanan tafiyarsu ne." Koda yafito an kammala shirya komai shi kad'ai ake jira, ya bud'e murfin mota ya shiga tareda addu'a a bakinshi." Anan suka tayar da mota suka d'auki hanyar Ibadan." Cikin Amincin Allah da yardarsa suka isa garin Ibadan lafiya, a barikin sojoji suka sauka aka basu masauki cike da girmamawa da karamci." Shalele na farkawa daga barci misalin k'arfe 10:30am hankalinta na wurin Mahmud domin a daren jiya tayi mafarkinshi suna cikin wani lambu suna shanawa cike da so da k'aunan junansu." Toilet ta fad'a tayi wanka tafito ta tsantsara kwanliya ta Jan hankali, batare da tayi sallah ba, domin yusra sallah bata dametaba saitaga dama takeyi." Tana fitowa kai tsaye d'akin Mahmud ta nufa, tana tura k'ofa, taga baya nan babu alamun kayanshi." Cike da tashin hankali da firgici tashiga diba ko INA a d'akin amma bbu alamarshi, Ta koma da baya da baya idonta yana zubar da hawaye kai tsaye ta nufi d'akin daddy a lokacin yana tare da mmy mahaifiyarta suna hutawa." Kai tsaye tashiga d'akin batare da tayi tunanin wani abuba, ko sallama babu,kai tsaye ta fad'a d'akin, ta Tarar da momy kwance a kan jikin daddy tana shafarshi." Ganinsu hakan bai dametaba, kai tsaye ta fad'a kan gadon tayi wurin Daddy da yana ganin shugowarta yayi saurin janye momy daga kan jikinshi, Ya janyo rigarsa ya sanya yana kallonta yayi mata nuni taxo gareshi." Tana hawa kan gadon momy ta dubeta cike da takaici da jin haushi domin ita kanta rashin tarbiyar yusra yana damunta, gaba d'aya Alhaji Atiku ya sakantata, bata da tarbiya ko kad'an, Mik'ewa tayi tsaye ta kai masu harara snn ta fita ta bar masu d'akin." Tana ganin fitar momy ta fad'a kan jikinshi ta fashe da kuka mai sauti. Tana fad'in "daddy yayi tafiyarshi dama yana fad'amun baya sona wai ni nakasasshiyace, daddy meye aibuna wanda Mahmud baya sona? , mena rasa Wanda bn caccaci so a wurin Mahmud ba?"" Pls daddy Dan Allah ka taimakamun Mahmud ya zama nawa mallakina ni kad'ai." Bubbuga bayanta daddy yakeyi cikin sigar lallashi da kwantar da hankali, yace "daina kuka shalele, "Mahmud ba tafiyarshi yayiba suntafi wurin trening, So nawa kikeso na fad'a maki cewa mahmud ya zama naki." Ki daina d'aga hankalinki kina zubarda hawayenki a kan wani Mahmud can, waye mahmud? Waye mahaifin mahmud?" Alhaji Hassan, duk a k'ark'ashin ikona suke." Ko Alhaji Hassan kikace kinaso, wlh sai kin aureshi bare d'ansa." Kud'i mulki k'asaaita basu sanyaki zubar da hawayeba, k'aryane wani d'a namiji yasanyaki kina zubar da hawayenki a banxa." Tashi kitafi d'akinki, kibani nan da wata biyar a lokacin sun kammala trening sunfito da sakamako mai kyau kinga a lokacin sai ayi maganar aurenku da shi." Sai a lokacin ranta yyi sanyi, tad'aga daga kan jikinshi sukayi ido biyu suka sakarwa junansu murmushi, tace "daddy kabani number shi." Wayarshi daddy ya lalabo ya shiga contact dinsa ya lalabo number mahmud ya bata, Ta karba ta Sanya a wayarta tana dariya tana jin dad'i snn tafita." ***************** Mahmud sunfara trening cikin nasara, da taimakon Allah, Mahmud mutum ne mai son Addini. Domin duk abunda sukeyi da zarar lokacin sallah yayi zai ajiye yayi sallah, wnn dalilin yasa a cikin barikin na sojoji suka nad'ashi a matsayin limamin masallacinsu" Baidamu ba illah yaji dad'i hakan da akayi mashi, Zamanshi a bariki yana fahimta mutane da dama wad'anda 'ya'yan musulmai ne, amma basa son ibada sunfi maida hankali wurin aikata Sab'o kamar xina da shaye2." Dan haka baidamu da ya zauna a cikinsuba, Abokinshi d'aya ne sulaiman, Sulaiman mutum ne mai son Addini, Dan haka abotansu tazo dai2 da mahmud." Da zarar sundawo daga wurin trening idan sukayi wanka sukaci abinci sukayi sallah, Basuda wurin zama sai a bakin massaci tareda sulaiman zasu fara fira." Sulaiman zaifara bashi lbrin matarshi fareeda da d'ansu d'aya Ammar irin ynda yayi kewarsu, mahmud yana tausaya mashi domin ya fahinci yana matuk'ar son iyalinshi." Shi kuma Mahmud ba wanda yake tunani tana sanyashi dariya sai dijama, Hakan zai zauna yayita bawa sulaiman labarin dijama, Sulaiman yana dariya wani lokacin harda rik'e ciki." Saboda yawan labarin dijama da yake yawanyi ko a d'akin barcinsu gaba d'aya d'akin ba wanda baisan dijamah ba, a bakin Mahmud." Wani lokacin yana bawa sulaiman labarinta yana dariya, Sulaiman ya dubeshi yace "Ayyah k'anwar nan taka ba 'yar gida za'ayiba kuwa?" Mahmud yyi murmushi yace "karufamun asiri duk Wanda ya aure dijama dare d'aya zata kasheshi da fitinarta." Sulaiman ya kuma sakin dariya yace "ni kuwa sai naga tsantsar soyayyarta da k'aunarta a tare dakai," Wata kalar dariya mahmud yasaki Wanda baisan yanayintaba, yarasa dalili duk lokacin da ake mashi hirar dijama saiya tsinci kansa cikin farin ciki." "Dole naso dijama saboda 'yar uwatace jininace, duk a cikin k'annena babu Wanda nkeso sama da dijama saboda tunda aka haifeta Allah ya d'oramun sonta, amma soyayya irin ta 'yan uwantaka ba Irin taka da fareeda ba." Ni har yanzun ba'a haifamun matar da zan aura ba, Ya k'are maganar yana dariya." Sulaiman zaiyi magana kenan, wayar Mahmud ta d'auki k'ara, yacirota a Aljihunsa yana dibawa yaga bak'uwar number ce d'agawa yayi had'ida yin sallama." Yusra dake gefe d'aya kwance akan lallausar gadonta, tanajin tattausar muryanshi ta lumshe ido ta janyo pillo ta rungume tasaki ajiyar zuciya snn takashe murya tace "hello honey nasan zakayi mmkin ganin kirana a dai dai wnn lokacin Ba abun mmki bne dan masoyiya ta kira masoyinta kasani " *ina sonka*." Dogon tsaki yasaki had'ida fad'in shed'aniya kawai Allah ya shiryeki, Yayi saurin kashe wayar shi" Ya maida kallonshi a kan sulaiman dayaga tarin tambayoyi a fuskarshi." Anan yashiga bawa sulaiman labarin duk abunda ke faruwa, Sulaiman ya girgiza sosai snn yace "kadage da Addu'a muma zamu tayaka, domin irin wad'an nan matan shed'anune." Mahmud yace "Allah yafita." ***************** Yau ake zuwa visting makarantar su dijama, Mahmud yana lissafe, da kwanakin Ya d'aga waya yakira Abba yake shaida mashi, Abba yayi dariya yace kwantar da hankalinka mahmud ga momynka can a kicin tana shirywa dijama lafiyayyen abinci yanZun tamutafi." Dariya Mahmud yayi yace "to Abba Allah ya k'ara girma, dama na d'auka Momy ta mntane, kar a k'i jemata safiyar gobe kuganta ta dawo d'auke da a kwatin kayanta." Abba yayi dariya yace " shikenan kun renamun ummie na baZatayi hnkaliba kuke nufi." Suka saki dariya gaba d'auqnsu, snn mahmud yayi mashi sallama yakashe wayar." [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_)😅 Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *21* Momy ta kammala shirinta tsaf, cikin wata atamfa Holland. Green colour Wanda tayi mata kyau matuk'a." Abba da fateema kuma suna palo suna xaman jiranta." Fitowarta daga d'akin kenan, yayi dai dai da shigowar Khalil, Sanye da wata dakkiyar shadda Wanda tayi mashi kyau, ta mayar da shi kamar wani babban mutum, Daga wurin d'aurin auren abokinshi yafito." Abba ya d'aga kai ya dubeshi yace "yawwa Khalil tunda Allah yakawoka mutafi kayi driven d'inmu, xuwa makarantarsu dijamah." Tunani yashigayi wai dama bata gidan ne?" Gske kwana biyu yaji gidan ya xama normal ba hayaniya ba k'auyanci" Ba yanda ya iya tunda umurnine daga wurin Abba, Yashiga mganar zuci, yana fad'in, Amma gskya Abba dakasan halin da nake ciki yanxun da ka barni natafi na sauke buk'ata ta, dan wlh Allah a matse nke." Ya riga da ya ajiye 'yan matan da zai huta dasu, A gidan Ahmad yanxun hakan uzurce yake kud'i yazo d'auka. Ya koma wurinsu." Ba yanda ya iya hakan ya kalli Abba ya mirgina kai, yace "to Abba." Had'ida duk'awa ya d'auki kulolin abincin da momy ta shiryawa dijama yanufi mota dasu." Driven yakeyi sannu a hankali, yanda Abba ya umurce shi yayi, gaba d'aya hankalinshi yana wurin baby's dinshi, wad'an ya ajiye suna zaman jiranshi, gasu sabbin kamu ne a wurin dinner abokinshi ya samosu Yana cikin tunanin hakan, sai ga kiran Ahmad a Wayar shi, Yana kallon wayar na ringing a gefen hannunshi amma ya k'i d'agawa, a hankali yake satar kallon Abba dake gaban mota zaune a kusa da wayar." Karo na biyu Ahmad ya kuma kiran wayar saida ta kusan tsinkewa bai da niyar d'auka, Abba ya juya yana kallon screen d'in wayar yaga an rubuta ( _Best friend Ahmad_ ). Abba yace meyasa bazaka d'auki kiran Ahmad ba?" Kasan cewar mahaifin Ahmad abokin Abba ne sosai, Abban yana matuk'ar ganin natsuwa da kamala Ahmad. Domin a duk inda Ahmad ya ci karo da Abba, sai ya cire hular kanshi ya durk'usa har k'asa ya gaida Abba cike da girmama da natsuwa." "Abba yace "Ka d'auka mana." Gaban Khalil ya yanke ya fad'i Dan yasan maganarda Ahmad zaiyi mashi, Ya kai hannunshi zai d'auka kenan wayar ta tsinke, Anan take ya sauke ajiyar Zuciya yaci gaba da driven d'inshi yana addu'a Allah yasa kar ya kuma kiranshi." Kiran ya kuma shigowa a karo na uku." Cike da fad'uwar gaba cikin sanyin jiki ya d'aga wayar had'ida yi mashi sallama cikin natsuwa kamar wani na Allah." Yanayi yana satar kallon Abba, "Yana fad'in inajinka abokina "Dan Allah sababin kayan nan da nakawo maka, ka ajiyemunsu Karka bari kowa ya kwada mun kayana, daga ciki kuwa har da kai, Saboda kasan kafini girma, da zarar kasanyasu bud'ewa zasuyi, Kuma sanin kankane bana sanya kaya idan har suka bud'e." Yanzun ina kan hanya zan kai Abba da momy unguwa ynzun zan dawo." Ahmad najin hakan ya gane maganar abokinshi a Inda ta nufa, Yace "karka damu abokina a inda ka ajiye kayanka suna wurin bantab'a maka ba, Saboda nima inada irinsu yanzun,hakan sanye nake dasu a jikina, kai dai Sai kundawo Allah ya tsare INA gaida Abba da momy, sukayi sallama ya ajiye wayar." Ya kuma satar kallon Abba, yaga ya maida hankalinshi a karatun jaridarshi yana murmushi a fuskarshi, Shima murmushin yyi ya sauke ajiyar zuciya yaci gaba tuk'in motarshi sannu a hankali [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_)😅 Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *22* Dijama da tunda safiya ta waye Senior Rukayya ta bata labarin yau 'yan gida suke zuwa _visiting_ Murna takeyi da tsalle zata ga Momy da Abba, senior Rukayyah sai dariya take yi mata, irin ynda take tsalle kamar wata 'yar baby." Can kuma sai tab'a fuska Senior Rukayya ta tambayeta "meya faru." tajuya Ta kalli senior rukayya dake yi mata kitso tace "Allah yasa Abba yazomun da tsohuwa dan nayi kewarta da yawa, A Daren jiya harda mafarkinta nayi." senior rukayya tasan da lbrin tsohuwa a bakin dijama. Da zarar an zauna zaman fira, dijama batada lbrin da takeyi sai na tsohuwa da yaya mahmud, Dan haka duk cikin fad'in makarantar duk Wanda yasan dijama to yasan tsohuwa da yayanta mahmud," Senior rukayya tace "daina b'ata fuska khadija, zagiga tsohuwa insha Allahu." Anan senior Rukayya ta gyara dijama tayi mata kitso da kunshi, tayi mata wanki da goga, ta kaita tayi wanka ta tashirya mata cikin uniform d'inta wad'anda sukayi mata mugun kyau, fuskarta tafito farinta ya Kuma k'aruwa, duk sauran wann k'auyancin ya fita a jikin dijama." Wanda a yanzun duk wanda ya San dijama a da ya ganta a yanzun da wuya ya iya ganeta, saboda tafara zama dijama yar boko." Senior Rukayya tana kammala shiryata sai ga kira a bakin k'ofa, . cewa khadija hassan tafito yan gidansu suna nemanta." Cike da farin ciki wanda ya kasa b'oyuwa a fuskarta tabi bayan d'an aiken cike da murna da jin dad'i." A can ta hango momy da Abba da fateema zaune a mota, cikin farfajiyar makarantar, Suna ganinta suka saki murmushi gaba d'ayansu suka bud'e murfin motar suka fito, amma bnda Khalil da hankalin shi baya wurin ya tafi wurin kallon wata prefet da ya ganta ta cika dam, K'irjin nan nata cike yake da dukiyar Fulani, hakan hips d'inta sun bayyana cikin hijabinta." Kallonta kawai yakeyi yana lashe baki, a nan take gabanshi ya mik'e cikin wandonshi yayi saurin sanya hannu ya rik'e had'ida d'ora kanshi a kan sitiyarin mota yana sauke numfashi a hankali." A guje ta Rugo ta rumgune momy tana dariyar jin dad'i sann tasaketa taje wurin dady shima ta rumgumeshi cike da murna, snn ta rumgume fateema tana dariya tace "sister nayi missing d'inku." Fateema tace "muma hakan munyi missing dinki sister." Anan ta shiga waige waige momy tace "mekike nema ummie?" Ta turo baki tace "ina yaya mahmud banganshi ba, bayan shi yace da zarar nayi wata d'aya zaizo yacireni a wnn karantar ya mayardani gida kusa daku." Momy ta rik'a hannunta tace "eyyah ummie Yayanki baya gari, yayi tafiya ya tafi wurin trening d'in soja kiyi mashi Addu'a Allah yabashi sa'a." Dijama ta turo ido waje tace "soja tab lallai kuwa zai k'aro mugunta." Suka sanya dariya gaba d'ayansu snn suka nemi wuri suka shinfid'a k'atuwar darduma suka zauna gaba d'ayansu Suna dariya, momy tana yaba Kyan da taga dijama tayi kamar ba itaba." Khalil da ke zaune cikin mota, cikin ma wuyacin hali, ya d'aga kai yana kallon su momy, A can ya hangosu zaune wuri d'aya sai fira sukeyi suna dariya harda Abba a hankalinsu a kwance, tareda wata 'YAR farar yariya kyakkyawa." Yace "ko ina kuma momy tasan wancan yarinyar 'yar beauty?" Meyasa bazasu aiketa ta nemo masu Wanda sukazo nema ba suyi su sallameta mutafi." Cikin jin haushi ya bud'e murfin motar ya fito ya nufi wurinsu." Yana zuwa a gefen dijama ya zauna had'ida k'ura mata ido yana mata kallon tsaf, samanta da k'asanta, yake kallo irin kallon nan nasu na 'yan duniya, bai San lokacin da ya d'aga hannunshi ba ya shafi gefen fuskartaba yace _fine girl_ Yana murnushi yace momy INA kika San wnn beautyn tana da kyau." Dariya suka saki gaba d'ayansu, Dijama da Dama ta tsaneshi ta harareshi ta murgud'a baki tace baraka kallah, masha Allah, karka cinyemun kyau sai gani sai hange." Yanayin ynda take tsiwar yayi matuk'ar yi mata kyau, sai gani yayi ta kuma burgeshi, Yana murmushi ya kalli Abba da momy yace "momy wnn yarinyar ta burgeni sosai, ina kamu" Duk lokacin da Abba ya bani umurni Na nemo matar aure to itace zab'ina, Momy 'yar k'awarki ce?" Momy tayi dariya tare da fateema, ganin bai gane dijama bace wacce ya tsana saboda k'auyancinta." Abba kuma yanajin hakan sai da gabanshi ya yanke ya fad'i, dajin kalaman khalil akan dijama, Meyake son faruwa ne a nan gaba a cikin familynsa?" Murmushi ya k'akaro ya dubi khalil yace "baka ganeta bane k'anwarka ce fa dijama." Da sauri khalil ya kuma juyawa yana kallonta cike da mmki, ya kuma kai hannunshi zai kuma shafar gefen fuskarta Wanda tafi burgeshi." Da sauri dijama taja da baya tana harararshi cike da tsiwa tace " _dant touch me_🖐🏿 * *tofah 'yar gidan tsohuwa da turanci*🤗🤗 *iya comment d'inku iya typing d'inku*🤷‍♀ [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_)😅 Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *23* Ta mik'e da sauri tabar mashi wurin, ta koma gefen Abba ta zauna a kusa da fateema." Khalil ya kuma kallonta cike da burgewa, Da murmushi d'auke a fuskarshi yanunata da hannu yace _are you a dijama 'yar gidan tsohuwa_?" Ta langwab'e kai cikin tsiwa, tazaro ido tace _are you seprise_?" Had'ida murgud'a mashi baki." Kuma zaro ido yayi waje cike da mmki, yana kallon d'an k'aramin bakinta mai tsiwa." Pink colour shar dashi, Ya langwabe kai yana kallonta, had'ida lashe Baki, domin jiyakeyi kamar yaje ya kamota ya rungumeta ya tsotse d'an k'aramin bakinta yakeji." Abba yace " _Gud_ ummie na yau xanyi baccin farin ciki, A yau ganau nake ba jiyau ba, da kunnuwa na guda biyu naji ummie nah tana zaro turanci, kai Allah Na gode maka ina ma mahmud yana kusa da yafi kowa farin ciki da wann ranar." Dariya tasaki tace "Abba saboda Mahmud kawai na dage nakeso na iya turanci, saboda ya daina cemun mai kwanyar kifi, Kuma ya daina zagina da turanci, saboda kawai dan yaga banajin abunda yake cewa." Abba yayi murmushi yace "Allah yak'aro ilimi mai yawa mai amfani ummie nah " Ta amsa da "Amin Abba nah, Can kuma ta marairace fuska tace "Abba tsohuwa fa?" Duk Na kwanta bacci sai inyita mafarkinta." Abba yayi murnushi yace "tana nan lfyarta k'alau jiya ma nadawo daga tofar." _Next month_ idan za'a kuma zuwa visiting zanje Na d'auko mki ita muzo tare ki ganta." Khalil ya nisa ya d'auke idonshi daga kallon dijama da yakeyi tun d'axun, ya maida kallonshi a kan Abba yace Abba"mai yasa kace brother zaifi kowa murna da ganin dijama hakan?" Abba yace "saboda yafi kowa son yaga ta tsaya tayi karatu, wanda zata inganta rayuwarta,dashi, Mahmud ya shirya d'aukar ko wanne irin mataki domin ganin Ummie tasamu ilimi mai yawa mai amfani wanda ko ina ne a cikin fad'in k'asar nan Dama wajenta." "Kai fa?" Abba ya tmbayeshi." Snn kuma dijama ta shice shi ya raineta tun tana k'aramarta, yafi kowa shak'uwa da ita duk a cikin family." Khalil yayi shuru yana tunanin wani Abun, Jin da yayi Abba yace dijama ta mahmud ce gaba d'aya yaji ranshi ya b'aci, Yaja doguwar ajiyar zuciya, yace "Abba dijama bata brother bace, Dijama ta kowa ce a cikin family 'yar uwar kowace kowa yana da dangantaka da ita, bashi kad'aiba Amma Abba idan kana fad'in dijama ta brother ce sai naga kamar a kwai wata manufa." Abba ya tsure shi ido yana kallonshi, yana kuma karanto wani Abu a tare dashi, Sai da ya d'auki minti biyu yana kallonshi snn yace "eh ba k'arya kafad'aba Khalil akwai wata manufar, Kuma Karka kuskura ka tambayeni ko wacce manuface, amma abunda nakeso Na fad'a maka shine duk abunda kake na sartawa ryuwarka akan ummie da mahmud to hakan ne babu ko tantama." Kai kuma sai ka cire naka banzan tunanin da kakeso kafara a yanzun." Abba ya kalli dijama da ta mayar da hankalinta a can wurin fateema suna fira suna dariya." Yace "ummie Na tashi ki d'auki kayanki kije ki kai hostel ki ajiye kidawo muyi sallama tafiya zamuyi." Cikin shagwab'a tace "Abba ni xan biku mutafi, yaya mahmud yace da zarar nayi wata d'aya zai zo yacireni a makarantar nan gaba d'aya." Momy ta rik'o hannunta cikin sigar lallashi take cemata "yi hak'uri ummie idan Wanda ya kawoki ya dawo shi da kansa zai cireki mu nan da kika ganmu bama da ikon cireki batare da mahmud ya aminceba." Khalil yanajin furucin momy ya mik'e tsaye a fusace yanufi mota ya bud'e ya shiga ya rufe had'ida d'ora kanshi a kan sitiyari yana tunanin wai meke shirin faruwa dashine?" Runtse idonshi yayi, amma babu abunda yake gani sai kyakkyawar fuskar dijama, tare da d'an k'aramin bakinta." Tafiyar da yyi a fusace Zuwa mota, Abba da momy suka bishi da kallo, suka juyo a tare suka had'a ido suka kalli junansu, ko wannesu da tambaya a bakinsa." Fateema ta katse masu tunani tace Abba wai meyake damun yaya khalil ne naga kamar yayi hushi yatafi." Momy tace "kije ki tambayeshi mana ai gaya can a mota saiya fad'a mki Dijama da bata kula dashiba, tace "sister tayani mud'auki kayan nan mutafi d'aki Na ajiyesu." Anan suka Shiga d'ibar kayan shopping d'in da Abba yayi mata tareda d'aukar kulolin abinci suka nufi hostel dasu." Senior Rukayya tana kwance a kan gado, kasan Cesarwar ba 'yar garin nan bace bata sa ran za'a zo mata visiting, taga dijama ta shigo da kaya nik'i nik'i kamar Wanda za'a bud'awa wani k'aramin shago." Da sauri ta duro daga kan gadon tashiga taimaka masu suna ajiyewa bayan sun gama ajiyewa Senior rukayya ta kalli fateema ta kuma kallon dijama tace "khadija wnn k'anwarki ko?" Dijama tayi dariya tace "k'anwatace uwarmu d'ayan ubnmu d'aya fateema ne sunanta." Senior rukayya tayi murmushi cike da burgewa domin kuwa sunyi matuk'ar burgeta, tace "kunban sha'awa kamarku d'aya." Anan fateema ta gaida ita, ta amsa tana dariya had'ida dafa k'afad'arta tace "Abba ya kawo mana ke nan mana." Batace komaiba illah tayi dariya, dijama tace "yawwa Anty kizo mutafi ki gaida Abba da momy nabasu lbrinki." Cikin minti biyar senior rukayya ta sanya uniform d'inta tafito tabiyosu dijama." A bakin mota suka hangosu tsaitsaye alamar fitowar su kawai suke jira zasu tafi." Senior rukayya taje ta durk'usa ta gaida momy da Abba, Suka amsa mata cike da kulawa, tare da yimata godiya kula da takeyi da dijama." Abba yaciro dubu biyar ya mik'a mata dakyar ta amsa had'ida yimashi godiya." Sukayi masu sallama suka bud'e mota suka Shiga, idon dijama ya cika da hawaye, Ganin zasu tafi subarta." Khalil da ya tsura mata ido yana kallonta ya kasa d'auke idonshi daga gareta ganin zubar hawayenta da yayi, bai San lokacin da ya bud'e mota yafitoba, cikin sauri ya nufota yana Neman ya rungumota ya lallashe ta ta daina kuka." Tana ganin hkan tayi saurin Jada baya tana wurga mashi kallon tsana, had'ida ya tsine bki cike da tsiwa tace "wai meye hakan ne?" Gskya yya Khalil INA ganin yau kamar ba kanka d'ayaba, Karka mnta dijamace fa 'yar k'auye Wanda ka tsana a kan komai a ryuwarka to meye nason ka tab'ani?" Kafa rik'e girmanka kafa sanni sarai bana barin bashi idan naga ana neman a shiga hak'k'ina." Turus yaja ya tsaya yana kallonta a maimakon yaji haushi. Kalamanta saima ya tsinci kansa da yana sakar mata murmushi." Ya sanya hannu a Aljihu ya ciro kud'i masu ywa wad'anda shi kanshi bai San adadinsuba ya mik'awa Senior Rukayya yace "kici gaba da kula da ita ynda ya kamata zandawo wani sati." Senior Rukayya tana wani rangaji da rangwad'a had'ida kashe murya, Duk a tunaninta da Mahmud take magana, tace "kula da k'anwarmu ai dolene baka da Matsala indai wnn ne," Jin ta canza murya tana wani fari da ido, Khalil ya d'aga idonshi ya d'orashi a kanta, yana mata kallon tsaf, saman ta da k'asanta." Ganinta yayi wata 'yar ramammiya tsaye take wuri d'aya kamar 1 bata da inda namiji sai tab'a yaji d'an taushi a jikinta gaba d'ayanta bata da wani abun burgewa." Ido biyu sukayi da ita yayi saurin gauda idonshi daga kallonta domin shi har ga Allah irin wad'an nan matan haushi suke bashi, duk Neman matansa baya son irin wad'an nan, Wanda zaka dinga dambe da k'asusan jikinta, Kuma irinsu sai zurfin tsiya kamar kafad'a rijiya idan kashigesu." Dijama ta wurga mashi harara tace "kadawo wurin wa?" Wlh Allah ko kadawo bazan fitoba mugu kawai, ko ka d'auka na mnta tsanar da kakeyi mun, tare da muguntar da kakeyimun?" ta murgud'a bki tace "karka kuskura kadawo domin bana buk'atarka." Abba da ke cikin mota suna hango shi, sun dai gansu Suna magana amma basajin abunda Suke fad'i." Fitowa Abba yayi ya kira sunanshi, Khalil yayi saurin juyowa da sauri yana kallon dijama ya wuce yanufi mota ya tayar, Gaba d'ayansu suna d'aga mata hannu itama tana d'aga masu idonta yana zubar da hawaye." Tafiya sukeyi ba Wanda ke magana ko wannensu da akwai abunda yake tunani a ranshi, a hakan har suka isa Gida, cikin farfajiyar gidan wurin ajiye motoci khalil yayi parking yafito ya bud'ewa Abba da momy k'ofa suka fito batare da sun kulashi ba, suka nufi cikin gida, Yana ganin tafiyarsu ya koma mota yafigeta da k'arfi ya nufi gidan Ahmad." Kai tsaye suka shiga babban falon gidan kowanne ya nufd'akinshi domin watsa ruwa ya huta." Abba bayan ya kammala wankanshi sanye yake da jallabiya, ya kwanta rigigine a kan gado yana tunanin abubuwan da suka yita faruwa tsakanin khalil da dijama da irin magagganun da khalil yayita yi." Momy ta turo k'ofa tashigo da sallamarta, ya amsa mata ta nemi wuri ta zauna a kusa da shi." Ta dubeshi cike da kulawa tace "Abban yara, katashi Inaso zamuyi magana.". Abba ya mik'e zaune had'ida da kallonta." Itama d'in shi take kallo suka fuskanci junansu, Snn tayi kyaran murya ta kwantar da murya cikin lumana, tace "Abba yarah, meka fahimta tsakanin khalil da Ummie?" Abba yace "ban fahimci komaiba illah sakarcinsa da yakeso ya fito mana dashi abunda bazai tab'a yiwoba." Domin bai isa ya sanyani na karya Alk'awarin dana d'aukarwa d'an uwanaba, kafin yabar duniya, Tun lokacinda aka haifi Ummie na d'auketa nayi mata hud'uba, na sanya mata suna nana khadija, marigayi ya furta da bakinshi 'yace "Allah ya rayaki Nana khadija matar mahmud, Ya juyo ya kalleni mukayi ido biyu da shi, ya dafa kafad'ata yace "yaya ko bayan bana raye, nana khadija matar mahmud ce Mahmud shine mijin khadija." A lokacin naji dad'i nayi murna, sosai, hankalina bai kuma kwanciya ba sai bayan mutuwar d'an uwana naga ynda Mahmud yake kula da ummie da irin son da yake nuna mata, bayan gaba d'ayansu ba wnda yasan da wnn mgnar har zuwa ynxun da nake fad'a mki." Karyane khalil yaxo daga baya ya karyamun Alk'awarin da na d'aukarwa d'an uwana. Bai isaba wlh sai dai soyayyar ummie tasan ynda zatayi dashi, ko kuma keda kike mahaifiyarshi ki lurar dashi kibashi hak'uri, Dan wlh ko hkri bai isa na bashiba." Momy taga Abba ya d,auki zafi sosai, taja doguwar ajiyar zuciya tace "Allah yabaka ikon ai watar da wasiyyar d'an uwanka." Yace "Amin cike da sanyin murya." Ta kuma kallonshi cikin taushin murya tace "har ynxun bazanyi k'asa da murya ba wurin nemawa khalil Alfarma a wurinka akan ka amince ya fitar da matar da yakeso a aura mashi ita, domin samun kwanciyar hankalinshi da namu baki d'aya." Idan har kayi dibo da yanda yake yiwa 'yan mata wani kalar kallon a gaban ni da kai ya isa ya tabbatar maka da khalil ba irin mazan da za'a jamasu dogon lokacin da zasuyi aure ba." A razane ya d'ago kai ya dubeta, yace "wai ni ko hajiya Bilkisu meyake damunki ne?" Sau nawa kikeso nayita fad'a mki khalil bai isa aureba, Kina hana saurayi mai lafiya yak'i kallon 'yan mata?" Ko kuma so kikeyi da zarar yaga macce ya rik'a sunkuyar da kanshi k'asa, Ki kuma zuwa kicemun kina ganin yaron can baya da lafiya mutashi tsaye munema mashi magani." To bari inyi maki mai kankaf, ko bayan raina banyafe khalil yayi aure yanzunba har sai ya kammala karatunshi ya samu aiki Wanda zai zama madogara gareshi da iyalinshi baki d'aya." na gama magana tashi Dan Allah kitafi d'akinki ina buk'atar Hutu." _tofah Abba ya d'auki zafi_🤔 Bata kuma yin maganaba illah ta mik'e tsaye ta nufi d'akinta ranta duk a dagule." ***************** Akwana a tashi ba wuya, mahmud har yayi wata uku da fara trening d'inshi, A kullum Yusra da sonshi take kwana take tashi, Duk wata hanya da macce zatabi domin ganin taja hankalin d'a namiji a waya ko a chat amma a banza takeyi." Kullum da sabon photon da take tura mashi a chat tare da kalaman soyayya masu sanyi, wanda da ita da wanda yake zindir basuda wani banbaci." Duk lokacin da mahmud ya bud'e pic d'inta sai ya runtse idonshi saboda tsaraicinta da yake gani, tareda tsine mata Albarka, daga k'arshe yyi blocking d'inta, Dama kuma baya d'aukar kiran wayarta." Hakan da yyi mata ba k'aramin d'aga mata hankali yyiba, a rayuwarta bbu d'a namijin da ya tab'a wulak'antata kamar Mahmud, kuka takeyi sosai irin yanda soyayya Mahmoud ta addabeta a zuciyarta" Idan ya San wata ai bai San wataba." K'arfe d'aya da rabbi na dare tashiga shirya birthday d'inta gobe takeso zatayi shi misalin k'arfe biyar na yamma kuma harda mahmud take buk'atar yazo, Ko Dan saboda ta kalle kyakkyawar fuskarshi taji sanyi a ranta." Tunda k'arfe 6:30am ta dura d'akin daddy baiko tashi daga barciba ita ta tasheshi, tana shiga shaida mashi yau ne ranar zagayowar ranar haihuwarta." Zumur ya mik'e zaune yana murmushi yana fad'in happy birthday my daughter, ya janyota zuwa jikinshi, yace mekikeso na shirya maki natayaki murnar zagayowar ranar haihuwarki?" Ta kuma shagwabe masa a jiki tace "daddy Abu d'aya nakeso kayi mun." Yace fad'eshi shalele kinfi k'arfin komai gareni." Tace "daddy so nakeyi mahmud yazo yau d'in nan domin ya tayani murnar zagayowar ranar haihuwata idan kayi mun hakan daddy to ka gama bani gift d'ina na wnn shekarar wanda zanfi jin dad'insa a kan komai." Murmushi daddy yayi ya d'anyi Jim kad'an yana tunanin fitowar mahmud a yanzun suna cikin trening dai dai yake da rugujewar wata uku da yayi yana wahalar trening d'insa Kuma bayason ganin b'acin ran shalele gwara ya faranta mata rai, Ran kowa ya b'aci daga ciki kuwa har da ranshi." _BARKA DA JUMA'A DA FATAN KOWA YA WAYI SAFIYAR JUMA'A LAFIYA_ [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_)😅 Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *24* Can kuma yaja dogowar ajiyar zuciya ya kalli Yusra ya sakar mata murmushi, da ya tuna _weekend_ akeyi su mahmud a yanzun basa aikin komai sai hutu." Yace "shalele indai wnn ne bkida matsala kisanyawa ranki kamar kina tare da mahmud a yanzun hkan." Barima kijiyewa kunnenki." Ya lalubo wayarshi a k'ark'ashin pillownsa, Yashiga contacts d'inshi, ya danna lambar shugabansu mahmud wanda yake kula da duk wani motsinsu da lafiyarsu." Hands free ya sanya wayar ynda zata iyajin maganar da ke fitowa daga cikin wayar." Cikin girmamawa oga yake gaida Alhaji Atiku, Cike da kulawa yake amsawa, Snn ya shaida mashi yana buk'atar mahmud Hassan yazo Abuja yanzun nan yana nemanshi." Zubewa k'asa oga yayi kamar Alhaji Atiku na ganinshi, yashiga bashi hak'uri, Yana cewa "idan wani laifi yayi ranka ya dad'e ina rok'ar mashi Alfarma dan Allah ayi mashi hak'uri kar a d'auke manashi a nan, Yaron hazik'ine yana da kwaxo sosai wurin trening gashi da son Addininshi." Ranka ya dad'e mahmud yana Neman yafiyarka tuba yakeyi bazai sakeba." Alhaji Atiku ya saki dariya, yace "ba abunda Mahmud yayimun sai Alheri, Neman da nake masa sak'o nkeson na bashi _hand to hand_ Batare da kowa yasan komaiba, karka damu gobe zaidawo gareku, abunda nakeso da kai kabashi mota lafiyayya ayimata full da mai. wanda zai iya kawoshi Abuja ya kuma maidashi batare da wata matsalaba." Oga ya sauke ajiyar zuciya yace "angama ranka ya dad'e." Snn Alhaji Atiku ya kashe wayar, yana kallon shalele had'ida kashe mata ido d'aya, Dariya suka saki gaba d'ayansu ta kuma fad'awa jikinshi ta rungumeshi tana fad'in nagode daddyna kana faranta mun rai, kana yimun duk abunda nkeso, Allah ya k'ara maka yawancin rai da nisan kwana ." ***************** Mahmud yana zaune tare da sulaiman suna hirarsu kamar ynda suka saba idan basuda aikinyi." _massage_ yagani ya shigo a wayarsa, kamar bazai duba ba kuma dai ya tsinci kansa da yanaso yaga ko wanne irin sako ne." Bak'uwar number yagani karon farko dariya yaga anfara sanyawa kamar haka." _Hhhhhhhh sweetyna kenan na fad'a maka duk abunda nakeso sai na sameshi, kashirya zuwa garin Abuja ynzun nan domin tayani murnar zagayowar ranar haihuwata wanda na shiryashi domin kai, domin inyi tozali da kyakkyawar fuskarka mai cike da Annuri, byee sai kazo_ Cikin bak'in ciki da takaici ya gama karanta massage d'in d'aga kansa da zaiyi yyi ido biyu da ogansu, Yace "mahmud Hassan sak'o daga _commondent General_ ya mik'a mashi key d'in mota yace ynzun nan yana nemanka garin Abuja." Idon mahmud suka rikid'e zuwa launin ja, ya d'aga kai ya dubi ogannasu sai da yayi kamar ba xai karb'i key d'in ba, Tunawa yayi da hud'ubar da Abba yayi mashi, "kayiwa Alhaji Atiku biyya tamkar shi ya haifeka, KA kuma d'auke shi tamkar ni mahaifinka, karka sab'a mashi ko kuma KA b'ata mashi." Sai da ya runtse idonshi sann ya bud'esu, yasanya hannu ya karb'i key d'in motar a hnnun ogan nasu, snn Oga yyi tafiyarshi." Mahmud ya mik'e tsaye had'ida kallon sulaiman wanda shima shi yake kallo," Sulaiman yace "aboki mai yake faruwa ne?" Mahmud yayi murmushin yak'e wanda yafi kuka ciwo yace "Abokina ba lokacin da zanyi maka bayani, kayimun Addu'a sauka lafiya, amma kuma yau zandawo komai dare, Yana kaiwa nan ya wuce ya shiga mota ya tayar ya d'auki hanyar Abuja." A yau Yusra cike take da murna da farin ciki, duk Wanda yasan Yusra ya kalli fuskarta a yau yasan farin cikinta na yau daban ne." Hotel ta sanya aka kama mata naji da gani wanda ake Alfahari da ita a cikin garin Abuja." Gaba d'aya friends d'inta saida ta gayyatosu da abokanen holewarta maza da mata, tana shaida masu masoyinta wanda zata aura, yana kan hanyar tahowa." Gaba d'aya holl d'in anzagaye shi da babban kalanda mai d'auke da pix d'inta Dana mahmud wanda tasanya aka had'a mata shi, Sunyi masifar yin kyau dama Yusra kyakkyawa CE, to bare kuma mahmud." K'arfe biyar da rabi kowa ya halarci wurin daga ciki kuwa harda ita, kid'e kid'e kawai kakeji yana tashi ko wacce budurwa rungume da saurayinta ana holewa wasu kuma suna manne da juna suna shan shisha." A can sama take zaune tana kallon kowa d'aya bayan d'aya tana d'an kurb'a lemo a hannunta, tanayi tana kallon agogon dake d'aure a hannunta, lokaci na tafiya har ynxun sweety bai k'arasoba to ko lfy?" Tashiga tmbyar kanta." Mahmud da gudu yakeyi ba kakkautawa Allah dai ya tsareshi ya shigo garin Abuja lafiya." Kai tsaye gidan Alhaji Atiku ya nufa, ya tarbeshi cike da murna da farin ciki, anan yke shaida mashi dalilin kiran nashi, da yyi shalele ce takeyin birthday, Ta d'aga hnkalinta sai kazo ka tayata murna." Murmushi yak'e kawai yyi baice komaiba, Amma cikin zuciyarshi jinta yakeyi kamar ta fashe saboda bak'in ciki." Alhaji Atiku baidamu da yanayin da mahmud yake cikin saba, Illah ma sai dariya yakeyi domin yasan yau shalele zatayi barcin farin ciki, taga abin sonta Batare da b'ata lokaciba ya shiga yimashi kwatancen inda take, Yace " Idan kuma bazaka ganeba bari na had'aka da sojoji suyi maka rakiya." Yayi saurin girgiza kai yace "nasan wurin ranka ya dad'e." Alhaji Atiku yasaki dariya yace yau kuma fannin aiki KA mayar dani, KA ajiye daddyn a gefe kenan." Bai tanka mashiba illah ya mik'e tsaye ya fito, had'ida ce masa daga can zan wuce." Bai jira amsar Alhaji Atiku ba ya Juya ya fita a fusace, yana jinjina son zuciya irin ta wnn mutumin." Alhaji Atiku yana ganin fitar mahmud cike da b'acin rai ya mere baki yace "indai shalele tasamu abunda takeso duk wnda ranshi zai b'aci matsalarshi." **************** A guje yaja motar yanufi hotel d'in, ynda yashiga wurin a guje mutane sai k'ok'arin kauce masa sukeyi." " *YUSRA*."!!! Yashiga filin da ake tsakiyar taron, Ransa a b'ace daga jin yadda amon muryar sa take fita zaka San yana cikin mummunan b'acin rai." Yusra yaci gaba da kiranta har sai da ya isa inda take yayin da kowa hankalinsa ya koma kansa ana kallonshi, wurin yayi tsit." Sai mmki akeyi wnn ai shine mijin da tace zata aure wanda aka manna photunansu." Kallonshi takeyi cikin wata siga ta so da k'auna, ganinshi da tayi taji sanyi a ranta, dama tasan za'ayi hakan saboda ta fahimci mahmud yanada zafi idan ranshi ya b'aci." Murmushi takeyi tana shan ( _Juice_) d'inta tana kallonshi dama ta zaci hakan daga gareshi Dan hka bata damuba, bare ta amsa kiran da yake Mata." Wnn ya k'ara k'ular dashi yaje har gabanta suna kallon juna, abinda takeso kenan ta kashe masa ido d'aya tana masa murmushi, tana shan juice d'inta." Tuni zuciya ta kuma k'uleshi tsakanin tsanarta da haushinta da kuma k'inta suka k'ara d'arsuwa a zuciyarsa bai San lokacin da ya d'aga hannu ya kwad'a mata mariba, y kuma d'auki wani cup a wurin dake cike da juice ya watsa mata a fuska da k'arfi." Saida ta razana tayi saurin mik'ewa tsaye a firgice, duk kunya ta isheta gashi jama'a kewaye dasu, Ranta ya b'aci ta harareshi, Meye haka mahmud?" Wnn wani irin wulak'ancine hakan a gaban bainar jama'a." Nafad'a maki har abada bazaki tab'a samunaba, Saboda bana sonki bana k'aunarki, bakya cikin tsarin Matan da nkeso na aura, dakeda banzar rayuwarki Baku tab'a ban sha'awaba, karki sake yin kuskure da gaggaci a kuma kirana, domin zanyi mki abunda yafi wnn." Ya d'aga kai ya kalli kalandar pix d'insu da aka zagaye wurin dasu, ya nufi wurin ya shuga yagawa yana zubarwa k'asa." Ya kuma yimata kallon bnxa ya watsar, Gaba d'aya jikinta a waje yake tamkar tsirara take, yace "banida abinda zanyi da macce irinki bakya cikin irin matan da zan zab'awa 'ya'yana a matsayin uwa, Na tsaneki yusra na tsaneki, Yana gama fad'in hakan ya juya yatafi had'ida yin wurgi da table d'in dake gabanta wanda aka jera mata kek da lemunmuka, Tana ganin yayi tafiyarshi tabishi cike da bacin rai idonta yana zubar da hawaye, tana fad'in "kayi kad'an Mahmud aurena ya zame maka dole idan kaga ka auri wata a duniya to nice, 'Ya'ya kuwa in har zaka haifi su to ka tabbatar da nice uwarsu, Idan bana cikin matan da kakeso, ni Kai kana cikin tsarin irin mazan da nkeso." Kuma ni yusra ina samun abunda nkeso kota halin k'ak'a don Haka ka sanyawa rywrka nice matarka." Snn wnn cin mutumcin da kayimun a bainar jama'a a ranar da nake liyafar murnar zagayowar haihuta bazan mnta dashi ka d'au bashi." Wnn shi zaisa na nanuna maka isata, in kuma maka dole ka shirya rywar aure dani kota girma kota arziki." Bai sauratetaba ya shiga motar sa ya bule ta da hayak'i da k'ura yayi tafiyarsa yabarta cikin bak'in ciki da b'acin rai ga Wani rad'ad'in sonshi da ke mata zafi a zuciyarta idonta ya kad'a yayi jawur, Ta kasa kukanma kunya kamar zata kasheta tayi da nasanin Zuwan da yayi, Dakyar ta iya tanufi motar ta, tashiga sauran k'awayenta da jama'a da ke gurin suka taru suna bata hak'uri, Amma bata saurare suba da k'arfi ta taja motarta tanufi gida Allah dai ya kiyaye ta isa gida lfya🤔 [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_)😅 Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *25* A wann ranar ta d'agawa kowa hankali, mu samman mahaifinta da hankalinshi yyi mummunan tashi. Sai lallashinta yakeyi da ban hak'uri." Sai da tasamu natsuwa ta tsagaita kukanta snn yashiga tambayarta, "shalele meya faru?" Waya tab'aki?" Meke maki ciwo?" Me kikeso?" Rinannun idanuwanta ta d'aga sukayi ido biyu da mahaifin nata wnda take kwance a kan jikinsa, "Daddy zaka bani abunda nakeso kamar yanda ka d'aukar mun Alk'awari?" "Zan bki shalele duk abunda kike buk'ata." Hawaye ya kuma ciko idanunta tace. "Daddy Mahmud nakeso, Daddy inaso ka aura mun mahmud nan bada jimawaba, daddy Mahmud yaci mutum cina ya wulak'antani cikin bainar jama'a sai dai duk da hakan bnji soyayyar sa ta ragu a zuciyata ba sai ma buri da shauk'in na mallaki namiji irin sa." Yyi murmushi "haba shalele Dama akan wnn kike b'ata ranki? Mahmud kinzama matarshi bazan gaji da fad'a maki hakan ba Ki sa aranki kece matar mahmud, Mahmud bashida wata mata bayanke ko yanaso ko baya so." Abunda nakeso dake karki kuma kiran wayarshi, duk ynda kikeji a kan sonshi a ranki ki danne ki sanyawa zuciyarki dangana kibani nan da wata uku kigani a lokacin Mahmud, zai zama mijinki zaki mallakeshi cikin kwanciyar hankali da lumana." Mik'ewa tayi tana tsalle tare da tsananin murna ganin tasamu abunda takeso, domin da zarar daddy yayi mata Alk'awarin zaiyi mata Abu tabbas ba makawa saiya matashi koda rayuwar wani zata salwanta." Mahmud zan nuna maka iya karka, ta fad'a tana murmurshi snn ta tashi ta tafad'a d'akinta." ******************* Allah ka d'ai ya saukeshi garin ibadan lafiya irin yanda yake gudu a mota." Misalin k'arfe 10pm ya sauka, kai tsaye d'akinsu ya nufa ya Tarar da sulaiman a kwance yana waya da matarsa uwar d'ansa, abin sonsa, sai dariya yakeyi cike da jin dad'i." Bai lura da Mahmud ba sai ganinshi yayi ya shigo ya fad'a toile." Da sauri yayi mata sallama ya kashe wayar yashiga zuba ido yana jiran fitowar Mahmud." Mahmud dake cikin toilet ya sakarwa kanshi ruwan sanyi sai sauke ajiyar zuciya yakeyi tare da lumshe idanuwanshi." Sulaiman yaji shurun yayi yawa ya kwankwasa masa k'ofa, Sai a lokacin mahmud ya sauke ajiyar zuciya yayi arwala ya fito da jallabiya sanye a jikinsa sai da ya fara gabatar da sallolin da ake binsa snn ya mik'e ya je kusa da sulaiman da ya k'ura mashi ido yana kollonshi ya zauna " Sulaiman ya kasa hak'ura ya kalleshi cike da kulawa yace "abokina wai meyake faruwa ne?" Mahmud ya juya ya kalleshi yayi murmushi, anan yashiga fad'a mashi duk abunda ke faruwa." Sulaiman yace "babu abunda ya kamata muyi shine Addu'a domin bayan tafiyarka oga ya dawo yake tambayata katafi?" Nafad'a mashi "eh katafi amma ranka baiso tafiyarba. Oga yayi murmushi yace "Allah ya tsareka, Allah yasa baka fad'a tarkon commondent ba, domin ya fiya Son kanshi." Mahmud yace "komai son Kansa da yakeyi bazai tursasani akan nayi abunda bana so bana k'auna ba Wlh in har saina aure "yarshi nafison na ajiye aikin sojan da nkeyi, Dama ni bana ra'ayin aikin soja Abba ne da momy sukeson hakan, kuma na d'auki Alk'awarin duk abunda su keso znyi masu, zanyi biyyah garesu koda kuwa ni banaso, kai koda daga aikatashi shine silar rasa rayuwata indai akan mahaifana ne naji na gani." Yana cikin maganar ne wayar hannunshi ta d'auki k'ara yana dibawa yaga shugaban makaranta ne." Sai da yaja dogon nishi ya kalli sulaiman yace "dijama ta janyo mana wata fitina wata k'ilama ya koreta daga makarantar." Sulaiman ya saki dariya domin shi har ga Allah labarin dijama dariya yake bashi, Yace ka d'auki wayar mana meyasa zaka yanke hukunci a kan abunda baka sani ba." Jiki a sab'ule ya d'aga wayar had'ida yimashi sallama." Tunkafin shugaban makaranta ya fara magana mahmud yafara da cewa "dan Allah shugaba kayi hak'uri karka koreta na fad'a maka duk lokacin da tayi wani abun abata kashi Wanda zai sanya dole ta shiga hankalinta, idan akwai ma abunda yafi duka ayi mata shi." Shugaba yyi dariya yace "kwantar da hankalinka Mahmud ai yanda kasan Nana khadija a da yanxun ta wuce nan bbu wani Abu da takeyi a yanzun bayan karatu domin kuwa idan kaji yanda bakinta yake fitarda turanci sai ka rantse da Allah kace ba ita bace." Abunda yasa nakiraka a dai dai wnn lokacin, kiranka nayi domin na fad'a maka gobe ne akeyi masu hutu Wanda nasan bakusaniba sai kuzo Ku d'auketa da misalin k'arfe 10am Murmushi mahmud kawai yakeyi a fuskarshi godiya yashiga yiwa shugaba har lokacin ya kashe wayar, Duk abunda ake fad'a sulaiman ya naji a waya, shima dariya yakeyiwa mahmud jin tunkafin shugaba yafara yin magana mahmud ya rigashi yana bashi hak'uri.' Saboda anriga da ansan dijama matsalace, Mahmud yace dijama anyi hankali? Tab da sake wata k'ila dai kwanto ne tayi masu saboda dijama fitina ce." Sulaiman yace nidai ina rok'on Alfarma da abani dijama na aureta nayi ta biyu da ita, Koda dai nayiwa wife d'ina Alk'awarin baxan mata kishiyaba." Mahmud yace "ai kuwa idan kanasonta na baka amma ka shirya rabuwa da matarka ta girma da arxiki idan ba hakan ba to zakuyi rabuwar rashin arziki, Dan na rantse maka dijama saita cinnawa gidanka wuta dakai da mtarka da d'anka duk sai kun k'une tana gefe tana kallonku saboda fitina." Sulaiman ya kuma sakin dariya yace " wnn dijama na matsu na ganta." Mahmud yace ai ganinta zakayi, a hakan sukaci gaba da firar dijama har bacci ya d'aukesu gaba d'ayansu." ******************* 7:30am Mahmud ya kira Abba yake shaida masa yau ne akeyiwa su dijama Hutu atafi a d'aukota." " Abba ya kalli momy suka saki murmushi,Abba yace "yi hak'uri Mahmud ynxun shirin da nkeyi kenan da kaina zanje na d'auko maka dijamarka." Gaban mahmud ya yanke ya fad'i yace "Abba dijamata fa kace?" Tab Allah ya tsaran INA zan iya da fitinar dijama." Abba yana murmushi yace "kuma fa hakan ne, bari kawai natafi na d'aukota sukayi sallama Mahmud ya kashe wayar," Khalil da shigowarsa kenan yaji Abba na waya yasan da Mahmud yakeyi irin ynda yaga yana sakin fuska yana dariya, maganar da taja hankalinsa gareshi itace "bari naje na d'auko maka dijamarka." Gabansa yaji ya fad'i ransa ya b'aci "wato dijamarsa harma ta zama tasa?" Yayi k'ok'arin saita Kansa, ya durk'usa k'asa ya gaidasu harda wani sunkuyar da Kansa k'asa, Suka amsa mashi cike da kulawa." Yace "Abba kabar shi natafi na d'aukota, Abba yasaki murnushi yace "ai na d'auka makaranta zaka tafi?" Yace "bama da karatu ynxun sai zuwa 3pm Abba yace "OK to katafi ka d'aukota Allah ya tsare." Fateema ta fito cikin kwanliyarta ta atamfa Wanda tayi mata kyau sai wani k'amshi humra take fitarwa mai d'aga hankalin lafiyayyan d'a namiji," Humra momy ce Wanda itama bata shafata sai idan zata kasance tare da Abba, saboda da zarar ya shak'i k'amshinta hankalinshi zai d'aga yajishi yana son ya kasance da ita." tashiga d'akinta ta d'auka ta sanya momy bata saniba." Tana k'arasowa wurin k'amshin humra ya kuma k'ara game pallon." K'amshin yana dukan hancin khalil gaba d'aya hankalinshi ya yatashi cikin minti biyu idonshi ya rikid'e zuwa launin ja wata irin wutar sha'awa yaji ta taso masa." A kasalance ya juya ya kalli fateema yace "ubnwaye yabaki wnn turaren da kika sanya?" [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_)😅 Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *26* Yayi kanta zai daketa, yana fad'in idan bakije kika cire kayan nan masu kamshin wnn turarenba saina k'akk'aryaki." Momy tace "karka kuskura ka daketa, meta maka?" Ina ruwanka da turaren da tasanya, Da Allah malam wuce katafi inda zakaje lokaci yana tafiya." Abba ya tsura mashi ido yana kallonshi ganin ynda idonshi ya canxa, a nan take duk yafita hnyacinsa." Bai kuma yin maganaba ya juya ya tafi, Fateema tace Dan Allah yaya kayi hak'uri katafi dani yanxun zancire kayan,nayi ynda kace, sai da ya kai bakin k'ofa snn ya juyo ya sakar mata harara yace "wlh bbu inda zanje da keba." Ya sa kai ya fita." Gaba d'aya baya cikin hanyacinsa wata kalar sha'awa take fisgarsa, Wanda har yake tunanin baya iya zuwa inda zaitafi batare da ya samu sukunin abunda ke damunsa ba." Ji yayi mararshi ta k'ulle mashi da sauri yayi parking gefen titi yana sauke numfashi a hankali, sai da ya samu ta lafa mashi snn ya d'aga waya yakira budurwan shi Ashanty baby yanzun itace budurwar da yakeji da ita kasan cewa shine mutum na farko da ya bud'eta a Leda." Dama tana kusa da inda yake cikin minti goma ta iso wurinshi, Yana ganinta kamar wani mayunwacin zaki, tun a motar ya fara shafarta yana tsotsar bakinta zuwa Brest d'inta jikinsa har wani rawa yakeyi kamar Wanda yaga nama." A hankali ta cireshi daga jikinta ta lallab'ashi ya tayar da motar suka nufi gidan Ahmad." Baibi ta kan Ahmad ba kai tsaye d'akinsa ya nufa inda yake holewarsa, Gadan gadan yanufi Ashanty ya shiga cire mata kayan jikinta, Ya kamota ya jefa a kan gado ya shiga aika mata da sak'onninsa." Sai da ya gama biyan buk'atarshi yajishi ya samu natsuwa snn ya tashi yayi wanka ya Sanya kayanshi had'ida mik'awa Ashanty kud'i masu yawa, Girgiza kai tayi tace "Khalil INA sonka kasani INA baka kaina ne Saboda soyayyar da nake maka ba dan kud'iba Dan Allah Khalil karka yau dareni." Murmushi yayi ya shafa gemunsa yace "nima hakan karki damu dani dake mutuwa kad'ai ce zata rabamu." Yana kaiwa nan ya ajiye mata kud'in a gefen gado, yace kiyi amfani dasu ki hau abun hawa. Sauri nkeyi Abba ne ya aikeni, bai tsaya yaji abunda zata fad'aba yayi tafiyarshi ya shiga motarsa ya nufi makarantar su dijama." Dijama na can zaune wuri d'aya tana kallon wad'anda ake zuwa d'auka d'aya bayan d'aya, Sanye take cikin uniform wad'anda sukayi mata kyau ta tufke gashin kanta a tsakiyar kai tayi acuci maxa, Babu kwanliya a fuskarta amma da zarar ka ganta saita burgaka saboda _beautifull face_ d'inta, idonta xara Zara farare fes da d'an k'aramin bakinta, k'atuwar _school bag_ d'inta goye a bayanta, gefenta kuma akwatin kayanta ne." Can ta hango Khalil ya shigo da mota, bai ganta ba tana ganin shine yaxo d'aukarta taja dogon tsaki had'ida murgud'a baki kamar yana ganinta, tace "wnn d'an rainin hankalin yazo d'aukata?" Yi tayi kamar bata ganshi ba, shi kuma sai dube dube yakeyi yana tunin ina zai ganta?" Cikin d'alibai yake kutsawa yana dube dube ko zai ganta, tana can gefe d'aya tana kallonshi tana harararshi tare da mere mashi baki☹." Senior Rukayyah ta hangoshi ta nufoshi tana rangwad'a tace "ina yini yayanmu." Lfy glau yace had'ida sauke ajiyar zuciya tare da shafe zufar da take fito mashi a fuska Ya kalleta yace "banga dijama ba, nayi nemanta bn gantaba, pls Dan Allah tayani nemanta." Murmushi tayi had'ida fari da ido, ta kalli inda dijama take zaune, ta nuna mashi ita," Bai kuma bi ta kantaba ya nufi wurin dijama da saurinshi." Tana hangoshi ya nufo wurinta ta had'e fuska ta sunkuyar da kai k'asa tana duba wani littafin turanci dake rik'e a hannunta." Kallon fuskarta yakeyi Wanda gaba d'aya ta tafi da imaninshi, Har yazo dafda ita bai San lokacin da ya kai gurfane a gabanta ba, had'ida d'ora hannunshi a kan face d'inta yashafa yace "beauty kin wahalar dani wurin nemanki." mik'ewa tayi da sauri ta taja da baya tana harararshi cike da tsiwa tace "wacece beauty?" Sunana ne bakasani ba?" Daka ce na wahalar da kai ai ina ganin ba dole nayi maka. Danasan kai zakazo d'aukata dana shiga motar haya na koma gida da kaina." Duk Wanda ya nuna maka tsana da rashin so komai zai iya aikata maka, A shirye nake da duk abunda kayi mun sai na rama." "Yi hak'uri yace da ita." Tana kaiwa wnn taja a kwatinta tayi gaba, Da sauri ya mik'e tsaye yanufeta harda d'an gudunshi ya karb'i akwatin ya rik'e yanufi mota dashi." Bayan ya sanya akwatin a but Ya zagaya ya bud'e mata k'ofa ta shiga snn ya shima yashiga zai tayar da motar kenan senior Rukayyah ta matso daf da murfin motar tana kashe murya tace "yaya Mahmud ko sallama bbu?" Kallo ya bita da shi ya d'an saki fuskarshi yace "eyyah kiyi hkr na mnta bamuyi sallama ba, amma sai dai ba Mahmud bane, Khalil ne k'anin Mahmud." Xaro ido tayi tana kallonshi tace "kai amma gskya Kuna kama sosai da junanku, Bai bari ta kuma yin wata magana ba ya Ciro kud'i masu yawa ya mik'a mata yaja motarsa yayi tafiyarshi." Tafiya sukeyi sannu a hankali Khalil yi yake yana kallonta jinsa yakeyi kamar ya sace ya gudu saboda yanda take burgeshi." Dijama kuma ta kauda kanta gefe d'aya sai kallon titi takeyi, Domin jinta takeyi kamar a k'aya, take ta matsu ta ganta a gida." Ganin tsanarshi yayi a idonta ya fahimci bata son ta had'a ido dashi, kuma ba hakan take yiwa mahmud ba." Yaja gefen hanya yayi parking, yana kallonta cikin wata siga Wanda yake yaudarar yan mata da ita." Su yakeyi ta juyo su had'a ido, dashi amma tak'i." Jin yayi parking a gefen titi tayi saurin jiyowa cike da tsiwa da kuma k'inshi a ranta, tace "malam lafiya meke faruwa?" Ido ya k'ura mata yana kallon d'an k'aramin bakinta Wanda yakeji kamar ya kamota ya rungumeta ya tsotse mata shi, ya kashe murya had'ida langwab'e kai cikin murya k'asa k'asa yace "meyasa kika tsaneni?" Meyasa bakyason had'a ido dani menamaki?" Na rok'eki ki manta da duk wani abu da yafaru a can baya ki d'aukeni a matsayin d'an uwanki kamar yanda kika d'auki mahmud." Danida Mahmud duk d'aya ne a wurinki, amma sai nake ganin tsananin tsanata a idonki." Da sauri ta juyo ta kalleshi ta wurga mashi harara snn tace "ka daina had'a kanka da yaya Mahmud domin kuwa bai tab'a tsanata kamar yadda ka tsaneni ba, bai tab'a nunawa duniya cewa baya k'aunataba kamar yadda kanunawa duniya baka k'aunata Gaba d'aya rayuwarka babu abunda ka tsana sama dani, Dan haka har abada bazan tab'a mnta k"iyayyarka gareniba." Kasanyawa rayuwar ka na tsaneka kamar ynda kaima ka tsaneni." Yaya Mahmud yafiye munkai, nesa ba kusaba, bazaka tab'a kaiwa matsayin yaya Mahmud a wurinaba." Tana kaiwa nan taja dogon tsaki had'ida murgud'a baki ta kawar da kanta gefe d'aya." Runtse idonsa yayi yana tunanin magagganunta domin sunyi mashi ciwo sosai ya rasa abunda zai furta mata Wanda zai ganar da ita cewa yanzun ya canza ya daina k'inta a ransa, asalima yanxun komai nata burgeshi yakeyi." Ganin shurun yayi yawa baya da niyar tafiya ta kuma juyawa ta kalleshi cike da tsana tace "idan baka tashi tafiya ba ni zanfita na samu abun hawa na k'arasa gida. Ko kuma wlh infita na Tara maka jama'a in sanya ayi maka dukan tsiya daga k'arshe kuma nayi tafiyata." Tana k'ok'arin bud'e k'ofar ta fita, sanin halinta da yayi yasa shi yayi saurin rik'o hannunta yana fad'in yi hak'uri dawo mutafi,." Laushi Da yaji a hannuta ya sanyashi ya kasa sakin hannun nata, illah ya kafeta da ido, Burinsa d'aya ne ta kalli cikin idonsa, yasan dolene jikinta yyi sanyi, Saurin fisge hannunta tayi cike da tsiwa tace "meye hakan?" Idan ka kuma kuskuren rik'amun hannu, ni kad'ai nasan abunda zanyi maka." Numfashi ya sauke a kasalance yace "yi hak'uri." Yaja mota suka nufi gida." Momy ta shirya mata abinci kala kala da sallama ta shigo falon cikin natsuwa, kamar ba itaba." Fateema ta rugo da gudu ta rungumeta tana dariyar jin dad'i saura kad'an su fad'i k'asa gaba d'ayansu Khalil yashigo d'auke da akwatinta yana ganin hakan ya dokawa fateema tsawa yace " Dan Allah malama ki saketa karki jimata ciwo." .jiki ba kwari fateema ta saketa ta Shiga ja da baya, dijama ta juya ta kalleshi ta murgud'a maki tace "INA ruwanka kafa fita a harkata halina yana nan ba wai barshi ba, Taja hannun fateema suka bar wurin, momy tafito daga kitchen tana oyoyo ummie na sannu da zuwa." Ta zame daga jikin fateema ta Durk'usa k'asa ta gaida momy, abunda bata tab'a yiba." Cike da mamaki momy take amsa gaisuwarta tare da jijjina kai tabbas makarantar kwana akwai yiwa yara tarbiya." Tunda dijama ta fara hankali tabbas kowa zaiyi hankali." Mommy tace "kishiga ciki kicire uniform kiyi wanka kiyi sallah snn kufito muci abinci a lokacin Abbanku ya dawo daga masallaci." To tace a ladafce snn tanufi d'akinsu tare da fateema." Byan ta shirya suka fito tare da fateema suna labari suna dariya suka nufi dining table inda Abba da momy da khalil suke zaune suna zaman jiransu." Wurin Abba ta nufa ta durk'usa k'asa ta gaida shi. cike da mmki yake kallonta da murmushin jin dad'i a fuskarshi." Yana murmushi yace "wnn ummie nace kuwa?" Kai masha Allah naji dad'i sosai Wanda baya misaltuwa, Inama mahmud na nan dayaga ikon Allah." Khalil Wanda ke cin abinci yyi saurin d'aga kai ya kalli Abba, yana mmkin duk lokacin da ake maganar dijama sai ansanya mahmud a ciki." Meyasa shi ba'a dangantashi da ita." Momy ta katse mashi tunani tace "idan bakacin abincin ya kamata katashi kawai kayi tafiyar ka." ya d'an Sosa kai yaci gaba da cin abinci, Kowa da plate d'in abincinsa a gabanshi yanaci wurin yyi shuru, dijama ta d'aga kai ta kalli Abba tace "Abba wai yaushe ne yaya mahmud zai dawo?" Abba yyi murmushi yace ya kusan dawowa saura wata biyu yanzun." "Allah sarki yaya mahmud harnayi kewarshi, Ko da dai ba ragamun yakeyi ba." Ta kuma b'ata fuska." Dariya suka sanya gaba d"ayansu abba yace aidama akan karatu ne kuma ummie na ynzun ta wuce raini." Khalil bai tsaya yaji k'arshen maganarba jiki a sab'ule, ya mik'e tsaye yace "Abba momy natafi mkranta, idonshi a kan dijama." Suka had'a bki sukace "Allah ya bada sa'a." Amin yace ya sanya kai ya fita, dijama ta wurga mashi harara domin babu abunda ta tsana a rayuwarta sama da khalil, Shine mutum na farko da ya tab'a nuna mata tsana da kyamata a fili." Yana fitowa bakin get wurin da zai d'auki motarsa sai ganin 'yan matansa yayi a gabanshi su biyu wad'anda gaba d'aya ya mnta da tarihinsu." Zaro ido yayi cike da mmki yana kallonsu yana mmkin ya'ayi suka San gidansu." Waige waige yashiga ko Allah yasa ba Wanda ya gansu, Kuma yasan ynxun Abba zai iya fito." [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_)😅 Writing By *UMMU SAFWAN* ( _FareedaBasheer_) *27* _Khalil da Yusra sunayiwa masoyansu barka da juma'a da fatan kowa yyi juma'a lafiya_😉😊😄 Ganin ba Wanda ya gansu, Kuma idan sukayi yunkurin komawa komai zai iya faruwa domin kafin sufita daga get d'in gidan har Abba ya fito." Daga ganin ynda suke mashi wani kallon ya fahimci akwai abinda ya kawosu wurinshi." Nuni yayi masu da subiyoshi, Da sauri yake tafiya ya nufi b'angarensu suna biye dashi a bayan shi" D'akinshi ya bud'e suka shiga suka samu kujera suka zauna kowacce ta d'ora k'afa d'aya kan d'aya." Daf dasu yazo ya zauna yana kallonsu d'aya bayan d'aya, duk ya jek'e da xufa ya kwantar da murya a hankali yace salma da mariam meya kawoku gidanmu?" Ya akayi kukasan gidan nan?" Suka had'a baki sukace "kana mmki ne?" Ai wnn ba abun mmki bane gareka ma yaudari, ka d'auka ka samu banza wad'anda zaka yaudara kayi tafiyarka ka banxartar dasu." Gamu gabanka ko wacce daga cikinmu tana d'auke da cikinka na wata biyu." Murmushi yayi irin nasu na 'yan duniya ya karkace kai yana Sosa gemonshi, Yace "haba 'yan matana nasaba da jin irin wnn barazanar a wurin wad'anda ma suka fiko, kuma bbu abunda suka iyayi." Kunsan wani Abu kuwa?" kunyi matuk'ar burgeni da kukayi tunanin wnn barazanar." Abunda Baku saniba shine ba ko wacce macce khalil yake zuba kwansa a cikinta ba." Ya taso daga inda yake zaune ya dawo tsakiyarsu ya janyosu zuwa jikinsa ya rungumesu yana shinshinan turaren jikinsu cikin wata siga mai rigitarwa, ko waccen su sai lumshe ido takeyi." Yana ganin hakan yasa kesu yace "da kunfad'a mun gaskiya, cewa zakuyi kwana biyu kun daina d'ad'd'anar dad'in zumar khalil mai rikitarwa." Ya kuma janyosu gaba d'aya zuwa jikinsa ya matsesu tsaf yana shafa ko waccensu." Tunani sukeyi ya akayi yasan da hakan?" Tabbas khalil jarumin namiji ne Wanda kwana biyu idan ya barka saikayi ta jin kewarsa, Kuma duk mazan da zasuyi ma'amala dasu bazasu tab'a samun kamar khalil ba wurin sarrafa macce domin taji dad'i." Sarrafasu yakeyi cikin wani salon mai wuyar misaltuwa, ko waccensu ta fita a hanyacinta sai nishi suke fitarwa dama kwana biyu sunyi missing din jin dad'i." Dijama bayan ta kammala cin abincinta ta mik'e tsaye tace "momy bari natafi mu gaisa da Baba maigadi lokacin da na dawo baya nan ina ganin yana masallaci." Fitowar da tayi taga khalil ya wuce b'angarenshi tare da wasu 'yan mata wad'anda suka sanya wando ya d'ame masu a jiki kamar ba 'ya'yan musulmaiba." Mmki tashigayi ta rik'e baki🤔 Tace tab Ashe Dama wancan d'an rainin hankalin d'an iska ne?" Ai kuwa sai nabisu naga abunda yake aikatawa." Hakan ta biyo bayansu bai lura da itaba har suka shige d'akinsa ya turo k'ofa, Ya manta bai sanyawa k'ofar key ba." Dijama ta lab'e a jikin k'ofar duk abunda suke fad'a tanaji a kan kunnenta, Rife baki tayi a lokacin da ta lek'a kanta a k'ofar d'aki, abunda tagani ya firgitata batasan lokacin da ts zunduma ihu ba ta zuba a guje." K'afarta d'aya ta darje zata kife rufda ciki, saiji tayi ta fad'a a jikin mutum, Sauke ajiyar zuciya tayi ganin bata fad'i k'asa ba, ta d'aga kanta sama domin ganin ko waye ya taimaketa." Khalil ta gani rungume da ita yakafe ta da ido yana kallonta." Cikin razana tayi saurin kwace jikinta, tace "tab'ani da kayi banyafeba." Kuma duk abunda kake aikatawa naganewa idona sai na fad'awa Abba da mommy." Tanaja da baya yana nufarta, saida ya danganeta a bango ya matseta ya had'a goshinsa da nata, Karan hancinsu ya had'e dana juna duk kanninsu sunajin saukar numfashin junansu." Runtsu idonta tayi tana sauke numfashi da sauri2 hanjin cikinta har wani motsi sukeyi saboda tsoro." Yace wakike cewa baki yafeba?" Bari nayimki abunda kikaga inayiwa wad'anda kike lek'a." Ya kuma matseta ya lalubo bakinta ya sanya a bakinshi yashiga tsotsa, wani irin cizo ta gantsara mashi Wanda yasa yyi saurin sakin bakinta da Sauri." Tace "Allah ya isa banyafeba, na tsaneka." Ta sanya hannu biyu iya k'arfinta ta tureshi, zata tsare yayi saurin rik'o hannunta yadawo da ita jikinsa yace "duk kika kuskura kika fad'awa Abba da mommy abunda kika gani, Abunda zanyi mki sai yafi wnn." Yasaki hannunta ta zuba a guje, Ta gabansu mammy tawuce da gudu suka bita da kallo suna mmki meya faru take gudu?" Abba yyi dariya yace "mai hali baya fasa halinsa, suka sanya dariya gaba d'ayansu." Koda khalil ya koma d'akinsa bai Tatar da suba, sunyi tafiyarsu ya sauke ajiyar zuciya ya d'auki key d'in motar sa ya fita." Kai tsaye inda yake tsammanin zai gansu a makaranta a nan ya samesu, sunyi tsaitsaye suna zarar ido, da alama akwai abunda suke cewa." Yanayin parking ya fito a hasale, ya nufi wurinsu, yasanya hannu biyu ya rik'o gashin kan kowacce su, yashiga ja, yana tafiya dasu, sai ihu sukeyi amma shi ko a jikinsa, Can nesa da mutune ya kaisu inda ba wanda zai iya ganinsu, ya wurga masu harara tare da kwad'awa ko waccensu mari, Yace "muna fukai kawai nafiku iya iskanci, Duk wancce ta kuma yink'urin iskoni gidanmu, da wani bnzan k'azafinta sai naci uwarta." Kun d'auka duk abunda nkeyi bansani bane?" A cikinku a kwai wacce na tab'a kusanta?" Taxi kawai mezanyi da macce Wanda tazama taxi kowa da kowa shiga yakeyi." Gurfane suke gabansa suna bashi hkr snn ya kuma yawosu ya had'a Kansu wuri d'aya ya kwafra suka kuma sakin wata k'arar wahala snn ya barsu nan yayi tafiyarshi ya shiga aji." Kai tsaye dijama toilet ta nufa ta d'auko brush da makilin tashiga darzar bakinta tana hawaye had'ida Allah ya isa." Sai da ta kusan k'arar da makilin guda, snn ta d'urk'usa bakin famfo tana kuskure bakinta dai dai inda khalil yayi ta tsotsa, sai kuka takeyi tana aika mashi da Allah ya isa bata yafeba." Bayan tagama wanke bakin ta fito ta fad'a kan gado ta kwanta tana shisshikar kuka har bacci ya d'auketa." Misalin k'arfe 8:pm kowa a gidan yayi sallah, Dukansu sunfito domin cin abincin dare." Akan dining suke ko wanne ya sanya plate d'in tuwon shinkafa miyar a gushi a gaba suna fira suna dariya." Khalil kuma sai yi yakeyi yana kallon dijama har yanzun yanajin laushin bakinta a cikin bakinsa, gashi d'an k'arami dashi ya kuma lashe bakinsa, kamar wani maye☹ Da zarar sunyi ido biyu dijama sai ta wurga mashi harara had'ida murgud'a mashi bki." Wayar khalil ta d'auki k'ara yana dubawa yaga Ashanty ce yak'i d'agawa Har sau uku ana kiranshi yak'i d'agawa Abba ya lura da hakan ya kallesa yace "meyasa bazaka d'aga ba?" Ya d'an Sosa kai yace "Abba Ahmad ne kuma nasan maganar da zaiyi min." Dijama ta kallesa ta mere baki tace "su Ahmad mnya, yayi saurin d'ago kai ya kalleta tace Wlh zantona idan ka kuma hararata." Abba da mommy sukayi saurin kallonta, Abba yace "tona mana ummie nah mekikeso ki fad'a?" *Allah ya sadamu da Alherin dake cikin wnn safiya ta juma'a* [28/04, 20:51] Sadiya Aliyu Fbk: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_)😅 Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_) *28* Kowa ya maida hankinsa a kan dijama yana sauraren abunda zata fad'a." Sai kallon khalil takeyi, Tace "infad'a ko inyi shuru?" Mammy da Abba suka had'a baki sukace fad'a mana." Khalil sai zarar ido, yakeyi kamar Wanda yyi k'arya ya had'a gumi, ya kuma had'e fuska ba wani alamar wasa a tare dashi." Ta karkace kai cike da tsiwa tace "zanfa tona." Mommy tace tona mana ummie meya faru?" Gani yayi tana gyaran baki alamar zata fara mgna, tonawar zatayi kuwa, Ya shiga tunanin abunda zaiyi ya fitar da kansa." Yayi saurin ture plate d'in tuwon dake gabansa ya fad'i K'asa Gaba d'aya abinci ya zube k'asa duk ya b'ata masa jiki, K'afarsa ya rik'e yana fad'in wash k'afata." Hankalin kowa ya koma kansa anayi masa sannu, Kuma marairacewa yayi yana fad'in "wash mommy k'afata, da sauri Abba ya shiga diba masa k'afar Wanda ba wani abu da yakeji gareta." Sai da ya ga ya d'auke hankalin su gaba d'aya zuwa gareshi. Sun mnta da maganar dijama snn ya sauke ajiyar zuciya ya mik'e tsaye yana d'ingisa k'afa ya nufi d'akinsa." Kallo dijama ta bishi dashi tana mmki a gaban idontafa ya ture plate d'in abinci, kuma bbu wani Abu da yasame shi a k'afarsa, Tab tace lallai yaya khalil babba ne." Zaka warke ka dawo ne." Bayan ya wuce ne ya shiga d'akinsa kai tsaye akan gado ya fad'a yana sauke ajiyar zuciya. Yana murmushin samun nasara ya tserewa tarkon dijama." *GA WNN YA TAYAKU FIRAR DARE* 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar Gidan tsohuwa_)😅 Writteng By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *29* Murmushi yakeyi idan ya tunada dijama a lokacin da take cewa In tona." Sai ya tsinci kansa yana mai sakin dariya, Ya mirgina a kan gadonsa tare da rungune pillow." Tabbas ko ba'a fad'a masa ba yasan ya kamu da son dijama, Wanda ita kuma yake ganin matsananciyar tsanarshi a idonta." Dogon nishi yaja ya kuma rungume pillow yace "dole ki soni dijama domin ni nakine bakida wani miji a fad'in duniyar nan Wanda ya wuce ni, Ni nakine ke tawace." Yana cikin wnn tunanin bacci b'arawo yyi awon gaba dashi." Tun daga lokacin wasan b'uya ta Shiga tsakaninsa da dijama, Koda zasu fito break fast, 9:am har ya karya yayi tafiyarsa, Darana kuma lokacin da zaici abincinsa har suntafi makarantar islamiya, da dare sai bayan ya tabbatar da sun shige yake shigowa yaci abinsa yayi tafiyarsa." Gudun kar su had'o da dijama ta tona masa asiri a gaban Abba da mommy, kamar ynda tace." Hakan sukaci gaba da yi da ita har zuwa lokacin da hutyn makarantar su ya k'ara zata koma." Duk wani shige da ficinta a kan idonsa takeyinsa yana kalllonta wani Abu idan tayi shi yayi dariya wani kuma ta yaji ta kuma Shiga ransa." Yana lissafe da hutun makarantar ta ya k'are, lokacin da ya taso daga makaranta ya biyo ta wani katafaren store yayi mata siyayyar kayan makaranta masu yawa ya shigo dasu, A lokacin Mahmud ya turo yaronsa da siyayyar duk wani Abun da yasan tana buk'ata ya saya mata." D'an Aiken yana fita kenan, Khalil ya tsaya da motarsa ya shiga jido kaya yana shigowa dasu." Ido Abba da mommy suka bishi dashi cike da mmki basuyi masa maganaba sai da ya gama shigowa da kayan gaba d'aya snn ya nemi wuri ya zauna a kusa da mommy yana fad'in wash nagaji da yawa." Suka bishi da ido cike da a yar tambaya???" Sai da ya natsu snn Abba ya kalleshi ya nuna kayan da ya ajiye tsibi guda, yace "wa d'an nan kayan fa na meye?" Khalil yayi murmushi yace "Abba Nana khadija. na sayomawa." kasan cewar hakan yake kiranta yanxun ya tsani a kirata da dijamar nan, Yaci gaba da cewa domin ina lissafe da gobe ne suke komawa makaranta." Abba ya kalleshi da kyau yace Ummie ta gode amma sai dai kayi hak'uri anrigaka." "Meye aka rigani Abba?" Ina nufin ka kwashi kayanka kaje ka mayar dasu a inda kasawosu domin kuwa Mahmud ya rigaka, babu abunda bai sawo ya turo akawo mata taba kamar yanda ya saba a koda yaushe. Ba kamar kai daka tsira ynxun da rana tsaka." Khalil bazan gaji da fad'a maka a kan kacire Abunda kakeso ka fito dashi a rana tsakar nan ba." Dan haka ka kwashi kayanka ka mayar dasu a inda kafito dasu, Ya fahimci inda maganar Abba ta nufa. Ransa ya b'aci amma kuma ya danne yace "Abba wai menayi?" Naga kamar duk an tsaneni a gidan nan?" Sai a lokacin mommy tayi magana tace "khalil kazo ka dakemu kawai ka huta." Tunda har tambayar abunda kayi kakeyi, ai ina ganin kafi kowa sanin Abunda ke cikin ranka Wanda bazai tab'a yiyuwaba, Dan Allah malam tashi ka kwashe mana kayan nan naka wad'anda suka tare mana filin wuri kasan inda dare yayi maka dasu." Jiki ba kwari ya mik'e tsaye cike da b'acin rai idonshi ya rikid'e zuwa launin ja." Yashiga kwasar kayansa yana xubawa a mota." Washe gari, dijama ta kammala shirinta cikin uniform ta fito sukayi sallama da mommy, da fateema." Abba da kansa ya d'auketa ya nufi mkranta da ita." Bayan sun wuce ne khalil ya fito cikin da kakkiyar shadda 'yar ubansu sai k'amshi yake zubawa, ya durk'usa har k'asa ya gaida mommy, snn yace "Nana khadija tafito muwuce kawai na shirya." Mommy ta kallesa da kyau tayi murmushi irin nasu na manya tace " ai tuni Abbanku ya tafi wurin kaita." Saurin d'aga kai yyi ka kalli mommy Wanda itama shi take kallo, ganin b'acin rai a fuskarsa ta zaro ido tace "meyafaru ne Khalil?" "Ba komai yace had'ida mik'ewa tsaye jiki ba kwari yace "natafi makaranta." Mommy tace break fast d'inkafa?" D'an juyowa yyi yace "banajin yunwa idan naje can zansamu wani Abun da zanci." "To Allah ya bada sa'a inji mommy ta bishi da kallo tana tausayin d'an nata." ************** A kwana a tashi ba wuya a wurin Allah. Yau ne ake bikin rantsar dasu mahmud a aikin soja." In da sun kammala trening d'insu cikin nasara da taimakon Allah tare da sanya hannun Alhaji Atiku Mahmud ya fito da babban muk'ami." Bikin rantsar dasu akeyi a garin Abuja inda aka tara manya mutane shuwa gabanni da 'yan siyasa domin shaidarwa." Abba da mommy da khalil da fateema duk Suna wurin a zazzaune inda suke hango Mahmud zaune cikin uniform d'in soja wad'anda suka yi mashi masifar kyau sai kallonsu yakeyi yana murmushi farin ciki." Gefensa d'aya kuma sulaiman ne, shima zaune yana hango matarsa da d'ansa yana aika masu da murmushi." Kiran sunansu akeyi d'aya bayan d'aya, ana rantsar dasu tare da fad'in muk'amin su a kuma basu ta kardar shaida." Abba yana tare da Abokinsa Alhaji Atiku suna fira sai godiya yake masa." Shuru Abba yayi saka makon sunan Mahumd da yaji ana kiran tare da muk'amin da yaji ba'a kira kowa dashiba, Ya kuma kashe kunne domin ya k'arajin abunda ake fad'i." _"CAPTAIN MAHMUD HASSAN TOFA_ yaji ana fad'i, sai ganin Mahmud yayi ya taso yana murmushi aka Shiga rantsar dashi." Abba bai San lokacin da ya rungume Alhaji Atiku ba sai godiya yake masa, domin duk matakin da yaga Mahmud ya taka dasa hannun Shi a ciki." Alhaji Atiku yace "ka daina yimun godiya mahmud d'ana ne. Babu abunda bazan iya yimasa a rayuwa ba" Idan ina da rai da lafiya mahmud sai ya hau kujerar da nake kai a yanxun ta commondent general." Abba yaji dd'i sosai har yakejin a rayuwa babu abunda ba zai iya yiwa Alhaji Atiku ba." Hkan dai akayita rantsar dasu, d'aya bayan d'aya, snn daga k'arshe aka sallamesu da cewa kowa yatafi gida sai nan da wata d'aya idan kud'insu suka fito za'ayi posting d'insu wurin da zasu fara aiki, domin su fara yiwa k'asa aikinta." Gidan Alhaji Atiku su Abba suka nufa, gaba d'ayansu, A inda aka shirya masu liyafa kala kala, cikin karamci." hakan suka taru gaba d'aya har Alhaji Atiku da matarsa suka shiga cin abincin." Abba ya duba baiga yusra ba ya dubi Alhaji Atiku yace "Alhaji Atiku wai ni ina 'yata ne yusra bngantaba?" tun a can nakeson na tambayeka hankalina ne ya d'auku." Dariya Alhaji Atiku yyi yace 'ai Shalele ta tafi England wurin hutawa, .d'azun da muke waya da ita nake gaya mata yau ne ake bikin rantsar da yayanta Mahmud rigima ta sanyamun tana kuka wai meyasa ban fad'a mata ba, domin ta shiryawa mahmud kyautar da zata bashi domin tayashi murna." Abba yace "gskya ba'a kyautawa yusra ba mutum da yayanshi." Suka Sanya dariya gaba d'ayansu." Mahmud bai kulasu ba sai cin abincinsa yakeyi Wanda yakejinsa kamar yana cin magani." Domin gaba d'aya ya tsani Alhaji Atiku da duk wani Abu da yafito daga gareshi sboda yafiya son kansa da yawa." Hakan suka kammala cin abincin ko wannensu ya mik'e tsaye had'ida yi masu sallama, Abba sai godiya kawai yake tare da mommy suka fito." Motar Khalil Abba yashiga tare da mommy, Khalil kuma ya shiga motar mahmud tare da fateema da mahmud d'in gaba d'aya suka d'auki hanyar kano." K'arfe goman dare suka sauka garin kano, Gaba d'ayansu ko wannensu a gajiye yake." Suna sauka kai tsaye ko wanensu ya nufi b'angarensa domin ya watsa ruwa ya huta." Mahmud yana shiga d'akinsa kai tsaye toilet yashiga yayi wanka yafito ya shinfid'a abar sallah yayi sallah sann ya fad'a kan gadonsa ya kwanta tare da sauke ajiyar zuciya, babu abunda ya fad'o masa a rai a dai dai wnn lokacin sai dijamah." Murmushi yayi domin shi kansa ya so ya ganta, yga ynda ta koma Allah yasa dai tayi hankali ta kuma daina rashin ji." Da tunani gobe idan Allah ya tashesu lfy zaije har mkrantar ya kaimata ziyara." Washe gari bayan yayi shirinsa cikin k'ananun kayansa wad'anda suka karb'i jikinsa suka fitar masa da mazan takarsa na jirumin maza, cikakken soja, Inda yake ajiye turarensa yanufa, sai ganin wani kalar turare yyi Wanda shi bai San yana da irinsaba, baima tab'a ma'amala da irin turarenba." D'auka yayi ya fesa a jikinsa saiji yyi wani k'amshin dad'i yana fita a turaren." Lumshi idonsa yyi domin k'amshin turaren ya sanyashi farin ciki, da har yna tunawa da wasu abubuwa da sukayita faruwa na farin ciki." Cikin nishad'i ya fito yanufi babban falon gidan, kowa da kowa ya hallara domin k'aryawa shi kad'ai akejira." Durk'usawa yayi har k'asa ya gaida maihaifansa, snn khalil da fateemah suma suka gaidashi cike da girmamawa, yana murmushi ya amsa masu." Anan ya jawo kujerar da ke kusa da Khalil ya zauna suka fara yin break fast," Bayan sun kammala ne mahmud yace wa Abba, Abba zanje makarantar su dijama na dubata." Gaban Khalil ya fad'i yayi saurin d'aga kai ya dubi mahmud ya kuma sunkuyar da kansa k'asa." Abba yyi murmushi yace "ya kamata kuwa, amma idan kayi ido biyu da ummie na zakasha k'orafi." Snn idan kadawo, ya kamata ka shirya katafi tofa wurin tsohuwa ka gaida ita, domin tana yawan yi mun k'orafi a kanka." Dariya mahmud yyi yace "tsohuwa matsala ni har na mnta da ita." Abba ya turo ido waje had'ida kallon mommy ya nunata da yatsa yace "wnn ce matsala, Mahmud ya rik'e baki yana dariya yace "Abba mommy nan ce fa?" Abba yace b'ace mun dagani Mahmud karna sab'a maka." Ai uwa batafi uwaba😊 Suka Sanya dariya gaba d'ayansu ya mik'e tsaye ya kalli Khalil yace muje ka rakani d'an uwa." Ba ynda Khalil ya iya hakan ya mik'e tsaye, yabi bayansa, Abba da mommy suka bisu da Addu'ar adawo lfy." Suka d'auki hanyar makarantar su dijama." Suna cikin ofishin shugaban makaranta suna hira, Mahmud nayi masa godiya hak'urin da yyitayi da dijama suka rik'eta batare da sun kuretaba." Shugaba dariya kawai ykeyi, Khalil kuma yana zaune gefe d'aya yana murmushin da yafi kuka ciwo." Wata siririyar murya tayi sallama ta shigo, ciki natsuwa, Wanda Khalil yanajin muryar sai da gabansa ya fad'i domin yasan mai wnn muryar ko ba'a fad'aba dijama ce." Cikin uniform dinta take Wanda sukayi mata kyau tana shigowa cikin natsuwa ta fara cin karo da Khalil ta had'e fuskar had'ida murgud'a baki domin bata lura da Mahmud ba dayake zaune a kusa da Khalil duk a tunaninta Khalil ne yazo ya aika akirata." Mahmud kuma ya tsura mata ido yana kallonta saboda mmkin ynda yaga ta canza masa kasa yin magana yyi." Idonta ta wurga cike da tsiwa ta kalli kusa da Khalil d'in tayi ido biyu da Mahmud, Wata kalar dariya tasaki tare da ihu cike da murna tayi kansa ta fad'a kan jikinsa tana fad'in oyoyo yaya Mahmud I miss you." Runtse idonsa Khalil yyi ynajin wni Abu na masa yawo a zuciyarsa." Mahmud bai San lokacin da ya maida ita a jikinsa ya rungumeta tsaf yana sauke ajiyar zuciya Wanda bai San yana yintaba cike da farin ciki. Ya lumshe idonsa." 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar Gidan tsohuwa_)😅 Writteng By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *30* Sai da suka d'auki kusan minti biyar a hakan snn mahmud ya cireta a jikinsa, had'ida rik'e mata hannu still idonsa a kanta yana kallonta yana murmushi." Gefensa taje ta zauna a kusa dashi akan kujera ta zuba mashi ido tana kallonsa tana murmushin farin ciki." Can ta nisa taja dogon ajiyar zuciya tace "shine ka kawoni nan kayi tafiyarka inda bnsan kowa ba, bayan kayi mun alk'awarin cewa danayi wata d'aya zakazo ka d'aukeni ka cireni ka cireni a wnn mkrantar. Meyasa katafi ka barni?" Bata barshi yayi maganaba taci gaba da cewa, had'ida kallonsa "tab yaya kaga ynda kayi kyau kuwa?" Dama hakan aikin soja yake sanya mutum yayi kyau ya zama kamar balarabe?" Dafe kai yayi, yace "dijamah halinki yana nan har ynzun baki canxaba." Ta marairace fuska cikin shagwab'a Wanda ta kuma yi mata kyau tace "Allah na canza ka tambayi uncle kaji. Ganinka ne kawai sanyani nishad'i Dan Allah yaya karka tafi kabarni kai fa kayimun Alk'awari." Magana takeyi amma kallonta yakeyi irin ynda take shagwab'a abun yyi mta kyau saiji yyi ta kuma shiga ransa, Tunda aka haifi dijama yake sonta domin duk a cikin qannenshi yafi sonta a kan kowa, rashin jin da takeyine da rashin karatu yake had'ashi da ita, yake nuna mata kamar baya sonta domin kawai ta tsaya tayi karatu. Ya kuma rik'o hannunta ya mik'ar da ita tsaye zuwa jikinsa, hakan ya yasanya khalil yasaki wayar hannunsa bai saniba, saka makon wani a zababben bugun zuciya da yaji k'irjinsa nyi masa.' Mahmud bai lura da shiba hankalinsa na wurin dijama sai zuba masa shagwab'a takeyi tana kan k'afarsa zaune." Labari take bashi na Anty rukayya irin karamcin da tayi mata da taimako." Mahmud yace "wnn Anty rukayyah Allah ya biyata, Akira mun ita nayi mata godiya." Tasaki dariya Wanda sai da khalil ya runtse idonsa, Tace "yaya Ashe kaga wnn turaren a d'akinka." Ya kalleta cike da mmki yace "kece kika ajiyeshi?" Ta langwab'e kai Wanda yin hkan ya k'ara mata kyau tace "tsarabarka ce Dana ajiye maka, lokacin da akayi mana hutu, saboda nasanka kana da son turare, shine na ajiyema a d'akinka Dan kadda fateema tace nabata." Khalil najin hakan hnkalinsa ya kuma tashi wayar hannunsa ta kuma sub'ucewa ta fad'i a karo na biyu, duk ta farfashe glass d'inta, wnda yasa hankalin mahmud ya dawo Kansa, Yace "subuhanallah." D'an uwa meke faruwa?" Ya akayi hakan ya faru?" Khalil da idonsa yyi masa ja, gaba d'aya duk haushin mahmud yakeji, wato bai Masan ko maike faruwa ba kenan." Dakewa yyi ya k'irk'iro murmushin Dole yace "nima bnsaniba tana hannuna ta fad'i." Dijama ta kallesa sukayi ido biyu ta wurga masa harara ta kawar da idonta." Khalil na ganin hakan ya mik'e tsaye yace brother bari natafi mota na jiraka kaina keyimun ciwo." Mahmud yace "eyya sorry to kaje ka zauna kajira yanzun zanfito sai mutafi gida." Mahmud ya kalli dijama yace "bakiyiwa yayanki sannu ba?" Ta shagwab'e fuska tace " ai shine." Khalil najin tace hakan tun kafin ta k'arasa fad'in abunda zata fad'a yayi saurin ficewarsa, ya bar wurin domin duk a tunaninsa tonawar zatayi." Mahmud yace "ai shine me?" Meya mki?" Ta turo bki tace "ai shine ya tsaneni baya son ya bud'i ido ya ganni." Mahmud yyi murmushi yace "wnn kuma saboda bakyason karatu shiyasa kowa yake nuna mki baya sonki." Amma tinda ynxun kina karatu kowa zai shirya dake." Khalil yana shiga mota ya had'a kansa da sitiyarin mota, zuciyarsa na k'una, wani kalar azababben son dijama yakeji a ransa Wanda idan ya rasata jiyakeyi kamar zai iya rasa rayuwarsa." Photon dariyar da takeyiwa Mahmud da shagwab'a da yanda suka rungume juna yake gani a idonsa, ko ba'a fad'a makaba da zarar ka gansu a hakan zaka tabbatarwa kanka da cewa masoya ne suna son junansu kuma sun shak'u da junansu." Mahmud bai fito ofice d'in shugaba ba sai da yayi masa kyauta ta ban mmki snn ya nemi Alfarma da amayar da dijama aji uku tunda ya fahimci cewa tana da k'ok'ari sosai kuma tayi girma aji d'aya." Anan take Shugaban mkrnta ya Amince domin shi kansa yyi wnn tunanin domin ya yaba da karatun dijama domin tana d'aya daga cikin d'aliban da makaranta take Alfahari dasu." Anan sukayi sallama mahmud yafito tare da dijama ta biyoshi tayi masa rakiya sai shagwab'a take zuba masa tare da yimasa k'orafin ita dai a fitar da ita a mkrantar nan." Murmushi kawai mahmud yakeyi tare da bata hak'uri." Ahakan har ta kaishi bakin Mota, khalil ya had'a kansa da sitiyari yanajin duk abunda suke fad'a zuciyarsa na suya." Mahmud ya shiga mazaunin direba ya zauna had'ida yimasa sannu snn yaja motar suka tafi, tare da yiwa dijama Alk'awarin cewa zai dawo nan da sati d'aya." Cike da farin ciki yake tuk'i, ya rasa dalilin farin cikinsa sai murmushi yakeyi yana shafar sajansa." Khalil yana lura da hakan, sai ji yayi kansa ya kuma Sara masa." Ahakan har suka kawo gida kai tsaye khalil ya bud'e murfin mota ya fito batare da yabi ta takan mahmud ba bare ya kallesa kai tsaye b'angarensa mahmud yaga ya nufa." Ido Mahmud ya bisa dashi yana mmki, tare da tambayar kansa duk ciwon kan ne hakan?" Ko dai da akwai abunda yake damunsa."? ****************** Wata d'aya da rantsar dasu mahmud a aikin soja kud'ad'ensa suka fito, masu yawa wad'anda har ya rasa abunda zaiyi dasu. Snn kuma anyi posting d'insa a inda zai fara aikinsa a nan cikin garin Abuja tare da commondent general, dashida abokinsa sulaiman." Mahmud najin hakan yasan da akwai wata ak'asa domin iya d'an zaman da yayi da Alhaji Atiku ya fara karantar wasu halayansa." Abba da momy sai murna sukeyi, ba'a turashi wata k'asaba dama abunda sukejiwa tsoro kenan, sunsan barinsa da akayi a garin Abuja da'ayi da sa hannun Alhaji Atiku sunyi farin ciki sosai, Basuyi k'asa a gwaiwaba Abba da momy suka shiga mota suka sameshi har gidansa a garin Abuja suka kuma yi masa godiya, Abba yayi godiya sosai ya nunawa Alhaji Atiku farin cikinsa a fili, yace "hak'ik'a Alhaji Atiku kai Abokine na kwarai Wanda samun irinka sai an tona, nagode sosai ina rok'on Allah yabani abunda zan saka maka da wnn halacci da taimako da kayi mana." Wata irin dariya Alhaji Atiku ya saki a ransa yace "anxo wurin Dama abunda nakeso naji kenan." A zahiri kuma ya b'ata fuska yace Alhaji Hassan godiyar ta ishini hakan, kanaso ka nunamun cewa mahmud d'anka ne?" Idan ba hakan ba karka kuma yimun godiya a kan abunda nayiwa d'ana." Hakan ya rufewa SU Abba baki, daga nan sukayi sallama suka d'auki hanyar gida." Ranar Monday ya fara aiki a garin Abuja a ofice d'in Alhaji Atiku. Hakan shima sulaiman duk a tare suke aikin a wuri d'aya aka ajiyesu." Aiki suke akan gaskiya domin sun d'aukarwa k'asa Alk'awarin cewa xasuyi aiki a kan gaskiya musamman mahmud." 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar Gidan tsohuwa_)😅 Writteng By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *31* Zaman da mahmud yakeyi a office d'in Alhaji Atiku ya fahimci mutum ne marar adalci Wanda baya tausayin na k'ana dashi." Muddun kaga Alhaji Atiku yana sakar maka fuska tare da kyautata wa. To tabbas akwai abunda yake buk'ata daga gareka." Mahmud ya fahimci cewa Alhaji Atiku mutum ne mai yawan mu'amala da mata Kuma yafison matan aure, Agaban idonsa zai aika akira masa matar yaronsa Wanda ya kwad'aitu da ita, Yayi mata barazana da cewa ko ta Amince masa tabashi kanta ko ya sanya a kashe mijinta." Hakan wasu matan ke amince masa, da zarar ya dad'addani xumar macce tayi masa to shikenan zai san ynda yyi ya d'auke mijinta, daga garin yyi posting d'insa can wani gari mai nisa inda ba zai iya tafiya da matarsa. Ta anan Alhaji Atiku zai samu dama ya dinga kasancewa da ita." Wnn mugun halin nasa ya kuma sanyawa mahmud yaji ya tsanesa ya kuma tsane duk wani Abu da yake fitowa daga garesa yana masa biyayya ne kawai saboda umurnin da Abba yabashi." Yau ne Yusra take dawowa daga England, Inda aka shirya mata kwarya kwaryar liyafa. Alhaji Atiku baya zaune baya tsaye sai kai da komo yake yana murna yau zaiga shalelensa." Mahmud yabawa umurnin yaje ya d'aukota airport, Baiyi masa gardama ba, ya d'auki key d'in mota yana sanye da uniform d'insa ya nufi airport." Xuwansa kenan jirginsu ya sauka yaja wuri d'aya yayi parking yafito hard'e da hannunsa a k'irjinsa, ya jingina a mota, yana kallon duk Wanda ke fitowa a jirgin d'aya bayan d'aya." A can ya hango ta tafito sanye cikin k'ananun kaya riga da wando wad'anda suka d'ame mata ajiki, duk ilahirin surar jikinta a waje take." Idonta sanye da k'aton glass bak'i kanta ba ko d'ankwali Kai da ka ganta sai ka rantse da Allah kace ba 'yar musulmai bace." *yasin yau wuyar typing nkeji kuyi hkr da wnn*🤓🤓 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar Gidan tsohuwa_)😅 Writteng By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *32* Kallo d'aya yayi mata ya kauda idonsa gefe, Domin baya son ya kuma kallon nakasanshen jikinta wnda ta ke tallatashi a kan titi." Baiyi yunk'urin zuwa ya tarbotaba kamar ynda sojoji suke mata." Waige waige tashigayi tana Neman wad'anda daddy ya turo mata domin su d'auketa, amma bataga kowa ba." Anan take ranta ya b'aci, ga zafin rana yana dukanta duk ta had'a zufa, Mahmud yana gefe cikin inuwa yana kallonta cike da tsana, bazai iya zuwa ya tarotaba bare ta ganshi duk lokacin da ta hangoshi da kanta tana iya zuwa sutafi." Ranta ya b'aci ta d'aga waya takira Daddy cikin hushi, "daddy halan bakayi farin ciki da dawowata bane kabarni cikin rana tana dukana." Ya kwantar da murya "haba shalelen daddy ai daddy bai isaba, ki duba naturo mki masoyinki Mahmud domin yazo ya d'aukeki, ki dubashi tun d'azun yazo wurin kinsan halinsa wani irin kalar hali garesa Wanda da wuya ka iya gane inda ya dosa." Kidubashi yana wurin, Bata jira ta kuma jin abunda yake fad'aba, ta kashe wayar da sauri Domin jin ya ambaci sunan mahmud." Duk wayar da takeyi da abunda take cewa mahaifinta Mahmud yana kusa da ita jingine a motarsa yana kallonta, kuma yana jinta, bata ganshiba, ta gabansa tabi ta wuce janye da kwatin kayanta amma ko kallo bata ishesaba." Hand bag d'inta ta sub'uce ta fad'i k'asa a gefen k'afarsa, cikin sauri ta duk'a domin ta d'auka tayi tozali da zararan ya tsun k'afarsa wad'anda suna d'aya daga cikin abunda yake burgeta a jikinsa." Bata d'auki jakarba tayi saurin mik'ewa da sauri cike da murna tayi kansa ta rungumasa tana fad'in "haba sweety duk ka wahalar dani wurin nemanka a she kana tsaye kana kallona." Bata k'arasa maganartaba ya finciketa da k'arfi daga jikinsa yayi wurgi da ita, sai da ta kusan fad'uwa k'asa. Ya juya yyi shigewar sa mota ya zauna ransa duk a jagule yake, yana jiran tashigo su wuce." d'ago kai tayi ta kallesa, ta kuma kallon mutanen dake kallonsu mafi yawansu duk sunsanta sunsan ko waye haifinta." Dakewa tayi ta k'ak'aro murmushin dole ta kuma duk'awa ta d'auki kayanta ta nufi motar Wanda tuni ya tayar da ita yana Neman tafiyar sa." Da kanta ta bud'e but ta sanya kayanta abunda bata tab'a yiba a rayuwarta, snn ta zagayo tashiga gidan gaba had'ida kallon fuskarsa Wanda take burgeta tayi murmushi." Mahmud bai dubeta ba illah ya yatayar da mota ya d'auki hanyar gida." Kallonsa tayi taji wani irin sonshi ya durar mata a zuciya, ta kashe murya tace "akan sonka na shirya d'aukar duk wani Abu daga gareka, INA sonka kuma sai ka aureni ko da kai baka sona." Da sauri ya juya ya kalleta yyi mta kallon tsana, yace "ni kuma na tsaneki bana sonki saboda ke nakashashiyace, ki daina yaudarar kanki akan cewa sai kin aureni, har Abada bazan tab'a aurenki ba." Baki cikin tsarin matar da zan aura." Yana kaiwa nan, bai kuma saurarenta ba yaja mota da k'arfi saura kad'an kanta ya daku a motar irin ynda ya fisgeta." Idonta ya cika da hawayen Kalmar da ykirata da ita ta nakashasshiya, Ta kallesa ta d'aga murya da k'arfi tace "karya ne mahmud niba nakashasshiya bace, Ka dubeni da kyau inada cikar halittar da akeso a kowacce macce." Murmushi ya saki Wanda ya kuma fitar mashi da kyawon fuskar sa, ganinta da yyi cikin b'acin rai yasanya rayuwarsa tayi Kai tsaye gidansu ya nufa inda aka shirya mata kwarya kwaryan liyafa daddy tare da mommy zaune suna jiran isowarta gefen Dama da hagonsu sojoji zagaye dasu." Ana ganin isuwarsu ko wanne soja yanufi motar domin tarbo shalele." Batabi takansu ba kamar ynda tasaba yi masu, ko kallo basu ishetaba bare ta amsa gaisuwar da suke mata kai tsaye wurin daddy ta nufa ta rungumeshi had'ida sakar masa kiss a gefen kunci," Shima cike da murna ya kuma k'ank'ameta yana mata oyoyo suna dariya, Tajuyo ta kalli mommy tace hy mommy snnu da gida." Kallo d'aya mommy tayi mata ta kauda kanta, domin ta tsani rayuwar da 'yar tata take gudanarwa Dan hakan take cewa bata sonta daddy ne kawai yake sonta." Mahmud na ganin hakan, yayi Allah wadai da rayuwar da suke gudanarwa ya kuma jin tsanarta da ta mahaifinta ya mere baki had'ida Jan dogon tsaki ya bar wurin." Wuri yasamu nesa dasu ya zauna amma duk abunda ake gudanarwa yana gani." Zaune yake yana latsar wayar hannunsa pix d'in dijama yake kallo wad'anda yayi ta d'aukarta tana sanye da uniform a lokacin da ya je makarantarsu, kallo yakeyi yana murmushi har ya mnta da b'acin rain yusra." Sallama yaji anyi masa a gefensa d'aga kai da zaiyi wazai gani fareeda ce matar sulaiman janye da yaronsu." Cikin fara'a da sakin fuska ya suka gaisa har da d'an zolayarta yyi, yana fad'in bata iya kwana biyu idan bata sanya sulaiman a idoba." Tana dariya tace "eye naji Dan Allah jeka ka kiramun shi." Shima dariyar yakeyi yace bara na taimaka mki nkira mki shi." Ya mik'e tsaye ya nufi inda sulaiman yake a can kusa da Alhaji Atiku ya take masa baya hannunsa rik'e da bindiga saboda tsaro." Sulaiman mutum ne Wanda baya wasa da aikinsa a cewarsa aikinsa shine gatansa shine uwarsa shine ubansa marayane gaba da baya, a hannun k'anin mahaifinsa ya tashi Wanda shima talaka ne abincin da zasuci wuya yake masu." Kuma a hakan ya aurawa sulaiman 'yarsa fareeda Wanda suka tashi cike da soyayyar junansu." Da taimakon Allah kamar da wasa aka fitar da form d'in soja fareeda ta sayar da kayan d'akinta tabawa mahaifinta ya sayawa sulaiman form d'in, Cikin ikon Allah sunansa ya fito, wnda gashi a yanzun ya fara wadata a aikin soja, domin ya sayawa k'anin mahaifinsa k'aton gida ya kuma bud'a masa babban shago na sayar da atamfofi." Kai tsaye mahmud ya tunkari wurin inda akeyin liyafar domin kiran sulaima, yusra tana ganinsa takar masa murmushi tana Neman ta bar wurin tazo wurinsa, Alhaji Atiku na ganin hakan yayi saurin rik'o hannunta ya dawo da ita a inda take yana mata magana k'asa k'asa Wanda su kad'ai sukasan abunda suke cewa." Mahmud bai damu dasuba kai tsaye wurin sulaiman ya nufa yashiga yimasa magana cikin harshin turanci cewa fareeda tazo gata can tana jiransa." Jin hakan sai da yasaki murmushi jin dad'i yacewa Mahmud ya kaita masaukinsu da ke nan cikin gidan can layin sojoji, ya ajiyeta, Had'ida kawo mata ruwa da abinci tasha kafin yazo." Murmushi Mahmud kawai yyi ya juya ya tafi, Idon yusra akansa tanajin wata kalar wutar k'aunasa tana ruruwa a zuciyarta domin mahmud jarumi ne daga ganinsa zaiyi jarumta wurin tafiyar da macce a kan gado." Tunshigowar fareeda wurin idon Alhaji Atiku ya sauka a kanta, yana ganinta yaji gaba d'aya hanlinsa ya tashi so yakeyi kawai yajishi ya kad'aice da ita." Mahmud na tafiya ya kalli sulaiman ya masa nuni da hannu a lamar yaje wurin matarsa ya kuma zaro kud'i cikin aljihunsa dubu ashirin ya mik'a masa yace kasaya mata kayan motsa baki." Cike da murna sulaiman ya runsuna ya karb'a yana godiya, yatafi wurin fareeda." Da isarsa mahmud yana fitowa daga d'akin, Cikin murna sulaiman ya tareshi yana dariya yana fad'a masa Alherin da Alhaji Atiku yayi masa." Gaban mahmud ya fad'i ya zaro ido yace "ina fatan baiga shigowar fareeda ba?' Sulaiman yasaki dariya yace "maiya faru idan har ya ganta?" Mahmud yace "no bakomai tambaya ce kawai nayi, yayi wucewarsa, yana tunanin tambas Alhaji Atiku fareeda yagani tunda har yabawa sulaiman kyautar kud'i, Dama hakan yakeyi da zarar ya kyallara ido yaga matar yaronsa in dai har ta kwanta masa zai dinga yiwa yaron nasa Alheri na Jan hankali." ******************* Bayan an watse daga wurin liyafar kowa yakoma wurin aikinsa, Alhaji Atiku da shalale sai zuba mashi shagwab'a takeyi akan wutar son mahmud dake ruruwa a zuciyarta." Ransa ya b'aci ganin ynda shalele take zubar da hawayenta akan wani d'a namiji kuma yaronsa, Wanda yake da iko dashi har da mahaifinsa." Janyota yayi a jikinsa ya shiga share mata hawayen da ke zuba a fuskarta yace "daga yau kukanki ya k'are indai akan mahmud ne." Wayarsa ya d'auka yashiga kiran number Alhaji Hassan mahaifin mahmud." Abba yana ganin wayar Alhaji Atiku tunkafin ya d'auka sai da yasaki dariya snn ya daga wayar had'ida sallama, Alhaji Atiku ya amsa masa yana mai sakin fara'a a fuskarsa." Bayan sun kammala gaisuwar ne Alhaji Atiku yake shaida masa gobe yyi sauri yazo garin Abuja akwai meeting da zasuyi game da harkokin siyasa." To Abba yace yana mai d'auke da fara'a da jin dad'i a fuskarsa, snn sukayi sallama ko wanne ya kashe wayarsa." Ya juya ya kalli yusra yasaki dariya mai sauti yace "nayi mki Alk'awarin bazaki tab'a Neman wani Abu kirasaba, ki sanyawa rayuwarki a gobe za'a tsayar da ranar aurenki da Mahmud ko yaso ko baya so wnn matsalarsa ce." Washe gari bayan Abba ya sauka garin Abuja sunshiga meeting da manya yan siyasa, anan take da San hannun Alhaji Atiku aka tsayar da Abba a matsayin d'an takarar gwamna. Kasan cewar Alhaji Atiku shikeda jama'a dan haka ko wanne d'an takara yakeyi masa biyayya." Sauran mutunen wurin sun Amince da zab'en Alhaji Atiku anan aka umurce Abba da ya biya kud'in k'ungiya naira milyan talatin." Abba yayi shuru domin baya da miliyan talatin, ganin shurun da yayi yasa Alhaji Atiku ya fahimce cewa baya dasu, yasaki murmushi a ransa domin hakan yakeso ya gani." Anan take Alhaji Atiku ya cika cak d'in kud'in ya bayar." Zaro ido Abba YAYi cike da mmki zaiyi magana Alhaji Atiku ya dakatar dashi alamar yayi shuru idan aka tashi akwai maganar da zasuyi." Bayan kowa ya watse daga meeting d'in akabar Alhaki Atiku da Abba a office d'in Abba sai godiya yake zuba masa wanda har yarasa abunda zai fad'a." Alhaji Atiku ya dafa kafad'arsa yace dainayi mun godiya hakan ta isheni, kasani duk abinda nayi maka ban fad'i ba saboda kai abokinane kuma aminina na gaskya. Komai nawa ina iya mallaka maka shi a kyauta" Wnn dalilin yasa saboda mu kuma dank'on zumunci mu ya d'ore har d'iya da jikoki na yanke shawarar mu had'a 'ya'yanmu Aure mahmud da yusra." 🌹 *DEEJAMA*🌹 Writteng By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *33* Abba yayi murmushi ya kalli Alhaji Atiku yace " kayi tunani mai kyau, Alhaji Atiku Amma sai dai bntari numfashinka ba, Sai dai d'anka Mahmud yana da wacce zai aura 'yar k'anena marigayi husaini Wanda muka d'aukarwa junanmu Alk'awarin tun kafin Allah ya karb'i rywarsa zamu had'asu aure domin k'ara dank'on zumunci mai d'orewa." Alhaji Atiku yayi murmushi mai cike da wata manufa, yace " bakomai zan bata hak'uri akan cewa duk ynda take sonshi ta hak'ura da shi, Allah ya bata dangana." Abba duk yaji ba dad'i da yatuna da irin halaccin da taimakon da Alhaji Atiku yayi masa." Idan ya hana mahmud ya auri yusra tambas ya nuna rashin halaccinsa garesa." Alhaji Atiku ya mik'e tsaye a hasale ya kalli Abba yace "to Alhaji hassan ni zantafi sai munyi waya kuma." Abba ya rik'o hannunsa ya dawo dashi ya zauna yayi murmushi yace Alhaji Atiku ka fahimce mana kasan girman Alk'awari Wanda idan bancika shiba Allah zai iya kamani ta ko wacce hanya." Banak'i mahmud ya auri yusra bane, yusra da muhmud dukansu 'ya'yana ne, Na Amince Mahmud ya auri yusra, Amma bayan ya aureta ko yaushene ko nan da shekara nawa ne zai aure Ummie yyi ta biyu da ita." Sai a lokacin Alhaji Atiku yasaki dariya yace "wnn ba Matsala bace aidama namiji macce hud'u aka umurce sa da yyi, amma dani da kai munsanya rangwanci mun zauna da macce d'aya, Suka sanya dariya suka tab'a." Daga k'arshe sukayi sallama, Abba ya neme Alfarmar da aturo masa Mahmud ya sameshi a kano akwai maganar da zaiyi dashi, Snn daga k'arshe sai ansaya ranar auren nasu." Hakan suka rabu Alhaji Atiku zuciyar sa cike take da farin ciki shalelensa ta samu abunda takeso." Alhaji Atiku yana Shigar da motarsa a harabar gidansa yaci karo da fareeda da sulaiman yana d'auke da d'ansu Ammar xaiyi masu rakiya zuwa Tasha domin su shiga mota zuwa sokoto." Alhaji Atiku Yana ganinta yaji gaba d'aya hankalinsa ya tashi akanta burinsa kawai shine ya yajishi a kanta." Kasan cewa fareeda cikakkiyar macce ce mai siga da haiba tana da jikinta irin na manya mata wanda duk namijin da yayi ido biyu da ita idai lafiyayyene sai yaji wani abu a tare dashi game da ita." Horn ya dinga yimasu yana lasar baki kamar wani maye, alamar SU dakata sulaima ya lura da abunda yake nufi yayi saurin yi mata magana sukaja gefe d'aya suka zauna." Da sauri ya ajiye motarsa wurin ajiye motoci ya fito yanufesu idonsa akan fareeda yana mata wani kallo na k'urullah." Fareeda na lura da kallon da yake mata anan take taji ta tsaneshi, bata son had'a ido dashi.' Sulaiman ya sare masa alamar girmamawa, ya amsa masa yana murmushi still idonsa akan fareeda." Ya kalli sulaiman yace "ina zakuje hakan?" Sulaiman yace "ranka ya dad'e zanraka ta tasha ta shiga mota zata koma gida ne." Alhaji Atiku yace "meyasa bazata dawo nan da xamaba kamar ynda wasu daga cikinku sukeyi?" Murmushi kawai sulaiman yyi, Alhaji Atiku yanuna masa wani d'aki inda ba kowa a cikinsa a can nesa da tsohon d'akinsu, A kusa da wasu matan sojoji, yace ka ajiye matar ka a can duk abunda kuke buk'ata akwai a ciki." Snn duk lokacin da ta buk'aci zuwa ganin gida tana iya zuwa ta dawo, INA ganin hakan ya fiye maku sauk'i." Godiya sulaiman ya shiga yimasa tare da Addu'ar Allah ya k'ara girma." Fareeda itama ta d'an k'ak'aro murmushin dole tayi masa godiya snn suka juya suka nufi inda ya nuna masu d'in." Suna tafiya Alhaji Atiku idonsa a kan fareeda yana kallon yanda take tafiya k'ugunta na juyawa." Mahmud da shigowarsa kenan yaci karo da Alhaji Atiku tsaye wuri d'aya yana kallon wani wurin yana lasar baki yana murmushi." Inda yake kallo shima mahmud yabi wurin da kallo fareeda yagani da sulaiman suna tafiya, Gabansa ya yanke ya fad'i domin yasan bbu Wanda yake yiwa wnn kallon sai fareeda daman yasan hakan sai ya faru." Ya kuma matsawa daf dashi cike da takaici yace "ranka ya dad'e ko kasanta ne,?" Cikin raxana ya juyo yana ganin mahmud ne ya had'e fuska yace "mekace Mahmud ne?" D'an murmushi Mahmud yyi na gefen baki yace "no cewa nyi meya faru na ganka a nan tsaye?" Alhaji Atiku yyi murmushi had'ida Sosa kai yace "kai nake nema, ka shirya gobe katafi kano Alhaji Hassan yana nemanka kuma idan katafi kabari sai ka huta kayi sati biyu snn kadawo." Mahmud ya had'e fuska yace "ranka ya dad'e baxanyi sati biyu ba Saboda baya daga cikin dokokin aikina in har bani da kaina narubuta hutuba Na d'aukarwa k'asata Alk'awari xan tsaya nayi aiki a kan gskiya. Dan haka bbu wani dalili da zai sanya natafi gida na zauna na huta har tsawon sati biyu ." Yana kaiwa nan bai jira Alhaji Atiku yyi magana ba yyi tafiyarsa, ya barsa a nan tsaye, yana mmkin mahmud, Tunda ya fara aikin soja har zuwa yanzun da yake a matsayin commondent bbu wani yaronsa dayake tsayawa gaba da gaba ya nuna baya tsoronsa ya kuma fad'a masa magana ynda yaga Dama kamar Mahmud, kuma abun mmki sai ya tsinci kansa da kasa yimasa hukunci." Hakan ya juya yayi shigewarsa ciki, da shigarsa yaci karo da yusra zaune akan kujera ta d'ora k'afa d'aya kan d'aya da k'atuwar wayarta a hannunta da alamar chatting takeyi, tana zaman jiran shigowarsa domin daga yau ta gaji da Alk'awarin da yake mata akan cewa mahmud natane amma kuma har ynxun baizama na ta d'inba kullum idan tayi ido biyu dashi jitakeyi kamar taje ta rungumeshi ta kuma jin wani sabon son shi yana dirar mata a zuciya." Yana ganinta yasaki dariya tare da fad'in shalelen daddy Albishirinki Nazo mki da wani Albishir Wanda sai kinbani kyauta." Mere baki tayi had'ida ya mutsa fuska tace "ina saurarenka daddy." Yanayin ynda ta amsa masa sai baji dad'iba. Amma kuma sai ya tunkareta ya zauna kusa da ita, Yace "yau mahaifin Mahmud yazo mun zauna dashi ya Amince mun da cewa ya yarda mahmud ya aure ki" Wani irin tsalle tayi had'ida kwatsa ihu ta fad'a kan jikinsa cike da murna, tace "daddy yaushe aka sanya ranar bikin namu." Ya kalleta yasaki dariya domin yaji dad'in ynda ya ganta cikim farin ciki, Yace "ba'a sanya ranaba sai nan da kwana biyu idan mahmud ya dawo daga kano inda yake nemansa sai nkira mahaifin nasa mu sanya ranar bikin naku.": Kuma k'ank'ame shi tayi tana dariyar jin dad'i tana fad'in "ina sonka daddy na saboda kana bani duk abunda nkeso, muddun ka aura mun mahmud hak'ik'a kagama mun komai a rayuwa." Daddy ina son mahmud so mai tsanani soyayyar da bantab'ayin irintaba, hawaye suka dinga zuba a fuskarta." Yashiga shafe mata hawaye yace "daina kuka kinsamu mahmud, mahmud ya zama naki." ************ Bayan Abba ya dawo gida yake gayawa mommy an tsayar dashi a matsayin d'an takarar gwamna, da kuma irin d'inbin alherin da Alhaji Atiku yyi masa da yabiya masa makudan kud'in kungiya da aka nema." Mommy taji dad'i sosai ta kuma sanyawa Alhaji Atiku Albarka." Sai da tayi shuru ta natsu fuskarta cike da farin ciki snn Abba ya kuma kiran sunanta cikin natsuwa, yashiga shaida mata manufar Alhaji Atiku akan yaransu." Anan take fuskar mommy ta canxa tace "Sam bazai yuwoba yarinyar da bata da tarbiya, za'a had'ata da mahmud." Anan Abba yashiga lallashinta yace tayi hak'uri "tabari Mahmud yazo idan anyi masa magana ya nuna baya ra'ayinta to bazamuyi masa doleba sai dai Alhaji Atiku da 'yarsa su hak'ura. Idan kuma ya Amince saikiyi hkr kibisu da Addu'a, ita shiriya ta Allah ce." Mommy taja bakinta tayi shuru Dan ita har ga Allah bata son mahmud ya auri yusra." **************** Akwana a tashi ba wuya a wurin Allah Deejama anshiga ss2, Ilimi ya samu Arabic da boko, Duk Wanda yasan deejama a da ya ganta a yanxun ba zai ganetaba, domin ta girma ta waye ta zama cikakkiyar budurwa 'yar birni maiji da kanta." Duk wata halitta ta cikakkiyar 'ya macce ta fito mata gata dogowa fara kyakkyawa k'irjinta ya cika hakan k'ugunta idan kagani masha Allah." Deejama ga aji domin a halin yanzun bata fiya son yawan magana ba sosai Amma har idan taga za'a shiga hak'inta Zata dawo dijamarta ta ainahi ta kwatarwa kanta 'yanci." Hakan yasa Khalil ya kuma fad'awa cikin matsanancin Sonta, wnda a yanda yakeji akanta komai yana iya aikatawa in har zai sanya ya mallake ta Deejama itace macce da yake tsarawa rayuwarsa xai yi rayuwar aure da ita Deejama tana d'aya daga cikin Matan da samun irinsu sai antona, domin da zarar kayi ido biyu da ita zaka fahimci akwai wani sirri a tare da ita Wanda ba ko wacce 'ya macce ke tare da shiba." Ya dad'e yana ganinta a mafarkinsa, ya dad'e yana nemanta Ashe k'anwarsa ce jininsa ce, 'yar uwarsa ce Dan haka duk duniyar nan ba Wanda ya isa ya hanashi ya aure deejama." Duk wani katanga da Abba yake masa a kanta, duk wani killaceta da akeyi idan aka gansa yashigo gida to ayi agama domin babu wnda ya isa ya aure dijama Indai yana numfashi a doron k'asa." ***************** Abba Ganin hankalin da deejama tayi da natsuwarta, yasa Abba yaji dad'i sosai ya kuma samun natsuwa da ita, Wnn dalilin yasa ya saya masu mota d'aya ita da fateema ya Sanya aka koyawa ko wannensu, idan dijama ta zo Hutu itake amfani da ita idan kuma ta koma makaranta fateema ke amfani da ita." A yanxun anyi masu hutun zangon k'arshe wanda daga sun koma zasu shiga ss3 Zaune take a babban falon gidan sanye take da k'ananun kaya riga da wando 'yan fakistan Wanda sukayi mata kyau, hannunta rik'e da k'atuwar wayarta Wanda Abba ya saya mata, kunnenta sanye da airface tana sauraren karatun Alqur'ani tana tilawa had'ida gyad'a kanta duk Wanda ya ganta hakan sai ya rantse da Allah wak'a ce take saurare tana gyad'a kai." Hkan Al'adarta take bata son sanya manya kaya irinsu Atamfa ko lass ko shadda a jikinta tafi son k'ananun kaya, a cewarta mnya kaya nauyi suke mata ajiki." Fateema ce tafito cikin shirinta sanye take da atamfa ta yafa gyalenta irin Atamfarta yellow, hannunta d'auke da handbag d'inta tafito ta kalli inda dijama take kwance a kan doguwar kujara kamar wata sarauniyar kyau, tace "sister nashirya mutafi kawai." Kallonta dijama tayi tayi murnushi tace " kin karb'o kud'in a wurin mommy?" Fateema tace "ai tun jiya Abba ya bamu kud'in yace idan basu isaba muyi masa waya a can wurin shoping d'in zai turo akawo Mana wasu kud'in." Girgiza kai tayi bata kuma yin maganaba illah ta d'auki mayafin kayanta tayi Rollin dashi fuskarta ta fito kamar balarabiya suka shiga sukayiwa mommy sallama suka fito, dijama ta shiga mazaunin direba ta tayar da motar suka tafi." Bayan sunyi shoping d'in a hanyarsu ta dawowa gida motarsu ta tsaya akan titi, dijama dake driven ta dafe kai cike da takaici ta juya ta kalli fateema tace "sister meke faru haka?" Fateema tace "mufita mugani." Hakan suka fita suka bud'e motar suka shiga d'an gyara wurin da suke tsammanin shike basu matsala, Suka dawo suka shiga motar dijama ta kunna ai kuwa ba mmki gani sukayi motar ta tashi." Basu d'aga daga inda sukeba horn kawai sukeji yana tashi gabansu da bayansu, abun mmki dibawar da xasuyi gosulo ne mutane cincirindo gabansu da bayansu suna jiran SU kauce daga kan titi." Hankalin fateema ya tashi ta zaro ido waje tace "munshiga uku sister diba kiga mutane ynda suka zagayemu duk mu muka tsayar dasu, Dan Allah sister tayar da motar muyi tafiyarmu mubasu wuri." Deejama tayi murmushi domin ita abun burgeta yayi ganin duk itace sanadiyar tara wnn gosulon." Tace wlh ban tashi tafiyarba a yanzun." Sai ma tabud'e glass d'in tsakiyar motar ta tashi tsaye ta fito ta sama tana kallon cincirindon mutanen da ke wurin d'aya bayan d'aya." Haushi ya kama mutane wani mutum matashi ya hasala ya fito ya nufota yana nunata yana fad'in "ke 'yar gidan ubnwaye da zakiyiwa mutane tsaye a kan titi saikace gidanku anayimaki magana kin kuma gyale mutane." Ta kallesa ta ya mutsa fuska cikin tsiwa tace "ni 'yar gidan ubanka ce idan kuma ka isa kacika marar kunya kazo ka janyemu daga nan." Ai kuwa mutane kamar jira sukeyi kowa ya taso yana fad'in abunda ke cikin ransa itama tana mayar masu tace kuma bazata janye daga kan titinba sai dai kowa ya kwana anan." Hankalin fateema ya kuma tashi ta fashe da kuka da ta kuma juyawa ta kalli mutanen dake wurin, Tashiga had'a dijama da Allah akan suwuce sutafi idonta yana zubar da hawaye ita dai fateema bata son tashin hankali da hayaniya." Dijama ta doka mata tsawa tace "yimun shuru sanlatacciya to bantashi tafiyarba." Mahmud da Ya yafito daga Abuja duk a gajiye yake, ya matsu ya Ganshi ya isa gida domin ya watsa ruwa ya huta gashi indai ya kammala abunda yakeyi yau zaikoma bakin aikinsa ko kwana baZaiyiba saiyaga iyakar Alhaji Atiku domin ya gano manufarsa a kan fareeda." Wnn gosulo ya tsayar dashi saiyi yakeyi yana kallon agogon hannunsa dogon tsaki yaja yana mmkin abunda ya haifar da gululon har ynxun ba'a fara tafiyaba kowa yana nan ynda yke atsaitsaye." Hayaniya yajiyo a can gabansa inda baya iya hango abunda ke faruwa amma da alamar kamar fad'a ne akeyi." Ya bud'e murfin motarsa ya fito yana sanye da uniform d'insa na soja, da saurinsa ya dinga ratsa mutane yana k'ok'arin isa inda yakejin fad'an na tashi." Da kyar yasamu ya isa wurin abun mmki deejama ya gani tsaye akan mota sai tsiwa take yiwa mutane ta tare hanya." Dibonsa ya kai a cikin motar wa zai gani fateema ce zaune wuri d'aya sai matsar hawaye takeyi." Dijama na juyowa cikin masifa tayi ido biyu da yaya Mahmud yana k'ok'arin isowa inda suke daga ganinshi a hasale yake." Ta zaro ido waje cike da tsoro tace "sister munshiga uku yaya mahmud." Fateema ta juya ta kallesa cike da tsoro shike nan kin janyo mana duka.' Da sauri deejama ta shiga mota taja da k'arfi, ko kafin mahmud ya kawo wurin su tabar wurin a guje." Kallo yabisu dashi ya girgixa kai yayi masu alamar zansa sameku a gidan." wato duk da ake cewa dijama tayi hankali mai hali baya fasa halinsa." Mutanen wurin suka fahimci ganinsa ne yasa tabasu hanya ai kuwa suka shiga yimasa godiya, shi kuma yana basu hak'uri." Snn kowa ya fara tafiya, wurin uxurinsa." 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'yar gidan tsohuwa_)😅 Writteng By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *34* *Bntab'a tinanin hakan kuke bin labarin nan ba, kai amma naji dad'i so sai ina godiya gareku masoyana Ummu Safwan na sonku irin sosai d'in nan, ina fatan kunfara shirye2 Azimi Allah kasa zakuzo har zamfara kukawo mun kayan Aximi nah ngd Sosai da kulawa😍😍😍* A guje suka iso gida dijama nayin parking har rigaggen fita sukeyi daga motar, da gudu suka wuce mommy a falo suka shige d'akinsu suka turo k'ofa had'ida sanya key." ko wacce ta fad'a kan gado tana sauke mumfashin gudun da tayi, fateema ta kalli dijama tace "kingani sister ynxun kinjanyo mana duka a wurin yaya Mahmud." Dijama ta kalleta tasaki dariya tace "tab amma dai wallahi ke matsoraciya ce, ke da tsayawa zakiyi ya dakeki?" Ai wallahi muddun kikaganni na tsaya yaya Mahmud ya dakeni to ba k'aramin mamayata yayi ba." Dan ina ganin har ya koma Abuja bazai sanyani a idoba bare ya dakeni." Fateema tace "to yaxamu yanxun?" Dijama tace "ke dai kibarmun komai a hannuna duk abunda kikaga nayi kema kiyi domin kisamu ki tserewa dukansa." Fateema tace "to cike da tsoro, bayyane a fuskarta." Cikin mmki mommy tabisu da kallo da alamar tambaya d'auke a fuskarta, Mik'ewa tayi zata nufi d'akinsu domin taji meya samesu suke gudu haka?" Sallamar mahmud ta tsayar da ita, da yashigo yana zarar ido ina xai gansu, Anan take samu amsar tambayar ta akansu, illah ta nunawa Mahmud d'akinsu tace suna ciki sun kulle sun sanya key." Girgixa kai yyi yace zaku fito ne kusameni yau sainayi maganin rashin jinku, musamman ke dijama." Snn yasamu wuri ya xauna akan kujera had'ida durk'usawa ya gaida mommy cike da girmamawa." Mommy ta amsa mashi cike da kulawa had'ida tambayarsa aikinsa." Lafiya glau yace " had'ida tambayar Abba da Khalil." Mommy tace "Abbanka ya fita amma ba nesa ya tafiba ynxun zai dawo." Khalil shima ya fita yace mun ya tafi gidansu Ahmad abokinsa." Ta kallesa tace "laifin me su fateema suka aikata a wajen ne." Anan yashiga bata labarin gosulon da suka had'awa mutane akan hanya." Mommy ta rik'e baki cike da mmki tace "wad'an yara Allah ya shiryamun su." Mahmud yace "Ameen." Amma duk na rik'asu sai sungane kuskuren da sukayi." Snn yace "yawwa mommy wai Neman me Abba yake yimun maike faruwa ne?" Mommy ta mere baki da ta tunada da domin auren yusra ake nemansa." Tace "nima bansani ba kabari kawai sai Abban naku ya dawo." "To yace "had'ida mik'ewa tsaye yace "bara nashiga na nayi wanka naci abinci kafin Abba ya dawo." *************** Alhaji Atiku yana ganin mahmud yayi sallama dashi ya tafi , ya sauke ajiyar zuciya dama ganinsa ya hanashi zuwa wurin fareeda domin ya aiwatar da nufinsa." Amma ynxun tafiyar nan tashi tabashi damar yin duk abunda yakeso da ita batare da wani shamaki ba." Misalin k'arfe biyar ya rubuta posting letter ya aika aka kira masa sulaiman ya mik'a masa takardar, sulaiman yana dubawa yaga anyi posting d'insa a can nesa da gari, wani bank ne zaije ya kula dashi." Murmushi yyi ya kalli Alhaji Atiku yace "ranka ya dad'e mainayi kuma akayi posting d'ina." Murmushi Alhaji Atiku yayi ya juya kujerarsa yace "bakayi komaiba sulaiman Alheri ne zaka samo a can, wnda saikayi farin ciki da hakan, ka kwantar da hankalinka karka damu bawani dad'ewa zakayiba sati d'aya ne zuwa biyu zakayi sai ka dawo." Murmushi sulaiman ya kuma yi yace "nagode ranka ya dad'e Allah ya k'ara girma, ya juya ya fita." Alhaji Atiku yabi bayan shi da kallo, yana murmushin samun nasara." Misalin k'arfe 7:pm sulaiman ya gama shirya kayansa tsaf a kwati, ya kalli fareeda dake rugume dashi ita Sam bata son yatafi ya barta, Yashiga bata hak'uri da kwantar mata da hankali cewa ba dad'ewa zaiyi ba sati d'aya ne zaiyi ya dawo ta kula da kanta." Ya duk'a yyiwa Ammar kiss a goshi wnda yake kwance barcinsa kawai yake yi, Snn ya fita fareeda tayi masa rakiya har motarsu ta ma'aikata ya shiga ya tayar tana d'aga masa hannu har yafita daga gidan snn ta koma cikin d'akinta." Duk abunda sukeyi Alhaji Atiku yana kallonsu ta k'ofar d'akin sa yana kuma k'arewa fareeda kallo yana had'iyar miyau." Misalin k'arfe 10pm kowa dake wurin ya shige ya kwanta, haka itama Fareeda bayan ta gama waya da mijinta taji ya sauka lfy, snn hnkalinta ya kwanta, suka gama hirarsu snn sukayi sallama." Taja doguwar ajiyar zuciya, Ta d'auko Ammar daga k'uryan d'aki ta shinfid'a katifa a falo ta kwantar dashi tare da bud'e k'ofa domin susha iska sakamakon zafin da akeyi kuma ba wutar NEPA." Itama kwantawar tayi bata ankaraba bacci ya d'auketa." A can cikin baccinta taji kamar ana shafata, Da sauri ta bud'e idonta domin tabbatarwa kanta, ai kuwa ido biyu sukayi da Alhaji Atiku daga shi sai jallabiya da gajeren wando." Zatayi yunk'urin guduwa ya tarota ya rungumeta yana sauke wani irin numfashi, Yana fad'in "karki gujeni fareeda tun lokacin da na d'ora idona a kanki naji nakamu da matsannaciyar sha'awarki, ki Amince dani zakiji dad'ina, Zan mallaka maki duk abunda kike buk'ata a rayuwa dake da iyayenki da mijinki sulaiman dukanku zakuji dad'i domin zan wadataku zan mayar daku abun kwatance a gari, daga wnn ranar bazaku tab'a tsayawa dogaro ga Albashin sulaiman ba." Idan kuma kikak'i Amince mun to kisani rayuwar mijinki abun sonki sulaiman tana cikin had'ari mutuwa ko rayuwa." A razane ta kalleshi, hankali tashe, Snnu a hankali ta xame jikinta daga nashi tace "banason mijina ya mutu, INA son mijina." Yasaki dariyar samun nasara, Dama duk matan da yake ma'amala dasu da mutuwar mijinsu yake masu barazana sai kuwa ya samu sa'ar miyan buk'atarsa." Yace "yanzun kuma rayuwar mijinki tana hannunki." Ta girgixa kai tace "na Amince bara namayar da Ammar k'urya na kwantar dashi na fito." Yana murmushi yana lasar baki yace "ina jiranki." Ta duk'a ta d'auki Ammar tanufi bithroom dashi, tana Shiga ta rufo k'ofa had'ida sanya sakata da key. Ta fashe da kuka tana fad'in Azzalumi Allah bazai barka ba." Har Abada bazan tab'a amincewa da mummunan nufinka akaina ba", kuma kasani rayuwar sulaiman tana wurin Allah ba wurinka ba fasik'i kawai mazinaci." Alhaji Atiku yashiga dukan k'ofa yana fad'in fareeda bud'e kiji nafasa yimaki komai, Sai ma tayi shuru ta daina yin mgana illah ta rungume Ammar taci gaba da kukanta." Ganin batada niyar bud'ewa ransa ya b'aci ya juya ya kalli katifar da ta tashi akanta a dai dai Inda ya Tarar da ita a kwance, Dai dai wurin yaje ya kwanta ya kefe yana kuma jin wutar sha'awarta tana fisgarshi." Tanajinsa bai fita daga d'akinba tanajin yanda yake sauke wani irin nishi Wanda baya misaltuwa, Har bacci ya d'auketa, Sai kusan sallar asuba snn ya fita ya koma b'angarensa. Da sak'e sak'e a ransa, akanta, shine bai samu natsuwa ba sai da ya kwanta bacci yayi mafarkin fareeda yana biyan buk'atarsa da ita snn koda yatashi yasamu natsuwa." **************** Rashin dawowar Abba da wuri shi yasanya mahmud ya kwana a garin kano." Misalin k'arfe 10am yafito daga wanka shiri yakeyi domin ya tarar da Abba kadda ya kuma fita basuyi maganar da zasuyiba, domin yau yakeso ya koma bakin aikinsa." Bayan ya kammala shiryawa yayiwa mommy waya yace "aturo masa dijama takawo masa break d'insa, Mommy tace ai tunkafin ya tashi daga bacci dijama da fateema suka tafi makarantar islamiya." Murmushi yyi ya kashe wayar domin ya gano dalilin sammakon zuwa makarantar nasu." Zaune yake a falonsa yana goge takalminsa yana kallon talabijin." Sallamar Abba yaji ya turo k'ofa yashigo, Da Sauri ya mik'e tsaye cike da girmamawa ya amsa masa sallamar gabansa na fad'uwa." Saboda yasan ba k'aramin Abu zai kawo Abba har ciki d'akinsa ba." Abba ya wuce kai tsaye ya samu kujera ya zauna yana murmushi, mahmud yaje ya durk'usa k'asa ya gaidashi Tare da cewa "Abba lafiya kazo da kanka aida kabari Nazo nasameka shirin da nakeyi kenan." Murmushi Abba ya kuma yi yace "nasan da hakan Mahmud domin duk a cikin 'ya'yana INA Alfahari da kai, Naxo ne da kaina domin nuna maka mahimmacin maganar da zamuyi da kai." Anan Mahmud ya sunkuyar da kai ya kuma natsu yana sauraren Abba." Abba yace "Mahmud inaso ka natso kayi dogon tinani akan Alhaji Atiku, Ya kyautata mana fiye da tunaninka Wanda koda husaini na raye a duniya iya abunda zaiyi mun kenan." Alhaji Atiku ya bijiromun da wata magana Wanda nakasa yimasa musu akanta saboda diboda d'inbin Alherinsa garemu, Alhaji Atiku ya nunamun cewa yana so ya had'a aurenka da 'yarsa yusra domin muk'ara dank'on zumunci a tsakaninmu, na Amince masa da hakan wnn dalilin yasa nace ya turomun kai naji ra'ayinka in har baka buk'ata na rantse da Allah mahmud bazan tab'a yi maka abunda baka soba, sai dai Alhaji Atiku da 'yarsa su hak'ura." Kansa a sunkuye yaji Ransa yayi mummunan b'aci, wani irin b'akin ciki da zuciya yaji yana taso masa amma sai ya daure yayi k'ok'arin saita kansa ya d'ago kai had'ida murmushin k'arfin hali domin kadda Abba ya fahimci wani abun." Yace "bakomai Abba tunda har ka amsa masa da cewa ka Amince, Nima na amince zan aureta tunda kana son ayi hakan." Abba yayi murmushin jin dad'i yace "Allah yayi maka Albarka Allah ya d'aukaka a duk inda kake." Ameen yace "yaji dad'in Addu'ar da Abba yayi masa, babban burinsa a kullum shine ya dinga ganin farin ciki a kan fuskar mahaifan nashi, indai zasuyi farin ciki akan Abu to ko maiye shi zai iya aikata masu." Bayan Abba ya fita mahmud ya koma ya kwanta a kan doguwar kujera zuciyarsa cike da bak'in ciki da b'acin rai, idanunsa jawur zuciyarsa na bak'i bbu alamar farin ciki ko kad'an a Tare da shi, shi kad'ai yasan wane irin b'acin rai ya binne a zuciyar sa, Sai da ya samu natsuwa snn ya mik'e ya d'auki key d'in motarsa ya fita, yayi wa mommy sallama da Abba suna sanya mashi Albarka yafito ya shiga motarsa ya d'auki hanyar Abuja." Yana fita a guje da motarsa SU dijama suna dawowa daga makaranta." Dijama tabishi da kallo ganin yanda yake Jan mota duk saitaji ba dad'i a ranta domin ta fahimci akwai abunda yake damunsa, Tasan yaya mahmud baya gudu da mota wani lokacin har shikeyiwa Khalil fad'a idan ya kamashi a hanya yana gudu da mota." Tsaye tayi tana kallonsa har sai da ya b'acewa ganinta snn ta girgixa kai ta tsinci kanta da fad'in "Allah ya tsaremun kai yaya mahmud a duk inda ka nufa." Juyawar da zatayi tayiwa fateema magana, Tuni fateema tayi shigewarta gida tana murna yaya mahmud yayi tafiyarsa bai dakesuba ya manta." Khalil tagani tsaye a gabanta ya tsura mata ido yana kallonta kamar yanda yasaba a duk lokacin da ya ganta a cikin gida ko a waje." Dogon tsaki taja had'ida kai masa harara tayi wucewar ta cikin gida, bata kuma bi takansa ba." Bayanta yabi tana tafiya yana kallonta yana kuma jin wani zazzafan sonta yana fisgarsa." Tafiya takeyi jikinta duk a macce yake hakan tashiga falon gidan kamar wacce kwai ya macewa a ciki. Mommy tasama zaune akan kujera tana kallo, Azahiri zaga ganta tana kallo amma kwata kwata hankalinta baya wurin TV, ya yatafi can wurin tunanin Mahmud da aure masa yusra da za'ayi Wanda itama kwata kwata bata son auren Dan dai ba yanda zatayi ne sai dai kawai Addu'a." Dijama ta kalli mommy tace "mommy naga yaya Mahmud ya fita, ina zaitafi?" Mommy ta k'ak'ro murmushi tace "wurin aiki zai koma kuyi masa Addu'ar sauka lafiya." Dijama tace "Insha Allah lfy glau zai isa, Allah ya kaishi lfy." Mommy tace "Ameen." Had'ida kallon dijama cike da kulawa." ***************** Abba na zuwa office ya d'aga waya yakira Alhaji Atiku yake shai masa yayiwa mahmud magana ya Amince Dan Haka asanya ranar auren domin ayi a huta.' Alhaji Atiku yaji dad'i Sosai Wanda hakan yakasa b'oyuwa a kan fuskarsa." Anan take suna tsaida ranar aurensu nan da wata hud'u masu zuwa, daga k'arshe suka yiwa junansu sallama suka kashe wayar." Alhaji Atiku yana fad'awa yusra zokaga murna da farin ciki sai dariya takeyi tana rawa Dan dad'i zata mallaki abinda tafiso akan komai a rayuwarta." K'arfe 5: pm Mahmud ya sauka garin Abuja, lfy kai tsaye d'ansu yanufa wnda a ynxun shi kad'ai yake zaune cikinsa, Kai tsaye toilet ya fad'a ya yyi yasakarwa kansa ruwan sanyi ko da zaiji dad'i a ransa, yana fitowa ya shinfid'a darduma domin yyi sallah." Bayan ya kammala sallar ne wayarsa ta d'auki k'ara yana dubawa bak'uwar number ya gani sai da yayi kamar bazai d'auka ba, sai kuma ya yatsinci kansa da son ya d'aga yaji ko waye." D'auka yyi ya kara a kunne, Wata murya mai taushi yaji tayi sallama, _"Assalamu Alaikum yaya da fatar ka sauka lafiya."_ Ajiyar zuciya ya sauke domin ko a mafarki yaji wnn murya yasan dijama ce, Lumshe ido yayi ya saki murmushi yace "lfy glau, ai dole kikirani tunda kinji dad'i Kin tserewa hukuncina.' To bnmanta ba zandawo." Tasaki dariya mai sauti Wanda sautin muryarta sai da yasanya yashi lumshi ido da sauri ya kashe wayar ya ajiyeta gefe." Still mmurmushi yakeyi ya rasa dalilin murmushin nasa." _hmmmmm muje zuwa aboka naina Ummu Safwan CE_ 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_) 😅 Writteng By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *35* Wayar sa yaji ta kuma yin k'ara yayi saurin kai hannunsa da sauri zai d'auka domin a tunaninsa dijama ce ta kuma kiransa." Yana murmushi ya d'auki wayar, Abba yagani, a kasalance ya d'aga wayar yakara a kunnensa had'ida yin sallama." Cikin natsuwa Abba ya amsa sallamarshi yace "Mahmud ina fatan ka sauka lafiya." "Lafiya k'alau Abba, yace had'ida yin murmushi." Abba yace "yanxun muka kammala waya da Alhaji Atiku, mun tsayar da ranar aurenku nan da wata hud'u masu xuwa ko hakan yayi maka?" Sai da gaban mahmud ya fad'i jikinsa ya soma rawa saboda bak'in ciki, ya zaro ido waje yyi shuru na tsawon minti biyu, Snn yayi k'ok'arin saita muryansa yace "Abba duk yanda ka yanke dai dai ne bana da ja, hkan da kuka sanya yayi Allah ya nuna mana lokacin." Abba yaji dad'in kalamansa yace "Allah ya shi maka Albarka mahmud hak'ika zakaga haske a rayuwarka." Yana kashe wayar idonsa yayi jawur ya burxar da iska mai zafi, Ya D'aga kansa sama yana kallon silin zuciyar sa tunkushe da bak'in ciki, da takaici, ***************** Tunda sulaiman yatafi kullum sai Alhaji Atiku ya isko fareeda a d'akinta yana mata maganar banza, Amma bata kulashi sai dai tayi shigewarta d'aki ta sanya key tayi kwanciyarta tana jinsa a falo sai kusan asuba yake fita." Satin sulaiman biyu a inda aka turashi, amma baiga alamar za'a janyeshi a wurin ba, gashi kullum da tunanin fareeda yake kwana dashi yake tashi." Yana samun sauk'in tunanin ta ne a duk lokacin da yakira wayarta yaji tace tana cikin k'oshin lafiya." Wanda ita kuma fareeda tana b'oye masa abunda Alhaji Atiku yake mata ne saboda kwanciyar hankalin sa, yasamu na tsuwa a wurin aikinsa." Mahmud yyi mmki sosai ganin har yanxun sulaiman bai dawoba, Idan yatafi ya tambayi fareeda ko tana fuskantar wata matsala a gidan sai tace masa A'a ba wata Matsala." Yana yawan sanya ido akan Alhaji Atiku koda zaiga wani alamar da zaisanya ya fahimci wani abun tsaninsa da fareeda, Amma abun mmki baya ganin wata alama, Abunda Mahmud baisaniba Alhaji Atiku dare yakebi idan kowa ya kwanta ya isko fareeda Domin Alhaji Atiku da zarar mahmud na tare dashi suna aiki duk wata hanya da zaisanya yagane wani mummunan Abu a tare dashi a dannewa yakeyi." Amma duk da hakan mahmud bai barshiba yana sanya ido akansa." Duk wata hanya da Alhaji Atiku zaibi, duk wani tsoratarwa da ya kamata yayiwa fareeda domin ganin yasamu biyan buk'atarsa yayi amma bawani haske, hakan yanuna masa da cewa fareeda taurin kai ke gareta tafison mijinta ya rasa ransa akan tabada kanta." A wnn Daren ya mamayeta ta mnta bata rufe k'ofa ba, yasameta ya fad'a mata kai tsaye aikuwa suka dinga kokawa har Allah ya bata sa'arsa ta turoshi waje ya fad'i k'asa yayi targad'e a k'afa, bata damu da hakan ba, ta rufe d'akinta." Alhaji Atiku Yaji bak'in cikin jimuwar da yayi, a k'afarsa ta kumbura tayi haushi Wanda ko takalmi baya iya sanyawa, A maimakon ya hak'ura da mugun nufinsa akanta , saima yaji wata wutar sha'awarta tana ruruwa a zuciyarsa, Wanda a yanda yakejinsa ko ta tsiya ko ta arziki sai ya ku sanceta yasamu biyan buk'atar sa a kanta." Washe gari safiyar Monday ko wanne ma'aikaci shiri yakeyi domin ya tafi wurin aikinsa." Alhaji Atiku a office d'insa mahmud ne zaune a gefensa yana rubuce rubucen takardun wani kes da akeyi wani yaro da yayiwa wata k'aramar yarinya fyad'e." Alhaji Atiku yana kan babban kujerarsa yana juyata idonsa sanye da glass, Tunda mahmud ya yasanya ido ya ganshi a hakan ya San da akwai abunda ke damunsa, ya mere baki domin a duniyar nan babu abunda ya tsana sama dashi." Gaidashi kawai yyi yawuce ya zauna akan kujerar da yasaba zama yaci gaba da aikinsa." Wani dogon numfashi yaji yaja da k'arfi, Wanda sai da mahmud yyi saurin juyowa ya kallesa, ya sanya hannu ya d'auki wayar dake a jiye a gabansa, Number sulaiman ya shiga kira, Sulaiman dake can cikin 'yan uwansa abokanan aikinsa suna aiki." Sai ganin kiran Alhaji Atiku yayi da Sauri ya d'auki wayar ya kara a kunnensa cike da girmama yake gaida shi." A taik'aice Alhaji Atiku ya amsa masa, Wanda yin hakan sai da gabansa ya fad'i." Yace "sulaiman duk abunda kakeyi kazo yanxun nan ina nemanka." Cikin girmamawa sulaiman yace "to ranka ya dad'e." Ya kashe wayar." Ba'ayi awa biyu ba sai ga sulaiman ya iso gaban Alhaji Atiku." Mahmud na ganin sulaiman ya kuma juyawa ya kalli Alhaji Atiku ya tabbatarwa kansa akwai matsala." Ya kashe kunne yana sauraren laifin da sulaiman yayi wanda har ya b'atawa Alhaji Atiku rai hakan." Sulaiman ya sarewa Alhaji Atiku cikin girmamawa da kwazo. Ya amsa masa tare da d'an sakin fuskarsa." Yanuna masa kujera alamar ya zauna." Sulaiman yaje ya zauna, Alhaji Atiku ya cire glass din idonsa ya kalli sulaiman da kyau yace "kasan dalilin kiran da nayi maka kuwa?" Sulaiman ya runsuna tare da girgixa kai yace "A'a ranka ya dad'e." Alhaji Atiku yyi murmushi, yace "ina tayaka murna kayi dacen macce kamila wanda tasan darajar aure ta kuma rik'e mutumcin ta na 'ya macce." Tabbas samun irin matar ka fareeda a cikin mata sai antona Karkayi ko kwanto a kanta, a duk inda ka ajiyeta kayi tafiyarka a fad'in duniyar nan ni na tabbata fareeda zata tsare mutumcin ta da aurenta." Mahmud ya zaro ido." Gaban sulaiman ya fad'i. Yace "ngd ranka ya dad'e." Alhaji Atiku ya kuma sakin dariya yace "d'auki wayarka ka kirata kafad'a mata cewa kadawo tasameka a office d'ina kana nemanta." Sulaiman bai musaba ya d'aga waya yakira fareeda dake harhad'a kayanta tana kuka Ammar, goye a bayanta domin ta d'auki d'amarar daga yau tabar wurin nan kenan gida xata koma gaban iyayenta." Sai ganin wayar sulaiman tayi. k'ok'arin saita kanta tayi dan kadda ya fahimci wata damuwa a tare da ita, wanda zata tayar masa da hankali yakasa yin aikin sa." Ta d'auki wayar had'ida sallama. Yanajin muryarta ya fahimci akwai abunda ke damunta." Yace "fareeda kisameni a office d'in oga ina jiranki." Bai jira amsarta ba ya kashe wayar." Cikin minti biyar ta ta iso office d'in, tana zuwa tayi ido biyu da Alhaji Atiku ta wurga masa harara, bata gaida shi ba, Ta kalli Mahmud dake zaune gefe d'aya yana rubutu amma duk ilahirin hankalinsa na wajensu." Tace "mahmud ina kwana." Sai a lokacin ya d'ago kai ya kalleta ya amsa mata had'ida tambayar ya Ammar?" Tak'i gaida Alhaji Atiku sulaiman yayi mmki zaiyi mata magana akan ta gaida shi, Alhaji Atiku ya katse masa hanzari da yace "malama fareeda ga wuri ki zauna." Tak'i ta zauna tayi tsayenta tana hararar sa. Cike da tsana." Da kyar ta bud'e baki tayi magana cikin muryar kuka tace "mazinaci baya da martabar da xai bani wuri na xauna." Sulaiman yayi saurin kallonta ya kuma juya ya kalli Alhaji Atiku cike da ayar tambaya a fuskarsa." Murmushi yyi ya kalli sulaiman yace "karkayi mmkin yanda kaji tana yimun mgna hakan da takeyi shi yake kuma sanyawa ina jinta a raina." Tun lokacin da na turaka inda kake aiki a yanxun, Nake bibiyar matarka akan ta amince mun na kad'aice da ita amma ta k'i." Nayi mata alk'awari iri iri har na k'ara maka girma na kuma mallaka maka dukiya mai tarin yawa, amma matarka fareeda tak'i amin cemun." Ni kuma Allah ya sanya min sha'awar matarka wanda a yanda nkeji idan ban kusance taba kamar zan mutu." To shawara gareka ga matarka nan a gabanka ka sanyata ta amince dani a yanxun na kusanceta, idan ba hakan ba kacire mun uniform d'in jikinka na koreka daga aiki." Idan kuma ka Amince na kad'aice da ita, To ka sanyawa rayuwarka gaba d'aya zuri'ar ku, Kun warke daga cikin k'angin talauci *hmmmmm talaka bawan Allah*😭😭 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_) 😅 Writteng By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *36* Ido Suleiman ya k'ura mashi cikin bak'in ciki da ta kaici idonsa ya cika da hawaye jikinsa ya soma rawa, Ya janyo fareeda ya rungumeta a jikinsa sai da suka d'auki minti biyu a haka snn ya janyeta a jikinsa." Ya sauke hular kansa ya ajiyeta a kan tebur d'in Alhaji Atiku ya cire rigar jikinsa ya ajiye masa akai ya dubeshi da kyau yayi masa kallon tsana yace "wlh dana bari ka kusance matata a gaban idona gara Allah ya amshi rayuwarka." Alhaji Atika na zab'i matata akan aikina, kuma kasani arziki da talauci duka na Allah, Allah ne, Shike bawa wanda yaso." Kana amfani da kujerar da Allah ya baka kana fasik'anci da matan aure, kasani ni sulaiman nine mutum na k'arshe da baxaka tab'a mntawa daniba." Matata tafiyemun komai a rayuwata mutum cin matata fareeda yafiye mun duk wani Abu da mallaka a rayuwata." mazina ci fasak'i wlh Allah ba zai barka ba, sai ka ga k'arshenka." Sai kayi mummunan k'arshe, Bara na fad'a mka magana ta k'arshe, ni da ka d'aukeni talaka har kakeso kayi amfani da talauci na domin ka ketawa matata handinta ka zalunceni, To kasani bana zalunci kuma duk Wanda ya zalunceni wlh Allah ba zai barshiba, bana boka bana malam amma KA rubuta KA ajiye yanda na ajiye aikina kai ma saika ajiye naka a lokacin da kake cikin jin dad'in sa." Ynda nacire uniform d'in nan a gabanka, hakan za'a mik'o maka takardar sallama daga aiki a gaban bainar jama'a." Sai a lokacin Mahmud ya wurgawa Alhaji Atiku kallon tsana, cike da k'unar zuci, Ya kuma kallon sulaiman yace "sulaiman barshi a hakan, Na tabbata abun da yyi maka bazai tab'a samun kwanciyar hankali ba." Ya rubuta mashi cak d'in kud'i miliyan biyu tare da wata takarda ya mik'a mashi "yace ga wnn kayi amfani dasu, Wnn takardar ka kaiwa Abba zankirashi a waya nayi bashi bayani." Kud'in da na baka kayi amfani dasu kasayi gida a cikin garin kano, da kaida matarka,Ku zauna Idan KA kaiwa Abba wnn takardar zai gane abunda nke nufi, zai yi amfani da ita ya d'oraka akan manajan kamfaninsa na sarrafa atamfofi na tabbata zakaji dad'i sosai Kuma xaifi maka wnn wulak'antattacen aikin mai cike da cin amana da zalunci da kuma son kai." Bantab'ayin nadamar kasan cewata a k'ark'ashin wnn azzalumin mutumin ba sai a yanzun." Idon Mahmud sukayi ja ya taso yazo har gaban Alhaji Atiku cike da b'acin rai, ya dubeshi ido cikin ido, yace kayi Arziki ni mai biyayya ne ga mahaifana, wlh da ba dan hakan ba Alhaji Atiku wnn ranar sai ka gane kuskurenka." A hakan kake tunanin zan aure 'yar ka har na had'a zuri'a da kai mazinaci Azzalumi mai Neman matan Aure?" A hakan kake tunanin nayi mka biyayya na d'aukeka a matsayin suruki Wanda zai aure karuwar 'yarka nakasasshiya Wanda tayi gadon hali irin naka?" Kayi kuskure Alhaji Atiku, domin kuwa duk abunda kake ciki duk halin da kake ciki da irin mugayen abubuwan da kake aikatawa ina sane dasu." Da sannu za'ayi walk'iya muganka a rana a lokacin ni da kaina zan kuma turaka a tsakiyarta domin ta axabtar da kai." Alhaji Atiku sai zarar ido yakeyi duk da sanyin Ac da ke cikin office d'in amma sai zufa yake fitarwa." Mahmud ya juya ya kalli Suleiman yace "abokina katafi ka sanya kayanka Ku d'auki hanyar kano, ya mik'a masa key d'in motarsa yace "kayi amfani da wnn kafin nazo kano." Godiya Suleiman zaiyi masa Mahmud ya d'aga masa hannu yace "ba lokacin wnn kai dai kawai kaje kayi abunda nace." Hakan sulaiman ya fito office d'in Alhaji Atiku yana mai tsine masa Albarka tare da matarsa FAREEDA." Mahmud ya dubesa cikin tsana yace "nima idan ka isa ka kureni daga bakin aikina a yau, Dama domin Abba da mommy nke wnn aikin domin farin cikin su ba wai dan ina ra'ayiba." Kuma idan har ka isa da 'yarka, kamar yanda mahaifana suka isa dani, idan har 'yarka tanajin maganarka kamar yanda nakejin maganar iyayena, ka fad'a mata ka kuma shaida mata ni mahmud bana sonta ta janye maganar aure na da take so tayi." Idan kuma tak'ijin maganarka tafi k'arfinka tak'i yi maka biyayyah to ni zanyiwa iyayena biyayya zan aure ta amma KA iya tabbatar mata da cewa, har k'ara tayi zaman gidan yari yafi mata dad'i akan ta zauna a gida na a k'ark'ashin inuwata." Yana kaiwa nan ya fita ransa a b'ace." Alhaji Atiku ya dafe kai ya rasa abunda ke masa dad'i, Idonsa yayi ja ya rasa abunda yake masa dad'i a duniya, Meyasa mahmud yake masa hakan ne?" Meyasa baya iya d'aukar masa mataki a duk irin abunda yake masa?" Mik'ewa yayi a fusace ya nufi gidansa rai b'ace da ya tuna da magagganun da yayi masa akan Yusra." Da shigarsa ya tarar da ita zaune a falo ta k'ure velume d'in TV sai wak'a take saurare tana kad'a kai, ta lura da shigowarsa amma sai tayi kamar bata ganshiba taci gaba da abunda takeyi." Ransa ya kuma b'aci, yaje wurin TV ya kashe, ya juyo ya kalleta, ta turo bki shi take kallo, tace "daddy meye hakan xaka kashemun TV ina tsakiyar kallona?" Rab'awa tayi ta gefensa zataje ta kuma kunnawa, Ya doka mata tsawar da bai tab'a yimata makammaciyar ta ba, yace "karki kuskura ki kuma kunna tv nan, idan kuma kika kunna to ranki idan yyi dubu sai ya b'aci." Ya wuce a fusace ya nufi d'akinsa had'ida fad'in ki sameni ina son magana dake." Cike da mmki take kallon daddy,tana shakkun wai kuwa shine daddyn nata?" Bayansa tabi ta sameshi a d'akin nasa kamar ynda yace, ta nemi wuri ta zauna a kusa dashi tana kallonsa tace "gani daddy." Ya d'aga kai ya kalleta yace yusra, Tayi sauri kallonsa jin ya ambaci sunanta rabonda ya yakira sunanta hakan har ta mnta." "Yusra umurnin nake bki ba wai shawara ba, daga yau bake ba mahmud ki fitar da mahmud a ranki domin kuwa bazaki aure shiba." Yau mahmud yaci mutumcina ya wulak'antani yayi abunda har na mutu bazan manta dashi ba, ya kuma yimun mgna akan cewa in har na isa dake nyi mki mgana ki rabu dashi." Yusra kifitar da Mahmud a ranki domin bazaki aure shiba." Kuka ta fashe dashi tace "daddy Mahmud shine farin cikina rabani da Mahmud tamkar rabani da rayuwata ne, daddy Mahmud ko kasheni zaiyi yayi gunduwa gunduwa da naman jikina, naji nagani zan iya zama dashi a hakan." Duk abunda Mahmud ya maka daddy tsakaninku ne bai kamata ka sanya alak'ar aure mu a cikiba, Wlh daddy muddun kayi sanadin da narasa Mahmud to kasani kashe kaina kawai zanyi kaima ka rasani." Zaro ido yyi waje cike da tashin hankalin kalaman da take fad'i ya janyo ta a jikinsa yana fad'in "yi hak'uri shalele karki kashe kanki indai akan Mahmud ne tunda kinji kingani kin Amince zan aura mki shi." Anan ya rungumeta ya shiga lallashinta har ta hak'ura, ranta yyi sanyi, anan take bacci yayi awon gaba da ita." Ido ya tsura mata yana kallonta shine dai a rayuwa bbu abunda yake so sama da yusra, Yana son Yusra yana son farin cikinta. Ya rasa dalilin da yasa Mahmud baya sonta." Kalaman mahmud ya tuna dasu da yace idan har 'yarka tanajin maganarka kamar ynda nakejin maganar mahaifana kayi mata magana ta janye maganar aurena da takeso tayi. Wato idan ba'a janye ba kenan haka yana nuna batajin maganar shi?" Wai meyasa mahmud yake fad'amin magagganu wad'anda idan yana gabana nakasa ramawa sai dai idan nadawo gida su dinga damuna a raina?" Meyasa idan mukayi ido biyu Da mahmud nakejina kamar bana cikin natsuwa ta musamman idan ya kafeni da manyan idanuwansa masu k'unshi da wani kalar kallo?" Hmmm lallai kuwa mahmud kana cin darajar shalele nayi maka wani kalar so idan ba hakan ba da tuni anmanta da labarinka a doron k'asa." Fareeda ta fad'o masa a rai Yaji wani irin kunci ya fara danasanin nunawa sulaiman maitarsa a fili a kan matar sa yanxun gashi nan sunbar wurin batare da yabiya buk'atar saba, a kanta." ***************** Akwana a tashi ba wuya a wurin Allah lokacin bikin su mahmud da yusra gaba tuwa kawai yakeyi, shirye shiryen biki akeyi, a gidajen nan biyu musamman a gidansu yusra, Duk da mahmud baya son auren bai nunawa mahaifinsa ba, ko wasuba, ko a fuskarsa baxaka gane ba, hatta ita Yusra bai nuna mata komai ba ya bar abun a ransa." Alhaji Atiku kuma jinsa yake babu Wanda ya tab'a aura da 'ya a duniya nan sai shi, kud'i yake kashewa sosai duk abunda shalele tace tana buk'ata saiya saya mata shi." Gida ya k'era mata Wanda yake shine, nagani na fad'a, duk ynda tace tana buk'atar gidan ya kasance ahakan akayi mata." Wanda mahmud shi kuma yana ganin cewa da gske auren za'ayi ya, ya gina gidansa wanda yake ra'ayi a ransa, kuma ciki ya keson ya sanyata." Shima gida ne ba laifi yyi kyau sosai." Tunda dijama taji labarin auren mahmud ta tsinci kanta da Jin haushi, hakan zata samu wuri d'aya gefe d'aya ta rakub'e tayita kuka tarasa dalilin nata nayin kukan." Cikin kwanankin auren duk ta rame ta fad'a saboda tunani idan kuma ta tambayi kanta dalilin yin kukan sai ta rasa amsa." Inda shi kuma Khalil sai dad'i yakeji yana murna ganin mahmud zaiyi aure yasan da zarar yayi aure dole a aura masa dijama ta zama tashi." Musamman lokacin da tsohuwa tazo Yaji tana ruwan masifa a kan wnn auren da zaiyi domin ita har ga Allah bata son auren tafison ya auri dijama wanda suka tashi suna son junansu tun suna yara." Abba yake bata hak'uri da banbaki yana nuna mata irin d'inbin Alherin da Alhaji Atiku yayi masa idan har aka hana Mahmud yak'i auren 'yarsa kamar anyi msa butulci ne." Harda Khalil wurin bawa tsohuwa hak'uri akan tayi hak'uri Mahmud ya auri Yusra." Ba yanda ta iya hakan ta hak'ura, akaci gaba da shirye shirye bikin dijama tana makaranta." Tana Addu'ar Allah yasa kar'ayi masu Hutu sai bayan an kammala bikin snn." Shirin biki kawai akeyi amma da zarar KA ganshi baka cewa akwai abunda yake damunsa dangane da bikin, yana so baya so bazaka iya zaganewa." Yusra tashiga kokwanto da mmki ko dai ya hak'ura ne yanxun yana sonta?" Tana mmkin yadda ya kyaleta ba fad'a ba cin mutunci hakan yasata a tunani da was_ wasi." Shin meye a ainahin a xuciyarsa?" ya hak'ura ne ko kuma..?" Anya?" Nasan mahmud miskilin kansa ne, dole akwai abunda ke yawo a kwakwalwar sa da zuciyar sa." Dan haka ta yanke shawarar fuskantar sa, nan ta tsala ado na sosai me Jan hankali ta nufi Inda tasan zata sameshi a area su ta ma'aikata." Taci sa'ar samunsa zaune ya d'ora k'afafunsa bisa table d'in da ke gabansa k'afarsa sanye da talkaman su irin na sojoji jikinsa sanye da uniform ko ciresu bai yi ba alamar bai jimima da dawowo ba, Yana karkad'a k'afa ya hard'e hannu a k'irji, shi kad'ai yasan yanda yakeji a ransa." Tayi ta sallama yajita ya kuma ganeta ya amsa sallamar amma ko ta inda take bai kallaba, balle yasan da mutum a wurin." Tana ganinsa a hakan sai da gabanta ya fad'i, taji wani kalar sonshi yana dirar mata a Zuciya tace amma sai ta dake tace "Hy sweet heart, ina wuni mahmud d'ina." Yyi bnza da ita kamar da bango take magana, ta saki zuwa ta gabansa tana fuskantar sa amma har yanxun bai San ma tanayi ba." K'amshin turarenta kad'ai ya isa ya kashe zuciya, amma mahmud tamkar gunki duk kyan nan tayi Wanda shi kansa yasan tayi kyau amma ko kallo bata ishisaba." Sam bata burgeshi saima haushinta da yakeji tare da tsanarta a zuciyarsa." Ai kuwa haushi ya kamata kyalenta da yyi a gashi a rywar yusra ta tsani kyaluwa." Ta fusata ranta ya b'aci ta shiga mita tana bala'i dan dai kawai ya kalleta ya kulata." Bai kulata ya mik'e yayi mata kallon banza ya ce, "Inaso kisan Mijin da zaki aura, mutum ne da ko fishina da b'acin raina baki kai in baki shi ba." Kina da lokaci har yanzun in kina so zaki iya tsira daga sharrin auren Mijin da bai sonki ba, Don kuwa baxaki iya jurar wulak'anci da zaki fuskantaba." Cikin muryar kuka tace "meyasa baxaka soni ba?" Me na rasa?" Duk abinda akeso ga macce ina da shi, kadubeni da kyau ta mik'e tsaye tana juyawa gabansa." Ya kalleta a wulak'ance yabata amsa kai tsaye yace "bakida komai, kije kije ki sake kallon kanki in kin duba da kyau zakiga ke d'in nakashasshiya ce, maccen da bata da asali mai kyau, maccen da ta gama tallan kanta da tsiraicin ta ga mutanen duk duniya ta hanyar mummunar shiga da kike, Maccen da take mu'amala da maza tamkar mata, Maccen da bata kishin kanta balle addininta, Mace mai jin kai, macce mai girman kai da nuna isa, macce fitinanniya mai jin tafi kowa, illolin dake tattare dake sunfi rashin illarki yawa." Ke baki isa kisa in k'i yiwa mahaifina biyayya ba, zan aureki amma ki shirya fuskantar mummunar rayuwa tare dani ba." Tabbas kina samun duk abunda kike so, amma ki sanyawa rayuwar cewa bazaki tab'a samuna ba, domin a duniya ba komai ake nema ake samun sa ba.' Yana gama fad'i ya mik'e ya fita a fusace zuciyarsa na k'una." Cikin muryar kuka tareda d'aga murya tace "saurara kaji gskya ka fad'a ni ina samun duk abunda nkeso a haka rayuwata take life style d'ina kai baka isa kasa in canja ba, Burina ya cika kuwa in dai na aure ka nayi nasarar sakaka aure na ko kana so ko baka so, nayi nasarar tursasa namiji kamar KA miskili mai nuna ba Wanda ya isa ya juyashi ko yasa shi ko ya hanashi auren macce da baya so, Kyauna kuwa ina da tabbacin ko ynxun bai burgeka ba nan gaba in na mallake ka zan fara birgeka, Tafice ta gabansa tayi tafiyarta ta gyaleshi cikin bakin ciki da takaici, Tabbas yusra tayi nasarar cutar da shi, ta samu yadda takeso amma fa bazan kyaleta ba dole itama nakasa ta a inda zaifi mata ciwo 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_) 😅 Writteng By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Bashir_) *37* *LAST PAGE* *SAI BAYAN SALLAH ZANCI GABA IDAN ALLAH YASA MUNA DAGA CIKIN MASU YAWANCIN RAI DA LAFIYA,* *INA KUKE FRIENDS D'INA KU MATSO KUSA KUJI DUK WNDA YASAN UMMU SAFWAN TA B'ATA MASA RAI DAN ALLAH KU GAFARCENI, ALLAH YA AMSHI IBADARMU YA INTAMU CIKIN INTATTUN BAYIN SA AMEEN*👏👏👏 Hidimar biki akeyi saura sati d'aya a d'aura aure." Dijama tana lissafe, kullum cikin kuka take da damuwa friends d'inta sunyi tambayar duniyar akan ta fad'i abunda ke damunta Amsar da take basu d'aya ce babu komai, itama ta rasa abunda yake sanya ta kuka da damuwa." Wasa wasa har dijama ta kwanta ciwo saboda damuwar da tasanyawa ranta." Duk ta rame tayi bak'i." Hidima akeyi gadan gadan ana saura kwana uku d'aurin aure Abba yaje makarantar domin ya d'aukota ayi bikin da ita." Yayi mmkin ayanda yaga dijama ta koma, hankalinsa ya tashi da kan shi ya d'auketa ya sanyata a mota ko gida bai nufa ba kai tsaye asibiti ya nufa da ita." Emergency aka nufa da ita aka bata gado tare da sanya mata ruwa had'ida yi mata allurar bacci." Sai da tayi bacci snn likita yashiga yi mata aune aune, karon farko ya gano damuwa ce tayi mata yawa har ta kusan haddasa mata da ciwon zuciya." Cikin mmki Abba yace "damuwa?" Ya Shiga tunanin a duniyar nan meke damun ummie?" Me ummie ta nema ta rasa a rayuwa?" Yasan dijama marainiya ce damuwar rashin iyayen baxai hadda samata ciwon zuciya ba, tabbas akwai abunda yake damunta Wanda take b'oye mana." Sai a lokacin ya tuna da bai sanar da kowa yazo da ita asibitiba." Mommy ya kira yake shaida mata a lokacin tsohuwa tana kusa tanji duk abunda ake fad'i a wayar tun kafin mommy ta kashe wayar tsohuwa ta mik'e tsaye tana salati tace shi kenan mamuda ya kashe mun dijama sai da nace karya kaita bak'ar makarantar can ta kwana amma ya kafe a can zai kaita to ai ga irinta nan sauran kad'an ta mutu ba dan da Allah yasa hassan ya tafi yau ba, da sai dai akawo mana gawarta." Mommy ta kashe wayar tace "inna ki kwantar da hankalinki ba laifin makaranta bane ciwo ne kawai Allah ya d'ora mata, ba kuma laifin mahmud bane." Kai tsaye hanyar waje tsohuwa ta nufa da mayafinta a hannunta duk ta rud'e." Khalil taci karo dashi ya shigo da mota yyi parking, Yana ganinta hakan mayafi a hannu da alama a rud'e take ya saki dariya yace 'yar tsohuwa sai ina kuma haka naganki a rud'e mayafi a hannu?" Kai tsaye ta wuce shi tana masifa, tana fad'in dan Allah matsa kabani wuri kake tambayata tunda ba ajiyeni kayiba. Ta nufi wurin motarsa tana Neman bud'ewa ta shiga." Dariya ya dinga yi mata har da duk'ewa yana fad'in "wai yau meke damun tsohuwa ne." Mommy tafito cikin shirinta zata tafi asibitin tana ganin tsohuwa tana k'ok'arin bud'e motar khalil dake rufe tashiga shi kuma yana gefenta sai dariya yake mata." Mommy ta doka masa tsawa snn yashiga hankalinsa tace "maxa KA bud'e mata k'ofa tashiga kaja mutafi ka kaimu asibity dijama aka bawa gado bata da lfy." Cikin tashin hankali ya xaro ido waje ai bai san lokacin da ya bud'ewa tsohuwa mota ta shigaba itama mommy ta Shiga da sauri ya shiga shima yaja motar da sauri ya nufi asibity." Abba shi kad'ai zaune kusa da dijama Wanda sai bacci takeyi da ka ganta zaka gane ciwon ya dad'e a jikinta." Waya yakeyi da mahmud yana fad'a masa halin da dijama take ciki, Wani irin razana mahmud yyi Wanda sai da abokanan aikinsa suka kallesa, Sai fad'in yake meyasa meta Abba?" me akai mata?" waya tab'a ta?" metake so?" Ajere yake yiwa Abba wad'an nan tambayoyin wad'anda bai San yana yinsuba." Ganin hankalinsa ya tashi Abba yace KA kwantar da hankalinka Mahmud da sauki ciwon ba wai irin sosai d'in nan bane." Cewa yyi no Abba gani nan tafe yanxun nan ya kashe wayarsa ya mik'e cikin hanzari ya Shiga motarsa bai jira umurni daga Alhaji Atiku ba domin Mahmud har jira yakeyi yyi laifin da za'a koreshi daga aikin yake so." Kai tsaye hanyar kano ya mik'a." Duk wayar da yakeyi Yusra na kusa dashi bai San tazoba, ganin yanda ya firgice a nan take yana waya da alamar akwai Wanda baya da lafiya a cikin familynsu ta bishi da kallo ta ce Allah ya sauwak'e." Tayi yafiyarta." Khalil yana yin parking a harabar asibitin bai ko jira su mommy suka fito ba, ya rigasu fitowa da saurinsa ya nufi inda yake tunanin an ajiyeta, tsohuwa da mommy suna bayansa biye, mommy na kallonsa cike da mmki." Kai tsaye d'akin ya nufa yana zuwa wurin gadonta ya nufa, da niyar ya rik'ata ya rungumeta, Abba dake kusa da gadon ya dakatar dashi da cewa "khalil wai meye hakan ne?" Turus yaja ya tsaya yana kallonta idonsa a kanta yace "Abba meke damunta ne?" Abba yace "sai kaje KA tambayi likita yyi maka bayani." Bani zaka tsare kana tambaya ba kamar Wanda ya aikoni." Tsohuwa ta turo k'ofa suka shigo tare da mommy kai tsaye wurin dijama ta nufa tana shafa gefen fuskarta tana fad'in "shikenan mahmud ya kashe mun ke, Dama sai da na ce ba na son makarantar nan amma aka k'i bin maganata sbda an d'aukeni tsohuwa 'yar k'auye to ynxun ai ga irin abunda nayiwa gudu kenan." Mommy da Abba shuru sukayi, ba fad'an tsohuwa ba maimaita magana. Jinini😊 Khalil yace "dan Allah tsohuwa bacci takeyi idan kinsan fad'anki zakiyi kifita daga waje karki Tayar da ita daga bacci." Ai kuwa kamar khalil ya hura mata wutar fasifa tashiga yi, "ubanka ne zai fita wajen bani ba, Kai tsayuwar me kakeyi a nan duk KA wani d'aga hankalinka sai kace Wanda aka cewa ta mutu." Bai tanka mata ba sai ma ya fita ya nufi office d'in likita domin ya tambaye shi meyake damunta." Likita yyi mashi mayani kamar yanda yyiwa Abba, Khalil ya fito yana mmki to me zai sanya dijama damuwa?" Hakan dai jiki ba kwari ya nufi d'akin da take a kwance, Kujerar da Abba ya tashi a nan yaje ya zauna had'ida tsora mata ido yana kallonta cike da tausayi." Jinsa yakeyi kamar yaje ya rungumeta yayi ta lasarta saboda so da k'auna da kuma tausayi ta da yakeji." Dijama kuma sai bacci takeyi, fuskarta tayi wani haske karan hancinta ya kuma fitowa ta rame sosai sai kuma ta kuma yin kyau." Awa uku suka kawo Mahmud garin kano, saka makon gudun da yakeyi baji ba gani kamar baya a hanyacinsa." Kai tsaye asibitin ya nufa inda Abba ya fad'a masa, kai tsaye d'akin ya nufa muradinsa shine ya ga halin da dijama take cikinsa." Yana shiga d'akin cikin wani taku, Wanda sai da ya dai dai ta natsuwarsa snn ya shiga da sallamar sa, Gaba d'aya ido ya dawo kansa cike da mmki, ya akayi yasani?" Murmushi yyi ya durk'usa ya gaida momy da tsohuwa, tare da yi masu ya mai jiki?" Mommy tace gata can tunda mukazo take bacci har yanxun bata farka ba." Har khalil ya gaji da zamansa ya yatafi ya dawo." Mik'ewa yyi ya nufi wurin gadonta, Ya k'ura mata ido cikin na tsuwa yake kallonta cike da tausayinta, ganin duk yanda ta rame ta fita hayyacinta, Yaja dogon ajiyar zuciya ya juya ya kalli mommy yace "mommy me likita yace "dan gane da abunda yake damunta?" Mommy tace "ban tambayi Abban ka ba, Tsohuwa da tayi shuru cike da jin haushin mahmud shiyasa ma a lokacin da yashigo da ya gaida ita ko amsa masa batayiba sai ma harararsa da takeyi Wanda shi kuma mahmud bai lura da hakan ba, domin ganin takeyi duk shine silar ciwon ta tunda ya kai ta makarantar bacci." Mik'ewa yayi ya nufi office d'in likita, Ya tambayi likita abunda yake damunta." Likita ya shiga fad'a masa abunda ya fad'awa Abba da khalil, Hannu mahmud ya dora a kuncinsa ya yi tagumi yashiga tunanin meyake damun dijama?" Me tasanyawa rayuwarta hakan ne Wanda har zai haifar mata da ciwon xuciya." Godiya yyiwa likita ya taso ya fito ya koma d'akin nata, Abunda basu saniba tun da Mahmud ya shigo d'akin k'amshin turarensa ya daki hancin dijama tun a lokacin ta farka daga bacci da takeyi." Zai shigo d'akin kenan ya hango khalil zai k'araso cikin saurinsa kamar baya ganin gabansa." Tsayawa yyi sai da ya k'araso a bakin k'ofar sann khalil ya lura da Mahmud, wani fad'uwar gaba yaji, amma sai yyi k'ok'arin saita kansa yace brother yaushe kazo?" Murmushi Mahmud yayi ya dafashi yace "d'an uwa rabin jiki, ai KA manta dani ko 'yar wayar nan KA daina kirana." Khalil yayi murmushi yace "ai ban isaba wlh na manta da kai exam ce ta ta hanani sukuni." Mahmud yace "eyya To Allah ya yabada sa'a." "Ameen khalil yace had'ida Rigan mahmud shigewa d'akin, Mahmud ya bi bayansa suka shiga a tare." Kai tsaye khalil wurin gadonta ya nufa, yana fad'in mommy bata farka ba har yanxun?" Mommy tace "bata farka ba, Ko sai ankira likita ne?" Shima mahmud wurin gadon ya nufa yana fad'in "ina ganin allurar da akayi mata ce ta bacci itace bata sake taba." Dijama najin muryar mahmud a kusa da ita, a hankali ta shiga bud'e idonta ta d'orasu a kansa, tana kallonsa idonta ya cika da hawaye." Shima idonsa a cikin nata ya kuma tsayawa daf da ita yana fad'in "sorry dijama sannu karkiyi kuka Allah shi zai baki lafiya, Ya sanya hannunsa ya shiga share mata hawayen fuskarta, yana mata sannu ji yakeyi kamar ya cire mata ciwon ya dawo da shi jikinsa, wani kalar tausayi yake mata Wanda bai San yana dashi ba." Nuni tayi masa da tanaso ta mik'e zaune, rik'ata yyi ta mik'e zaune had'ida gyara mata gashin kanta Wanda ya zubo ya rufe mata ido." Wani rad'ad'i khalil yakeji yanda yaga Mahmud yana rik'a dijama kuma mommy da tsohuwa duk suna zaune a gefe d'aya suna gani basuyi magana ba Amma ya lura idan shi yake mata haka da tuni an dakatar dashi, tare da nuna mashi b'acin ransu." Amma ga Mahmud nan komai ba'a ce masa ba har da wani gyara mata gashi yakeyi, a maimakon yaga bacin rai a fuskar mommy saima gani yyi tana kallonsu tana murmushi a fuskarta." Hankalinsa ya koma a wurin dijama a lokacin da take cewa "tana so ta sha ruwa." Da sauri khalil ya mik'a hannu ya d'auko ruwa ya tsiyaya mata a cup ya bata, Ko kallon inda yake batayi ba, mahmud take kallo gani tayi ya kuma yi mata kyau duk ya canxa mata kamar ba shiba." Khalil yaji haushi tare da bak'in ciki, ya nufi wurin bakinta da niyar ya bata ruwan tasha." Wata harara ta wurga masa mai cike da tsana snn ta kau da kanta gefe had'ida nok'e kafad'a alamar bata sha." Mahmud ya amshi ruwan ya nufi bakinta yace "kisha ko kad'an ne mana." Abun mmki sai ta bud'a baki mahmud ya yashiga bata ruwan sai da tasha ta k'oshi snn ta janye bakinta." Mahmud ya juya ya kalli mommy yace mommy da akwai abinci a zuba mata?" Mommy tace "fateema na kan hanya zata kawo yanzun." Khalil tsaye ya k'ame wuri d'aya wani kalar kishi yaji yana azalzalarsa, anan take idonsa ya soma rikid'ewa ya fara komwwa zuwa launin ja." Mommmy na lura da yanayin da yake ciki, amma sai tayi kamar bata ganeba." Suna hakan likita ya turo k'ofa yashigo, ya sameta hakan alamar sauki ya samu da mmki yake tambayarta ya hakan?" Murmushi kawai tayi, bayan ya kuma yi mata aune aune ya ga gaba d'aya ciwon zuciyar ya sauka, Murmushi kawai yyi ya kalleta yaga ynda mahmud yake bata kulawa kamar mata da miji, Murmushi ya kuma yi Domin ko ba'a fad'a masa ba yasan wnn dake zaune shine silar damuwarta." Likita yyi gyaran murya yace "ya kamata kowa ya watse ya koma daga waje abar mutum d'aya Wanda zai kula da ita, domin tana buk'atar Hutu." hakan yyi dai dai da shigowar Abba da fateema d'auke da kulolin abinci." Mommy ta mik'e tsaye ta kalli tsohuwa tace "inna waza'a bari a wurinta ya kula da ita?" Abba yace "mahmud ya tsaya ya kula da ita kafin zuwa anjima, Khalil najin hakan yyi saurin juyawa ya kalli Abba da rinanun idanunsa, Abba shi baima lura da yana wurinba. Sai a lokacin ya lura da shi da sukayi ido biyu." Abba yace "khalil me kakeyi a nan KA wani tsaya masu a kai, fito kaje massalaci ga sallah magariba can ana kira." Tsohuwa tace "ai kuwa shima Mahmud d'in bai kamata a barshi a wurin ba saboda idan aka barshi kuma k'ara sata zaiyi, Mahmud ya sanya dariya yace "tsohuwa kifita a harkata kinga ko da nazo ban kulaki ba, kema ya kamata ki kyaleni kamar ynda na kyaleki." Tsohuwa tace "kai d'in banxa, Dole KA kyaleni tunda Kasan abunda kayi, saboda mugunta iri taka, kai a makarantar kwana kayi karatu ne?" Dariya mahmud yasaki bai kuma kulata ba, dijama najin tsohuwa ta dage sai mahmud ya fita ya bar d'akin, sai dai ita ta zauna tayi jinyar tata." A hankali ta koma ta kwanta a kan gado ta janyo hannun mahmud ta rik'e gam had'ida lumshe idonta ta rufe su." Abba na ganin hakan ya saki murmushi irin nasu na mnya ya bud'e k'ofa ya fita, mommy ta bi bayansa, Likita ya kallesu yyi murmushi tunaninsa ya zama gaskiya, Ya kalli tsohuwa da bata lura da abunda ke faruwa ba yace "tsohuwa ya kamata ki shafawa kanki lafiya domin Wanda kike jinya ta zab'i Wanda takeso ya zauna a kusa da ita." Sai a lokacin tsohuwa ta lura da ynda dijama ta rik'e hannunn mahmud GAM kamar Wanda zai tsere mata. Tsohuwa ta mere baki tace indai mahmud gaki gashi Dafe da banjo khalil ya bar wurin domin shima ji yakeyi zuciyarsa tana wani harba masa saboda wani kalar rad'ad'i da yakeji." A tare suka bar d'akin tare da tsohuwa sai masifa takeyi da dijama a cewarta ta zab'i mahmud Wanda yake gana mata wahala yake dukanta ta barta." Masifa kawai takeyi tanufi wurin mommy da Abba suka shiga bata hak'uri, Ta gabansu Abba khalil ya wuce ya nufi motarsa ya figeta da k'arfi Wanda gaba d'aya hankalin mutanen dake cikin asibity ya dawo kansa, cike da tsoro mutane suka bishi da addu'a Allah ya sauke shi lafiya. Abba na ganin hakan hankalinsa ya tashi shima ya shiga tashi motar ya bi bayansa." Ido tsohuwa ta zaro waje cike da ayar tambaya ta kalli mommy tace "Hajiya Bilkisu shin wai meke damun khalil ne shi kuma?" Mommy tace "wlh inna nima kaina bansan abunda yke damunsa ba wani lokacin sai yyita wasu abubuwa gashi nan dai." Tsohuwa tace "to Allah ya kyauta ya kamata shima akaishi wurin likita ya dubashi daga ganinsa akwai abunda yake damunsa." Gudu khalil yakeyi har baya ganin gabansa, Allah ne kawai ya tsareshi ya kaishi gida lafiya." Yana yin parking Abba shima yana tsayawa da tasa mota, A tare suka fito, Abba ya nufeshi a fusace ya d'aga hannu ya kwad'a masa mari har sau biyu." Yace "bakada hankali be?" Kake gudu da mota haka akan titi baka damu da rayuwarka bane, Ya mik'a mashi hannu yace bani key d'in motata, tunda bakasan dajarar rayuwarka ba." Khalil ya dafe kunci cike da b'acin rai da bak'in ciki yace "duka a gidan nan ni kad'ai aka tsana, nikad'ai ake nunawa rashin so ya kamata akashe ni kawai kowa ya huta." Abba ya bishi da kallo yace "khalil mu mahaifan KA mune bama sonka?" Ni kake fad'awa magana?" To nagode." Abba ya koma mota ya shiga ya ya nufi asibity." Dijama kwance a kan gado hannunta rik'e da hannun mahmud Wanda shima ya tsinci kansa da kasa cire hannunsa daga nata sai ajiyar zuciya suke saukewa a tare." A hankali ya janye hannunsa daga nata ya wanda yasa tayi saurin bud'e idonta sukayi ido biyu dashi idonta cikin nasa wanda ko wannensu ya kasa d'auke ido da ga kallon d'an uwansa." Cikin jarunta ya tashi ya daga kan kujerar da yake ya koma gefen gado a kusa da ita ya zauna, still idonsa a kan nata suna kallon junansu, murmushi ya sakar mata had'ida hura mata iska a ido yace " wnn kallon fa na meye?" Runtse idonta tayi tana mai sakin murmushi, a fuskarta, Sunkuyawa yayi yasanya hannunsa ya shiga gyara mata gashin kanta. Da ya kuma zubowa a gaban goshinta, tare da Shafa beautiful face d'inta, K'amshin turarensa ya daki hancinta, bugun numfashinsu yana mugun numfashin junansu." Gaba d'ayansu suka tsinci Kansu cikin wani yanayi mai wuyar misaltuwa, D'an k'aramin bakinta yagani yana motsi tana murmushi, bai San lokacin da ya tsinci kansa da d'ora nashi baki akan nataba ya sakar mata kiss." Ko mai ya tuna oho yayi saurin tashi daga kan gadon ya dawo kan kujera ya zauna tare da saita kansa. Ya kira sunanta a hankali ta bud'e idonta tana murmushi ta kallesa, Yace "likita yace ciwon zuciya yake son kamaki, meyake damun?" Me kika nema kika rasa a duniya?" Ko akwai wani Abu da kikeso wanda har kike iya b'oye shi a ranki baki iya fad'a wanda har zai haifar mki da ciwon zuciya?" Ko aure kike so?" Tayi saurin girgiza kai had'ida turo baki, alamar shagwab'a." Ko kinfara soyayya ne saurayin yace baya sonki?" Idonta ya cika da hawaye tace "A'a wlh yaya." Ya kafeta da ido yace "karkiyi mun kuka, kifad'a mun kawai abunda yake damunki." Tace "wlh yaya ba komai k'azafi ne kawai likita yake mun." Yayi shuru na d'an wani lokaci snn ya nisa ya kira sunanta yace "ki daina sanya damuwa a ranta, idan kina buk'atar wani abun kiyi mun magana zanyi maki shi komai girmansa komai tsadarsa kinji ko." Ta d'aga kai alamar "to." Yayi murmushi yace "yawwa 'yar k'anwata Allah ya baki lafiya." Tayi "murmushi tana kallonsa, Snn yace "bara nayi sallah na dawo, Tunda naga ke bakyayi." Taji kunyar abunda yace "tayi saurin rufe fuskarta tana murmushi." Washe gari sauki ya samu ga dijama likita ya rubuta mata takardar sallama, Suka nufi gida da zuwansu gida batare da b'ata lokaci ba mahmud ya shiga yi masu shirin zuwa Abuja domin saura kwana biyu a d'aura aure sa KA San cewar ya saya wa su mommy gida wanda zasu sauka a cikinsa a can Abuja Hakan kuwa akayi suka d'unguma gaba d'ayansu har da Abba khalil ne kad'ai yace shi sai gobe zaixo, tare da abokinsa Ahmad, Dukansu suka shiga jirgi suka nufi garin Abuja." ******************** An d'aura Auren mahmud da Yusra akan sadaki naira dubu d'ari biyar, Inda ansha shagalin biki musamman b'angaren gidansu Yusra." Anyi wa Yusra jere a gidan da mahmud ya saya da kud'insa gida yyi kyau sosai biki na yar gata shalelen daddy." Duk dinner da akayi dawani Abu can da sukeyi mahmud ko lek'a wurin baiyiba yana kwance a d'akinsa cikin bak'in ciki da k'unci." Inda itama dijama daurewa kai takeyi tana shiga mutane amma jinta takeyi kamar ta fad'i saboda damuwa." Khalil kuma ansamu abokanan Amarya yan hannu sai murza barikinsu sukeyi dashi da Ahmad." Duk wanda yaga Yusra yasan tana cikin farin ciki ta mallaki abin sonta farin cikin rayuwarta." Tun dare aka kawo Yusra gidan angonta mahmud, Wanda tasha gyara na fitar Arxiki domin ta d'auki niyar sai ta mallaki mahmud ko yana so ko baya so." Ta rigada da ta gama tsuma jikinta da gyara yadda ya kamata ba irin shirin da tanadin da bata yiwa wnn dare ba da mijinta da ma rayuwar aurenta gaba d'aya." Tunda mahmud ya saka ko Kansa a falon gidan Wanda yake b'angarensa mallakinsa yaji wani irin k'amshi mai kashe zuciya da ta da hankali yana shigar sa yana ratsa shi, Tuni yaji jikinsa ya mutu ya tsinci kansa cikin wani irin hali na son kasancewa da mace." Wnn jarabben k'amshin yaji yana d'aga masa hankali, Ya dafe kai tare da rufe ido yana tunani a hankali yake tafiya, sai kuma jin wani sabon k'amshi na daban yana ratsashi, runtse idonsa yyi had'ida bud'ewa. Hannu yaji yana bin jikinsa ana shafashi tare da wani sabon k'amshi na daban, Hakan yasa yyi saurin juyawa dan ganin ko waye." Yusra ce tsaye gabansa tana yauk'i tayi wani irin bala'in kyau tare da shiga mai d'aga hankali da tsuma zuciya tana masa wani irin salo tare da murmushi mai jan hankali." Ido yasa mata yana kallonta daga sama har k'asa duk inda macce ta kai tq kawo Yusra ta wuce hakan, Ga wani salo mai tab'a zuciya da jiki da take masa to amma Sam baya jinta a zuciyarsa ko kad'an saima tsanarta da yakeji. Duk kau da kai da bala'in namiji da jarumtar sa bai isa ya kau da kai akan Yusra ba musamman ma a yanayin da take yanxun wani irin sexy dress da ta saka mai ta da hankalin." Mahmud bai kauda kai gareta ba kamar yadda ta zata sha wuya kafin shawo kansa da Jan hankalinsa, Sai taga tun a matakin farko ta tafi da imanin sa ya biye mata yana mqta wani irin Shafa da sarrafa jiki wanda yafi wanda ita take masa." Bata San cewa bayan jarunta da halitta mai kyau da Allah ya masa ba, yana da wani irin sirrin da duk 'ya macce da ta samu miji irinsa yana sarrafa mata jiki haka to bata da sauran wani damuwa a duniya." Tabbas yasan sirrin tafiyar da jikin macce. tuni ya gama rud'ata ta fita hanyacinta tana fitar da wani irin numfashi mai cike da shauk'i da sha'awa son kasancewa da shi." D'agata yyi cak tana wani irin yauk'i da fitar da numfashi mai ta da hankali mai sauraro, d'aki ya nufa da ita ya jefa ta bisa gado ya ci gaba da sarrafata jikinta ya gama mutuwa bata ko iya motsin kirki ba abin da take buk'ata illa taji mahmud a jikinta." A lokacin da ta gama fita hayyacinta sha'awarta ta kai k'ololuwa wurin tashi ya zame jikinsa daga nata tare da mata wani mugun kallo ya juya yayi tafiyar sa ya fita ya bar mata d'akin." Mahmud don Allah kar kai min haka." Bai saurare ta ba Ya mik'e ta bishi tana manne masa yayi saurin yakice ta ya jefar sai da tafad'i k'asa, tasa masa kuka." Mahmud zan mutu in ka kyale ni a wnn halin. Zan mutu. Mahmud ka taimakeni ni ga soyayyqrka ga sha'awarka ta d'aga min hankali fiye da tunanin KA." Ya juyo ya kafa mata idanun da suke k'ara haukatata tuni ta k'ara rikicewa ya k'ara haukatata tuni ta k'ara rikicewa da shi." Ta zurawa labbansa da faffad'an k'irjinsa ido tana kallo tana jin wani irin abu a jikinta hankalinta na kuma tashi." Kuka takeyi sosai tana rok'on sa ya kasance da ita tasamu sauk'in abinda takeji." Mugun kallo ya mata yace wnn abinda da kikeji sai dai ya kasheki ba wnn Daren kad'ai ba a ko wanne dare a kowanne lokaci da yanayi a cikin gidan nan haka zaki kasance cikin shauk'i da sha'awa baki da wanda zai kawar maki da ita, Hakan zakiyi ta kasan cewa har sai ranar da kika gaji kika hak'ura da aurena, Kije ki nemi wanda kika San zai iya kashe maki wnn wutar sha'awar da kullum sai na kunna miki ita a gidan nan sauk'in ki d'aya kiyi nesa dani zaki samu sauk'in jarabar dake damunki amma muddin kikayi kuskuren zuwa gabana zaki ci gaba da kasan cewa cikin wnn halin." Ina so kisani har abada ba komai ake nema ake samuba,a rayuwa Ni mahmud har abada ba baxaki tab'a samuna ba." Shalele kike ko meye sunanki tun da har kina iya Neman Abu kuma ki sameshi ki bugawa mahaifinkin waya ki fad'a masa cewa a buk'ace kike." Yana gama fad'i ya shigewarsa d'akinsa, yace "bazan rufe k'ofa ba in kina nemawa kanki wani tashin hankalin ki biyo ni." Da gudu ta bishi tana fad'in " KA tausaya mun mahmud sai ta so ta shiga d'in sai kuma dawo Baya tana magiya." Ta duk'e k'asa tana murk'ususu wutar sha'awar mahmud tana Azalzalarta Cikin hasata tace "sai na samu abinda nkeso mahmud ni ba mazan da nake muradi a waje a yanzun, mijina nakeso kuma shi nake sha'awa da muradi." Mahmud sai na sameka sai KA kusanceni sai na mallakeka, Sai na mallaki zuciyarka da gaggar jikinka ko ta tsiya kota arziki ko ta bala'i kota girma ko arziki KA saurara KA gani." Yyi mata wani matsiyancin kallo yace "Abbanki zaki fad'awa ya fad'awa babana cewa nak'i kwanciyar aure dake, yasani na kwanta dole dake?" Ko boka zaki bi ko malamai Idan kina tunanin hakan kinyi a banza domin kuwa baki San ko waye mahmud." Tasowa yyi ya zo daf da ita ya janyota ya rungumeta ya sanya harshensa a kunnenta ya shiga wasa da shi cikin wani salo, ai kuwa ta kuma birkicewa tana fitar da wani numfashi sama sama snn daga k'arshe ya yi jifa da ita gefe ya rufe d'akinsa yana jiyo nishinta da magiyarta." 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_ ) _BARKA Da Sallah my friends da fatan kowa yayi sallah lafiya cikin Aminci, Allah ya k'arb'i ibadunmu_ *Dedicated to* *Autar Ummah* *Manshart* *Mariam Tijjani* *Mum Muhibbat* *Maman Fatima* *Maman Sadeeg* *Sarah* *Billy Shantaly* *Aisha A mohd* *Biebedie* *Salma* *hafsy Mijina* *Leemart* *Maman Elham* _Da duk wad'anda ban ambata ba kuna raina da fatar kunyi sallah lfy?"_ *38* Nishi takeyi mai had'e da gurnani idonta a lumshe cike da sha'awa." Da kyar ta d'aga kai ta kuma kallon faffad'an k'irjinsa Wanda ya ke kuma ta yar mata da wutar sha'awarsa, tayi k'arfin hali cikin zafin zuciya tace "Ba boka ba malami ba kuma zan fad'awa daddy naba, amma namaka Alk'awarin sai na samu abinda nakeso daga gareka." Wani kallo ya kuma watsa mata mai d'auke da manufar bakida hankali, Yace "Ina nan ina jiranki Yusra inga ta inda zaki mallaki ko da k'ara min yatsa na balle gangar jikina da zuciyata, kina da aiki babba kifitar min daga b'angare ina son inyi bacci." Ganin bata niyar tafiya ya turo k'ofa ya rufe da k'arfi tareda wurga mata harara cike da tsana da kyamata." Kai tsaye toilet ya shiga ya sakarwa kanshi ruwan sanyi tare da sauke ajiyar zuciya, Yana tunanin abubuwan da zai dinga yiwa Yusra da zai sanyata da kanta zata nemi rabuwa dashi." Wanka yakeyi yana jiyo sautin kukan ta tare da magiyarta a k'ofar d'aki tana dukan k'ofa a kan ya tai maketa ya kusance ta ko sau d'aya, ne, ya fitar da ita cikin matsananciyar sha'awar sa wadda take addabarta takeji idan bai d'add'ana mata zumarsa ba a wnn Daren a yanda takeji bazata iya kai safe ba." Ganin baya da niyar taimaka mata bare ya ji tausayinta hakan ta hak'ura ta nufi b'angarenta mararta na mata ciwo sai murk'usu takeyi." A wannan daren Yusra tayi kwanan bak'in ciki da b'acin rai Wanda bata tab'ayi ba tunda uwarta ta haifeta, tashiga damuwa sosai kuka takeyi tana dukan gado, jitakeyi kamar ta d'auke numfashi a she aduniya akwai abunda zata nema ta rasa?" Meyasa daddy yayi mata k'arya yace duk abunda take so zata sameshi." Ta d'aga murya da k'arfi cikin muryar kuka tace "daddy ina son Mahmud kazo kabani mahmud, Mahmud ya zama nawa ya kusance ni a Daren nan." Hakan ta cigaba da kukanta, har tagaji tayi shuru ta Shiga k'ullawa, ta kunce ta sak'a wancan duk inda ta b'ullo sai taga ba fita." Duk yadda ta d'auki Mahmud ya wuce hakan, Namiji ne namijin gaske kuwa ba k'aramin Abu ne zai iya tab'a shi ba." Babban bak'in cikinta yadda soyayyarsa da sha'awarsa ke nuk'urk'usarta, hakan ta kasance tsawon dare ba bacci ta kunce ta k'ulla, bata da yadda zata samu sauk'i sai dai ta rufe ido tana tuno yanayin da Mahmud yasa ta ciki a lokacin da yake sarrafa jikinta." A b'angaren Mahmud shima baiyi bacci ba, babu abinda yake tunani sai dijama a lokacin da yakeyiwa mommy sallama tana kusa da ita gani yayi ta sunkuyar da kai k'asa takasa had'a ido dashi hawaye na zuba a fuskarta." Meyake damun dijama take kuka?" Me akayi mata ne Wanda take shiga cikin damuwa, kadda ciwon zuciyarta ya tashi." Da sauri ya lalubo wayarsa domin yana son ya San halin da take ciki a yanzun number ta yashiga kira Wadda yake tinanin iyanzun tayi bacci." Dijama kuma tun lokacin da mahmud yayiwa mommy sallama ya tafi, Ta tsinci kanta cikin tashin hankali da damuwa, wanda ta rasa dalilin shigarta." Kuka takeyi sosai fateema tayi tambayarta abinda ke damunta, Kanta ke ciwo kawai tace mata." Misalin k'arfe 2;30am kowa a gidan yyi bacci amma bnda dijama dake aikin kuka, tana tunanin yaya mahmud yau ne Daren farko sa yana can tare da matarsa cikin farin ciki." Wayar ta taji ta d'auki ringing a k'ark'ashin pillow, da kyar ta mik'a hannu ta d'auka tana mmkin waye mai kiran nata a cikin Daren nan?" Sunan yaya mahmud tagani a kan screen d'in wayar, Wata kalar ajiyar zuciya taja da k'arfi tasaki murmushi, kafin ta d'auki wayar har kiran ya tsinke." Can kuma wani kiran ya kuma shigowa, da sauri ta danna wayar ta kara a kunnenta, gaba d'ayansu suka sauke ajiyar zuciya a tare snn..... 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_ ) *39* Sai da suka d'auki tsawon minti biyar a hakan duk kaninsu suna jin saukar numfashin junansu a waya." Snn mahmud yaja wata doguwar ajiyar zuciya Wadda ta sanya Dijama saurin runtse idonta ta lalubo pilow ta rungume a jikinta." Da kyar ta bud'e baki Cikin dasanshiyar murya tace "Assalamu Alaikum." Jin sautin muryarta d'auke da sallama yasa shi yyi saurin mirginawa daga kwanciyar da yake Zuwa rufda ciki snn ya amsa mata sallamar." "Me yasa bakiyi bacci ba?" Kin kuwa San ko k'arfe nawa yanzun?" Shuru tayi batayi magana ba, tana tunanin to shima mai ya hana shi yin baccin bayan yau ne daren farkonsa tare da masoyiyarsa." Jin tayi shuru, ya kuma nisawa ya kira sunanta cikin kulawa "Nana Khadija meyake damunki kike shiga cikin damuwa?" Me kikeyiwa kuka d'azun a lokacin da nake yiwa mommy sallama?" Me kike so?" Me yake damunki wanda yake sanyaki shiga cikin damuwa Wanda bazaki fad'awa kowa ba daga ciki kuwa har dani." Shisshikar kukanta yaji yana tashi a kunnensa, A razane ya mik'e zaune cikin tashin hankali "Meya faru?" Ki fad'amun abinda yake damunki Wanda yake sanya ki damuwa kike kuka." Cikin da sasshiyar murya tace "ba komai yaya." K'arya kikeyi dijama akwai abinda yake damunki, Karki manta da Wanda kike magana kike fad'amasa haka, Muhmud ne Wanda ya reneki kamar yanda kika San uwa tana renon d'anta, ya ciyar dake ya shayar dake na kuma goyaki a bayana, to kisani nafi kowa sanin farin cikinki da damuwarki." Nafi kowa sanin jin dad'inki da rashinsa, nasan abinda kikeso da Wanda bakyaso, nasan farin cikinki nasan bak'in cikinki." Dijama akwai abinda kikeso Wanda kika kasa fad'i har yake Neman ya jefaki a damuwa." Ki fad'amun shi, komai girmansa komai kud'insa komai mahimmancinsa nayi maki Alk'awarin a duk inda yake a duk inda ake sayar dashi ko ake nemoshi nayi maki Alk'awarin zan kawo maki shi domin farin cikinki Kukanta ya tsanta tayi saurin kashe wayar gaba d'aya ta jefar da ita a gefen pillow taci gaba da kukanta." Kiran wayarta yayi yajita a rufe, Duk hankalinsa a she yasan tana can babu abinda takeyi sai aikin kuka agogon bango ya d'aga kai ya duba yaga k'arfe uku saura minti goma dare yyi sosai, Jinsa yakeyi kamar yaje ya lallasheta tayi shuru ta fad'a masa damuwarta." Hakan dai ya hak'ura ya kwanta cike da tunani da damuwa halin da dijama take cikinsa a halin yanzu." ****************** Washe gari tun k'arfe 8am ya shirya cikin wata dakakkiyar shadda Wanda ta k'arfesa yayi kyau iya kyau sai k'amshin turare yake fitarwa, ya fito, ya tarar da yusra zaune a pallow taci kwanliya cikin wasu k'ananun kaya wad'anda sukayi mata kyau Sosai rigar gaba d'aya k'irjinta a waje yake haka k'asan rigar duka cibiyarta a waje." Tana ganin fitowar mahmud Wanda Dama shi take jira yafito ta nufeshi ta rungumeshi tare da sauke ajiyar zuciya." Kallo d'aya Mahmud yyi mata cike da tsana yayi saurin cireta daga jikinsa tare da jefa ta a kan kujera yayi tafiyarsa." Kai tsaye gida ya nufa masaukin SU mommy, Da sallama ya Shiga gaba d'ayansu suna kan dining suna break fast, Tsohuwa kuma tana kan kujera sai masifa takeyi a kan tunda suka taho garin Abuja bata sanya Khalil a ido ba." Abba sai hak'uri yake bata yana kuma kwada kiran wayar Khalil ko Allah zai sa ya sameshi, amsa d'aya ce wayarsa a kashe take." Khalil yana can cikin hotel tare da abokinsa Ahmad hankalinsa a kwance 'yan mata uku ne a kansa ko wacce da inda take tab'awa a jikinsa, Shima hakan gaba d'ayansu sai sarrafasu yake cike da kwarewa, domin dukansu yana jinsu a dai dai a yanda yake son macce ta kasance." Mahmud Ya durk'usa k'[8/2, 1:12 PM] El-hajj✨✨✨: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_ ) *wnn shafin gaba d'ayansa nakine Queen Mary UMMU SAFWAN nayinki kamar yanda kike yinta* *40* Tsohuwa ta zaro ido tare da rik'e baki tace "yau naga ikon Allah, D'abi'ar yahodawa a gidan nan?" abinda nake gani a TV nake tsinuwa akansa yau gashi a gaban idona. Talkaminta ta lalubo ta wurgawa khalil tace "kai saketa Dan ubanka, KA ajiyeta nace, KA wani rungumeta a gabanmu kamar zaka mai data a ciki." Dijama najin hakan tayi saurin bud'e idonta sukayi ido biyu da Khalil tayi saurin fisge jikinta daga gareshi ta shiga ja da baya tana wurga masa kallon tsana, da gudu ta nufi d'akinsu kai tsaye ta fad'a kan gado ta fashe da kuka." FATEEMA dake zaune akan madubi tana kwalliya ta juya ta kalleta tashiga tambayarta abinda ke faruwa, Dijama tayi banza da ita taci gaba da kukanta, a ranta kuma tana tsinewa Khalil rungumar da yyi mata a gabansu mommy da Abba da kuma yaya mahmud Tsohuwa ta kuma wurga masa harara tare da tsino baki tace "Harda wani zabura kakeyi domin katarota zata fad'i, kana tunanin Kafi mamuda sonta ne, da kake k'ok'arin tureshi wurin tarbota." Khalil ya juya ya kalli tsohuwa yace "tsohuwa matsala tsohuwa fitina, tsohuwa jaraba, inbanda sa ido irin naki meye laifina a ciki domin kawai na taimaki k'anwata zata fad'i don gudun kadda taji ciwo." "Kai dallah rufemun baki marar kunyar banza da wufi Ai duk laifin Hassan ne sai da nace ya had'a da kai da mamuda ayi maku aure yace kai baka isa aure ba." To ai ga irinta nan idan kaje kajanyo masa magana ai sai yasan yanda zaiyi da kai." Nidai idan zan koma k'auye k"afata k'afar dijama da ita zan zantafi Dan banga abinda ake tsinana mata a nan ba in banda mugunta." Khalil yaja baya da sauri yaje kusa da Mahmud ya zauna yana fad'in "A'a tsohuwa karkiyimun baki, duka duka ni shekarata nawa da za'ayimun aure, ni karatu nakeyi so nakeyi sai nafara yi maki Allura da kaina snn zanyi aure." A lokacin matar da zan aura ta kammala karatunta." Tsohuwa tace "sai dai kayiwa Hassan gaya can a zaune Allurar ba dai niba." Abba ya nisa daga kallon da yakeyiwa khalil tun lokacin da ya rungume dijama yana karantar wani abin a tare dashi." Ya shiga maganar zuci Ko dai maganar mommy gaskiya ne da take cewa ayiwa Khalil aure." Wata zuciyar kuma tace "khalil nawa yake, meyasani a cikin aure, Kawai taimakon k'anwarsa yyi batare da wata manufaba." Mommy kuma tasan abinda yafi wnn ma khalil zai iya, Sai dai ta furta a zuciyarta tace Allah ya shirya." Abba yace "Allah khalil mudun ina kusa da kai idan KA kuma bari inna tana magana kana mayar mata sai na matuk'ar sab'a maka." Sun kuyar da kai yayi yace Abba ayi hak'uri bazan kuma." Snn ya durk'usa ya gaidasu suka amsa amma banda tsohuwa da sai masifa takeyi tana harararsa Juyawa yayi ya gaida mahmud da ke ta faman dannar waya gaba d'aya ya rasa abinda yake masa dad'i, jiyakeyi zuciyarsa na suya. Da kyar mahmud ya d'aga kai ya dubeshi yana murmushi ya amsa masa tare da tambayar abokinsa Ahmad da suka zo a tare, Yace yana can masauki bai tashi daga bacci ba, nima tsohuwa nan ce ta tayar dani." FATEEMA ce ta fito tayi kwalliyar cikin atamfa wanda tayi mata kyau, ta durk'usa ta gaida mahmud da khalil, Snn ta dubi mommy tace mommy mun shirya." Mommy tace "ina ita ummin take ne?" Fateema tace "tana d'aki yanzun zata fito Bari naje na kirata." Ta juya ta nufi d'akin." Lallashin dijama tashigayi tare da kwantar mata da hankali ko da dai bata San abinda takeyiwa kuka ba, amma idan da sabo ta saba da ganin kukan dijama a ko da yaushe a ko wane lokaci, har mamaki takeyi kamar ba dijamar da tasani bace jaruma mai fitina Wanda kafin kaga zubar hawayenta aikine babba." Hakan ta lallashe ta tasamu tayi shuru ta gyara mata kwalliyarta sann suka fito." Mommy ta dubi mahmud tace gidanka zamuje muyiwa matarka sallama daga nan sai su gaisa da inna domin yau da la'asar zamu koma gida." Murmushi kawai yayi sai a lokacin ya tuna da yana da wata mata, Ya mik'e tsaye yace "to mommy naso kubari sai an kwana biyu koda zaku koma gida." Tsohuwa tayi "karaf tace to bazamu bari ba yau zamu tafi gida, Kuma nayi iya tabbata maka dijama bazata koma makarantar kwanan nan Wanda ake shanye jinin mutane kai nafa fad'a maka k'afa ta k'afarta a tare zamu koma k'auye muci gaba da zamanmu kamar yanda muka saba, Diba ka ga yarinya duk ta rame ta kod'e kamar wacce batada jini ajiki wnn zaluncin da mai yayi kama." Ta gefen ido mahmud yake kallon dijama da ke zaune a kusa da mommy, Snn Abba yace "ai tunda kowa ya shirya sai mutashi mutafi." Mota biyu suka shiga da motar Abba da motar Mahmud kai tsaye gidan mahmud suka nufa." Da sallama suka shiga gidan amma ba Wanda ya amsa masu saboda ba kowa a cikin pallow Yusra tana birdromm a kwance tana waya da Aminiyata tana bata shawarwarin hanyar da zatabi ta samu Mahmud yazama nata." Sautin magana taji a can pallow yasa tayi saurin yin sallama da ita tamik'e da sauri tana sanye da gajeren wandon iya cinya da tare da wata Riga Wanda wa ita wa babu duk d'aya." Wnn shigar da takeyi ba wani abin mamaki bane ga duk Wanda ya santa domin a cewarta manyan kaya nauyi suke mata a jiki." Cikin tafiyarta ta yanga da Jan hankali ta nufi pallow." *kuyi hkr dani Dan Allah wasu hidimomi ne suka sha kaina amma da zarar na kammalasu zaku dinga ganin posting dina ako da yaushe* [8/2, 1:13 PM] El-hajj✨✨✨: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_ ) *41* Kai tsaye tanufi pallow tana tafiya tana girgiza tana yanga, A can ta hango mutane Zazzaune a kan kujera, Mahmud yana tsiyaya masu lemo a cup, daga ganin alama kasan suna da fahimmanci gareshi." Sai da tazo dafdasu a can tayi tozali da Abba, fara'a tasaki a fuskarta, ta nufi wurinsa domin ta gaida shi, don shi kad'ai tasani a cikin mutanen da tagani zazzaune a pallow, amma daga ganin mommy ta fahimci cewa itace mahaifiyar mahmud sai kuma Khalil wanda ta sanshi tun a wurin partty kasancewar ya gabatar mata da kanshi a matsayinsa na k'anen Ango, Bayan hakan kuma da zarar ka kalli Khalil da mahmud zakaga suna matuk'ar kama da junansu sosai." Sai kuma kyawawan 'yan mata da tagani guda biyu wad'anda suka ci kwalliya, musamman dijama data hard'e k'afa d'aya kan d'aya tana mata wani kallo na bakida tarbiya." Mahmud yayi saurin doka mata tsawa tun kafin ta kai da zuwa wurin Abba, yana Jifanta da wani kallon tsana, Wanda yasa tayi saurin dakatawa da zuwa wurin, jikinta ya soma rawar tsoro." Ya nunata da hannu rai b'ace yace "dibeki kidibi jikinki, ki kuma dibi kayan da ke sanye a jikinki a hakan zaki tunkari mahaifana da sunan zaku gaisa dasu?" Kina so ki nunawa duniya cewa bakida tarbiya kenan, kina kuma so ki nunawa mahaifana cewa banyi dacen matar aureba." Ya kuma doka mata tsawa yace "Dan Allaha malama kije ki suturta jikinki, ki sanya kayan mutumci snn kifito Ku gaisa." Sai a lokacin taji kunyar kayan dake sanye a jikinta, jiki sab'ule ta juya tana tafiya ko ina na jikinta yana motsowa." Gaba d'ayansu saboda jin kunyar shigar da tayi ko wannensu ya kauda kai daga kallonta amma banda Khalil, Da ya karkace kai ya k'ureta da ido yana k'arewa surar jikinta kallo a zuciyarsa yana fad'in brother yayi dacen mata amma gaskiya zai huta a wurin can." Tsohuwa kuma saboda mamaki da Al'ajabi kasa magana tayi, xaune take wuri d'aya a kan kujera ta rafka tagumi, tarasa abin fad'a, Can ta nisa ta kalli mahmud dake zaune daga ganinsa akasan ransa a b'ace yake tace "kai kuma irin matar da KA aura kenan?" Ta rik'e baki tace "Allah mai iko yau naga abinda mmki, naga abinda bantab'a gani ba a duniya." Kowa yayi shuru yana sauraren tsohuwa a zahirin gaskiya kuma kowa da abinda yake tunani a ransa musamman mommy da tun farko bataso aurensa da Yusra ba sabida rashin tarbiyarta da kuma sangartarta uwa uba rashin kamun kai, Dan dai ba yanda zatayi ne, Abba ya riga da ya goyi bayan sai anyi auren." Abba shima abin mmki yake bashi Ashe Dama Yusra bata da kunya hakan bai saniba?" Ashe bata da tarbiya bai saniba?" Da yasan hakan take gudanar da tarbiyarta da bbu abinda zaisanya ya amince da buk'atar Alhaji Atiku, na aurawa mahmud ita." Amma yaji dad'in tsawar da Mahmud yayi mata akan taje ta suturta jikinta wnn shi zaisanya tasan ba dai dai ta aikataba ko da a nan gaba idan wasu bak'in sukazo bazata tab'a tunanin ta fito a hakan ba." Mommy taja dogon numfashi daga tinanin da takeyi ta kalli mahmud dake zaune tace "meyasa KA dokawa matarka tsawa wanda har ya sanyata tayi saurin firgita a gabanmu?" Karka kuma yimata tsawa hakan Idan tayi wani abin da ba dai dai ba janta zakayi wuri d'aya KA zaunar da ita cikin hikima da kwantar da hankali ka nuna mata abinda tayi bata kyautaba, KA Nuna mata yanda kakeso ta kasance, zatafi fahimta Baka dinga yi mata tsawa kana disgata a gaban bainar jama'a ba, hakan da kakeyi bayada kyau ko a addini." Sunkuyar da kai yayi yace "mommy kiyi hak'uri bazan kuma ba." Murmushi tayi tace "Allah yashi maku Albarka ya Baku zaman lafiya da hak'uri a zaman aurenku." Aka amsa da Ameen amma banda dijama da tsohuwa." Tsohuwa ta mik'e tsaye tana gyara mayafinta tanufi hanyar waje, tana fad'in "ni da yake ba uwarka bace Wanda ta tsungunna ta haifeka, A lokacin da nake magana ai kyaleni kayi, kayi banxa dani, Amma da uwarka tayi maka magana sunkuyar da kai k'asa kayi kana saurarenta daga k"arshe kuma kashiga bata hak'uri." To na bar maka gidanka, na barka da marar kunyar matarka mai yawo tsirara a gaban bainar jama'a. Kai kan bakayi dacen mata ba, a hakan za'a aura maka 'yar uwarka a kawo maka ita, wnn fitsararriyar matar taka ta b'ata mata tarbiya, Gaba d'ayansu kowa ya d'aga kai yana kallon tsohuwa Abba da mommy sai rok'on Allah sukeyi Allah yasa kadda tsohuwa ta furta abinda ba yanzun sukayi Alk'awarin fitar dashiba." Tsohuwa na ganin kallo ya dawo kanta komai ta tuna ohoo tayi saurin Jan bakinta tayi shuru." Shima mahmud d'in yashiga mmkin wace 'yar uwa tashi za'a aura mashi?" Idan kuwa da gaske ne, So akeyi a kashe masa rayuwa baza"a barshi ya zab'i wacce yakeso ba?" A gaskiya a wnn karon sai dai Abba ya hak'ura domin bazai tab'a Amince masa ba." Dijama najin hakan sai da gabanta ya yanke ya fad'i, tashiga tashin hankali, Wace 'yar uwace tashi Wanda za'a kuma aura masa?" Khalil kuma da yasan kwanan zancen ya kuma had'e rai, yana kallon tsohuwa yana jiran ta furta wata magana wanda batayi masa ba a tsakanin dijama da mahmud a nan take zai bata amsa domin kuwa babu wani Wanda ya isa ya aure dijama bayanshi, a yanda yakejin dijama a ransa komai yana iya aikatawa in har zai sanya ya sameta ya aureta tazama mallakinsa." cike da mmki mahmud ya Mik'e ya nufi wurin tsohuwa yana fad'in "yi hak'uri tsohuwa kidawo ki zauna ba kyaleki nayiwaba, ai ke kinsan bana kyaleki." Fad'amun naji wacece kuma za'a aura mun?" Tsohuwa tace "bazan fad'aba sainaji shak'a da bak'ura." Mahmud yace "Allah yabaki hak'uri 'yar tsohuwa mai ran k'arfe." ganin kusan minti 30 yusra bata fitoba, Mommy da Abba suka mik'e tsaye Abba ya riga fita yana masu sallama snn mommy tare da su dijama, Mahmud y bisu da kallo yace mommy bazakujira tafito Ku gaisa ba?" Mommy tace idan tafito KA gaida ita sai mun sake dawowa, tafita SU fateema suka bi bayanta tareda Khalil, wanda duk yaji haushin tafiyar da akayi batare da Yusra tafito ya kuma kallonta ya tattacewa brother irin matar da ya aura." Hakan ya rakasu mota Khalil yajasu suka nufi gida kowa da abinda yake sak"awa a ransa." A fusace ya juya ya shiga gida, kai tsaye d'akinta ya nufa yana huci, kwance ya tarar da ita kan gado tana latsar wayarta hankalinta a kwance." Zuciya ta kuma rufeshi ya fisge wayar yayi jifa da ita saida screen d'inta ya farfashe snn ya fincikota da k'arfi ya kwad'a mata mari har sau biyu yana furta , " na tsaneki bana sonki ko a lahira bana fatan nayi tozali da macce irinki nakashashiya marar tarbiya." Kin wulak'anta mun iyaye wad'anda darajarsu kikaci har aka d'auramun wulak'attacen Aurenki,a kaina amma a yau sune kika bari zaune a parlour suna zaman jiranki." kisani iyayena k'annena kakata wlh sune farin cikina, kuma yanda kika wulak'antasu sai na wulak'antaki na kuma wulak'anta ubanki." Ya kuma kwad'a mata mari a karo na uku, ta rik'e kunci tana kallonsa tana kuka, Ta nufoshi ta shige a jikinsa ta cimuimuye shi, tana "fad'in KA kasheni mahmud KA kasheni nace Domin kawai nace ina sonka? ,KA kasheni na huta, amma kasani ko yanzun KA kasheni nacika burina na aureka, kai mijina ne ni matarka ce sai dai bak'in cikina d'aya da har yanzun ban...... Bata iyar da maganar da takeyiba taji saukar belt a jikinta abinda tunda uwarta ta haifeta bata tab'a jiba." Kuka takeyi sosai tana Neman d'auki dakyar tasamu ta fita d'akin da gudu ta fad'a d'aya d'akin ta rufe ta sanya key tashiga kuka tana birgima, a maimakon tayi nadamar aurensa da tayi sai ma wani sabon sonshi taji yana taso mata. A zuciya." _Hmmmmm so hana ganin laifi_ Da zuwansu Abba gida suka hau shirya kayansu zuwa gida, Amma banda Khalil da yace sai zuwa anjima zai taho idan Ahmad ya shirya." Cikin ikon Allah suka sauka gida lafiya, Washe gari tsohuwa itama ta hau shirya kayanta harda na dijama zasu koma Tofa, Abba da mommy suka shiga bata hak'uri dakyar aka samu tsohuwa ta hak'ura amma da sharad'in za'a fitar da dijama makarantar kwana." Abba ya ameence da hakan, Dama kuma saura mako d'aya sufara jarabawar k'arewa." ************* Sulaima da matarsa Fareeda kud'i sun zauna hankalinsu ya kwanta har fareeda ta kuma haihuwar 'yarta mace fadila." Babu abinda zai iya cewa Abba da mahmud sai godiya domin A yanzun Abba ya wuce mahaifin Abokinsa, ya zama mahaifinsa mahmud yawuce Abokinsa ya zama d'an uwansa, Tin lokacin da sulaima ya d'ora ido a kan dijama yaji yakamu da sonta, Kuma duk irin rashin ji da yakeji mahmud yana fad'a akanta bai ganshi a tare da itaba. Asalima na tsuwa ya gani a tare da ita da kamala, Macce Wanda bata son yawan suruto da damuwa, Bai taushi hannu ba kai tsaye ya same Abba ya fad'a masa k'udurinsa a kan dijama, Abba yanuna jin dad'insa sosai a kan hakan kuma ya Amince a kan yaje ya nemi so a wurinta." Alhaji Atiku hankali ya kwanta shalelensa ta aure Wanda takeso, Amma wata damuwa d'aya da take damunsa tun lokacin da ya kori sulaiman daga wurin aiki bai kuma samun nutsuwa da kwanciyar hankaliba." Da zarar ya shiga ofice d'insa zaiji gaba d'aya hankalinsa ya tashi baya iya zama yayi aikin da ya kawoshi, a cikin tashin hankali zai fita daga office d'in ya koma gidansa A yanzun abin ya cutara kwata kw zauna ata baya k'aunar yabi Kota kusa da ofice d'in bare ya shiga cikinsa ya yayi aiki." [8/2, 1:13 PM] El-hajj✨✨✨: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_ ) *42* ~~ Gaba d'aya yaransa abin yana damunsu, sun shiga cikin damuwar canzawar da oga yayi, a lokaci d'aya, amma banda Mahmud, dako a jikinsa aikinsa yakeyi ba ja da baya." Yanzun kimanin shekara d'aya kenan Alhaji Atiku office d'insa ya gagaresa zama Ga kuma lokacin siyasa ya kunno kai ana buk'atar taimakon commandan d'in sojoji, domin a bawa k'asa tsaro." a duk lokacin da shugaban k'asa yayo aike a sanar ya tura jami'an tsaro sojoji ba'a tarar dashi a office." Anan take sak'o ya iso wurinsa daga shugaban k'asa, akan cewa andakatar dashi daga aiki har sai zuwa lokacin da yaje ya nemo lafiyarsa snn yadawo bakin aikinsa." Cikin kwana biyu aka Dora mataimakinsa mai adalci, ai kuwa cikin sati d'aya komai ya fara tafiya dai dai akan gaskiya." Tun lokacin da sak'on sallama daga aiki ya tarar da Alhaji Atiku ya shiga rud'u da tashin hankali, babu abinda yafi d'aga masa hankali sai ce masa da akayi yaje ya nemo lafiyarsa." Kuwa yakeyi yana d'aga murya tare da kai komo paloow zuwa birdromm yana fad'in " naje na nemo lafiyata hauka akace inayi ne?" ko zaucewa akace nayi?" Sam bazai yiwoba inaji ina gani da raina da lafiya ta a saukeni daga kan kujerata, Da k'arfi yashiga doka Kansa a bango, mommy mahaifiyar Yusra tana gefensa tana magiya akan yayi hak'uri yabi komai a sannu, sai k'ok'arin fisgoshi takeyi amma ina yafi k'arfinta." Sallamar mahmud taji yashigo pallow wanda rabon da yazo gidan tun kafin a d'aura masa auren Yusra." Hango Alhaji Atiku yayi yana magagganu yana doka kansa a bango cikin hanzari ya nufeshi, Yana fad'in subahanallahi Daddy meyake faruwa?" Mommyn Yusra tace "Dan mahmud KA taimakamun ka janye shi daga wurin KA zaunar dashi." Da kyar Mahmud ya samu ya janyeshi ya kwantar dashi a kan kujera, Ya kafeshi da ido yana fad'in sannu daddy, "Mommy meya sameshi?" Alhaji Atiku ya zabura ya tashi zaune yace "mahmud wai ni za'a dakatar daga wurin aiki, ni Alhaji Atiku, sai kuma yayi shuru." Shuru mahmud yayi ya yana tunanin irin dubban mutanen da shi ya kora da kansa, ashe Ba dad'i." "Daddy kayi hak'uri KA barwa Allah komai, idan kayi dibo da irin mutanen da kayita sallama daga aiki, ina ganin suma hak'urin sukayi suka barwa Allah, Kaima ya kamata kayi hak'uri tunda kaine mai sallama gashi sallamar tazo kanka." Magagganun da mahmud yakeyi sune suka dawo da tinaninsa, Ashe dama hakan akeji idan aka dakatar da mutum da ga aiki?" Yanzun duk wad'anda ya kora haka suka zauna cikin bak'in ciki da tashin hankali?" Babu wanda ya fad'o masa a rai sai sulaiman wanda tun lokacin da ya koreshi ya kasa zama cikin kwanciyar hankali, gaba d'aya natsuwa ta k'aura cemasa, Hakan sulaiman ya tsinci Kansa a cikin tashin hankali,a lokacin da ya koresa?" yana da labarin irin wuyar da yasha kafin ya samu aikin, ba dan komai sai dan yayi dogaro da kansa ya kuma tallafi mahaifansa." Mahmud ya katse masa tunani da yake cewa, daddy kayi amfani da shawarar da suka baka kaje asibity a diba lafiyarka ko ba komai kana buk'atar ganin likita ko Dan ayi test din jininka a fad'a maka halin da kake ciki domin kuwa silinda maiyi maka hidima a office ban yarda da lafiyarta ba." Yana kaiwa nan ya mik'e tsaye yace "Allah ya tsare gaba daddy, Shalele tana gaida kai." Yyi wuce warsa." Tashin hankali Alhaji Atiku ya kuma shiga da yaji kalaman da Mahmud ya fad'a masa yana nufin bai yarda da lafiyarsa kenan? Wai mai yasa mahmud yake tunkararsa gaba da gaba ya fad'a masa magana, Ya tsinci kansa da kasa d'aukar masa mataki?" Wacece silinda kuma?" kaddai ace yana ganin lokacin da yake hutawa da abokiyar aikinsu?" Rud'u ya kuma yashiga, yana fad'in karya ne, lafiyata glau babu abinda yake damuna." mommy ta matso kusa dashi ta zauna tashiga kwantar masa da hankali cikin kalamai masu taushi snn da kyar ta samu ya kai kwance akan kujera bacci b'arawo yayi awon gaba dashi." **************** Yau ake yin bikin kammala makaratun su dijama Wanda za'a had'e tare da walimar saukarsu, Khalil sai kai da komo yakeyi, duk wani abinda dijama da fateema suke buk'ata Khalil ya sawo ya ajiye masu." Hakan sulaiman shima ya taka rawar gani wurin tashi gudunmawa." Khalil yana lura da take taken sulaiman a kan dijama, ya fahimci sonta yakeyi, wnn dalilin yasa idan zasuyi had'uwa goma wuri d'aya baya iya masa magana sab'anin da, Idan suka had'u har hira sukeyi har da 'yar wasa a tsaka ninsu." Shima sulaiman hakan ya fahimci khalil ya fad'a matsananciyar soyayyar dijama wanda yake ganin dijama a yanzun alurace cikin ruwa mai rabo ke d'auka, Dan haka duk wani shariyarshi yaje yayi abarsa bai damuba Allah ya ba mai rabo sa'a." Wanda ita kuma dijamar gaba d'aya duk abinda ake baya gabanta burinta d'aya Allah yakawo yaya mahmud lafiya wanda tun asuba da sukayi waya ya sanar da ita cewa gashi a kan hanyar zuwa, amma kadda ta fad'awa Mommy da Abba sai dai kawai su ganshi yazo." Gashi yanzun har kusan k'arfe 10am bai isoba, kowa ya hallara a wurin amma banda dijama wanda ta shirya cikin wani lesi ruwan madara wanda Abba ya d'unka masu iri d'aya tare da fateema, d'inkin riga da saket ne, sunyi matuk'ar kama jikinta k'ugunta ya fito tare da k'irjinta wad'anda suka bayyana a cikin rigarta sunyi tsaitsaye sun cika cikin rigar, Fateema ta dubeta tace kai sister kinganki kuwa yanda kikayi kyau?" Dijamah ta d'an saki murmushi tace "nagode sis aikema kinyi kyau kinma fini kyau." Fateema ta rik'e baki tace wace ni, aini nasan kinfini komai bama zan had"a kaina da keba." Dijama ta d'an ya mutsa fuska ta dubi wayar hannunta, Snn tace "daina fad'ar hakan dani dake duk d'aya, Ganin lokaci yana tafiya Abba ya soma kiransu suyi sauri sufito, Fateema ce bata iyar da kammala shiryawa ba, Ta dubi dijama tace "lah kinga sister hijabanmu suna d'akin Momy kije ki d"auko mana kafin na sanya kayana." Mik'ewa dijama tayi da waya a kunnenta tana gwada kiran yaya mahmud ko Allah zaisa kiran ya shiga, Amsa d"aya ce ake bata wayar a kashe take." Ta cikin babban falon gidan ta wuce zata shiga d'akin mommy bata lura da mommy da Abba da Khalil da sulaiman ba, gaba d'aya hankalinta baya tare da ita yana a wayar ta, zaune suke suna jiran fitowarsu." Tafiya takeyi tana wani juyi, idan kagani sai KA d'auka da gaggan takeyi kuma ainahin tafiyar ta kenan, Ga k'irjinta a cike Dana shanu gata doguwa fara kyalkyawa, masu karatu duk yanda zan misalta maku dijama ta wuce nan." Duk yanda Khalil yake tunanin dijama sai ma gani yayi ta wuce nan, Haka sulaiman da ya k'ureta da ido yana kallo." Wani kallo Khalil yake mata irin nasu na 'yan duniya wanda suka San qualities d'in cikakkiyar mace." Wani kishi ya tasowa Khalil ganin yanda sulaiman ya kafeta da ido yana kallonta, Shima sulaiman hakan, Atare suka juya suka kalli junansu suka sakarwa junansu harara." *IYA COMMENT D'INKU IYA TYPING D'INKU*🤷🏻‍♀🤷🏻‍♀🤷🏻‍♀ [8/2, 1:13 PM] El-hajj✨✨✨: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_ ) *43* Abba na ganin hakan yayi gyaran murya ya kuma dibonsu a tare gani yayi ko wanne jiyakeyi kamar ya had'iye d'an uwansa, Yace "ya kamata kutashi Ku isa wurin kafin muk'araso." Gaba d'ayansu suka kalli Abba, Mommy tace "ya kamata ku isa wurin tin yanzun domin kuga yanayin taron gamu nan zuwa yanzun idan suka kammala shiryawa." Jiki ba kwari kowannesu ya mik'e ya d'auki key din motarsa ya fita, domin zaman da sukeyi a wurin ko wanne yaci Alwashin a motarsa dijama zata shiga." Tsohuwa ce tafito daga d'akinta wanda yake masauki ne a gareta a duk lokacin da tazo, Itama cikin shirinta na zuwa walima." Tana fitowa taga Abba da mommy zaune, a pallow Sai da ta lalubo goronta a Jakarta ta gutsara snn ta kalli Abba tace "wai tun d'azun me ake jirane, ba'a tafiba Har na kwanta bacci na tashi, Duk a tinanina har kuntafi kun barni." Mommy tayi murmushi tace "wamu nan ai bamu isa mutafi mu barkiba, Inna." Abba ya k'ara da cewa "sai dai a fasa walimar." Tun d'azun zaman jiran fitowarsu mukeyi." Tsohuwa bata ce komaiba illah ta nemi wuri a kan kujera ta zauna, tana kallon TV tana cin goronta." Da sauri dijama ta fito d'akin mommy sanye da k'atuwar hijabi mai hannu ruwan madara kalar lass d'inta, Hannuta rik'e da d'aya hijabin fateema zata kai mata, Sai a lokacin ta lura da Abba da mommy da kuma tsohuwa dake zaune a gefe d'aya." Mommy tace "karfa kub'ata mana lokaci, Ku muke jira tun d'azun kun barmu a zaune." Ta had'a da d'an saurinta tanufi d'akinsu domin ta mik'awa fateema hijabinta tana fad'in "yi hak'uri mommy ai mun kammala shiryawa." A kofar d'akin ta tarar da fateema ta mik'a mata hijabin snn suka fito suka shiga motar Abba, tsohuwa ce gidan gaba, snn gaba d'ayansu har da mommy suka shiga gidan baya Abba yajasu suka nufi makarantar." Motar Khalil ce a gaba snn mortar sulaiman, a tare suka shiga makarantar ko wanne yanaji da kansa suna nunawa junansu isa." Khalil ya fara fitowa cikin isa da gadara, ya nufi office d'in shugaban makarantar domin ya biya kud'in duk abinda ake buk'ata, gaisawa sukayi da shugaba, Ya shiga tambayarsa nawa ne kud'in?" Dame dame ake buk'ata?" Shugaba yace "ai tuni, Yayanka yazo yabiya harda kyauta ya mana mai tsoka, kai munji dad'i sosai ubangiji Allah ya biya yayanka shima ya bashi wad'anda zasu taimakesa." "Ameen yace a tak'aice, tare da mayar da kud'insa a Aljihu." Yafita yana mamakin wanne yayan NASA?" Shi dai yasan brother bai zoba, to kodai sulaiman ne yayi masa rigage." Hmm lallai kuwa zai nunawa sulaiman ba'a ja dashi a fagen Neman macce." Motar Abba ta tsaya a harabar makarantar taro yayi taro mutane an hallara manya da 'yan siyasa, Abba yana d'aya daga cikin manyan bak'i wad'anda ake jiran isowarsa, Haka itama mommy da tsohuwa suka nufi wurin mata iyayen yara suka zauna cikin manyan mata 'yan gayu." Suma su Dijama suka nufi wurin d'alibai 'yan uwansu suka zauna." Anan aka fara gudanar da abinda ya tarasu a wurin." Ko wanne d'alibi yana cikin farin ciki amma banda dijama da sai murmushin yak'e takeyi hankalinta na wurin yaya mahmud, rashin ganinsa da batayi ba." Abinda batasani ba shine, tun k'arfe 8am mahmud ya dura garin kano, bai zame ko ina ba sai makarantarsu kai tsaye wurin malaman ya nufa wad'anda dama sunsanshi sunsan matsayinsa a wurin su dijama. Anan yashiga tambayar shugaban makaranta duk wani abin da ake buk'a." Shugaba yashiga yimasa lissafi, anan take ya cire kud'in ya biya, tare da tashi gudunmawa." Gefe d'aya yaja ya zauna yana kallon kowa d'aya bayan d'aya, A can ya hango motar Khalil da sulaiman, Har zuwa lokacin da Khalil yashiga office d'in shugaban makaranta, mahmud yana ganinsa ya shiga office d'in yyi murmushi yace "yaro man kaza." Jim kad'an yaga Abba ya shigo tare da mommy da tsohuwa." Snn ya hango dijama ta fito tare da fateema, ko wanne ya tafi wurin zamansa ya zauna." Cigaba akayi da bikin, yana gefe d'aya yana kallon kowa d'aya bayan d'aya." Nana khadija hassan yaji ankira domin ta bud'a taro da karatun AlQUR'ANI Dijama ta fito jiki a sanyaye tana tafiya a hankali, Ta gefen tsohuwa tabi zata wuce tsohuwa ta d'an mangareta a k'afa tana magana k'asa k"asa "ki d'aga k'afa kiyi tafiya, Kina tafiya kamar wacce kwai ya fashewa a ciki." Dijama ta waiga ta kalli tsohuwa tasaki murmushi, Snn ta kuma juyawa taci gaba da tafiyarta a hankali mai cike da yanga da rangwad'a." Khalil da sulaiman ko wanne ya kafe ta da ido cike da birgewa, Hakan shima mahmud wanda tun tasowar ya kafe ta da ido yana kallonta domin gani yayi tayi masa wani irin fitinannin kyau, wanda baya misaltuwa d'aga ido yayi yaga duk ilahir mutanen dake wurin kallonta sukeyi." Wani abin yaji ya taso masa, a zuciya bai San lokacin da Yaja dogon tsaki ba tare da had'e fuska yace "dama tasan za'a kalleta ne shiya sa tak'i sanya lik'abi." Tunaninsa ya tsinke a lokacin da yaji k'ira'ar Alqur'ani yana tashi cikin wata siririyar murya mai dad'in sauraro." Lumshe idonsa yayi ya kuma bud'esu ya kalli wurin tabbas dijamace 'yar gidan tsohuwa ke karantun Alqur'ani, Wayarsa ya Ciro daga Aljihunsa yana murmushin farin ciki ya shiga d'aukarta camer videos." Bayan ta kammala karatun qur'anin ta kuma bud'e taron cikin harshen turanci." Duk wani masoyin dijama a wurin idan ya ganta sai yaji ta burgeshi ta kuma Shiga ransa." Mahmud bai San lokacin da ya mik'e tsaye ya nufi motarsa ya d'auko babban kyautar da yazo mata da ita wanda shi kad'ai yasan kome a ciki." Fuskarsa cike da farin cikin da baya misaltuwa ya nufi cikin taron, Sai da yazo daf da ita wanda yayi dai dai da kammala warta, Fuskarsa cike da annuri, ya Mik'a mata kyautar. Ganin hakan gaba d'aya wurin a kad'auki tab'i, domin sun burge mutane, kuma shine mutum ba farko da ya fara bata kyauta girmamawa." K'ureshi da ido tayi cike da farin ciki snn ta sauk'e ajiyar zuciya snn ta d'an runsuna alamar girmamawa ta k'arbi kyautar tana godiya " Hakan da sukayi ba k'amin burge mutanen wurin sukayi ba, aka shiga d'aukar photo na Abba da mommy da tsohuwa sai murmushin jin dad'i sukeyi suna mamakin yaushe yazo?" Hakan shima sulaiman murmushi yakeyi, Wanda khalil yacika saima yatashi daga inda yake kallonsu ya koma motarsa yayi zamansa, zuciyarsa na tafasa." Hakan kowa yayita bata kyauta yana jinjina mata da yaba mata a kan k'ok'arinta." Taro yayi taro mutane anci ansha an wadata dijama da fateema sunsamu kyauta ta ban mmki, wanda da zarar anbawa dijama kyauta idan ta k'arb'a tayi godiya Mahmud take mik'amawa, yin hakan ba k'aramin dad'i yake yiwa Abba da mommy ba." Bayan antashi daga taron kowa yana k'ok'arin shiga motarsa tareda iyalansa domin su isa gida." Sama da k'asa aka nemi Mahmud da dijama aka rasa, Abba ya shiga kiran number mahmd yaji ko da suna tare amma gaba d'aya daga number shi harta dijama a kashe take." Acan bakin get Abba ya hango wucewar motar sa tare da dijama a gaban motar, Itama tsohuwa ta hangosa ta nuna da hannu da baki tace "wncan ba mamuda bane?" Gaba d'aya kowa ya juya ya kallesa mommy tace "shine kuma ina ganin kamar a tare suke." Khalil ya cika ya burzar da iska mai zafi cike da jin haushi yace "amma bro meyasa yyi hakan ya kamata ya sanar zai tafi da ita." Tsohuwa tayi karaf tace "ina ruwan ka?" Yak'i ya sanar d'in, meye naka a ciki?" Ta dubi Abba tace "Hassan shiga mota KA kaimu gida, Ai shima mahmud d'in zurfin cikine dashi wanda ba inda zai kaishi." Sulaiman yana gefensu a tsaye, FAREEDA sai waya take masa, akan yyi sauri ya dawo ta kammala abinci, murmushi ya saki ya d'an runsuna yyi wa su Abba sallama ya shiga motarsa yyi tafiyarsa." Khalil yanajin tsohuwa ta dakatar dashi, Cikin jin haushi da takaici shima ya nufi motarsa, Abba ya lura da yanda yake wani ciccira idonsa yayi ja, Ya dakatar dashi yakira sunansa tare da nunashi da hannu yace "Khalil muddun kasake kayi mugun gudu to kasani da kai da mota sai dai kagani a abokananka." [8/2, 1:14 PM] El-hajj✨✨✨: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_ ) *44* *DEDICATED TO MSS HAFSY stylishlady*💋 Turo baki yayi yace "to ni Abba ya akeso nayi ne?" Sai nake ganin kamar duk an tsaneni, kawai a kasheni a huta." Mommy tace "khalil mu kake fad'awa magana?" Abba yayi shuru ya k'ureshi da ido yana kallonsa." Tsohuwa tace "eh lallai yaro ka girma wuyanka ya isa yanka, ai abinda ya rage maka d'aya ne kazo KA dake mu kawai sai ka huta." Fateema tace "kefa tsohuwa baki kashe wuta sai dai ki kuma rurata." Tsohuwa tace "yi mun shuru, rufemun baki me kika sani ke kuma?" Mommy tana gefen mota tsaye tana kallonsu batayi magana ba." Snn Abba ya bud'e mota ya shiga, dukansu suka shiga harda tsohuwa da har yanxun masifar takeyi bakinta yaki yayi shuru." Khalil yana ganin Abba ya Shiga mota shima ya mirgina kai cike da jin haushi, ya tayar da mota suka fita a tare." Motar Abba ke gaba Khalil na biye dashi a baya, Abba yana kallonsa a dubi." Hanyar makaranta Abba yaga khalil ya nufa yana tafiya da mota a hankali kamar wanda baya da lafiya." Girgiza kai Abba yayi, Yashiga magana a zuciyarsa dole ne a sake sabon zama domin kuwa Khalil ya fad'a matsananciyar soyayyar ummie, wanda a yanda yake gani a idonsa komai zai iya faruwa idan baisameta ba." Dogon nishi yaja wanda yayi dai dai da karya kwanar gidansa." Duk a tunaninsu zasu tarar da motar mahmud ajiye a kofar gidan amma abin mmki basu ganshi ba, bai isoba." Ko wanne yaja bakinsa yyi shuru, daga ciki kuwa har da tsohuwa, da ta mere baki tayi shigewarta gida." Mahmud kuma bayan antashi daga taron idonsa na wurin dijama, yana ganin irin malamai da d'alibai ko wannesu k'ok'ari sokeyi sukawo jiki wurin ta domin suyi photo, kasan cewar makarantar had'e take da maza da mata." Duk inda dijama ta wurga sai biyarta sukeyi suna hotuna, can ya hango wani malami wanda tun d'azun ya kame wuri d'aya cikin wasu k'ananun kaya, duk motsin da yayi idonsa na kanta, wurinta Yanufa yana murmushi yana kuma gyara kwalar rigarsa, dijama tana ganinsa itama ta sakar masa murmushi tace uncle Salis ina wuni." Ya kuma sakar mata murmushi ya amsa tareda matsowa kusa gareta yana fad'in Nana khadija yar farar yarinya kyakkyawa makaranta zatayi rashinki da kewarki inama zamuyita zama dake hakan." Zaro ido tayi alamar shagwab'a tana murmushi "karka damu uncle ai ba'a rabuba ana tare." D'an sunkuyawa yayi kusa da ita ya d'aga wayarsa ya d'aukesu photo suna murmushi." Mahmud yana ganin hakan ya taso daga inda yake zaune ya nufo wurinsu, a dai dai lokacin da uncle ke cewa nana khadija ki amince na dinga zuwa gidanku mudinga gaisuwa." D'aga kan da zatayi tana murmushi domin tana matuk'ar ganin mutuncin uncle salis, ya taimaketa sosai a kan karatunta, ido biyu sukayi da mahmud tsaye a kusa da ita ya sanya hannuwansa biyu a aljihun wandonsa, Yana kallonta tareda wurga mata wata kalar harara." Jikinta ya fara rawa ta soma ja da baya tana fad'in "dan Allah yaya kayi hak'uri." Uncle ya juya ya dubi Mahmud dake tsaye wurin d'aya kallo d'aya yayi masa sai da antar cikinsa ta motsa, Tare da fad'uwar gaba, kasancewar mahmud namijine jarumi k'akkarfa mai kwarjini." Sulalewa uncle yayi yayi tafiyarsa bai kuma yin magana ba." Ita kuma dijama sai hak'uri take bashi Tana ja da baya. Ganin ba wanda ya lura dasu, tana Neman tara mashi jama'a ya doka mata tsawa, Sai gani tayi ya zamar mata mahmud dinsa wadda tasani ada." ya zaro mata rinanun idanunsa yace "duk kika kuskura kika kuma d'aga k'afa daga inda kike, Babu abinda zai hana na kakkarya k'afafun idan na kamaki." Tsayawa tayi cak." ta k'ureshi ido cike da tsoro jikinta na rawa "dan Allah yaya mahmud kayi hakuri." Ya d'aga k'afarsa cike da k'asaita yana tafiya guda guda, ya isa wurinta ya rik'o hannunta ya jefata a mota ya zagaya mazauninsa yaja motar suka fita makaranta." Gudu yake da mota kamar zai tashi sama, wanda gaba d'aya hankalin dijama ya tashi ta sadakar kasheta kawai zaiyi domin ganin b'acin ransa wanda bata tab'a ganiba." Hankalinta ya kuma tashi a lokacin da taga ya d'auke hanya wanda bata gida ba." "Yaya dan Allah kayi hak'uri na tuba, wlh Allah Uncle d'inmu ne, idan k'arya namaka ka tambayi FATEEMA zata fad'a maka." Wani wawan murki yaja a gefen titi a can cikin uguwar GRA unguwarda ko kasheka za'ayi ba wanda zai taimakeka." Kifa kanshi yyi a kan sitiyarin motar sai da ya d'auki minti goma a hakan snn ya d'aga kai ya dubeta ya wurga mata wani irin kallo da rinanun idanunsa wanda sai da hantar cikinta ta murd'a ta kasa yin magana ta dinga d'aga hannu alamar yayi hak'uri ta tuba." Hannu ya d'ora a kan bakinsa alamar tayi shuru🤫." [8/2, 1:15 PM] El-hajj✨✨✨: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writing By *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basheer_ ) _DEDICATED TO MAMAN SADEEQ MARUBUCIYAR MUHIM HAK'IK'A LITTAFIN MUHIM YA NI SHAD'ANTAR YA FAD'AKAR DAMU KINYI NAMIJIN K'OK'ARI WURIN BAJE FASAHARKI DA HIKIMARKI WURIN ZUBA WNN LBR NKI ALLAH YA K'ARA BASIRA DA KWARIN IDO MUNAYINKI IRIN SOSAI D'IN NAN_ *45* Jiki na rawa ta sanya hannunwanta biyu ta rufe bakinta cike da jin tsoro." Ido ya kureta dashi, wanda itama shi take kallo, snn yace "bayan matsayinsa na uncle d'inki meye kuma matsayinsa a wurinki?" Muddun kika kuskura kikayimun k'arya saina tattakaki a wurin nan ba Wanda zai rama maki?" "Wlh Allah yaya na rantse maka da Allah babu wani abu a tsakaninmu." Shuru yyi yana kallonta yana karantar gaskiyarta." Snn yaja dogon nishi tare da mik'a mata handkerchief d'insa fari mai cike da k'amshin turarensa mai sanyin dad'i. yace "to naji na yarda share hawayen fuskarki, kuma ki natsu magana zanyi da ke." Amsa tayi da sauri tashiga gogewa, k'amshin turaren ya daki hancinta tayi saurin lumshe ido, tare da sauke ajiyar zuciya." Ya dubeta yace "Dijamah meyake damunki?" Da yake sanyaki a damuwa?" Meyake hanaki bacci?" Meyake damunki wanda yake sanyaki rama?" Wanda har ciwon zuciya yake Neman kamaki?." A kwai wanda yake matsa maki a gida ko yake takura maki daga ciki kuwa har da Khalil?" Ko aure kikeso akwai wanda kikeso wanda bakya iya tunkararsa ki fad'a masa cewa kina sonsa?" Fad'a munshi kowaye ko mai matsayinsa nayi mki Alk'awarin sai na nemo maki soyayyarsa a duk inda yake domin farin cikinki." Maganar da yakeyi jitayi kamar ya daka mata mashi a zuciya, idonta ya shiga zubar da hawaye cikin muryar kuka tace " ni bana son kowa bana soyayya da kowa." Tana k'ok'arin bud'e murfin mota ta fita, saboda wani abin datakeji yana taso mata a zuciya." Da sauri ya rik'o hannunta wanda harta bud'e murfin motar ta zira k'afarta waje zata fita, wani abin taji ya tsikareta jin hannun yaya mahmud rik'e da hannunta, Wanda shima hakan yaji wani shocking naratsa shi tun daga saman kanshi har k'asanshi, Wanda yasanya shi yayi saurin lumshe idonsa, cikin dasashiyar murya mai cike da kasala yace "karki sake kifita a motar nan." Jiki ba kwari ta tsaya cak." daga fitar da zatayi, still hannunsa na cikin hannunta ya kasa sakinta." Ido ya kureta dashi yana kallonta, yana kuma kallon d'an k'aramin bakinta Wanda taketa faman jujjuyashi tana gunguni, wanda ya kasa jin abinda take fad'a "Matsa hannunta yayi da k'arfi, wanda yasa tayi saurin juyowa gaba d'aya ta dubeshi, tana ya mutsa fuska, "me kike fad'a?" Allah yasa kikeyi mun?." Ya kuma matse hannun wanda taji zafi sosai tasaki 'yar k'ara tana fad'in "wlh ba Allah ya isa naimaka ba." "To mekikace?" turo baki tayi a shagwab'e idonta yana zubar da hawaye tace "bance komai ba." Baya son ganin hawayenta, ya d'an sassauta rik'on da yayi mata. Tare da janyo fuskarta dai dai saitin fuskarsa karan hancinsa yana gugar karan hancinta, gaba d'aya numfashinsu ya gauraye da na juna, dukansu sunajin saukar numfashin junansu. Runtse idon tayi tanajin wani abu yana mata yawo tun daga kanta har xuwa k'asanta." Iska ya dinga hura mata a ido cikin wani salo wanda shima kansa bai San yana yinsaba." "Daina kuka k'anwata, ya shiga share mata hawaye da d'aya hannunsa, kinsan yayanki mahmud yafi kowa sonki, kuma baya son ganin b'acin ranki." Bata san lokacin da tasaki murmushi ba tare da sauki ajiyar zuciya. Ta janye fuskarta daga tasa." Ido ya bita dashi da murmushi a fuskarsa, Ya kuma gyara zamansa cikin tattausar murya yakira sunanta, "Nana khadija bana son ganinki cikin b'acin rai da damuwa, Ki cire komai a ranki ki tsaya kiyi karatu, bana son kina kula samari, har sai kin kammala karatunki wanda da zarar kin kammala kin kai matsayin da kikeso ki kai, ni da kaina zan zab'a maki Mijin aure wanda zai rik'emun ke tsakani da Allah batare da cutarwa ba." Gabanta ne ya fad'i, ta d'aga kai alamar to." "Kinyi mun Alk'awari bazaki kula kowa ba bare kuyi soyayya?" Ta d'aga kai alamar "eh." "Gud yace tare da kai hannunsa ya Shafa gefen fuskarta yana murmushi "yawwa 'yar k'anwata dan haka nake jidake sosai." Cikin sigar lallashi yace mekike so na saya maki?" Fad'a mun naji ya kara kunnensa saiti bakinta." Murmushi tayi ta rufe idonta da tafin hannunta tace "bakomai." Shima murmushin yakeyi yana kallonta cike da burgewa domin yana son macce mai Alkunya ba kamar Yusra ba." Tayar da mota yayi ya fara tafiya juyawa yayi ya d'an dubeta still hannunta na kan fuskarta tana murmushi, kuma burgeshi tayi cikin sigar zolaya yace "oh 'yargidan tsohuwa da jin kunyar yaya mahmud?" A manta lokacin da aka turomun Buba d'an maigari." Kuma rufe fuska tayi tana murmushi." Shima murmushin yakeyi yanayi yana kuma kallonta yana tuk'i, Yau jinsa yakeyi cikin wani yanayi na farin ciki Wanda bai tab"a tsintar kansa cikinsa ba." Ta wani babban store ya biya da ita, yayi mata siyayyar kayan more rayuwa snn ya suka nufi gida." **************** Da sallama suka shiga cikin palo gidan, Wanda gaba d'ayansu suna palon zazzaune harda sulaiman dake zaman jiransa." tana gaba yana biye da ita a bayansa rik'e da manyan ledodi a hannu." Ido kowa ya zuba masu yana kallonsu, ganin kowa ya zuba masu ido yasa , Dijama tayi sum sum ta shige d'akinsu, Mahmud ya zagaya kusa da sulaiman ya zauna, ya bashi hannu suka gaisa da yar dariya d'auke a bakinsa, Snn ya maida kallonsa a wurin Abba da mommy yace "Abba barka da hutawa." Murmushi Abba yayi yace "yawwa mahmud kundawo?" Tsohuwa tayi karaf tace " ai mun d'auka a can zaku kwana." Shin wai ma INA kuka tafi." Kallonta mahmud yayi, Yayi murmushi yace "meye ruwanki da inda mukatafi tunda kin San ba sayar da ita zanyi ba." Ya kuma har zuk'a tsohuwa, tashiga masifa tana fad'in aikin banxa aikin wofi, idan kana fad'in abunda ke cikin ranka kafad"a idan kuma baka fad'i zurfin ciki ba inda zai kaika." Dariya mahmud ya saki mai sauti yace "tsohuwa mai ran k'arfe me kuma zan fad'a?" "Bansani ba tace had'ida wurga masa harara, ta ci gaba da cin goronta." Taja bakinta tayi shuru." Gaba d'aya Palon yayi tsit." Abba yayi gyaran murya yace "mahmud dama zaman da mukeyi a nan gaba d'ayanmu kai muke jira." Abba ya dubi sulaiman yace "D'an uwanka sulaiman yanuna yana son k'anwarka, Ya sameni yayi mun magana yana sonta da aure." Abba bai rufe bakiba mahmud yace "wacece ko fateema?" "Ba fateema yakeso ba ummie yakeso, shine nace zanyi maka magana naji ta bakinka." Juyawa yayi ya Wurgawa sulaiman wani kallo, wanda shi kuma sulaiman ya sakar masa murmushi." Abba yace "ina sauraronka meye shawararka ko kanada wata magana wanda zakayi a kai." Cikin wani yanayi na b'acin rai Wanda baya misaltuwa ya dubi Abba yace "indai shawarata ake nema Abba to ban amince da ayiwa dijama aure a yanxun ba domin kuwa karatu zatayi wanda zata tallafi kanta da kuma maraicinta." Sulaiman yayi karaf yace "na yarda na Amince ko nan da shekara nawa ne bayan ta kammala karatun zan aureta." Cikin b'acin rai da jin haushi Mahmud yace "ni kuma ban amince ba, Ban amince ta aureka ba domin kuwa kayi mata tsoha." Dan kuwa dijama bazata auri tsoho kamarka ba mai mata da 'ya'ya." Tsohuwa tayi karaf tace "idan ka hana ya aureta kai zaka aureta ne?"...... Gabansa ne ya yanke ya fad'i da jin maganar a bazata a bakin tsohuwa." Mik'ewa tsaye yayi cikin fushi da b'acin rai yace "maganata ta k'arshe ban amince sulaiman ya auri dijama ba, domin kuwa ni na riga da zab'a mata Mijin aure wanda zaiyi dai dai rayuwarta." Yana kaiwa nan ya d'auki key d'in motar sa ya fita a fusace." Tsohuwa ta d'aga murya cike da masifa a yanda zai jita tace "zurfin cikin banxa da Wufi anaso ana kaiwa kasuwa dama kafito fili kafad'i abinda ke cikin ranka yafiye maka sauki." Dariya sulaiman ya saki yace "rabu dashi tsohuwa da bakinsa zaiyi magana a nan gaba." Dariya shima Abban yakeyi yace "mahmud namijin gaske Wanda da wuya ka gane abinda yakeso da Wanda baya so." Mommy tace "ai wnn miskilanci ne ke damunsa ba komaiba, Sulaiman ya kuma sakin dariya yace "Abba kubani nan da wata d'aya mahmud zaiyi magana da bakinsa a kan dijama." Abba yace "Allah yasa danafi kowa farin ciki domin babban burina d'aya ne a rayuwa na aiwatar da alk'awarin da na d'aukarwa d'an uwana." ngd sulaiman Allah yayi maku Albarka gaba d'ayanku, aka amsa da Ameen gaba d'aya palon." _Abin mmki dama sulaiman soyayyar dijama ba da gaske yakeyiba_ _wato had'in baki ne sukayi da Abba domin su fahimci inda mahmud ya dosa a kan dijama wanda har sai yafito ya nunawa duniya cewa yana sonta_ _amma kuma naga mahmud zurfin ciki garesa anya zai iya_ Ina jiran comment dinku masu karatu." [8/2, 1:16 PM] El-hajj✨✨✨: 🌹 *DEEJAMAH* 🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writteng by *UMMU SAFWAN* (Fareeda Basheer) *46* Tuk'i mahmud yakeyi sai jan tsaki yake tare da burzar da iska mai xafi yana share gumi." Gaba d'aya jinsa yyi baya iya awa d'aya a cikin garin kano, kai tsaye ya d'auki hanyar Abuja, sai gudu yake zubawa." Yana dafda shiga cikin Abuja dare ya masa dolensa ya nemi wata hotel ya kwana domin tunawa da magar Abba da yake yawan yimasa akan ya daina tuk'in dare." Juyi yakeyi akan gadon yana hasko fuskar dijama, ya kuma mirginawa zuwa ruf da ciki, maganar Abba ta fad'o masa a rai a kan sulaiman, wani dogon tsaki yaja ya mik'e tsaye ya fad'a toilet yana fad'in Sam baxai yiwoba dijama baxata tab'a auren sulaiman ba." Wani tafasa yaji zuciyarsa nayi masa Wanda ya rasa dalili, Ruwan sanyi ya sakarwa kansa yana lumshe ido tare da sauke ajiyar zuciya, Yusra kuma na ganin dare yayi mahmud baidawoba tashiga tashin hankali, Tun lokacin da sukayi aure bai tab'a kwana ba a gida ba, ko da dai ba kulata yakeyiba baya son ganinta amma ganinsa da takeyi kullum yana sanyata farin ciki." Da kyar tasamu safiya ta waye mata, amma ba mahmud babu labarinsa." Kuka takeyi sosai ta d'auki waya takira Daddy, Ba sallama bare gaisuwa cikin muryar kuka da tashin hankali tashiga fad'in , "Daddy mahmud bai kwana a gida ba." Nashiga uku daddy kaje kasanya a nemomin Mahmud a duk inda yake, daddy kai kayi mun Alk'awarin duk abinda nakeso zansamu, daddy ina son mahmud amma mahmud baya sona baya kulani baya son ganina a kusa dashi daddy kasanya Mahmoud dole ya soni ya kuma kulani." Runtse ido yayi yanajin bak'in ciki da k'unci kukan da tilon yarsa takeyi, Da kyar ya bud'e baki yayi mata magana "shalele daina kuka mahmud lafiyarsa k'alau yaje kano wurin bikin kammala makarantar k'anwarsa dijamah." Kisanya ido yau mijinki xai dawo gareki, kuma ki kwantar da hankalinki zanyi masa magana dole ya dinga kulaki dole ya soki idan ba hakan ba nasan matakin da zan d'auka daga shi har mahaifin nasa." Cikin d'aga murya tace "no daddy nasan halinka kana da zafi sosai, nasan KA baka da tausayin nak'asa da kai karkayiwa mijina illah, karka kuri mijina daga aikinsa, idan kuwa ka aikata hakan to kasani nima bazaka sameniba, domin kuwa farin cikin Mahmud shine nawa, tana kaiwa nan takashe wayar tana kuka tare da share hawayen fuskarta." Shuru tayi tana nazarin maganar daddy dayace mahmud ya tafi kano wurin bikin kammala karatun k'anwarsa dijamah, tashiga maimaita sunanan dijama? To wacece dijama a wurinsa?" Tabbas tana yawan jin sunan dijama a bakinsa, Wani lokacin da zarar yashigo gida yana fara'a a waya a kunnensa yana dariya to daga k'arshe zataji yace Cikin sigar zolaya "sai anjima yar k'anwata dijama 'yar gidan tsohuwa, ita kuma tana masa shagwab'a bata son yana kiranta da wnn sunan shi kuma yana dariya." Tabbas ba iya k'anwarsa kad'ai ta tsayaba akwai wani Abu a tsakaninsu." Idonta ya kuma yin ja wani sabon kishi taji ya taso mata hawaye na zuba a idonta tashiga fad'in "na rantse da Allah duk macce da tace zata rab'i mijina nayi alk'awarin sai na kasheta da hannuna." Sallamar Aminiyarta tajiyo a bayanta da gudu ta tashi ta rungumota ta kuma fashewa da wani sabon kuka, Lubcy ta sanya hannu tashiga share mata hawaye tana fad'in "daina kuka Yusra duk abinda yake faruwa nasani inajin lokacin da kike fad'awa daddy, Dibeki dan Allah babu abinda kika rasa a duniya kina da kyau kina da kud'i, kina da ilimi, akwai Alhazai yan gayu masuji da kud'i da k'uruciya wad'anda ke iya biyawa ko wacce irin macce buk'atarta, amma kinzo kin mak'alewa mahmud sai wulak'antaki yakeyi yana juyaki kamar sitiyarin mota." Wai mekika gani a jikinsa ne kika wani mak'ale masa ne?" Dan haka ni kika ganni kwata-kwata bana sha'awar aure a rayuwata saboda babu abinda ke cikin rayuwar aure sai bak'in ciki da tashin hankali." Wani kallo yusra take bin lubcy dashi, duk cikin magagganunta babu Wanda tafi b'ata mata rai kamar metagani ajikin mahmud da tawani likemasa." D'aga mata hannu tayi tace "Dakata lubcy bana son haka,akwai abinda nagani Kuwa a jikinsa Wanda ke bazaki ganeba." Snn Kuma bana buk'atar mazan waje mijina nakeso shi kad'ai nakeso na mallaka domin shi nakeso a rayuwata akan komai daga ciki Kuwa har da kaina." na d'auka zuwa kikayi kibani shawara ta yanda zan mallaki mijina. a matsayinki na Aminiyata wacce na yarda da ita zuwa kikayi kibani shawara hanyar da zanbi mijina ya soni ya kuladani ya Kuma amince mun, ya yarda dani a kan cewa ni masoyiyarsa ce." Lubcy taga b'acin rai k'arara a idon Yusra Wanda bata tab'a ganiba, Tabbas Yusra tayi nisa bata jin kira, ta sauke ajiyar zuciya ta dafata tace "yi hak'uri Yusra na fahimceki, na fahimci yanda kikeji a kan mahmud, zan baki shawara ta yanda zaki mallaki Mahmud ya zama naki Cikin sauki batare da Kinsha wata wahala ba." Sai a lokacin Yusra ta sauke ajiyar zuciya ta maida hankalinta gaba d'aya wurin lubcy." Suna cikin sak'awa da kwancewa sukaji tafiyar mutum a bayansu, Da sauri suka waiga suga mahmud ne ya shigo ko ta inda suke bai kallaba yayi tafiyarsa d'akinsa." Lubcy ta bishi da ido tana kallonsa, tabbas mahmud namijine, namijin gaske Kuwa, mai razana 'yan maxa bare 'yan mata." Murmushi Yusra tasaki da taga yanda jikin lubcy ke rawa dataga shigowar mahmud, Dafata Yusra tayi tana dariya tace "kwantar da hankalinki lubcy ai baiji abinda muke cewa ba, kijirani nashiga wurinsa na fito sai muci gaba da maganarmu." Lubcy ta zaro ido waje tare da mik'ewa tsaye ta d'auki jakarta da tallakaminta ta kalli Yusra tace "sauran bayani zan kiraki a waya muk'arasa, bata jira abinda Yusra zataceba tayi fice warta gidan." Kallo Yusra tabita dashi tana murmushi duk rashin kunyar lubcy ganin Mahmud ya firgitata." Juyawa tayi tanufi d'akin mahmud Wanda tayi sa'a bai sanya key ba, Koda tashiga yana toilet yana wanka murmushi tayi ta zauna a gefen gadonsa, Wayarsa ta gani a kan gado ya ajiye ta ta sanya hannu ta d'auka tashiga Gallery tana diba hotona, Gabanta ne ya yanke ya fad'i da ta dinga ganin hotonan wata kyakkyawar yarinya tana murmushi, can kuma taga wani hoto Wanda sukayi tare da mahmud a motarsa ya d'an sunkuyo kusa da ita suna dariya gaba d'ayansu, aka d'auke hoton Tashin hankali tashiga Wanda baya misaltuwa tadinga ganin hotonan da sauri da sauri kafin ya fito, Wani hoto taci karo dashi na wata yarinya 'yar k'auye daga ganin hoton a k'auye aka d'auke shi, Abin bai kuma d'aga mata hankaliba sai da taka mahmud ya goya yarinyar a bayansa suna dariya aka d'aukesu hoton." Jawo hoton tayi ta k'urawa yarinyar ido "tabbas wnn itace a cikin hoton farko da tafara gani "Wnn wacece?" Meye matsayinta a wurinsa?" Daga ganin wa'dan nan hoto nan sun nuna tana da mahimmaci a rayuwarsa, toko itace zab'insa wanda yakeso a ransa?" Babu wacce ta fad'o mata a rai sai sunan dijama 'yar gidan tsohuwa, tabbas ita ce tashiga furtawa tareda mik'ewa tsaye, tana kallon hoto nan." Kira ya shigo wayar taga ansayawa number sweet sister ta tabbatarwa kanta dijamar ce ta kira shi" Sauri tayi ta d'auki wayar tare da karawa a kunnenta tana saurare." Dijama tana jin an d'auki wayar tafara maganarta mai sanyi cikin shagwab'a "yaya shine kayi tafiyarka ko sallama bamuyi ba, na ajiye maka wani Abu Wanda idan KA ganshi saikaji dad'i a ranka amma fitowar da zanyi tsohuwa take fad'amun kayi tafiyarka, ko wani abin naimaka pls kayi hakuri kaji yayana." Dum gaban Yusra ya fad'i jikinta ya soma rawa saboda masifar kishi, Dijama taji anyi shuru baiyi maganaba ta janye wayar a kunnenta ta kuma kallo ko ya kashe wayar ne, taga ba kashewa yayi ba, cikin siririyar murya tace network problum yaya kanajina?" Yusra tace "karkiga laifin network yanajinki maganace kawai baya iyayi, saboda yana cikin wani sabon network mai wuyar misaltuwa Wanda duk Wanda ya haushi bayaji baya gani har sai lokacin da ya sauka." Dan haka Wanda kike nema yana kan network baya da lokacin kowa har sai lokacin da ya sauka a kai, Ta kashe wayar tare da tsurawa wayar ido sautin muryar dijama namata yawo a kai." Wanda yayi dai dai da fitowar mahmud daga toilet d'aure da towel a jikinsa gaba d'aya gashin jikinsa ya kwanta a kan kyakkyawar farar fatarsa." Ido ta k'ureshi dashi tana kallon kyakkyawan jikinsa tare da faffad'an k'irjinsa tana lasar baki saikace mayya." Shi kuma kallon tsana yake mata tareda tambayar ubanme take masa a d'aki, Idonsa ya d'ora akan wayarsa dake hannunta, zaro ido yayi 😳 alamar kin rainani yayi kanta." [8/2, 1:16 PM] El-hajj✨✨✨: 🌹 *DEEJAMAH* 🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writteng by *UMMU SAFWAN* (Fareeda Basheer) *47* Ya mik'a mata hannu yace "bani waya na." Faffad'an k'irjinsa take kallo Wanda yacika da gashi a kwance kwanin ban sha'awa, Wata kalar sha'awarsa ce ta dirar mata, Tana matuk'ar son mahmud, Mahmud yayi mata yana d'aya daga cikin kalar mazan da take so jarumai masu iya sarrafa macce kota ina." Ganin ya nufota gadan-gadan tayi sauri ta tura wayar cikin bra d'inta, Ko ba komai tasan dole ya sanya hannu a ciki ya d'auko wayarsa." Mahmud yana ganin hakan ya gane manufarta, hannunsa ya d'aga ya kwad'a mata mari tare da mik'a mata hannunsa yace "bani wayana." Zabura tayi a gigice tayi cikin jikinsa ta rungumesa tare da d'ora kanta akan k'irjinsa idonta yana zubar da hawaye tana fad'in "ina sonka Mahmud koda zaka kasheni." Tsaye yayi yana kallonta cike da mamaki ta yanda take kuma tusa kanta a k'irjinsa." Wani marin ya kuma tsinka mata tare da cireta daga jikinsa yayi jifa da ita a bakin k'ofa." Wanda yasa tasaki wani kalar kuka mai sauti." Ya nufeta gadan gadan ya mik'a mata hannu yace "bani wayata." Jiki na rawa ta ciro wayar a cikin boos d'inta ta mik'a masa tana matsar hawaye." Karb'a yayi tare da wurga mata wata kalar harara mai cike da tsana, Yace "bana sonki Yusra bana son ganinki na tsaneki nakasasshiya marar tarbiya." Tashi kifitarmun daga d'aki jarabbiya babu abinda zanyi da nakasasshin jikinki Wanda kike yiwa duniya talla kowa ya gama gani." Tunkarota ya kuma yi, zai kuma dukanta Tana ganin hakan tayi saurin mik'ewa tsaye da sauri ta bud'e k'ofa ta fita waje da gudu tsaye tayi a bakin k'ofa tana kallonsa wata k'aunarsa takeji tana kuma ratsata, ta sanya hannunta ta shafe hawayen dake mata ambaliya a fuska tace "koda kasheni zakayi bazan gaji da furta maka ina sonka ba, Mahmud ina sonka kuma bazan daina sonka ba, Nayi Alk'awari sai na mallakeka sai na nuna maka iyakata a gidan nan sai na mallaki abinda nake so daga gareka." Sai na mallaki zuciyar KA da gangar jikinka ko ta tsiya kota bala'i kota girma kota arzik'i ka saurara KA gani." Belt d'insa ya lalubo yayo kanta a guje tabar wurin ta nufi d'akinta." Dogon tsaki yaja ya koma kan kado ya zauna tare da dafe kai🤦🏻‍♂ shi dai ya rasa yanda xaiyi da yusra." Wayar sa ya d'auka domin ya kira Khalil akwai sak'on da yakeso ya fad'a masa." Sunan dijama ya gani alamar takirashi, minti talatin da suka wuce, Fasa kiran khalil d'in yayi, Ya danna number dijama Yashiga kirata, duk da dai itama haushinta yakeji yanzun ganin yakeyi harda had'in bakinta sulaiman ya tunkari Abba da zancen aurenta." Kira uku yayi mata bata d'auka ba, ya Girgiza kai yace "lallai yarinyar nan sainayi maganin rashin kunyarta." Ya mik'e tsaye ya sanya kayansa ya nufi masallaci." Dijama kuma tin lokacin da taji muryar Yusra tashiga cikin damuwa, da tinani Me Yusra take nufi da yaya mahmud ya hau network d'in da bayajin Kowa a wnn lokacin?" Tana nufin yana tare da ita a shinfid'a d'aya Kenan?" Wato yana ganin kiranta kin d'auka yayi, sai dai yabawa matarsa wayar ta d'auka?" Wato yafi son matarsa akan d'an uwansa, kenan?" Wani hawayen bak'in ciki yashiga zubar mata, takai kwance rufda ciki tana kuka tana ganin kiran wayarsa yana shigowa a wayarta tak'i d'auka, saima ta kuma fashewa da wani sabon kuka mai sauti." Wanda yajawo hankali mommy da tsohuwa dake zaune a Palo wuri d'aya." Da sauri suka mik'e a tare suka nufi d'akin domin ganin lafiyarta." Kwance suka tarar da ita rufda ciki tana ta faman kuka bata San da shigowar suba." Mommy takira sunanta "Ummie meyake damunki?" Meyafaru kike kuka?" A hankali ta mik'e zaune tana goge hawayen fuskarta, tsohowa ta mere baki tace "zancen gizo ai bai wuce na k'ok'i." Maganar d'ayace wacce muka rasa mafita a kanta, Tayi ta gumi tace "oh ni Hadiza zamani🤔 ya lalace yaran yanzun inbanda zurfin ciki babu abinda suka ajiye." [8/2, 1:16 PM] El-hajj✨✨✨: *DEEJAMAH* ( _'Yar gidan tsohuwa_ ) Writteng by *UMMU SAFWAN* (Fareeda Basheer) *48* Tsohuwa ta kuma mere baki tace "Ke malama ki daina yimana kuka Addu'a ya kamata ki rink'ayi Allah ya yaye maku wnn zurfin cikin dake damunku, Idan ba hakan ba ninasan mafita." Ta juya ta fita." Mommy tabi tsohuwa da kallo tana murmushi, snn ta mayar da kallonta a wurin dijama taje wurinta kan gado ta zauna a kusa da ita, Tarik'a hannunta takira sunanta a hankali cikin sanyin murya tace "ummie meyake damunki fad'a mun damuwarki, me kikeyiwa kuka?" Rausayar da kai tayi cikin muryar tausayi tare da dafe kai tace "bakomai mommy kaina ne ya keyi mun ciwo." "Subahanallahi mommy tace " kinsha magani Kuwa?" Girgiza kai tayi tace "A'a." Mik'ewa tsaye mommy tayi cikin hanzari ta d'auko maganin ciwon kai tare da ruwa ta bata tasha." Tace "Ki daina sanya damuwa a ranki kinsan kina da matsalar ciwon zuciya, ki sanyawa ranki duk abinda kikeso koda baki fad'a mana ba munsanshi kuma zamuyi maki shi kinji ko." Ta d'aga kai alamar "to." Snn ta dubi mommy cikin murya k'asa k'asa tace "mommy me tsohuwa take nufi da zurfin ciki mukeyi?" nida waye muke zurfin Cikin?" Murmushi mommy tayi ta dafa kafad'arta tace "rabu da tsohuwa ummie kinsan halinta abin magana baya mata wuya, ki daina biyewa maganar tsohuwa." Ki kwanta ki huta kafin fateema ta dawo daga inda na aiketa, Snn mommy ta mik'e ta fita tareda rufo mata k'ofa." ***************** Bayan Mahmud ya dawo daga masallaci, still wayar dijama yaketa faman kira tak'i ta d'auka, daga k'arshe sai ma ta kashe wayar gabaki d'aya." Zaro ido yayi yarik'e. Baki yashiga maganar xuci "to me take nufi?" Meyake faruwa ne? Wanda yasa dijama bata d'aukar wayarsa?" Wayar mommy ya shiga kira itama bata d'aukaba kiran sulaiman ya shigo wayarsa, ya katse masa kiran mommy da yakeyi, Yana ganin sunan sulaiman a wayarsa yaji wani b'acin rai yazo masa ya harare wayar kamar sulaiman d'in yana ganinsa, Snn ya d'auki kiran ya kara a kunnensa batare da yayi magana ba." Dariya sulaiman ya saki yace "haba abokina Allah ya huce zuciyarka duk da bansan laifin da nayi maka ba kakejin zafina." Mahmud yace "don Allah malam kayi sauri ka fad'i dalilin Kiran nawa a dai dai wnn lokacin saboda ina da abinyi." Sulaiman yace "to sirikina tuba nakeyi, dama maganar d'aya dai ce ta k'anwarka kuma matata insha Allah, Yaci gaba da cewa Yaya Mahmud kaina bisa wuya ina Neman izininka da KA amince a sanya mana ranar aurenmu tunda muna son junanmu tsakanina da ita." Gaban mahmud ya yanke ya fad'i, ya d'an jingina a bango snn yace "wato kana nufin kun kammala komai rana kuke jira a sanya maku?" Sulaima ya gintse dariyarsa jin muryar mahmud kamar cikin tashin hankali" Yace "ai nasan kasan da hakan domin nasan Abba zai gaya maka." Mu yanxun amince warka kawai muke nema abokina." nasan a duniya babu abinda bazaka iya yimun ba, in har baifi k'arfinka ba." Mahmud yayi saurin dakatar da maganarsa a fusace yace "banda wnn na rantse da Allah idan har sai na amince snn zaka auri dijama sai dai KA mutu da sonta." Kai bari makaji dijama baxata aureka ba, nine Wanda zan aurar da dijama ga Wanda nakeso ga Wanda naga dama, Sam baka cikin tsarin mazan da nake buk'ata dijama tayi rayuwar aure dasu." Duk wani Abu naka da wasu kayanka wad'anda Abba da mommy suka karb'a gobe zanzo na mayar maka da abinka saboda ba Wanda yakeda hak'in ya zab'awa dijama Mijin aure sai ni, kuma ban zab'eka ba Dan baka d'aya daga cikin, ya na kaiwa nan ya kashe wayarsa." Zuciyarsa na tafarfasa ya rasa dalilin da yasa duk sulaiman yayi masa maganar aurensa da dijama jiyakeyi kamar ya had'iye xuciya,,saboda wani zafi da yakeji yana taso masa." Cikin k'unar zuci ya nufi gida, ya fad'a d'akinsa kai tsaye a kan makeken gadonsa ya fad'a ya kwanta rigingin yana kallon silin tare da tunanin kala kala. Idonsa yayi ja kamar garwashin wuta, yashiga tinanin wato k'arya dijama take masa da tace bata kula kowa?" Ashe soyayya takeyi da abokinsa har sun tsayar da maganar aure?" Yaushe dijama ta koyi k'arya?" Wani dogon nishi yaja ya lalubo wayarsa ya danna number ogansu Wanda aka canxa masu." Ringing biyu wayar tayi oga ya d'auka cike da girmamawa mahmud yake gaidashi tare da bashi girmansa, Oga ya amsa yana fara'a domin yana matuk'ar son mahmud saboda gaskiyarsa." Mahmud yashiga gabatar masa da uxirinsa yanaso ya bashi izini zaije kano yayi sati biyu." Oga yace "mahmud kafi k'arfin komai a wurina, amma kayi hak'uri kabari sai k'arshen wata katafi domin cikin satin nan akwai aikin da zan turaku kuyi mai mahimmaci." "To Mahmud yace yayi masa sallama ya kashe wayar tareda yin wurgi da wayar gefe d'aya, Can kuma ko meya tuna yayi saurin mik'a hannunsa ya kuma d'aukar wayar ya shiga kiran number Abba." Sulaiman kuma duk wayar da sukeyi da Mahmud Abba yana kusa yana saurarensu yana murmushin." Abba yace Allah ya kaimu goben ai nasan kafin gobe zai kirani a waya." Ai kuwa bai rufe bakiba sai ga kiran Mahmud ya shigo a wayar Abba, Abba ya kalli sulaiman suka saki murmushi a tare snn Abba ya d'auki wayar tare da karawa a kunnensa.........." [8/2, 1:17 PM] El-hajj✨✨✨: *DEEJAMAH* ( _'Yar gidan tsohuwa_ ) Writteng by *UMMU SAFWAN* (Fareeda Basheer) *49* Sallama mahmud yayiwa Abba cikin ladabi da girmamawa tare da gaidashi." Abba ya amsa masa tare da tambayarsa ya aikinsa." "Lafiya lau." yace snn ya d'an nisa yace "Abba naji wata magana a bakin Sulaiman gaskiya ne Kuwa?" Abba ya kalli sulaiman sukayi murmushi a tare snn yace "wace magana gaji daga cik Kenan?" dan kuwa magagganun yawa garesu." Gaban mahmud ya yanke ya fad'i yace "Abba wai cewa yayi kungama shirya komai ni kuke jira na amince a sanya ranar aurensa da dijama." Abba yace "tsohon zance kenan, ai tuni na dad'e da Sanya ranar aurensu wata biyu masu zuwa, Zan had'asu tare da fateema nayi masu aure na huta, tunda har sun samu wad'anda sukeso." Zuciyar mahmud tashiga suya, cikin b'acin rai yace "Abba in har inada iko kuma and'aukeni a matsayi Wanda ya isa da dijama Wanda yakeda iko da ita kamar yanda kake cewa a lokacin baya." Abba Ni dai ban amince dijama ta auri sulaiman ba sam." Abba yace "saboda me?" Meye dalilinka?" Shi sulaiman ba mutum bane?" Shin wai ma tsaya mahmud idan kace baxata auri sulaiman ba kai zata aura?" Gaban Mahmud ya fad'i.' Ya rasa amsar da zaiba Abba." Abba yaci gaba da cewa "ni baxanci gaba da ajiye yara a gabana ba ina kallonsu bayan ko wacce daga cikinsu ta isa aure." Auren dijama da sulaiman ba fashi nan da wata biyu masu zuwa, ko kashirya ko baka shiryaba." Abba bai jira amsar da Mahmud zai basaba yayi saurin kashe wayar yana kallon sulaiman suna murmushi, Sulaiman yace "bantab'a ganin mutum mai zurfin ciki kamar mahmud ba." Abba yace "Ayya kuwa zai fitar da abinda ke ransa Kuwa?" Sulaiman yace "xai fitar Abba kabani lokaci ka gani." Dijama na fitowa taji Abba yana waya da wani yana fad'a masa aurenta da sulaiman nan da wata biyu masu zuwa." Da baya baya ta koma tana ganin jiri ta fad'a d'akinsu tana sauke numfashi sama sama kamar wacce tayi gudu, Tunani tashigayi aurenta saura sati biyu?" Kuma da sulaiman?" abokin yaya mahmud?" Hawaye suka shiga zuba a idonta tana fad'in "ita bata son sulaiman bata tab'a sanyashi a cikin jeren maxan da take so ba." To ita idan ta auri sulaiman ya zatayi da Anty Fareeda matar da ta d'auketa tamkar k'anwarta ta nuna mata so, babu abinda bata iya mallaka mata a rayuwa Amma a wayi gari saboda butulci itace Zata auri mijinta." Sam bazai yiwoba wlh bata son sulaiman bata iya aurinsa." "To wa kikeso wazaki aure?" Zuciyata ta bata amsar maganrta." Yaya Mahmud ya fad'o mata a rai ta kai kwance ta saki kuka mai sauti." Da tuna da kalaman Yusra a lokacin da takira wayarsa." Shima mahmud ya kasa tsaye ya kasa zaune sai safa da marya yakeyi a tsakar d'aki yana girgiza kai, jinsa yakeyi kamar yayi tsuntsuwa ya dura garin kano, Amma ina ogo ya hana." A daren ranar baiyi bacci ba sai sak'awa yakeyi da kwancewa." Amma muddun yana raye dijama bazata tab'a auren sulaiman ba." Tambayar Abba ta fad'o masa a rai "kai xaka Aure tane?" Da fe kai yayi yace "sai dai inje in d'aukota, Ba wanda ya sani indawo da ita wurina." ***************** Khalil kuma tun a wurin bikinsu dijama Abba bai kuma sanyashi a idoba yau kwana biyu kenan." Kwata kwata ya daina kwana a gida hankalin Abba ya tashi yashiga tambayar mommy lafiya Kuwa Khalil yake?" Mommy tayi murmushi domin tasan halin Khalil sarai, tace "lafiyarsa k'alau kakira wayarsa kaji." Abba yashiga kiran wayar Khalil dake can kwace tareda budurwasa Ashanty suna holewarsu, dai dai lokacin da ya haye kanta kiran Abba ya shigo wyarsa." Yana kanta ya mik'a hannu ya d'auki wayar tare da saita natsuwarsa, yayi sallama tare da gaida Abba." Abba ya amsa yashiga tambayarsa "khalil lafiya k'alau kake kwana biyu baka zo gida ba?" A ina kake kwana?" Ina kake cin abinci?" Abba yashiga yi masa fad'a kasan bana son shashancin bazan, nawa kake kwata kwata shekarar KA nawa da har zakaje wani wurin ka kwana batare da ka sanar da muba." Khalil da bakinsa ke cikin bakin Ashanty yana tsotsa hannunsa d'aya yana rik'e da boobs d'inta yana shafa kan yana wasa dashi, D'aya hannunsa ne yake rik'e da wayar Abba yana saurarensa." Bakinsa ya cire daga cikin bakinta, dayaji Abba yayi shuru alamar ya gama fad'an kenan." Yace "Abba kayi hak'uri bawani wajen natafiba ina makaranta jarabawa mukeyi karatu mukeyi sosai da zarar mun kammala zandawo gida Abba KA kwantar da halinka." Abba yaji dad'i sosai yyi murmushi yayi masa Addu'a Allah yabada sa'a. Ya kashe wayarsa." Mommy najin yanayin maganar khalil ta fahimci halin da yake ciki sai dai kawai ta girgixa kai tace "Allah ya shirya." Abba yayi saurin juyowa ya kalli mommy yace "wai meyasa baki yiwa yaron nan kyakkyawar fahimta ne sai na dinga ganin a koda yaushe kina masa kallon rashin yarda nifa bana son haka." "Yi hak'uri mommy tacewa Abba, fahimta nace har yanzun bakayi ba a kan khalil." Kuma ai ni yanzun Addu'a ce nayi, masa nace "Allah ya shirya." "Ameen Abba yace tare da mik'ewa a fusace yayi shigewarsa d'aki." Kallo mommy tabishi da shi tayi murmushi itama tamik'e ta bishi domin ta lallashesa." Khalil najin Abba ya tsinke wayar." Ya saki murmushinsa na yan duniya, Ya kashe wayar gaba d'aya dan kadda a kuma nemansa yayi jifa da ita gefe d'aya, yaci gaba rabawa Ashanty aiki ba sauk'i." Saida suka d'auki lokaci mai tsayi suna Abu d'aya snn ya saurara mata koshi ba wai dan yagaji ba sai dai gani da yayi ta bashi tausayi tagaji sosai, Dan baya son yana hutawa da macce d'aya, yafison ya had'asu su biyu ko ukku idan wnn tagaji sai ya juya wurin wnn" Bayan sunfito daga wanka yana shafa mata mai a jiki, yana kuma k'ara shanshafa, yana matuk'ar son ashanty duk a cikin 'yan matansa ya fisonta a kan kowa saboda tafi gamsar da shi, Kuma ya shaida shi ya fara bud'eta a leda." Shafata yakeyi tana lumshe idon jin dad'i, har zuwa wurin k'ugunta zuwa saman cikinta, jiyayi cikinta yayi masa k'arfi ba kamar da ba dayake wasa da cibiyarta a kan taushin cikinta da laushinsa." Kuma kallon cikinta yayi yaga yad'an taso kamar macce mai ciki." Hannunsa ya Sanya ya d'an latsa cikin ai Kuwa yajisa da k'arfi ya zira hannunsa a cibiyarta yana wasa da ita kamar yanda ya saba, wani gantsewa tayi saboda zafin da taji cibiyarta nayi mata taja da baya." Kallo ya bita da shi tabbas Ashanty ciki gareta, sai yanzun ya lura da yanda cikinta ya girma ya fito." Kallonta yayi da kyau yakira sunanta yace "Aisha watanki nawa bakiyi period ba?" Murmushi tayi cikin shagwab'a da sakuwa tace "wata bakwai honey." Wani tabbulan yayi ya fad'o daga kan kujerar jikin madubi saboda razana da tsoro." Zaro ido yayi yana kallonsa yace "bakida hankali ne? Kin Kuwa san abinda kike fad'a?" Turo baki tayi tace "meyafaru honey?" "OK baki masan abinda yake faruwaba saboda kina dak'ik'iya kidahuma marar hankali so kikeyi kitonamin asiri." "Nifa bansan abinda kake magana a kansaba kuma ni kadaina kirana dak'ik'iya." Mik'ewa tsaye yayi zufa na zubo .masa duk da sanyin ac dake d'akin ya kuma kallonta yace "yo ai har k'ara dak'ik'iyar dake, kina d'auke da ciki harna tsawon wata bakwai baki saniba." [8/2, 1:17 PM] El-hajj✨✨✨: 🌹 *DEEJAMAH* 🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writteng by *UMMU SAFWAN* (Fareeda Basheer) *50* Murmushi tayi tace "nasani mana sai dai idan kaine baka saniba, To meye abin d'aga hankali honey dan ina d'auke da cikinka na wata bakwai?" "Ai ni duk a tunanina idan kasani murna zakayi da farin ciki ka kusan zama Baba zamu haifi d'an so." Bai san lokacin da ya wanke mata fuska da mariba yace "bakida hankali d'an shege zaki kira da d'an so?' Aisha ashe baki da hankali bakida tunani, so kike ki tonamin asiri a idon duniya." Da wani ido kikeso na kalli mahaifina Wanda yafi Kowa yarda da dani, ya Amince min d'ari bisa d'ari." Gabanta ya kai gurfane ya ruk'o hannunta yashiga bata hak'iri "Pls Aisha ki amince min mutafi asibity a zubar da cikin nan nayi maki alk'awarin bayan an zubar da shi zan aureki." Kallon cikin idonsa ta shigayi ta kuma tabbatar da cewa da gaske yakeyi, Tunawa tayi da wata k'awarta suwaiba itama a wurin zubar da cikin tarasa ranta." Tasan halin Khalil sarai idan tayi masa musu yana iya sanyawa a zubar da cikin kota tsiya kota arziki don ba mutumci garesa ba, sai dai ita ta rasa ranta." D'aga masa kai tayi alamar ta amince a zubar da cikin." Murmushin jin dad'i yayi yace "yanzun ki tashi mutafi asibity nayiwa likita bayani.' Shafa gefen fuskarsa tayi cikin wani salo na bariki tace "lah honey ai ba sai munje asibity ba, Bara na koma gida akwai wata k'awata Wanda ta kware sosai a Wnn harkar sai ta fad'a min maganin da zan sha wadda cikin zai zube cikin sauk'i batare da nasha wata wahala ba." Murmushin jin dad'i yayi yace "gud kinkawo shawara mai kyau, Yaciro kud'i cikin wata loka dubu d'ari ya mik'a mata yace "idan kina buk'atar wani abin kiyimun magana zankawo maki." Amsa tayi tana godiya snn ta mik'e tsaye ta sanya kayanta tayi masa sallama ta fita." Bayan ta fita ya bita da kallo yana dariyar mugunta "ubanwaye zai aureki?" Allah ya tsareni dana aure macce wacce nagama kwashe rabona akan hanya na kai ta gidana, da wacce tarbiya zata reni'ya'yana." Ya saki dariya mugunta yabita da harara kamar tana ganinsa yace "sakarai na dai samu cikin yafita a jikinki, na barki kuma har abada tunda naga alamar ko zariyar wando ta rab'eki sai kin d'auki ciki." Itama Ashanty tana fita, Ta sanya kud'in a jaka tace "baka da hankali khalil kana nufin inje wurin zubar da cikin in mutu kenan, Sam bazan iyaba nafison na barshi duk wata wahala da tsangwama da zansha a gida na yarda kuma na Amince indai har zan tsira da rayuwata da abinda na haifa." *************** Alhaji Atiku duniya ta juya masa baya yanaji yana gani abinda yafi k'arfinsa a da a yanxun nemansa yakeyi, 'yan mata abokanan holewarsa duk sunja baya garesa dama mafi yawan Matan da yake ma'amala dasu, Dukansu wasu daga cikiñsu matan yaransa ne, Wasunsu kuma Matan da suke k'arshinsa ne a wurin aikinsa, yanzun kuma duk sunja baya basa kulashi dama kulashin da sukeyi na dolene saboda suna son aikinsu dan kadda ya koresu." Juya masa baya da 'yan mata .sukayi abin yana damunsa ya k'ara sanyashi shiga cikin damuwa." Zaune yake yana nazarin irin matan da yake ma'amala dasu a rana d'aya amma yanzun ba ko d'aya dukansu sun gujesa." yau kam ya yanke shawarar zai fita da kansa yaje gidan mata ya nemo wasu sabbin babys wad'anda suka kware a harka." Hakan Kuwa akayi bayan sallar Isha'i yayi kwalliya cikin manyan kaya kamar wanda zaije wurin d'aurin aure ya fita, kai tsaye ya nufi gidan mata.' Gidan mata gidane da yayi suna a cikin garin Abuja duk wani shegen namiji mai kud'i ko milki ko wani muk'ami idan yna da buk'atar macce a nan yake zuwa ya zab'i babys wad'anda yakeso masu zafi, Gasu nan. A azube saika zab'a wacce tayi maka iya kud'inka iya shagalinka barikinka Aljihunka." Alhaji Atiku yana shiga wurin ido yayi kansa, mata suna ganin sa, sai girgiza sukeyi ta d'aukar hankali domin su burgeshi mafi yawansu dagà ciki duk k'awayen Yusra ne, kuma sunsan shi mahaifinta ne, Amma da yake bariki ce basu damu da hakan ba." ai kuwa bai kauda idonsa daga gare suba, abin nema yasamu sai wasar baki yakeyi yana k'arewa ko waccensu kallo, snn ya shiga zab'ar manyan mata guda biyu masu ji da kansu wad'anda komai yaji garesu ya kama d'aki a cikin gidan suka shiga holewarsu." *************** Mahmud aiki sukeyi gadan gadan, sun samu labarin akwai wani gidan mata da aka bude manya mutane suna zuwa wurin babu abinda ba'ayi a wurin." Ogansu ya sanya ayi masa bincikin wurin a gano iya abubuwan da akeyi a wurin kafin sufara kame." amma duk aikin da yakeyi baya cikin kwanciyar hankali idan ya tuna auren sulaiman da dijama Allah Allah yakeyi wata ya k'are lokacin da ogo ya d'ibar masa ya dira garin kano, Abu d'aya zaiyi shine ya sace dijama ya bar garin da ita yadawo da ita gabansa yaga Wanda zai d'aura mata aure da wani sulaiman can" **************** Tun ranar da Yusra taci duka a wurin mahmud ta farajin tsoronsa, ta zubar da makaman yak'inta domin ta fahimci mahmud ba irin mazan da ake tilassamawa bane akan dole sai ya so wani abin." Zama tayi, tayi naxarin abinda mahmud yakeso a jikin macce meyakeso a rayuwarsa." Pic d'in dijama ya fad'o mata a rai, gaba d'ayansu ba Wanda take sanye da k'ananun kaya dukansu manyan kayane atamfa da lesi wani harda hijabi." hakan ta d'aukar wa kanta zata fara shigar manyan kaya indai yin hakan zai sanya mahmud ya sota." Cikin kwana biyu ta dage da shiga kala kala ta manyan kaya wani lokacin harda hijabi take had'awa." Duk lokacin da ta kwatanci ya Kusan dawowa gida zata shinfid'a darduma ta dinga Jan carbi" saboda tasan mahmud mutum ne mai son ibada." duk da dai bata San abinda ake fad'aba idan ana Jan carbin ba." sai dai kawai ta dinga motsi da baki." Amma mahmud ko a jikinsa ko kallo bata ishesaba, wani lokacin idan ya dawo yasameta a hakan yana mmkin canjin da tayi matuk'a sai dai fa bai yarda wai da gaske ta canzaba, Ita kuma ta dage sai ta sashi ya yarda ta canza ta koma kalar matan da yake so." Duk wani kalar wulak'anci da yake mata, Bata tab'a nuna masa ranta ya b'aci ba, sai dai ta bashi hak'uri cikin k'ask'antar da kai, a duk lokacin da yake Gida zata dinga yawo da hijabi da carbi a hannunta da zarar ankira sallah zatayi sauri tayi arwala ta haye kan darduma ta dinga jera salloli ba adadi." ganin baya kulata, duk wata dabara tata da hikima ta k'are, Ta kan zauna ta kalli madubi ta kalli kanta da kanta ta kuma kallon halittar jikinta ko macce 'yar uwarta idan ta ganta saita kyasa bare mahmud saikace ba namiji ba?" To shi wani irin mutum ne?" Kuma lafiyar sa k'alau bashida ko nakasa?" ko ko tsabar miskilanci ne da jin kai yanuna mata shi namijin gaske ne yana iya controlling sha'awar sa?" Abin takaici kullum kamar ana k'ara hura mata wutar soyayyar sa da tsananin sha'awarsa a zuciyarta." Mahmud yana da Duk wani abinda za'a so shi, Tun daga kan halayyar sa har halittar da Allah yayi masa, Duk macce da ta mallaki irin mahmud kallonshi kad'ai intayi ya isheta farin ciki da godewa Allah wnn kad'ai ya isheta." Yusra tana bak'in cikin rashin mallakar mahmud gashi dai mijinta ne sunyi auren amma ya mata nisa yafi k'arfinta duk da kuwa kyaunta kud'inta ilminta maccen da maza ke rububin samun irinsu, amma Mahmud ko kallo bata ishesaba Yusra dai ta zama macce mai yawan ibada ga kyauta da sadaka duk wnn tanayinsa ne idan mahmud yana gida domin taja ra'ayinsa, Tafara samun nasararsa domin ta fara gani a fuskarsa ya rage jin zafinta, Tinda yanzun yana zama a palo yaci abinci Wanda yake sayowa duk safiyar Allah." Wani dare mahmud ya fito falo zai shiga kicin shan ruwa kamar yanda Al'adarsa take duk daren Allah. Mutum ne shi mai yawan shan ruwa." Karo yaci da Yusra a kwance a falo kan sallaya sai rawar sanyi takeyi, Zazzab'i ne ya rufeta." Ta gefenta ya rab'a ya wuce yashiga kitchen ya sha ruwansa ya fito, Har zai rab'a ta ya wuce ya kuma dawo domin yaga tana kan ibada ciwo ya sameta bari ya tausaya mata." Sunanta ya shiga kira "Yusra meyafaru?" Bakida lafiya ne?" Meke damunki?" Ya sunkuya yana tambayarta tareda rik'ota ya mik'ar da ita tsaye, mahmud akwaishi da tausayin mara lafiya." Tayi saurin k'ank'ameshi "mahmud sanyi lullub'eni zazzab'i ciwon kai." Mahmud karka gyaleni, karka tafi ka barni." nan ta dinga cusawa jikinsa tana sauke mai numfashi a fuska da kunnensa cikin salo mai ta da hankali, Biye mata yayi ya dinga mannata da jikinsa sosai yana goga jikinsa a nata." Tuni suka fita hayyacinsu duka , Yusra ta gama shigewa jikinsa tare da tsananin murnar yau zata samu nasarar abinda ta dad'e tana nema." tallabarta yayi cak ya nufi kan kado da ita, Yashiga sarrafata a hankali cikin kwarewa da gwaninta." Wani nishi take fitarwa harda 'yar kuwar jin dad'i." Mahmud ya zura mata ido tare da murmushin mugunta yana k'ara tsumata, sai faman sauke numfashi takeyi gaba d'aya ta cire kayan jikinta, ta rarumoshi idonta a rufe ta fara cire masa botes d'in rigarsa, Ta tsuma iya tsumuwa mahmud yakai k'ololuwar tayar mata da sha'awa." Yana ganin ta cire masa riga tana neman zuwa a kan wandonsa ya d'auko wani kyalle ya shak'a mata a hanci cikin minti d'aya bacci mai nauyin gske ya d'auketa." Ya kalleta yayi murmushin mugunta yace "Yusra da sauranki ki yaudari Mahmud." Zan nuna mki a duniya ba komai ake nema a samu ba har Abada bazaki tab'a samun mahmud ba." Ya maida rigarsa ya sanya ya sauka daga kan gadon yayi Arwala ya nufi masallaci domin gabatar da sallar asuba." Bayan ya dawo daga masallaci ya d'auki Yusra ya kaita d'akinta ya kwantar da ita bisa gadonta Tare da mata shiri tsab irin na marasa lafiya ya fita ya gyaleta a wurin yatafi wurin exeercise d'insa da yake kullum bayan ya kammala sallar asuba." Bayan ya gama yayi wanka ya shirya tsab cikin uniform d'insa na soja Wanda yayi matuk'ar yimasa kyau ya dace da hallittarsa da fatarsa, mahmud mutum ne mai kwarjini da farin jini ga al'umma, Haka nan kawai mutane ke sonshi koda kuwa baka sanshiba kallo d'aya zaka yimasa kaji ya burgeka kana k'aunarshi." Wayarsa ya d'auka yakira Alh [8/2, 1:17 PM] El-hajj✨✨✨: 🌹 *DEEJAMAH* 🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writteng by *UMMU SAFWAN* (Fareeda Basheer) *51* Hankalin Alhaji Atiku ya tashi tare da mahaifiyar Yusra." Cikin minti goma Alhaji Atiku ya kira likitansa tare da nurse ya d'aukosu suka nufi gidan yusra." D'agawar su kenan Abba ya tsaya da motarsa, Yana ganin inda suka nufa ya shima yabi bayansu yana tambayar ko lafiya?" Cikin k'ank'anin lokaci suka isa gidan, hankalinsu a tashe, Cikin gaggawa doctor ya shiga bata taimako, gefensa d'aya nurse ce macce itama tana taimakon." Yusra dai har oxygen aka sanya mata." A hankali ta dinga bud'e idonta a lokacin poder d'in bacci da Mahmud ya shak'a mata ya saketa, Dishi dishi take ganin mutane a tsaye tsaye a kanta." Kanta taji ya mata wani irin nauyi ga Abu a gark'ame a kan hancinta tayi hanzarin mik'ewa nurse d'in tayi saurin maida ta Tana fad'in "yi hak'uri madam sannu." hannu tasa ta fisge robar oxygen d'in da k'arfi tana masifa." "Meya sameni wayasa min wnn abin?" Jikinta taji ba kwari, bata da k'arfi ko da motsin kirki bata iyayi, Ta koma ta kwanta iyayenta sukayi kanta suna mata sannu, Alhaji Atiku duk ya rud'e yake sai tambayarta yakeyi meke damunta?" Abba ya shigo tare da sallama ganin Yusra a kwance ya tabbatar masa da bata da lfya." Suka gaisa da Alhaji Atiku, zai tambayesa abinda yake damun ta kenan doctor ya Turo k'ofa ya shigo bayan ya gama 'yan aune aunensa." Ya kalli Alhji Atiku da mahaifiyar Yusra yce "agaskiya ciwon zuciya yake son ya kamata, Shi yasa numfashinta yake d'aukewa." Alhaji Atiku yayi kanta da sauri cikin tashin hankali da rud'ewayana fad'in "ciwon zuciya?" "Yata kwaya d'aya tilo?" Yusra Duk abinda kikeso zamu Miki a duniya meke damunki da har kike tunani?" D'aga kai tayi ta kalli Mahmud da ya hard'e hannu a k'irji yana mata dariyar mugunta tare da d'aga mata gira." Wani irin haushinsa taji tare da sonsa mai tsanani sun shige ta lokaci guda ta lumshe ido hawaye na zuba zuciyarta na mata zogi da rad'ad'in abinda ya mata ga sonsa mai k'arfi a zuciyarta." Ga ciwon irin wulak'ancin da yake mata, Duk Kuwa da jin kanta da isarta, Bata ce komaiba ta kwanta kan k'afar mahaifiyarta ta saki kukan bak'in ciki da takaici." Tuni iyayenta suka k'ara rud'ewa ganin shalele tana kuka har da hawayenta." Mahmud ya matso kusa gareta shima da d'an rud'ewarshi Dan kadda Abba ya tuhumeshi yace " haba yusra in akwai abinda nake maki saiki fad'a min kai tsaye." Ko in a kwai abinda kikeso in miki ko in baki sai ki fad'a min kai tsaye ba sai kin b'oye a ranki ba ko kinyita bin wasu hanyoyi." Kifad'i kai tsaye duk abinda kikeso in kuma bazaki iya fad'amin ba, Ki fad'awa Abbanki ya fad'a min ko kuma ya fad'awa Abbana ya fad'a min." Wata harara ta dalla masa yana mata murmushin mugun ya fita." Anan iyayenta suka shiga tausarta tare da lallashinta duk a nasu tunanin da gaske mahmud yakeyi, Abba yaji dad'I sosai daya ga mahmud yana kula da ita ba tsangwama." Murmushin dole takeyi. To ya zatayi?" Gashi bazata iya fad'a musu abinda ke faruwa ba, Dolenta ta dinga dariyar dole tare da fad'a musu zata kiyaye." Tace Tunanin rabuwa da gida ne da tunaninka Daddy." Daddy yaje kusa gareta ya rungumeta yana Shafa bayanta tare da bata hak'uri, Sorry "shalelena kiyi hak'uri zaman gidan aure ba kamar zaman Gida bane, duk wacce kika gani hakan ta saba." Girgiza kai kawai takeyi tana tunanin mahmud, Mahmud ya rushe mata duk wani shirin ta duk abinda tayi masa kwanaki ladabin nan da canjin nan duk ya tashi a banxa duk hakan bai sa tasamu abinda takeso ba." Sai dai fa baxata hak'ura ba, ta dinga yi kenan har sai lokacin da ta samu nasara, Mahmud sai na nuna maka nima fitinaniya ce a kan abinda nake so." Abba yana ganin Alhaji Atiku rungume da Yusra ya bud'e k'ofa ya fita cike da mamakin Wnn rayuwar." Bayan Alhajj Atiku ya fita tare da mommy Yusra ta dinga k'ullawa tana sak'awa daga k'arshe ta d'auki waya ta kira aminiyarta dan ta kuma samun wata shawarar da zata kuma sanyawa ta kai ga abinda takeso." *************** Dijamah Cikin kwana biyu tashiga damuwa tun lokacin da taji Abba yana zancen aureta da sulaiman." Fateema ce taketa bata hak'uri tareda kwantar mata da hankali akan cewa tunda bata so yaya mahmud bazai bari ta aure shiba." Suna Zaune a d'aki Abba ya dawo daga Abuja sautin muryansa sukaji yana kiransu." Da sauri suka mik'e a tare cikin hanzari suka fito, suka durk'usa a gabansa." Abba ya dubisu yace "yanzun nadawo daga Abuja na biya ta gidan yayanku mahmud na tarar da matarsa bata da lafiya Dan haka abinda nake so daku Ku shirya kutafi Kuyi sati d'aya domin Ku taimaka mata kafin taji sauk'i." Gaban dijama ya fad'i a yanda takejin zafin Yusra a yanzun jitakeyi bazata iya koda kallonta ba bare har ta taimaka mata Dan bata da lafiya, waya sani ma ko ciki ne gareta, Aitamafi son ta mutu In har sai ta taimaka mata." Abba yace kunyi shuru baku bani amsaba, Itama fateema bak'in halinta take tunani na rashin tarbiya da son nuna isa." Fateema tace "to Abba yaushe zamutafi?" Abba yace "kushirya gobe dafe saina kaiku domin akwai abinda zankoma idar." Dijama ta d'aga kai ta dubi Abba, tace "Abba ni dai ayi mun hak'uri ba'a gobe zan tafiba, saboda kwana nan da ciwon kai nake kwana, idan Fatima ta tafi nan da kwana biyu zan biyo bayanta." Abba yace "kina shan maganinki kuwa?" Ta d'aga kai alamar "eh." Ya dubi fateema yace "kishirya da wuri saboda tafiyar safe zamuyi." Misalin k'arfe 1:30pm Abba ya isa garin Abuja, sai da ya fara biyawa ta gidan mahmud ya sauke fateema a lokacin mahmud baya nan yana wurin aiki Dama baya so su had'u saboda yasan k'orafin mahmud d'aya ne a kan dijama wnn dalilin yasa jiya yayi tafiyarsa batare da sunyi wata doguwar magana ba, Kai tsaye gidan Alhaji Atiku ya nufa domin aiwatar da abinda ya kawoshi." Da sallama fateema tashiga gidan, ta tarar da Yusra zaune a falo sanye da dogowar riga kanta babu d'ankwali ta k'ure volume tana kallo." Sallama fateema taketa famanyi Yusra bata san tanayiba, sai da taje kusa da ita ta dafata tana murmushi." A razane cikin tsoro Yusra ta zabura ta zafga wani irin ashar tana kallon fateema cike da mamaki tace "ke kuma daga ina kika shigo mun gida ba sallama sai dai na ganki a gabana." Fateema tace "yi hak'uri Anty nayita sallama bakijiba kin k'ure volume, ni sunana fateema ni k'anwar yaya mahmud ce, Abba yace bakida lafiya shine naxo na ganki ya jikin nki?" "Naji sauk'i tace "aiko bakiyi mun bayaniba naga kama a fuskarki, ya hanya?" Dan nasan tafiyar mota kikayi ba ta jirgiba." Fateema tace "Alhamdulillah, ina yaya mahmud?" Yitayi kamar batajitaba taci gaba da kallonta, Itama fateema kallon takeyi tana mmkin hali irin na Yusra na wulak'anci." Fateema macce ce Wadda batason fad'a da tashin hankali tana da sanyi sosai gaba d'aya itace ta d'ebo halin mommy duk a gidan." Suna Zane a hakan ba Wanda ya Kuma yiwa wani magana a cikinsu." .Mahmud yayi sallama ya shigo [8/17, 20:16] Washa: 🌹 *DEEJAMAH* 🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writteng by *UMMU SAFWAN* (Fareeda Basheer) *52* Kai tsaye wurin kayan kallon ya nufa ya cire jonin gaba d'aya ya juyo a fusace cikin masifa, Karaf yayi ido biyu da fateema wanda tunda ya shigo bai lura da ita ba." sakin murmushi yayi cike da mamaki ya shiga waige waige kamar Wanda yake neman wani abin." Murmushi takeyi tace "yaya sannu da zuwa." "Yawwa yace yana murmushin jin dad'in ganinta." Baki Yusra ta saki tana kallon fuskarsa ganin yanda yake murmushi yana fara'ar ganin k'anwarsa. ta karkace kai tana kallon fuskarsa tana murmushi domin murmushin da yakeyi ba k'aramin kyau yayi masa ba." Ido suka had'a yaga ta kure shi da ido kamar wata mayya ya wurga mata harara yaje kusa da FATEEMA ya mik'a mata hannu yace "taso mushiga daga ciki k'anwata." D'akinsa suka shiga tambaya ce tab a bakinsa, Kan kujera yayi mata nuni da ta zauna." Shima yaje kan gado ya zauna yana fuskantarta, "yaushe kika zo?" "D'azun misalin 1:30pm." "Waye ya kawoki?" "Abba ne kuma yayi tafiyarsa." "Ina dijama meyasa bakuzo tare ba." "Da a tare zamuxo tace "batajin dad'i ta fasa zuwan." "Meyake damunta ne." "Wlh yaya nima cikin 'yan kwanakin nan narasa abinda yake damunta wani lokacin ta zauna ita kad'ai tayita kuka sai na lallasheta tare da bata hak'uri snn takeyin shuru" "Karya kikeyi kinfi kowa kusanci da ita tunda a tare kuke kwana dan haka kinsan abinda yake damunta." Shuru tayi batayi magana ba." Yace "yawwa zan tambayeki kuma idan kika kuskura kikayimun k'arya daga baya na bincika nagamo gaskiya saina b'ata maki rai." Ta d'aga kai alamar "to." Yau she ne Abba ya sanya ranar bikin sulaiman da dijama?" "Wata biyu." "Harda ke za'a had'a yaushe kika samu miji?" Waye she?" Ishaq ne d'an gidan Alhji sanusi." Shuru ya d'anyi yana tunani." Snn ya nisa yace "ita dijama tana son sulaiman d'in?" Shuru fateema tayi ba batayi magana ba, Tsawa ya doka mata yace "na fad'a maki muddun kikayi mun k'arya saina sab'a maki." "Allah yaya bata sonshi kullum cikin kuka take akan za'a aura mata shi duk ta rame baka gantaba." "To Waye take so?" Ai nasan bata rasa Wanda take so a ranta kuma nasan kinfi Kowa saninsa." "Wlh yaya ban San kowa ba, bansan Wanda takeso ba asali ma duk Wanda yazo wurinta korarshi takeyi tace "anyi mata mijin aure." Amma kuma na fad'a mata ta kwatar da hankalinta muddun kasan da cewa bata son sulaiman baxaka bari a aura mata shiba." "Meyasa bata kirana a waya kuma idan na kira wayarta bata d'auka, sai dai ma daga k'arshe ta kashe wayar gaba d'aya?" Ina ganin tun lokacin da ta tab'a kiran wayarka Anty Yusra ta d'auka, ko mai ta fad'a mata nidai bansaniba naga ta ajiye wayar tana kuka to tun a lokacin ta kashe wayart a gaba d'aya bata kira ba'a kiranta." Mamaki yashigayi kwakwalwarsa ta d'au zafi, to me Yusra ta fad'awa dijama ne?" Da har ya sanyata kuka." Uban waye ma yasanyata ta d'aukar masa waya?" Yau zata gane kurenta Dan sai ta fad'a masa abinda tace mata idan ba hakan ba jikinta ne zai fad'a mata." Tunani ya shigayi ta hanyar da zai b'ullowa lamarin." Can yaja dogon nishi ya kuma kallon fatema yace "kinci abinci?" Ta girgiza kai alamar A'a yace "OK tashi mutafi gidan abinci muci abinci daga nan nayo siyayyar kayan abinci, tunda sai an kwana biyu zaki koma gida." Kallo tabishi dashi cike da mamaki tace "yaya gidan abinci Kuma?" Yace "eh ko bakyaci ne kin k'oshi?" Tace A'a na dai ga Anty Yusra zaune a falo bata dafa bane?" Dogon tsaki yaja yace "ke bana son yawan tambaya kinsan halina." Zamanta kenan 'yar gatace babu abinda ta iya sai kallo." Ya mik'e tsaye ya fita tabi bayanshi, a inda suka bar Yusra a nan suka same ta ta d'an gincira a kan kujera tana latsar waya da alama chatting takeyi tana murmushi." Tanajin fitowarsu ta d'aga kai ta kallesu ta taci gaba da abinda takeyi Dan tasan halin mahmud yanxun tana masa magana zai disgata a gaban k'anwarsa ta renata." FATEEMa tace "Anty muntafi sai mudawo." "Adawo lafya tace ta kalli Mahmud tace dear ka yomun tsaraba." "To yace batare da ya kalle inda takeba yayi ficewarsa, Ko amsa mata d'in da yayi Dan ganin fateema ne saboda baya so ta fahimci irin zaman da sukeyi." Gidan abinci suka nufa sukaci abinci suka k'oshi, snn ya biya kasuwa ya sayo kayan abinci wad'anda fateema zata dinga dafa masu kafin ta koma ya San cikin "yan kwanankin da zatayi a gidan kud'insa zasu d'an huta da sayen abinci." Koda suka dawo ana kiraye kirayen sallar la'asar, Yusra bata falon tare suka shiga kitchen yanuna mata yanda zatayi aiki da kayan wurin, Har zai fita ya kuma dawo yace "muje na nuna maki d'akinki kishiga kiyi sallah, dan nasan Yusra bata nuna maki." Bayan ya kwada mata ne, Yace "tuwon shinkafa nakeso kiyimun miyar wake, Kuma ki tsaya Ki kwantar da hankali yanda zaiyi dad'i Dan nasan dijama tafiki iya abinci." Turo baki tayi tace "Allah ni dai bata fini iyawaba sanin da kayi mun." Murmushi yayi ya fita tare da janyo mata k'ofa." Yanufi masallaci." Bayan ta kammala girkin ne tajera a kan dining taje d'akin Yusra domin ta kirata." Da sallama ta shiga d'akin tareda tura k'ofa, Kwance take akan gado tana waya tana dariya da Alama da k'awayenta takeyi, tana ganin FATEEMA tace "gata nan ma tashigo har d'akina ina zuwa bari naji abinda ke tafe da ita, sai anjima sai goben idan kunzo dan Allah kuzo gaba d'ayanku. Snn ta kashe wayar." Gaban fateema ya shiga fad'uwa dan ita har ga Allah tsoron Yusra takeji, ta d'an runsuna tace "Anty Yusra kifito muci abinci." Ta ya musta fuska tace "wni irin abinci kuma?" Nifa banacin wani kalar abinci idan bana gwangwaniba, Amma kije gani nan zuwa." Har Fatima ta kai k'ofar d'aki Yusra tace "Am meye ma sunanki fateema ko?" Idan kink'are cin abincin kizo ki gyaramun d'akina." To fateema tace a ladafce snn fita." Bayan sungama cin abincin ne, wayar fateema dake kusa da yaya mahmud ta d'au ringing da sauri ta mik'a hannu ta d'auka Dan tasan dijama ce ke kiranta ringing d'inta daban yake." Mahmud shima ya fahimci dijama ce ke kiran, ya gyara zama ya k'ure fateema da ido yana son jin abinda suke cewa." Jiyayi fateema na fad'in lafiya k'alau' yaya mahmud gashi nan zaune, Ya fahimci wato tambayarsa takeyi, amma bata iya kiran number sa kuma shi idan ya kira tata a kashe yakejinta, me take nufi ne?" Yana cikin tunanin yaga fateema ta mik'e tana magana da ita tanufi hanyar d'akinta tana dariya, binta yayi da kallo ya girgiza kai ya tashi ya fita zuwa massallaci domin yin sallar magariba." Dijama take tambayar fateema ya taga yanayin gidan, Ina wnn marar kunyar take?" tana nufin Yusra." Ai Kuwa fateema tashiga bata labarin tin zuwan ta gidan ko wurin zama bata bataba sai da ta zauna dan kanta bare tabata ruwan sha ko abinci, Wlh sis kwata kwata yaya mahmud baiyi dacen Mata ba, bata da mutumcin ko kad'an keni wlh har tsoronta nakeji." D'azun da nashiga d'akinta nafad'a mata tafito muci abinci, waya na sameta tanayi ina ganin da k'awayenta takeyi ai kuwa ta shiga fad'a masu ganinan na shigo a nan take sukayi sallama a kan sai gobe zasu zo nan gidan." Tsorona Allah nidai kada suzo suyi mun duka." Dijama ta lalubo wani ashar ta zunduma tace "amma wlh sis ke banza ce, matsoraciya." Banyi niyar zuwa garinba saboda wani dalili, amma yanzun kinsa naji inaso na ganni a cikin garin." Waye ita zata hana maki wurin zama bare ruwan sha." Na rantse da Allah mudun nazo gidan da hannunta sai ta d'ebo ruwa tabani nasha." K'aryar rashin kunya takeyi, ko a cikin marasa kunyar ita ba komai bace." A da na cire rigar rashin kunyata na ajiye, Amma gobe zan d'auketa na saka na taho garin abuja da ita, Kuma karki kuskura kifad'awa yaya mahmud zanzo." Batajira amsar da FATEEMA zata bata ba ta kashe wayar." [8/17, 20:16] Washa: 🌹 *DEEJAMAH* 🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writteng by *UMMU SAFWAN* (Fareeda Basheer) *53* Fateema kuma jikinta ne ya soma rawa jin dijama tace "zatazo tasan halin dijama bata d'aukar raini ita kuma bata son tashin hankali." Wayar dijama tashiga kira tajita a kashe kamar yanda tasaba kashe waya a koda yaushe sai dai idan ta tashi neman mutum ta kunna ta kirashi da sun k'are maganar da sukeyi zata kashe, to ko yanzun ta kashe wayar gaba d'aya." Ta gumi ta rafka kamar wadda akayiwa mutuwa tana tunanin zuwan dijama a gobe.' Tana hakan yaya mahmud ya turo k'afa ya shigo d'akin kai tsaye wurinta ya nufa ya zauna a gefen gadonta yana kallonta yace "fateema d'axun da dijama naga kuna waya metace maki." "Fateema ta d'an kallesa shi, tana nazarin wani abu a ranta shi dai yaya mahmud da zarar ya zauna baya da wata fira sai ta dijama, To yanzun kuma ko meye ruwanshi da maganar da sukayi a waya?" Katse mata tunani yayi da yace "amma ina ganin ke back kurma bace bare na tambayeki kiyi banxa da ni." Ke naganki lokaci d'aya duk kin birkice kamar ba'a hanyacinki kike ba lafiya meyasameki?" "Ba komai yaya cemun tayi tana gaida kai kuma idan zan dawo nayo mata tsaraba." "Batace zata zoba?" Tayi shuru ba amsa sai zarar ido takeyi kamar wadda tayi k'arya." "OK kiramun ita da wayarki kibani muyi magana ko Zata d'auka, Ba musu ta d'auki wayarta ta danna number dijama had'ida danna hands free " swech of ake cewa wayarta a kashe take." Runtse idonsa cike da b'acin rai, Babu Wanda yakejin haushinta sama da Yusra Dan duk ita ta janyo masa haka." A fusace ya juya ya futa daga d'akin kai tsaye d'akin Yusra ya nufa Wanda bai tab'a shigarsa ba tunda aka kawota." Tana kwance tana chatting a wayarta, sanye take da wata fitinanniyar rigar bacci da ita da babu duk d'aya." Tana ganinsa tayi saurin ajiye wayar tana murmushi jin dad'in ganinsa har cikin d'akinta." Mik'ewa tayi zaune ta kuma zame rigar daga k'irjinta boobs d'inta gaba d'aya suka bayyana, tana wani laud'e da jiki tace "dear lafiya kaxo da kanka aida kirani nazo." Kallon tsana yabita dashi ya kuma matsawa kusa da ita ya sanya k'afarsa mai sanye da talkami ya take d'aya k'afarta "yace ubanwaye yasa kika d'aukar mun waya da har za'a kirani ki d'auka." Me kikacewa dijama a waya lokacin da takirani." Ya kuma danne k'afar da k'arfi ya murza." Wata wahalalliyar k'ara ta saki tana "fad'in waye dijama ni ban ma santaba, kuma ni ban d'auki wayarka ba." K'ara take k'afar yayi ya sanya Hannunsa ya janyo gashin kanta ya rike da k'arfi, ai bata San lokacin da tasaki k'araba." "Fad'a mun abinda kikace mata a waya?" "Wayyo Allah na na Shiga uku sakeni xan fad'a maka." Yak'i sakinta "ce matayi baka da lokacin kowa a daidai lokacin da takira waya KA hau network." Dan Allah kayi hak'uri, ka karyamun k'afa." Ransa ya kuma b'aci ya kuma murza k'afa tare da fisko gashin kanta snn ya d'agata ya kalleta a wulak'ance yace "idan ke mayyace sai dai ki mutu dan kuwa bazan tab'a ciyowa gareki ba, Dubeki kidubi nakasasshen jikin nasha fad'a maki babu abida zanyi da jikinki bare har na hau network d'in da banaji bana gani." Ita wacce kika fad'awa hakan nafi son talkaminta d'aya a kanki." Ya fito a fusace yafad'a d'akinsa had'ida turo k'ofa da k'arfi." Kuka takeyi sosai k'afarta na mata zugin zafi, tare da kanta, Ga kuma zafin kalaman da mahmud ya fad'a mata, Talkamin wata 'yar k'auye yafita daraja a wurinsa." Wani irin tsanar dijama taji ta kuma lunkuwa a ranta." **************** Dijama kuma tana gama waya da fateema jitayi gaba d'aya ciwon da takeji ta warke, burinta d'aya ta ganta cikin garin Abuja." . Durowa tayi daga kan gadonda take kwance ta nufi falo domin sanarda Abba cewa tanaso taje gidan yaya Mahmud gobe kuma da kanta take so tayi driven." Abba da mommy da Khalil suna zaune a Palo Abba yana tambayar Khalil ya jarabawa Khalil ya sunkuyar da kai cikin ladabi idan kika ganshi sai KA rantse da Allah ko hannun a ka Sanya mashi a Baki baya. Cizawa, Yace "Alhamdullillah Allah ai munkusa kammallawa." Abba yace "Allah yasa a fito da sakamako mai kyau." Ya 'amsa da "Ameen." Dijama CE ta fito sanye cikin hijabinta har k'asa tana ganin Khalil ta had'r fuska bata ko kalli Inda yakeba saboda ya tsani kallon da yake mata kamar wani maye." Khalil yana ganin fitowarta ya k'ureta da ido yana kallonta "shi dai a duniya yana tsananin son Dijama, Sabida na tsuwarta da kyawota uwa uba tana da cikar halitta irin na many a mata wad'anda namiji zaiji fad'in hutawa dasu, Rana da wani sirri Wanda ba Kiwa ya San dashiba sai wanda ya kware wurin sanin macce." Kusa da Abba ta zagayo ta zauna ta runsuna ta kuma gaidashi tare da mommy ta d'an juyar da kanta wurin Khalil shima ta gaida shi tun kafin ta rufe bakinta yayi saurin amsa mata gaisuwa tare da tambayarta ya hutawa?" Banza tayi dashi tayi kamar batajishiba." Abba yace "Ummi ya k'arfin jikin?" Tace "Alhamdulillah Abba naji sauk'i sosai babu abinda yake yimun ciwo a yazun." Khalil "yayi karaf yace "Allah ya k'aro maki lafiya mai amfani." "Gamba d'aya falon suka amsa da "Ameen." Dijama tace "Abba zuwa nayi na fad'a maka tunda naji sauk'i gobe INA so naje Abuja gidan yaya mahmud nasame FATEEMA a can." Abba yace "ba komai Allah ya kaimu goben, To gamma sai dai Wanda zan samu ya kaiki saboda kinsan bana so kuna shiga motar haya." Khalil yace "Abba kabarshi zan kaita goben." "Jarabawar da kujeyi a makaranta fa?" "Ai Abba ba matsala zan iya zuwa na kaita na dawo." Dijama tace "Abba Wnn karon inason Inyi driven da kai yanda zan lalab'o har naga kai." Amma Abba idan akace yaya Khalil ya kaini ko mai zai iya faruwa domin ko shi kanshi idan yana tuk'i baya tafiya a hankali." Abba yace "haka ne ummi, Kumar kullum ina yimada magana a kan yawan gudun da yakeyi da mota, Tashi kitafi ki fara shirin gobe sai kiyi tafiyar asuba kafin Azahar kin kai, Allah ya kiyaye ya tsare hanya. Abba ya kalli Khalil da yacika ya saboda jin haushi yace "kai Khalil kaje kaje KA duba mata mortar da zatayi tafiya da ita mai lafiya idan babu mai kaje ka zubo mata Wanda zai kai ta ya kuma dawo da ita." "To ya amsa da shi ya tashi ya fita yana turo baki. Cike da jin haushi." *7:00am* Dijama tayi shirinta cikin tamfarta mai surkin ja da tsanwa, d'inkin Riga da siket Wanda sukayi mata kyau d'inkin yayi dai dai da jikinta, Bata d'aura d'ankwaliba illah ta d'auko d'an k'aramin gyalenta ja kalar atamfarta ta lullub'a akan gashinta wanda yasha kyara da mayukan gyaran kai masu kyau da k'amshi, tajashi gaba d'aya a bayanta ta sanya babban riban ta d'aureshi a tsakiyar kai yayi mata kamar tayi acuci maza ta d'auko Jakarta tare da talkaminta suma jajaye ta saka, Ta kuma feshe jikinta da turarunka masu k'amshi snn d'auko wani k'aton glass d'inta ta saka fuskarta Wanda ya Kuma fitar mata da Kyan fuskarta tafito hamshak'iyarta 'yar boko maiji da kanta." Ta fito hannunta d'aya d'auke da hand bag d'aya Kuma janye da akwatin kayanta, A falo ta Tatar da Abba da Momy suna zaman jiran fitowarta, Suna ganin ta fitowarta suka rakata har bakin mota suna mata addu'a sai da suga tafiyarta suna d'aga mata hannu snn suka juya suka koma ciki " Dijama tana ganin ta fito ta kunna wayarta ta kira fateema ta shaida mata yanzun ta taso tana kan hanya." Fateema tashiga jin dad'i da murna wani b'angare kuma gabanta ya shiga fad'uwa ita dai bata son tashin hankali." Yusra kuma koda safiya ta waye k'afarta ta kumbura a inda mahmud ya takata wurin yayi ja sosai ga wani ciwon kai dake damunta saka makon gashin kanta da mahmud yaja da k'arfi." Duk yinin yau bata lek'o wajeba, fateema ce duk tayi aikin gidan, Ta shiga hidimar d'ora abinci "yaya mahmud yace dambun shinkafa yakeso yaji kayan lambu irin yanda mommy takeyi." Tana kitchen tana aikinta taji sallamar k'awayen Yusra sunshigo, Tun daga kicin d'in tashiga amsa masu tana masu snnu da zuwa." Wani kallo suke jifarta da shi na wulak'anci, Snn d'aya daga cikinsu Wanda daga ganinta tafisu masifa ta dokawa fateema tsawa tace "ke INA matar gidan Wanda take da mallakin gidan bake ba 'yar ciku tsere." Fateema tace "Allah ya baku hak'uri tana ciki ta Nuna masu d'akinta." Tana ganin k'awayenta suka b'arke da kuwa da shewa, ta mik'e tana d'angisa k'afa ta suka fito falo gaba d'ayansu." Cike da mamaki suke kallonta ganin k'afarta ta kumbura idonta yayi ja kamar wacce taci kuka ta gaji." Suka Shiga tambayarta "meyake damunta tawani kod'e ta rame kamar wacce bata da lafiya. Ga Kumar ciwo a k'afarta wurin har ya kumbura." "Hmmm nishi ta sauke tare da dafe kai, Tace "ai kunfi Kowa sanin Matsalata a duniya mahmud ne." Ina son Mahmud INA son in mallaki mahmud INA son mahmud ya zama nawa mallakina Amma mahmud baya sona, Ku bani shawarar hanyar da zanbi ya soni na mallalesa na d'ad'dd'i zumarsa." Mere Baki sukayi suna kallonta, Suka had'a Baki suka ce "lallai kuwa kina da babban aiki a gabanki." Yaushe Rabon da muga ana irin Wnn soyayya wahala?" Aidan kina ajiye wata soyayya can gefe kifito ki wataya ki ajiye, Ga Maza nan a gari sai kin za b'a wad'anda kikeso kiyi huld'a dasu wad'anda zasu cire maki wani kwayin Mahmud." Malama ki kifito muje ki wataya an bud'e wanin gidan mata, Duk Kalar namijin da kike so zaki same shi a gidan, idan kuma soyayya ce, akwai Samari masu Jini a jiki wad'anda zasu kasheki da soyayya wadda har sai kin suma kin dawo Baki saniba akan dad'i." Tayi shuru tana saurarensu da Alama magagganun su sun fara Shigar ta." Me Kuma kika yimasa yaji maki ciwo a k'afa?" Ai kuwa tashiga basu labarin dalilin "akan wata 'yar uwarsa 'yar k'auye baku pic d'inta wayarsa Wanda ya d'auke a k'auyen." Tabd'i jam yanzun akan 'yar k'auye yayi maki wnn mikin?" Allah ya sauwake mudai kunna nama kid'a mucashe kafin yadawo." Ai Kuwa ta mik'e ta kunna masu suka rud'u gidan da kid'e kid'e kamar club." Duk magagganun da sukeyi FATEEMA tana kicin tana saurarensu. Cike take Rana mamakinsu da ban al'ajabi, tana Gudun kartayi dogon motsi su sameta a kicin d'in suyi mata duka." [8/17, 20:17] Washa: 🌹 *DEEJAMAH* 🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writteng by *UMMU SAFWAN* (Fareeda Basheer) *53* Fateema kuma jikinta ne ya soma rawa jin dijama tace "zatazo gobe, tasan halin dijama bata d'aukar raini ita kuma bata son tashin hankali." Wayar dijama tashiga kira ta fad'a mata kartazo tayi zamanta tajita a kashe kamar yanda tasaba kashe waya a koda yaushe sai dai idan ta buk'aci neman mutum xata kunna ta kirashi da zarar sun k'are maganar da sukeyi zata kasheta gaba d'aya ta ajiye, to ko yanzun ta kashe wayar gaba d'aya." Ta gumi ta rafka kamar wadda akayiwa mutuwa tana tunanin zuwan dijama a gobe.' Tana hakan yaya mahmud ya turo k'afa ya shigo d'akin kai tsaye wurinta ya nufa ya zauna a gefen gadonta yana kallonta yace "fateema d'axun da dijama naga kuna waya metace maki." "Fateema ta d'an kallesa, tana nazarin wani abu a ranta tace "shi dai yaya mahmud da zarar ya zauna baya da wata fira sai ta dijama, To yanzun kuma meye ruwanshi da maganar da sukayi a waya?" Katse mata tunani yayi da yace "amma ina ganin ke ba kurma bace bare na tambayeki kiyi banxa da ni." Ke wai meyasa meki naganki a lokaci d'aya duk kin firgice kamar ba'a hanyacinki kike ba, lafiya?" meyafaru?" "Ba komai yaya cemun tayi tana gaida kai kuma idan zan dawo nayo mata tsaraba." "Batace zata zoba kenan?" Tayi masa shuru ba amsa sai zarar ido takeyi kamar wacce tayi k'arya." "OK kiramun ita da wayarki kibani muyi magana ko Zata d'auka, Ba musu ta d'auki wayar ta danna number dijama had'ida danna hands free " sweech of ake cewa wayarta a kashe take." Runtse idonsa yayi cike da jin haushi da b'acin rai, Babu Wanda yakejin haushinsa sama da Yusra Dan duk ita ta janyo masa haka." A fusace ya juya ya fita daga d'akin kai tsaye d'akin Yusra ya nufa Wanda bai tab'a shigarsa ba tunda aka kawota gidan" .Tana kwance tana chatting a wayarta, sanye take da wata fitinanniyar rigar bacci da ita da babu duk d'aya." Tana ganinsa tayi saurin ajiye wayar tana murmushi jin dad'in ganinsa har cikin d'akinta." Mik'ewa tayi zaune ta kuma zame rigar baccin daga k'irjinta boobs d'inta gaba d'aya suka bayyana, tana wani lankwàsa da jiki tace "dear lafiya kaxo da kanka aida kirani nazo." Kallon tsana yabita dashi ya kuma matsawa kusa da ita ya sanya k'afarsa wadda yake sanye da talkami ya take d'aya k'afarta "yace ubanwaye yasa kika d'aukar mun waya da har za'a kirani ki d'auka." Me kikacewa dijama a waya lokacin da takirani." Ya kuma danne k'afar da k'arfi ya murza." Wata wahalalliyar k'ara ta saki tana "fad'in waye dijama ni ban ma santaba, kuma ni ban d'auki wayarka ba." K'ara take k'afar yayi ya sanya Hannunsa ya janyo gashin kanta ya rike da k'arfi, ai bata San lokacin da tasaki k'araba." "Fad'a mun abinda kikace mata a waya?" "Wayyo Allah na na Shiga uku sakeni xan fad'a maka." Yak'i sakinta "cemata nayi baka da lokacin ta saboda kana kan network." Dan Allah kayi hak'uri, kada karyamun k'afa." Ransa ya kuma b'aci ya kuma murza k'afar da k'arfi tare da fisko gashin kanta snn ya d'agata ya kalleta a wulak'ance yace "idan ke mayyace sai dai ki mutu ko kuma kicinye kanki dan kuwa bazan tab'a ciyowa gareki ba, Dubeki kidubi nakasasshen jikin nasha fad'a maki babu abida zanyi da jikinki bare har na hau network d'in da banaji bana gani." Ita wacce kika fad'awa hakan nafi son talkaminta d'aya a kanki." Ya fito a fusace yafad'a d'akinsa had'ida turo k'ofa da k'arfi." Kuka takeyi sosai k'afarta na mata zugin zafi, tare da kanta, Ga kuma zafin kalaman da mahmud ya fad'a mata, Talkamin wata 'yar k'auye yafita daraja a wurinsa." Wani irin tsanar dijama taji ta kuma lunkuwa a ranta." **************** Dijama kuma tana gama waya da fateema jitayi gaba d'aya ciwon da takeji ta warke, burinta d'aya ta ganta cikin garin Abuja." . Durowa tayi daga kan gadon da take kwance a kai ta nufi falo domin sanarda Abba cewa tanaso taje gidan yaya Mahmud gobe kuma da kanta take so tayi driven." Abba da mommy da Khalil suna zaune a Palo Abba yana tambayar Khalil ya jarabawa Khalil ya sunkuyar da kai cikin ladabi idan kika ganshi sai KA rantse da Allah ko hannun a ka Sanya mashi a Baki baya.iya Cizo, Yace "Alhamdullillah Abba ai munkusa kammallawa." Abba yace "Allah yasa a fito da sakamako mai kyau." Ya 'amsa da "Ameen." Dijama CE ta fito sanye cikin hijabinta har k'asa tana ganin Khalil ta had'e fuska bata ko kalli Inda yakeba saboda ta tsani irin kallon da yake mata kamar wani maye." Khalil yana ganin fitowarta ya k'ureta da ido yana kallonta "shi dai a duniya yana tsananin son Dijama, Sabida na tsuwarta da kyawonta uwa uba tana da cikar halitta irin na manyan mata wad'anda namiji zaiji dad'in hutawa dasu, Snn tana da wani sirri Wanda ba Kowa ya San dashiba sai wanda ya kware wurin sanin macce." Kusa da Abba ta zagaya ta zauna ta runsuna ta gaidashi tare da mommy ta d'an juyar da kanta wurin Khalil shima ta gaida shi tun kafin ta rufe bakinta yayi saurin amsa mata gaisuwa tare da tambayarta ya hutawa?" Banza tayi dashi tayi kamar batajishiba." Abba yace "Ummi ya k'arfin jikin?" Tace "Alhamdulillah Abba naji sauk'i sosai babu abinda yake yimun ciwo a yazun." Khalil "yayi karaf yace "Allah ya k'aro maki lafiya mai amfani." "Gaba d'aya falon suka amsa da "Ameen." Dijama tace "Abba zuwa nayi na fad'a maka tunda naji sauk'i gobe INA so zanje Abuja gidan yaya mahmud nasamu FATEEMA a can." Abba yace "ba komai Allah ya kaimu goben, To amma sai dai Wanda zan samu ya kaiki saboda kinsan bana so kuna shiga motar haya." Khalil yace "Abba kabarshi zan kaita goben." "Jarabawar da kukeyi a makaranta fa?" "Ai Abba ba matsala zan iya zuwa na kaita na dawo." Dijama tace "Abba Wnn karon inason Nayi driven da kai na yanda zan lallab'o har naga na kai." Amma Abba idan akace yaya Khalil zai kaini ko mai zai iya faruwa domin ko shi kanshi idan yana tuk'i baya tafiya a hankali." Abba yace "haka ne ummi, Kuma kullum ina masa magana a kan yawan gudun da yakeyi a mota, Tashi kitafi ki fara shirin gobe sai kiyi tafiyar asuba kafin Azahar kin kai, Allah ya kiyaye ya tsare hanya. Abba ya kalli Khalil da yacika fam saboda jin haushi yace "kai Khalil kaje KA duba mata mortar da zatayi tafiya da ita goben mai lafiya idan babu mai kaje ka zubo mata Wanda zai kai ta ya kuma dawo da ita." "To ya amsa." Tare da tashi ya fita yana turo baki. Cike da jin haushi." *7:00am* Dijama tayi shirinta cikin tamfarta mai surkin ja da tsanwa, d'inkin Riga da siket Wanda sukayi mata kyau d'inkin yayi dai dai da jikinta, Bata d'aura d'ankwaliba illah ta d'auko d'an k'aramin gyalenta ja kalar atamfarta ta lullub'a akan gashinta wanda yasha kyara da mayukan gyaran kai masu kyau da k'amshi, tajashi gaba d'aya a bayanta ta sanya babban ribon ta d'aureshi a tsakiyar kai yayi mata kamar tayi acuci maza ta d'auko Jakarta tare da talkaminta suma jajaye ta saka, Ta kuma feshe jikinta da turarunka masu k'amshi snn ta d'auko wani k'aton glass d'inta ta saka a fuskarta Wanda ya Kuma fitar mata da Kyan fuskarta tafito hamshak'iya 'yar boko maiji da kanta." Ta fito hannunta d'aya d'auke da hand bag d'aya Kuma janye da akwatin kayanta, A falo ta Tatar da Abba da Momy suna zaman jiran fitowarta, Suna ganin fitowarta suka rakata har bakin mota suna mata addu'a sai da suga tafiyarta suna d'aga mata hannu snn suka juya suka koma ciki " Dijama tana ganin ta fito ta kunna wayarta ta kira fateema ta shaida mata yanzun ta taso tana kan hanya." Fateema tashiga jin dad'i da murna wani b'angare kuma gabanta ya shiga fad'uwa ita dai bata son tashin hankali." Yusra kuma koda safiya ta waye k'afarta ta kumbura a inda mahmud ya takata wurin yayi ja sosai ga wani irin ciwon kai dake damunta saka makon gashin kanta da mahmud yaja da k'arfi." Duk yinin yau bata lek'o wajeba, fateema ce duk tayi aikin gidan, Ta shiga hidimar d'ora abinci "yaya mahmud yace dambun shinkafa yakeso yaji kayan lambu irin yanda mommy takeyi." Tana kitchen tana aikinta taji sallamar k'awayen Yusra sunshigo, Tun daga kicin d'in tashiga amsa masu sallama tana masu snnu da zuwa." Wani kallo suke jifarta da shi na wulak'anci, Snn d'aya daga cikinsu Wanda daga ganinta tafisu masifa ta doka mata tsawa tace "ke INA matar gidan Wanda take da mallakin gidan bake ba 'yar ciku tsere." Fateema tace "Allah ya baku hak'uri tana ciki ta Nuna masu d'akinta." Tana ganin k'awayenta suka b'arke da kuwa da shewa, ta mik'e tana d'angisa k'afa suka fito falo gaba d'ayansu." Cike da mamaki suke kallonta ganin k'afarta ta kumbura idonta yayi ja kamar wacce taci kuka ta gaji." Suka Shiga tambayarta "meyake damunta tawani kod'e ta rame kamar wacce bata da lafiya. Ga Kuma ciwo a k'afarta wurin har ya kumbura." "Hmmm nishi ta sauke tare da dafe kai, Tace "ai kunfi Kowa sanin Matsalata a duniya mahmud ne." Ina son Mahmud INA son in mallaki mahmud INA son mahmud ya zama nawa mallakina Amma mahmud baya sona, Ku bani shawarar hanyar da zanbi ya soni na mallalesa na d'ad'dd'i zumarsa." Mere Baki sukayi suna kallonta, Suka had'a Baki suka ce "lallai kuwa kina da babban aiki a gabanki." Yaushe Rabon da muga ana irin Wnn soyayyar wahala?" idan kina ajiye wata soyayya can gefe kifito ki wataya ki ajiye, Ga Maza nan a gari sai kin za b'a wad'anda kikeso kiyi huld'a dasu wad'anda zasu cire maki wani kwayin Mahmud." Malama ki kifito muje ki wataya an bud'e wanin gidan mata, Duk Kalar namijin da kike so zaki same shi a gidan, idan kuma soyayya ce, akwai Samari masu Jini a jiki wad'anda zasu kasheki da soyayya wadda har sai kin suma kin dawo Baki saniba akan dad'i." Tayi shuru tana saurarensu da Alama magagganun su sun fara Shigar ta." Me Kuma kika yimasa yaji maki ciwo a k'afa?" Ai kuwa tashiga basu labarin dalilin "akan wata 'yar uwarsa 'yar k'auye baku ga pic d'inta wayarsa ba Wanda ya d'auke ta a k'auyen." Tabd'i jam yanzun akan 'yar k'auye yayi maki wnn mikin?" Allah ya sauwake mudai kunna nama kid'a mucashe kafin yadawo." Ai Kuwa ta mik'e ta kunna masu suka rud'u gidan da kid'e kid'e kamar club." Duk magagganun da sukeyi FATEEMA tana kicin tana saurarensu. Cike take tana mamakinsu da ban al'ajabi, tana Gudun kartayi dogon motsi su sameta a kicin d'in suyi mata duka." *1:30 pm* Dijama tayi parking a harabar gidan mahmud, tun daga harabar gidan kakeji duma na tashi kamar club, Rik'e Baki tayi tace "ikon Allah lallai Wnn Yusra ba k'aramar shed'aniya bace." Sai da ta gyara parking d'in motarta snn ta bud'e Jakarta ta d'auko turare ta kuma feshe jikinta da shi, Snn ta kuma gyara zaman glass d'inta a fuskarta ta d'auko cingom a jakarta ta saka a baki snn ta bud'e mortar ta fito." Tafiya takeyi Cikin isa da yanga hannunta d'auke da hand bag d'inta tana cin cingom tashiga gidan. Kai tsaye babban Palon gidan ta dura Inda taji kid'a nata shi. Batayi sallama ba dan Tasan kotayi sallama bajinta zasuyiba, Mata tagani cike a falon suna sharholiyarsu, basu ma ganta ba, kai tsaye wurin TV ta nufa takashe." Gaba d'aya ido yayi kanta suna kallonta cike da mamaki Kun San dijama jinin mahmud ce Allah yayi masu kwarjini, Ido kawai suka zuba mata suna kallonta tana cin cingom.' Itama kallon nasu takeyi cikin glass d'aya bayan d'aya, snn ta tako cikin k'asaita tazo kusa da yusra ta zauna." Ta kalleta da kyau tayi murmushi tace "dama anfad'a mun idan bak'o Yazo gidan nan baya Samun wurin zama bare ruwan sha." Nasan kobaki sanniba kinga fuskar mijinki a tare dani, Dan kuwa idan kika Ganni tamkar kinga yaya mahmud, Da farko dai ni sunana Nana khadija ni bak'uwa ce a gidan nan k'isa nakeji kibani ruwa na sha." Yusra da ta cika tana kallon dijama, Dan ko bata fad'a ko ita waece ba ta gane ta. Tace "ba sai kinyimun bayanin kankiba naganeki dijama 'yar gidan tsohuwa 'yar k'auye, sai Kuma me?" Dijama tayi murmushi tace "naji dad'i da kika ganeni wnn ya nuna mun cewa kina da labarina Hakan yana nufin inada matsayi a gidan nan." Inajin k'isa kibani ruwa na sha." "Baki isaba, Baki isa naje ni yusra na d'ebo wa 'yar k'auye ruwa tasha ba." Murmushi Yusra tayi tace "yanzun zan nunamaki cewa ni na isa." Jakarta ta bud'e ta Ciro dalleliyar wayarta ta danna lambar yaya mahmud." Ta sanya handsfree." Mahmud dake Zaune a office yana aikin bincike, Amma gaba d'aya hankalinsa da tunaninsa suna wurin dijama, Ransa yana b'aci a duk lokacin da yakira number ta yajita a kashe." Wayarsa yaji tana ringing sai da ja dogon tsaki snn ya cirota a aljihunsa Dan ganin ko waye ke nemansa." Number dijama yagani a kan screen d'in wayarsa, Wani murmushi ya saki had'eda sauke ajiyar zuciya, ciki sauri ya d'aga wayar ya kara a kunnesa yana murmushi, Muryar dijama yaji,,,,,, *washi hannuna nagaji* [8/17, 20:17] Washa: 🌹 *DEEJAMAH* 🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writteng by *UMMU SAFWAN* (Fareeda Basheer) *54* Tana fad'in "Hello Yaya barka da hutawa ya aikin?" Cikin sauri Mahmud ya kuma yin murmushi yace " my blood sister lafiya k'alau yakike?" Tace lafiya k'alau, Zai kuma yin magana tayi saurin ka tseshi,tace "yaya gani a gidanka yanzun na sauka na taho ina jin yunwa da k'ishirwa, Amma Anty Yusra ta hana mun ruwan sha, bare abinci, da nayi mata magana ce mun tayi ban isa ta bawa 'yar k'auye ruwan sha ba." Wann ya nuna mun cewa bana da daraja da wani girma a gidan nan tun har za'a iya hanamun ruwan da zan sha a matsiyana na wanda tayi tafiya." "What." Yace Cikin tashin hankali mahmud yace "dijama yanzun haka maganar da kikeyi kina cikin gidana?" Murmushi tayi had'ida yin fari da ido tace "ina ciki yanzun haka yaya." Yace "OK kije kusa da ita yusra ki sanya handsfree zanyi magana da ita." Tace "ai ina kusa da ita kasan ni bana kyamatar duk abinda ya shafeka." Yace 'Nasani mana" Tace "kayi magana tana jinka, Mahmud cikin fad'a da masifa harda dukan teburin da yake gabansa ajiye yakeyi "Yusra kinajina umurni na baki ba kuma zan had'aki da Allah ba, Kije ki d'auko ruwa ki bawa dijama, tasha kiyi mata duk abinda takeso, idan ba hakan ba, duk kika kuskura kika bari na dawo baki aikataba saina lahira yafiki jin dad'i." K'awayenta suka zuba mata ido cike da mamaki, suna kallon ta tafiya zatayi ta d'auko ruwan tabata kuwa?" Yusra kuma sanin halin mahmud da tayi ba k'aramin abu bane a wurinsa idan ya dawo yasami labarin bata aikata abinda yace ba, k'aramin aikinsa ne ya mata rashin mutunci Kuma ita dai tana sonshi bazata iya rabuwa da shiba." Ta janye wayar a kunnenta, dijama ta sanya hannu ta karb'e wayarta tana kallon yusra tana murmushi, Yusra ta mik'e tana d'ingirsa k'afarta tanufi frege ta d'aukowa dijama robar ruwan faro ta kawo mata." Shewa abokananta suka shigayi suna fad'in wlh ke kin bada mata, yanzun kamar wnn yarinya ta isa ta sanyaki abinda bakiyi niyyaba Yusra batayi magana ba, zuciyarta cike take da bak'in ciki, Zata zauna dijama tace "hy Yusra kin manta baki d'auko mun cup ba." Shuru tayi tana kallon dijama cike da tsana jitakeyi kamar ta hauta da duka, Ta kauda idonta daga kallonta, bata niyar tashi." Dijama tace "OK baxaki d'auko ba kenan? Ta kuma d'aukar wayarta zata kuma kiran yaya mahmud ta fad'a masa." sai gani tayi Yusra ta mik'e da sauki tanufi hanyar kicin." Duk abinda akeyi fateema tana kicin tana kalllonsu tsoro ne fal a ranta." Yusra tafito da cup rik'e a hannunta ta ajiyewa dijama a gabanta, Dijama ta kalleta tace "kizuba mun kibani da hannuna na sha." Hakan zaisa naji dad'i kin karramani." K'awayenta sukace "kadda kibata kada Allah yasa tasha ruwan idan har sai kin zuba mata." Suka wurgawa dijama harara sukace Banxa 'yar k'auye." Dijama ta d'aga kai ta kallesu, Tace "ya kamata Ku iya bakinku kusan abinda kuke fad'a idan ba hakan ba, idan kuka kuskura kuka k'ureni tare da b'ata mun rai yanzun zan nuna maku irin nawa k'auyancin zan nuna maku cewa "eh lallai ni 'yar k'auye d'in CE." Ta juyo wurin Yusra tace "madam Yusra kizuba mun ruwa a k'ofi nasha." Tace "bazan zuba ba sai dai kada kisha." K'awarta tace "wlh karki zuba mata" Dijama ta d'aga hannu ta buge bakin k'awar wadda ta lura tafi kowa rashin kunya a cikinsu, Ta cire glass d'in idonta ta ajiye Jakarta a gefe tace yanzun zan nuna maki cewa ni 'yar k'auyen ce." Rik'e bakinta tayi da taji yana mata wani irin zugin zafi duk a tunanin hak'oranta sun zube." Hankalinta A tashe ta shiga janye a hnnunta daga kan bakinta tana nunawa 'yar uwata. Tace "diba mun kigani hak'ora na suna nan?" Ko sun zube." Ta diba mata tace suna nan basuyi komaiba." Dijama tana nan tsaye rik'e da k'ugu tana jiran Wanda zai tunkarota ta masa shegen duka." Tsaitsaye sukayi suna kallonta ko wannensu tsoron tunkararta yakeji." Ta kuma kallon yusra tace " ki salami k'awayenki su bar gidan nan tunda ba gidan ubansu bane." Idan ba hakan ba tayi shuru ta d'auki wayarta ta danna kiran number mahmud.' Mahmud da yake kan hanyar zuwa gida ya wani kiran dijama ya shigo, Da sauri ya d'auki wayar Yace "bata baki ruwanba?" .kibarta kawai ganin k'arasowa gidan yanzun INA kan hanya." Yusra najin hakan ta juya tA kalli k'awayenta ta shiga rok'onsu dan Allah su taimaketa suyi tafiyarsu tin kafin Mahmud ya shi go ya samesu." Kallonta sukeyi a alalace suka had'a Baki gaba d'ayansu sukace Yusra mu kike kora?" hak'uri take basu jikinta na rawa ta dinga mink'awa ko waccensu gyalenta da jakarta, Karb'a sukayi sunasakin baki suna mamakinta Ta yanda sukaga dinga ganin jikinta narawa kamar wacce taga mala'ikan mutuwa." Turasu ta shigayi da hannuta ganin basu da niyar tafiya, Dakatar da ita sukayi a fusace, "Dallah malama ki daina turamu ai ko baki turamuba dole ne mubar maki gidanku, Amma kisani indai kina tare da mahmud wata rana sai kin nememu." Suna kaiwa nan ko waccensu ta fita a fusace." Dijama na zaune a kan kujera ta d'ora k'afa d'aya kan d'aya zuciyarta fal da farin ciki, sai murmushi take saki a fuskarta." Ta kuma kallon Yusra tace "asirinki ya rufu tunda kika kori Wad'an nan 'yan Iskan k'awayen naki, Amma fa har yanzun baki zuba mun ruwa nasha ba." Ta Kuma wurgawa dijama harara cike da tsana, Ke Baki isa kisanya na kori k'awayena ba, na koresu ne saboda wani dalili nawa, Taja wani dogon tsaki "banxa 'yar k'auye, tajuya xata tafi" Dijama ta sanya k'afa ta hankad'eta ta fad'i k'asa rufda ciki, Tace "yanzun zan nuna maki abincin k'auye dana birni ba d'aya bane, Ina ganin bakisan ko wacece dijama ba, da baki isa ina fad'i kina fad'iba." Yusra dake kwance rufda cikin a tsakiyar falo k'afarta mai ciwo ta shiga yi mata zugin zafi, Cikin zafin rai ta mik'e daga kwance ta tunkaro dijama tana wani huci, ta d'aga hannu zata kwad'awa dijama mari." Dijama tayi saurin rik'e hannun da hannunta d'aya ta murd'e hannun, sai da Yusra tasaki yar k'arar wahala Dijama ta kuma d'aga hannu d'aya ta d'auke yusra da mari a fuska sai da gaba d'aya falon ya amsa da k'arar marin ji kakeyi tasssss.... Wanda yayi daidai da shigowar Mahmud falon shima yaji k'arar saukar marin, Dijama na ganin yaya mahmud tayi saurin sakinta tarik'e kunci tana matsar hawaye tace "ni zaki mara daga nace kixubamun Ruwa nasha?" Menamaki?" Me natare maki a gidan nan daga zuwa na yanzun ko hutawa banyiba?" Ta matso hawaye k'arya a idonta tace "Kiyi hak'uri idan zuwan da nayi gidan nan natare maki wani abun yanzun zan juya na koma Inda na fito." Mahmud dake tsaye ya k'urawa dijama ido, yana ganin zubar hawayenta jinsu yakeyi har Cikin ransa, Jikinsa har wani rawa yakeyi akan b'acin rai da jin haushin yusra." Cikin muryar b'acin rai yace "baxaki bar gidan nan ba sai dai ita ta barshi tunda ba gidan ubanta bane." Ya nufo Yusra cikin hushi yace "metamaki kika mareta lallai Kuwa yau zan Nuna maki cewa ke k'aramar Marar kunya ce." Duk'a ki tsiyaya mata ruwa kibata tasha, Idan ba hakan ba sai na lahira yafiki jin dad'i." Yusra da ta daskare tsaye wuri d'aya rik'e da kunci tana kallon dijama cike da mamaki da Al'ajabi, Wnn shi a kekira a dukeka kuma a hanaka kuka." Bata ankaraba taga mahmud ya Ciro belt d'insa na uniform d'in sojoji wad'anda ke sanye a jikinsa yanufo ta gidan gadan yana Neman dukanta dashi yana fad'in baxaki zuba mata ruwan tashaba?" Tasan zafin dake tare da belt d'in saboda tana ganin daddynta yana dukan b'arayi dashi wanda da zarar yayi masu d'aya dashi sai jikinsu ya farfashe da jini" Da sauri ta nufi wurin robar ruwa ta d'auki cup ta tsiyayawa dijama ta mik'a mata." Mahmud ya tsurawa dijama ido cike da jin tausayi "Cikin muryar lallashi yace "yi hak'uri k'arb'i kisha." Sai da ta juya ta koma kan kujera ta zauna snn Yusra ta Kuma matsawa kusa da ita ta mik'a mata cup d'in ruwan ta amsa ta kafa a bakinta ta shanye." Mahmud yace "kink'oshi ko ta k'ara zuba maki wasu?" Ta "girgiza kai a shagwab'ance tace A'a sun isheni." Snn ya juya ya kalli Yusra yce kina iya wucewa ki kama gabanki." Da gudu Yusra ta wuce tasaki wani irin kuka mai sauti, ta fad'a d'akinta." Sai a lokacin FATEEMA dake lab'e wuri d'aya ta fito tana zarar ido kamar wacce tayi k'arya😅 *kuyi hak'uri da Wnn nayafi gidan biki sai na dawo*🚶‍♀ [8/17, 20:17] Washa: 🌹 *DEEJAMAH* 🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writteng by *UMMU SAFWAN* (Fareeda Basheer) *masoyan deejama 'yar gidan tsohuwa inajin dad'in yanda kuke bibiyar labarin nan comment d'inku yana sanyani nishad'i da dariya musamman 'yan group d'ina UMMU SAFWAN HAUSA NOVELS Allah yasa ku anfana da darasin da ke cikinsa* *55* Mahmud ya matso daf da dijama itama dijama ta matsoshi kamar zasu rumgume juna saboda murna da farin cikin ganin junansu, Kome suka tuna oho ko wannensu yayi saurin dakatawa, da sauri ta juya baya idonta ya cika da hawaye." Cije baki yayi ya shafi gefen kan shi snn ya k'ak'aro murmushin dole yace "dijama 'yar gidan tsohuwa, Amaryar a wurin sulaiman barka da zuwa." Gaban ta ya fad'i da taji yakirata da amaryar sulaiman." Ta goge hawayen da suke neman zubo mata ta juyo da fuskarta tana kallonsa ta sauke ajiyar zuciya snn ta sauko daga kan kujera ta durk'usa k'asa tace "yaya ina wuni." Murmurshi yayi yana kallonta cike da burgewa, rabon da a durk'usa har k'asa a gaida shi har ya manta, Yace "lafiya k'alau 'yar k'anwata, ya hanya?" Tace "Alhamdulillah." "Kiyi hak'uri da abinda ya faru kadda kice yau zaki koma gida dan nasan halinki da zuciya." Taturo baki cikin shagwab'a tana magana k'asa k'asa "to ai halinmu d'aya dakai, Yana jin abinda tace yayi murmushi ya girgiza kai yace "halin ya motsa yau kenan." Ya juya kalli fateema da tayi tsaye tana kallonsu kamar gunki, yace "ke bakiga 'yar uwarki bane kika wani toge wuri d'aya kina zarar ido kamar wacce tayi k'arya." Sai a lokacin fateema tayi dogon motsi domin jinta takeyi kamar ba'a hanyacinta takeba akan tsoro, Ta matso kusa da dijama ta rik'a hannunta tana "fad'in sis sannu da zuwa." Dijama tayi murmushi tana kallonta tare da binta da hararar wasa, tace "sai yanxun kika ganni." Mahmud yace "ki kaita d'akinki tayi wanka ta huta snn kufito muci abinci." Ta rik'o hannun dijama ta d'auki Jakarta suka nufi d'akin." Suna shiga d'akin kai tsaye dijama ta fad'a kan gado tana fad'in "wash Allah na sis na gaji da yawa driven akwai wahala." Fateema ta sauke ajiyar zuciya ta zaro ido tace "yanzun da kanki kika tuk'o mota tun daga kano har Abuja?" Dijama ta mirgina ta janyo filo ta d'ora kanta a kai, Tace "kin d'auka Kowa irinki ne ma tsoraci? Fateema taja dogon nishi tace "sis wlh naji dad'i da kikaci uban k'awayen Anty Yusra, Kekinji irin magagganun da sukeyi suna zugata tare da bata shawarar banza." Ashe dama yaya mahmud ba sonta yakeyi ba ya aureta." Dijama tayi saurin mik'ewa zaune tana kallon fateema tace "bangane ba sonta yakeyiba." Anan tashiga bawa dijama labarin duk abinda taji yusra na fad'awa k'awayenta a kan Mahmud." Wani irin farin ciki dijama taji ta a cikinsa Wanda har ya kasa b'oyowa a fuskarta, tace amma fateema nayi mamakin jin Wnn maganar." Ba abin mamaki bane da kanki zaki ganewa idonki a cikin gidan nan." Fateema ta kuma nisawa ta kalli dijama tace "ni kuwa sis wnn irin kallo da naga kuna yiwa junanku dake da yaya mahmud na meye?" Sai naga saura kad'an ku rungume junanku, ni dai fateema yau naga abin mamaki iri iri a gidan nan azal ta kawoni." Dijama tayi dariya tace "ba wani kallo da kikaga munayi. illah gaisuwar da mukayi. To kona ma kallesa ya kalleni sai me?" Yaya mahmud nefa jinina, d'an uwana Wanda nafi shak'uwa da shi akan kowa, karki damu da irin kallon da kikaga munayiwa junanmu." Fateema tace "uhm ai na dad'e da gano ku mudai idan tayi wari maji." *************** Mahmud shima yana shiga d'akinsa kai tsaye kan gado ya fad'a yayi rigingine yau jinsa yakeyi cikin farin ciki, Wanda yasa shi ya manta da rashin kunyar da yusra tayi." Babu abinda yake hangowa sai kwayar idon dijama a lokacin da ta kafeshi da su tana kallonsa, Wani abunda yake hangowa a cikin idonta mai wuyar fasaltawa." Kuma mirginawa yayi ya janyo fillow ya rungume tare da runtse idonta yana murmushi." ****************** Yusra kuka takeyi kamar zata had'iye zuciya ta keji, irin wulak'ancin da Mahmud ya mata a gaban wata banzar k'anwarsa wadda take zargin sonta yake." Zata iya d'aukar ko wanne Irin wulak'ancin sa, idan daga Ita sai shine a gidan, Amma bazata tab'ata d'aukar yana wulak'anta ta a gaban mata 'yan uwantaba." Shawarar k'awayenta ta fad'o mata a rai, idan soyayya kike nema an bud'e wani Sabon gidan mata akwai maxa duk irin wad'anda kikeso wad'an da zasu kasheki da soyayya har sai kin suma kindawo baki sani ba a kan dad'i." Murmushin da yafi kuka ciwo ta k'ak'aro tace "bana son ko wannen namiji mahmud nakeso Mahmud nake so na mallaka shi kad'ai nakeyiwa kallon namiji, Amma yau zan tafi wurin dan naganewa idona ko dan nafita daga cikin b'akin Cikin da ke damun zuciyata." Ta d'auki wayarta ta kira k'awayenta ta shiga basu hak'uri, a kan abunda ya faru tace suyi mata kwatancen inda gidan matan yake gata nan zuwa anjima." Kuwa suka d'auka da shewa suna fad'in ko kefa, amma yaushe zaki zauna bak'in cikin d'a namiji ya kasheki da gatanki da kyawonki da komai naki." Haba komai ai yawuce Sai kinzo hajiya kizubo kud'i a jaka dan hutawa, murmushi tayi tace "kud'i ba matsalata bane." Snn ta kashe wayar." Misalin k'arfe 7:50pm Mahmud yana masallaci domin Al'adarsa kenan duk lokacin da yatafi sallar magariba baya fituwa a masallaci sai anyi sallar isha'i, Sai da Yusra ta kwatanci baya nan yana masallaci snn taci kwalliya ta fitar rai Cikin wasu k'ananun kaya Riga da wando wad'anda suka kama jikinta saika rantse da Allah kace ba musulma bace." Gaba d'aya jikiñta sai da ta wanke she da turarunka snn ta d'auki wani d'an figigin gyale ta yafa a kanta ta sanya talkaminta masu tsinin gaske ta d'auki Jakarta tafito. Gaba d'aya falon ba kowa a cikinsa suna kitchen suna hidimar abinci mahmud yace adafa masa tuwon samo da miyar kub'ewa d'anya, dijama ce yau ke girkin gaba d'aya gidan ya d'auki k'amshi." Yusra tayi ficewarta ba tare da Kowa ya gantaba, Bata tsaya d'aukar motaba saboda mahmud zai gane gidan ya duba wurin ajiye motoci bai ga mota d'aya ba." Hakan ta dinga tafiya a bakin Layin kasancewar unguwar GRA ce ba mutane sosai a cikinta, Waya ta d'auka ta kira k'awayenta akan suzo da Mota su d'auketa gata nan a kan hanya tafito, Ai kuwa Cikin minti 30 ta gansu a gabanta suka d'auketa suna Shewa suka nufi gidan Mata da ita." Gidan mata babban gidane wanda baya misaltuwa a kan girmansa, da fad'insa kota INA d'akunane birjek da kayan more rayuwa a cikin su." Gidan cike yake da Samari da 'yan mata ko wanne yana holewarsa, Wurin ajiye motoci sukayi parking suka firfito Yusra sai kallon wurin takeyi kota ina tana mamaki domin wurin ya burgeta sosai." A can ta hango wani shuga daddy babban mutum ya rungume budurwarsa ya matseta gam a jikinsa sai shinshinarta yakeyi ko ta INA ajikinta, yana kissing d'inta, Runtse idonta tayi da ta kalle su' wani abinda taji har cikin ranta, K'awayenta suna lura da yanayin da tashiga, Sukace kisaki jikinki ki holewarki kinga irin shuga daddys d'in can sunfi Kowa iya kashe macce a soyayya saboda sunsan jikin macce, sunsan lungu da sak'o na macce. Sunsan inda zasu tab'owa macce taji dad'i harta some." Kidiba kiga wancan yanda yake ma budurwasa harda fa lasheta yakeyi ta ko ina." Yusra ta kuma tsuma a nan take sha'awarta ta motsa dama tana da buk'atar d'a namiji." Suna nan tsaye gefe d'aya suna kallon duk Wanda ke shigowa da fita suna Kuma k'ara tsuma Yusra kafin sushiga wurin." Alhaji Atiku ya shigo da motarsa a hankali Cikin gidan yanayi yana rage glass d'in motarsa yana kallon 'yan Matan dake zazzaune sunajiran masu tayasu." A can nesa yayi parking ya fito da waya a kunnensa yana waya da wani abokinsa koma nace amininsa Wanda baya k'asar, jiya yadawo yake shaidawa Alhaji Atiku yadawo jiya yanzun hakan gashi a Abuja yaje gidansa anfad'a masa baya nan yanzun ya fito, Dariya Alhaji Atiku yasaki yace "yanzun kuwa na fito daga gidan gani nan nataho wurin hutawa kashigo wurin kawai abokina kaima ka huta akwai mata kala kala masu zafi duk irin wacce kakeso sai ka darje. Ka zab'a" Anan Alhaji Atiku ya shiga yimasa kwatance wurin, daga k'arshe sukayi sallama da cewa gayanan k'arasowa wurin yanzun." Zaro ido Yusra tayi hankalinta a tashe ta Shiga Nuna Alhaji Atiku da hannu tana fad'in wanake gani kamar daddy na." Suka had'a Baki sukace daddy ne mana, Ai daddy yana zuwa wurin nan, Ai wurin hutawar sa, kenan to Meye a ciki Dan kinzo a wuri daddy ya zo?" Ai sai muke ganin ko wanne daga cikinku lalurarsa ta kawoshi Kuma ai bai gankiba kema ki d'auka Baki ganshiba, Kowa tashi ta finsheshe, Wlh daddy yana burgemu saboda kansa a waye yake, ba k'arya daddy yana burgemu." Yusra bata k'ara tsinkewaba sai da ta hango budurwar Daddy ta rugo da gudu ta rungumeshi ai kuwa da sauri daddy ya kashe wayar hannunsa ya bud'e hannu biyu ya rungumeta, Ya d'ago kanta ya Sanya bakinsa cikin bakinta, Bata kuna tsinkewa ba sai da taga daddy ya d'auketa cak kamar jaririya ya nufi wani d'aki da ita yana dariya kamar gonar auduga." K'afafunta suka kasa d'aukarta tayi saurin yin baya ta kai jingine jikin mota. "Kinga yanda ake wayewa ko?" Wlh daddy yayi rayuwar daddy tayi Kansa a waye yake inji k'awayenta." Snn ko wacce ta nufi wurin saurayinta aka bar Yusra tsaye ita kad'ài tana jimami." Alhaji yasir naira abokin Alhaji Atiku ya shigo da motarsa cikin gidan, yashiga Kiran Alhaji Atiku ya fad'a masa gashi yashigo amma ina Sam bai d'aukaba daddy ya hau network." Wata kyakkyawar yarinya ya hango a wuri d'aya tsaye ita kad'ai, Yayi parking da Sauri gefe. D'aya ya nufi wurinta yana lasar Baki, Alhaji Yasir shima ba baya yakeba wurin Neman Mata fara gudu suke rabawa dashida Alhaji Atiku." Kai tsaye wurin Yusra ya nufa d'auke da kalaman bakinshi wad'anda yake amfani dasu wurin yaudarar macce." Cikin minti 20 ya saye zuciyar Yusra da kalamai masu Dad'i, Anan take ya kama d'aki yarik'a hanun ta suka nufi d'akin, Alhaji Atiku ya dawo cikin hayyacinsa ya yaga Kiran da abokinsa yayi ta masa, ya tashi ya Sanya kayansa, ya d'auki wayarsa yafito yacewa budurwarsa ta jirashi yanzun zai dawo." Fitowarsa ya hango Alhaji Yasir da wata tsaleliyar budurwa sunjuya baya suna tafiya, Da alama d'akin da ke gabansu zasu shiga, Ido Alhaji Atiku ya kure budurwar dashi yaga yanda take juya mazaunanta, hankalishi ya tashi cikin sak'an d'aya yaji yana buk'atar shima ya ganshi Tare da yarinyar, Dama sun saba hurd'arsu. A tare Suyi tarayya da macce d'aya, a lokaci d'aya idan Wnn ya sauka sai wnn ya hau." Ya Kama lashe baki da ya hango yanda Alhaji Yasir ya fara shafar d'uwawunta snn daga k'arshe ya d'auketa cak ya shige da ita d'akin." Cikin Sauri Alhaji Atiku ya d'aga waya yakira Alhaji Yasir yace "waton daga kwada maka hanya har kazama d'an gari, Wnn kyakkyawar fulawar da na ganga da itafa?." Amma gaskya ta nuna har tayi ja." Idan ka tsinke furen cikinta Ka d'an aramun nima na tsinka." Alhaji Yasir yayi dariya yace wnn fulawar ko kallonta bazaka kumayi ba, bare har ka sanya ran zaka tsinketa don Kuwa wnn tawace ni kad'ai bana iya had'ata da kowa, Ya kashe wayar ya shiga sarrafa Yusra." Ranar Sai da Alhaji yasir ya mayar da Yusra tamkar matarsa sai sarrafa yakeyi a yanda yakeso." Ita ma sai kuwar dad'i takeyi saboda Alhaji Yasir yayi mata a yanda take son namiji ya kasance mata a fagen soyayya." *Fad'ar Annabi ce duk abinda kayi wa 'yar uwani sai anyiwa taka 'yar, yana can yana b'ata 'yar UWANI , shima ana b'ata tashi 'yar* [8/17, 20:17] Washa: 🌹 *DEEJAMAH* 🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writteng by *UMMU SAFWAN* (Fareeda Basheer) *56* Mahmud kuma bayan ya dawo daga masallaci yaji gaba d'aya gidan k'amshin girki ya gauraye shi, Babu Wanda ya fad'o masa a rai sai mommy idan tana yiwa daddy girki hakan zaka dinga jin gida ya gauraye da k'amshi kota ina." Murmushi ya saki dan yasan wnn girkin dijama ne bana fateema ba, Bai k'ara tsinkewaba sai da ya hau kan dining table, Wani yawo ya had'iye tare da gyaran baki, dan kuwa har yaga nawar abincin yazo bakinsa." Dijama ta taso ta shiga zuba masa abinci, Ido ya bita dashi yana murmushi, bak'a ramin burgeshi tayi ba, domn yana matuk'ar son ya ganta ta sanya dogowar riga bak'a, Wani irin kyau yake ganin ta Kuma k'ara masa." fateema na kallon sa tana murmushi da ayar tambaya a bakinta." Bayan ta gama zuba masa abincin ta tura masa a gabansa tare da zuba masa sassanyan lemun kwakwa mai sanyi Wanda rabon da yasha irinsa tun da ya baro kano, Babu abinda yakeyi sai murmshi, a fuskarsa tabbas dijama renon mommy ce duk wani nau in kalar abincin mommy ta iya shi." Fateema ta mik'e tsaye tace "bara na kira Anty Yusra ta fito muci abinci." Dijama ta wurga mata harara tace "wlh bazataci abincin nan ba, matar da ta hana mun ruwa, Har zan dafa abinci na bata taci tabd'i jam sai dai tafito ta dafa da kanta." Mahmud baice komaiba sai lomar tuwonsa yake kaiwa a bakinsa yana lumshe ido." Bayan sun kammala cin abincin ne suka dawo falo suka zauna suna kallo, amma hankalin mahmud yana wurin dijama motsi kad'an idan tayi idansa na kanta. Jiyakeyi kamar ya saceta ya gudu." Anan suka raba dare suna kallo Wanda Mahmud ya lura da baiji motsin yusra ba wata zuciyar tace masa "wata k'ila bacci takeyi." Sai da dijama ta fara hammar bacci snn ya tashi ya kashe kallon tare da yi masu sai da safe, sai da yaga sun shige d'akinsu, Snn shima ya shige nashi d'akin yana kallon fuskar dijama yana murmushi yau yasan zaiyi kwanan farin ciki, da ace ba aikin bincike sukeyi a office ba, To babu abinda zai fitar dashi aiki gobe ba." Domin yanaso ya ka d'ai ce daga shi sai dijama dan yana da tarin magagganun da zaiyi da ita." **************** A ranar Yusra a can ta kwana, Alhaji Yasir yaji dad'in kasancewar sa da ita Wanda har yakejinsa baya iya rabuwa da ita, Itama Yusra gareta hakan ne taji dad'in kasancewa tare da Alhaji.yasir amma ba wai yana nufin ta fara sonshi ba ne A'a ita dai zuciyarta tana wurin mahmud shi kad'ai takeso baxata tab'a son wani nmijin kamarsa ba." Alhaji yasir ya cika wa yusra jakarta da kud'i wad'anda shi kansa bai san iya adadinsu ba." Yace ta d'aukar masa Alk'awari bazata kuma kula kowa ne namijiba sai shi kad'ai, idan tamasa haka yayi mata alk'awarin zai mata duk abinda take so a rayuwarta." Kuma kada ta kuma zuwa wnn gidan, ta bari idan ya shigo zaiyi mata waya ta zo ta sameshi." Murmushi tayi ta girgiza kai tace "ta yarda ta amince." Basu rabu da junansu ba sai da safe misalin k'arfe goma na safe snn suka fito daga gidan ya d'aukota a motarsa ya kawo ta bakin layinsu ya ajiyeta, Hankalinta a kwance ba wani tsoro a tare da ita, saboda tasan a dai dai wnn lokacin mahmud ya tafi wurin aiki." Kai tsaye cikin gidan, tashiga Wanda gaba d'aya gidan babu abinda kakeji yana yatashi sai k'amshin turaren wuta, tare da karatun Alqur'ani, Dijama da fateema suna falo zazzaune suna hira suka ga shigowarta cikin wnn shigar, Wanda bazaka tab'a cewa matar aure bace, Bako sallama ta rab'asu ta wuce tayi shigewarta d'akinta." Kallo suka bita dashi suna mamaki, dijama ta mik'e tsaye tace "lallai yau saina koyawa wnn yarinyar hankali da tarbiya ya zata shi go mana gida babu ko sallama." FATEEMA tayi saurin rik'ota ta ta zaunar da ita, tace "rabuda da ita sis bakiga irin shiigar da ke jikintaba, Ina ganifa ba a Gida ta kwana ba." Dijama ta zare ido tace. "To gidan ubanwa ta kwana?" FATEEMA tace "oh mata amma dai ki kyaleta yanzun ki barta sai wani lokacin." ***************** Abba da mommy suna ganin dijama ta taje Abuja suka shirya suka tafi Dubai domin had'owa mahmud kayan lefe." ***************** Khalil kuma tun lokacin da Ashanty tayi masa waya akan cewa sai ya kuma bata wasu kud'i wad'anda ke hannunta basa isarta a zubar da cikin." Cikin azama yaje wurin Abba ya shirya masa k'arya akan karatunsa, akan cewa makaranta sunce a bada kud'i, zasu saya wani abin." Abba mutum ne Wanda yasan zafin ilimi da mahimman cinsa, Dan haka a kullum idan yana tare da iyalinsa maganarsa d'aya ce a kan suyi karatu." Abba bai tsaya wani tambayaba ya tura masa dubu d'ari a account d'insa, Godiya Khalil yayi yaje ya ciro kud'in yakira Ashanty a waya tasame shi gidan Ahmad sai da suka gama shek'e ayarsu suka gaji snn daga k'arshe ya mink'a mata kud'in gaba d'aya." yace "ina fata wad'an nan suna isarki wurin zubar da wnn shegen cikin tare da nuna cikinta da hannu Wanda ya fito ya bayya ba laifi." Murmushi tayi tace "honey meyasa kake sheganta cikinka?" abinda kai kasani nima nasani jininka ne?" sai nake ganin ko haihuwarsa nayi bazaka so a kirashi da shegeba." Da sauri yatse mata magana tare da kallonta yace "bazaki tab'a haihuwarsa ba." dan kuwa abin kunya ne a gareni kamata a Ganni da d'an shege ace kuma nawa ne." "Daina d'aga hankalinka honey ai bakada matsala indai akan wnn cikin ne kamar anzubar dashi angama." Ta mik'e tsaye ta sanya kayanta ta d'auki kud'in da yabata ta saka ajaka tayi msa sallama ta fita tana masa murmushin mugunta, ta shafi cikinta tace "ina sonka baby nah baxan tab'a xubar da kaiba' Zan d'auki duk wani k'alubale da tsangwama da zan fuskanta a wurin mahaifina." Kasancewar mahaifiyar Ashanty ta rasu a hannun kishiyar uwarta take Wanda bata damu da tarbiyartaba, Dan ma mahaifinta malam Lawali yana tsaye tsayin daka ga iyalinsa, dan kuwa Ashanty ta taso cikin tarbiya da kamun kai had'uwarta da Khalil ne ya b'ata mata rayuwa gashi harda ciki ke gareta Wanda mahaifinta bai San dashiba, Kasan cewar Ashanty bata da girman ciki kuma kullum da hijabi take xama a gida." Hakan Ashanty ta dawo gida tare da kud'in da Khalil ya bata dama wad'anda yabata daga farko sunanan babu abinda tayi dasu ta ajiye, domin hidimar d'anta bayan ta haihu." *************** Mahmud ya dawo gida a gajiye, ya tarar da dijama kwance a falo ita kad'ai tana bacci da murmushi ya nufeta ya zauna a kusa da kujerar da take fuskantarta kallon fuskar ta yakeyi yana murmushi domin ganin yayi tayi masa kyau, sai yanzun ya kuma tabbatar da tabbas kamarsu d'aya komai nasu iri d'aya babbancin d'aya ne ita macece shi kuma namiji." Murmushi yakeyi sai ya d'aga hannunsa da niyar ya shafi fuskarta tareda gyara mata gashin kanta daya zubo saka makon d'ankwalin kanta da ya zame Sai kuma ya sauke hannun, ya fasa yana murmushi Fateema dake bayansa a tsaye tana kallonsa tana murmushi snn tayi gyaran murya tace "yaya sannu da zuwaa." Firgigit yayi kamar Wanda ya tashi daga bacci ya d'an sosa kai ya mik'e tsaye, Yusra ya gani a can gefe d'aya zaune ta d'ora k'afa d'aya kan d'aya tana kallonsa tana girgiza k'afa cike da jin haushi.' [8/17, 20:17] Washa: 🌹 *DEEJAMAH* 🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writteng by *UMMU SAFWAN* (Fareeda Basheer) *57* Wani kallo ya wurga mata mai cike da tsana, Yayi wuce warsa." Yusra itama ta murgud'a baki had'ida wurga masa harara tare da jan dogon tsaki, tace "ai dama nasan hakan Zata faru, Kuma na rantse da Allah baka isa KA aureta ba saboda ina sonka, kuma daddy na bazai bari KA aureta ba." Idan kuma KA kafe akan sai ka aure ta, Har kabari aka kawota gidan nan to kasani dani da kai da ita duk sai na cin nawa kanmu wuta dukanmu mun k'une kowa ya rasa." Dan kuwa babu wacce ta isa ta shigo gidan nan a matsayin matarka inaji ina gani kuyi rayuwar aure da ita." Tsaye Mahmud yayi yana kallonta cike da mamaki irin yanda yaga tana masa magana cikin rashin kunya." Juyawa yayi ya kuma kallon fuskar dijama dake bacci gani yayi da zarar ya biye mata yana iya tayar da ita daga bacci da takeyi, ya girgiza kai yayi juya yayi shigewarsa d'akinsa." Ta dawo kan fateema ta wurga mata harara tace "ke kuma muna fuka kinsaki ido wuk'i wuk'i kina kallona wuce ki zubo mun abinci naci yunwa nakeji." Fateema itama ta wurga mata harara tace "aikece babban funafukar kuma abinci bazan zubo ba dan kuwa bake kika girka shiba." "Keni kike fad'awa magana?" Ina matsayin matar yayanki?" Wanda muke kwana a gado d'aya dashi ai kuwa yau zanyi maganin rashin kunyarki." "Anfad'a maki kema ai yanzun kika gama yiwa yaya rashin kunyar." Yusra ta d'aga hannu zata kaiwa fateema mari, Sai gani tayi dijama tayi sauri ta rik'e hannun." Dama dijama ba bacci takeyiba jin tsayuwar motar mahmud ce yasa tayi saurin rufe ido kamar wacce takeyin bacci." Duk abinda Mahmud yake mata tana kallonsa." Ta murd'e hannun Wanda sai da Yusra tasaki 'yar k'ara snn dijama ta kwad'a mata mari har sau biyu." Bak'adan Yusra taji zafin marinba Wanda yasa ta kama dijama da kokawa." Sai da dijama ta d'agata sama ta kayar da ita k'asa, ta haye kanta tashiga dukanta, dama tana da haushinta." A guje fateema ta ruga ta fad'owa mahmud, Da sauri ya fito ya tarar da dijama a kan ruwan cikin Yusra sai dukanta takeyi." Da kyar mahmud ya samu ya b'anb'ari dijama a jikin yusra Wanda ta daku iya dakuwa sai shisshikar wahala takeyi." Tana ganin mahmud ya janye dijama daga kanta tayi saurin mik'ewa tsaye tana wurga masu harara gaba d'ayansu, Dama nasan mahmud baka sona ka kuma tsaneni amma kasani bazan gaji da furta maka Kalmar ina sonka ba." Koda zakayi gunduwa gunduwa da naman jikina, Kema 'yar k'auye mai k'arfi kamar namiji kisani baki daki banza ba, Ni nasan matakin da zan d'aukar maki a cikin gidan nan." Dijama Ta kuma yin kanta zata kuma dukanta mahmud yayi saurin rik'o hannunta ya nufi d'akinsa da ita." *kuyi hakuri da wnn da babu kwanda kad'an*👌🏻 [8/17, 20:18] Washa: 🌹 *DEEJAMAH* 🌹 ( _'Yar gidan tsohuwa_ )😅 Writteng by *UMMU SAFWAN* (Fareeda Basheer) *58* Akan kujera ya d'orata yaje kusa da ita ya zauna, Ganin ranta a b'ace yake ya mik'e tsaye ya nufi frege ya d'auko ruwa masu sanyi ya zuba mata a cup ya kara mata cup d'in a baki ya shiga bata ruwan da kansa." Sai da ta shanye, snn taja doguwar ajiyar zuciya mahmud ya ajiye cup d'in a gefe d'aya." Ido ya kafeta dashi yana kallonta jiyakeyi kamar ya rungumeta ya lallasheta." Cikin murya k'asa k'asa "yakira sunanta "dijama wai meke faruwa ne?" Kallonsa tayi ido cikin ido Wanda shima ita d'in yake kallo, Sai da suka d'auki kusan minti biyar a hankan ko wannensu ya kasa d'auke idonsa daga kallon junansu, Mahmud yayi k'arfin hakalin janye idonsa daga kan nata, Yace tambayarki fa nakeyi." Ta turo baki cikin shagwanb'a tace "Allah yaya kajawa matarka kunne ta daina shiga shirgimu idan taga munayi a gidan nan." Idan ba hakan ba Allah kafin na bar gidan nan sai nayi mata shegen dukan tsiya na koya mata hankali." Dariya taso ta sub'uce masa yayi saurin dannewa yace "ai kuwa bazaki yiwa matata duka a gaban idona ba." Da sauri ta juya ta dubeshi ta kuma had'e fuska tace "ni ina ruwana da matarka ce, Bakaji abinda take cemun ba ne?" "Metace maki ni banjiba illah kawai abinda naji cewar da tayi wai taga alamar sonki nakeyi. Kishi kawai takeyi saboda tana son mijinta." "Ta kuma had'e fuska "meye ruwana da son da take maka bazai haka na nad'a mata shegen duka ba, Wanda har saitayi fitsari." Ya kuma danne dariyarshi yace "ni kuma idan kikayi mata duka Naje na sami sulaiman shima na nayi masa shegen duka kamar yanda kikayi mata, saikiji idan da akwai dad'i." Mere baki tayi☹ tace "a haf idan karik'ashi kasheshi kawai kada ka barshi da rai." Dariya ta sub'uce masa yace "saboda me mijinki fane Wanda kikace kina Sonshi za'ayi maku aure Nanda wata biyu." Harara ta wurga masa ta gefen ido, tayi shuru bata bashi amsaba." "Kikace na kasheshi bakyason shi kenan? Nan ma tayi shuru ba amsa." "Dariya ya kuma saki yace "ina ganin dai dijama ta zama kurma, da har yaya mahmud yake. Tambayarta tayi masa shuru kamar batajinsa." Ta kalleshi tace "inJinka, matarka ce abin sonka ta b'ata mun rai, idan kuma ta sake maimaita hakan hmm ta yi shuru." D'an karamin bakinta yake kallo Wanda yake bashi sha'awa, Yace "ni kuwa banga abinda tayi maki ba, Illah kawai kishine taga mijinta yana sonki, Ke kuma na san bakya sonshi." Gabanta ne ya fad'i tayi saurin kallonshi "eh hakan ne mana yanzun kin daina son yaya mahmud d'inki, Wanda a lokacin baya bakya iya cin wani Abu batare da kin ajiye munba." Bazakiyi bacci ba har sai nazo kusa dake. Na lallasheki." a lokacin bazaki tab'a barin na janye a kusa dake ba kullum muna tare, duk wani Abu da kikeso nasani amma banda yanzun da kika daina sona kika manta dani kike yimun wani kallo na daban Wanda ada bansanki da shiba." Gashi yanzun har zakiyi aure Yaya Mahmud d'inki bai san Wanda zaki auraba sai daga baya, Bayan ank'are shirya komai har antsaida ranar bikinku." Ya zakiyi da shakuwar yaya mahmud dake cikin ranki?" Mahmud ya zaiyi da shak'uwar k'anwarsa Idan wani ya d'auke masa ita."?" Dijama kinban mamaki da har kike iya b'oyemu abinda ke cikin ranki." Wani abu yaji yana masa zafi a ransa, cikin minti biyu idonsa yayi ja, da Sauri ya tashi daga kusa da ita, ya koma kan gado ya zauna tare da dafe kai." Idonta ya cika da hawaye tayi saurin mik'ewa tsaye taje kusa dashi, Ta durk'usa tare da rik'o k'afafunsa hawaye na zuba a idonta. "Yaya kayi hak'uri, ba daina sonka nayiba asalima sonka ya kuma lunkuwa a raina sama da Nada, Kayarda dani, ka yarda da abinda zan fad'a maka bansan sulaiman yana sona ba, Sai da naji a bakin Abba bayan yariga da ya amshi maganarsa Amma ni ba wai ina son sulaiman bane har cikin raina, A'a kwakwata babu d'igon sonshi a rayuwata zanyiwa Abba biyayya ne na aure shi domin farin cikinsa koda hakan zai zamo rugujewar nawa farin cikin." Zaiyi magana kenan yaji kiran wayar Abba yana shigowa wayarsa." D'auka yayi tare da sallama, Ya gaida Abba Cikin girmmawa da biyayya." Abba ya amsa mashi yana murmushi da sakin fuska snn yace "gobe idan Allah ya kaimu su fateema sudawo gida, Domin shirye shiryen bikinsu kasan lokaci yana tafiya gashi har ankawo kayan lefen dijama saura na fateema, Sulaiman yayi k'ok'ari sosai KA kirashi a waya Kayi masa godiya." Runtse idonsa yayi yanajin saukar magagganun Abba kamar yana Daka masa mashi a xuciya." Cikin wata kasallaliyar murya ya amsawa Abba da "to." Yayi saurin kashe wayar tunkafin Abban ya kashe." Dijama dake gurfane a k'asa tanajin duk abinda Abba yake fad'i, Wani kuka tasaki mai sauti, Mahmud Kuma ya runtse idonsa saboda wani zugi da yake jin zuciyarsa nayi masa, Hannu ya sa ya d'ago ta ya mik'ar da ita tsaye ya zaunan da ita kan gado a kusa da shi tare da janyota a kan jikinsa, ya shiga bubbugan bayanta alamar tayi shuru, tare da sanya hannu yana share mata hawayen dake zuba akan fuskarta." Dijama ta lafe kan jikinsa kamshin turarensa tashiga shak'a mai dad'in gaske, Cikin minti d'aya ta name kukan ta rasa. Sai sauke ajiyar zuciya takeyi, Cikin dakakkiyar murya, Wanda shima a yanda yakejinsa dama kukan yayi ko zai rage rad'ad'in zafin da yake damunsa a ransa, Cikin muryar lallashi yake cemata "yi shuru daina kuka bana so Ganin zubar hawayenki, Baxaki Aure sulaiman ba tunda bakyason shi, Kin yarda da zab'ina." Gabanta ya fad'i ta d'aga kai alamar 'eh." Zan zab'amaki Mijin da zaiyi dai dai da rayuwarki Wanda zai kula dake ya Kuma tarairaiyeki ba kamar sulaiman ba." Zan zab'a maki miji Wanda zakuyi rayuwar aurenku a nan kusa dani, inda akoda yaushe INA taredake." Idan kika koma gida kifad'awa Abba cewa ke bakyason sulaima." Ta d'aga kai alamar "to." Anan dai suka dinga yiwa junansu musayar kala mai Wad'an da SU Kansu basu San abunda suke furtawa ba, Saboda sunshiga Cikin wani yanayi na tashin hankali mai wuyar misaltuwa." ************** Yusra tana Cikin d'akinta kwance tana kuka tarasa abinda zatayiwa mahmud ya sota." Ta rasa ta hanyar da Zata b'ullo masa ya amshi soyayyarta ta tabbatar masa tana sonshi." Amma a kullum burinsa a rayuwa ya ci mata mutumci ya tuzartata a gaban bainar jama'a." Tana nan kwace tana kuka ta na jin son Mahmud yana Kuma dawo mata sabo a ranta." Alhaji yasir yakirata a waya "yake. Shaida mata an jima su had'u a gidan mata." Misalin k'arfe 7 na dare ta shirya kamar yanda ta saba yin shigarta kamar ba 'yar musulmai ba, tafito duk a tunanin ta mahmud baya nan ya tafi massallaci kamar yanda ya saba, Mahmud kuma yau zuciyarsa a da gule take bayan ya kammala sallar magariba a masallaci, Kai tsaye gida ya dawo da sunan idan aka kira isha'i sai ya koma massalacin." Yana Zaune a falo yaga fitowar Yusra cikin shigarda tasaba Wanda ga duk Wanda ya Santa ba wani abin mamaki bane garesa." Tanufi hanyar FIta batare da ta lura da yana cikin falon ba." Kallo ya bita dashi mai cike da kyamata da jin haushi, ya shiga maganar zuci Wnn ce matarsa Wanda tagama tallar jikinta a titi kowa ya gama gani." Allah ya kyauta." Ya shiga tunanin to ko ina zataje a Wnn lokacin, wata k'ila gidan su ta nufa ta fad'awa ubanta halinda take ciki, Allah yasa yakirani a waya yace nakawo mata takardar sakinta da Kuwa nafi Kowa Murna da jin dad'i." Mamaki ya cika shi da yaga bata d'auki Mota ba." Ya mik'e tsaye tare da mere Baki yace ita tasani ko a kai zatayi tafiya." [8/17, 20:18] Washa: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _Yar gidan tsohuwa_)😅 Written by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basher_) *59* A dai dai ta sahu tashiga ya kaita gidan matan." A dai dai lokacin da Alhaji Atika ya d'aga da budurwarsa suka shige d'aki." Alhaji yasir yana ganinta ya saki dariya kamar gonar auduga, yaje da sauri ya rungomota tare da kissing dinta ta ko ina." Sai da ya gaji snn ya saketa yace "babynah barka da zuwa sarauniyar mata." Yanzun nan babban aminina yayi ta jiran ki k'araso Ku gaisa." Murmushi tayi tace "Allah sarki sai kuma wani lokacin." Ya kuma bud'e baki yana dariya tare da d'aga gira yace "baby na yau kinfi jiya kyau." Iska ta hura masa a ido tace "sirrin yana wurinka." Bata ankaraba yana dariya ya d'auketa ya nufi d'akinsu da ita Inda ya kama." A wann daren hakan sukayi ta aikata masha'arsu Wanda gaba d'aya Yusra ta manta da damuwar dake da munta.' Alhaji yasir sai raba mata aiki yakeyi cikin kwarewa sai kuwar dad'i takeyi." ***************** Bayan kwana biyu da rabuwar Ashanty da Khalil, kullum Khalil cikin kiran wayarta yakeyi sai yajita a kashe, Tun abin yana damunsa har ya kai ya zubar da maganar da cewarsa wata k'ila ta mutu wurin zubar da cikin." Murmushi yayi ya kuma gyara kwanciyarsa yace "ai gara ki mutu Ashanty da ki tuna mun asiri a idon duniya." Ya rufe idonsa yana murmushi har bacci ya d'auke shi." ****************** Mahmud da dijama da kyar suka ga safiya ta waye masu ko wanne da abinda yake tunani a ransa." hakan suka shiga shirya kayansu domin komawa gida." Fateema ce ke shirya kayan Wanda dijama take kwance rufda ciki sai sharar hawaye takeyi, Murmushi fateema tayi ta kalli dijama tace "wlh sis babu abinda yake damunku dake da yaya mahmud sai soyayyar junanku Wanda baku yarda da hakan ba." Da zaku cire zurfin ciki Ku tunkari Abba da Wnn maganar da ya fi kowa farin ciki." Dijama dake kwance tana jin duk abunda fateema ke fad'i, Wanda ita ta dad'e da Sanin Ta fad'a tarkon son yaya mahmud." Bata tanka mata ba illah taci gaba da sharar hawayenta." Mahmud shima kwance a kan gadonsa ya rasa abinda yake masa dad'I a duniya, Sai tunani yakeyi yana magana da zuciyarsa kadai a ce son dijama yakeyi?" Wata zuciyar tace "ai dama kana sonta tunda 'yar uwarkace, wacce kafi so duk a cikin k'ananka." A nan kwance fateema ta fito da kayansu a falo ta kwakwasa masa k'ofa' ya tashi jiki ba kwari ya bud'e.' Fateema ta d'an runsuna ta gaida shi snn tace "yaya mun kammala shiryawa." "Ina dijamar take?" Ya tambayeta." Tana ciki tana ta faman kuka na rasa abinda ke damunta." Rab'a fateema yayi ya nufi wurin dijama kai tsaye ya tura k'ofa ya shiga d'akin." Ya tarar da ita kwance tsakiyar gado tana sanye da doguwar rigar abaya bak'a Wanda tayi matuk'ar yi mata kyau." K'amshin turarensa ya daka mata hanci ya tabbatar mata da shine ya shigo." A hankali ta mik'e zaune tana sharar hawaye a idonta." Hannunsa ya mik'a mata alamar tazo gareshi, Jiki ba kwari ta nufeshi ta sauka daga kan gadon." Mik'ewa tsaye tayi tanufeshi kanta a sunkuye, Wani tausayinta yakeji a ransa tare da wani kalar Abu da yakeji yana fisgarsa a ransa." _Hmmmm. So ne mahmud Wanda baka yarda dashiba_ Nufarta yayi ya janyota zuwa jikinsa, ya d'an d'aga kanta sama yana kallon fuskarta yanda hawaye ke kwarara, D'an k'aramin bakinta kuma yana motsi alamar magana take so tayi kuka ya hanata." Aljihunsa ya duba yaga baya da hankacif a ciki, bare ya goge hawayen." Harshensa ya sanya ya shiga lashe mata hawayen da ke zuba a kan fuskarta Bai ankaraba ya tsinci harshinsa cikin bakinta karo na farko da mahmud ya taba shiga cikin wnn yanayin." Dijama kuma ta runtse idonta hawayen da ke zuba a idonta suka tsaya cak." Sai da suka d'auki kusan minti goma a hakan snn Dijama ta ankara da yanayin da suke ciki tayi saurin janye jikinsa daga gareshi." Wani irin nauyi da kunya suka ziyarcesa yayi saurin juya bayansa yanufi hanyar fita yace "kifito kutafi Wanda zai kaiku ya dad'e da zuwa." Ya bud'e k'ofa ya fita." Shafa bakinta tayi tasaki murmushi snn ta mik'e jiki ba kwari, ta fita." Gaba d'ayansu suna wurin mota ita kad'ai ake jira tafito." Cikin tafiyarta mai cike da yanga da k'asaita ta fito Ido mahmud ya zuba mata yana kallonta har ta k'araso wurin, Wanda tuni FATEEMa. Ta bud'e Mota Tayi shigewarta." k'ara sowarta wurin mahmud yayi dai dai da shigowar Yusra gidan a can ta kwana duk a tunanin ta, Mahmud ya tafi wurin aiki." Ganinshi da tayi sai da gabanta ya fad'i, Mahmud kuma yi yayi kamar bai gantaba ya bud'ewa dijama marfin mota tashiga cike da kulawa tana kallonsa yana kallonta, suna d'awa junansu hannu direba yaja suka tafi tare da yi mata Alk'awarin zaizo k'arshen watan nan komai zai kai k'arshe." D'akinta Yusra ta. Nufa hankalita a tashe duk a tunaninta mahmud zai biyota da masifa ya tambayeta gidan wa taje harta kwana." Sai safa da marwa takeyi a Cikin d'akin gaba d'aya cikinta a k'ulle yake." Amma abin mamaki sai jin k'arar fitar mahmud tayi, da sauri ta fito ta d'an lek'a kanta ta hangoshi sanye da uniform d'insa zai shiga mota da alamar wurin aiki zaitafi." Wata ajiyar zuciya ta sauke takoma falo ta zauna yau gida nata bakowa a cikinsa." [8/17, 20:18] Washa: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _Yar gidan tsohuwa_)😅 Written by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basher_) *60* Lefe ne Wanda ya amsa sunansa lefe mommy da Abba suka had'owa dijama da sunan sulaiman ya kawo mata." Babu abinda babu a cikinsa, Kaya ne masu tsada tareda gwala gwalai da zinari duk Wanda yaga lefen yasan kud'i sunyi kuka a wurin." Tsohuwa da tazo domin ganin lefen kallon kayan takeyi taga sunk'i su k'are saboda yawansu rik'e baki tayi 🤔 tace "Wnn ai b'arnar kud'i ne, kayan lefe shago d'aya wad'an nan kaya ai saitayi haihuwa goma bata d'unke wasu daga cikiba." Mommy tayi dariya tace "Inna ai yanzun zamani ya canza wad'an nan kayan ba komai bane idan kikaga wand'ansu kayan." "To Allah ya kyauta Ta kalli Abba tace "Hassan wai har yanxun mamuda bai baiyana yana son dijama d'in ba?" Abba yayi murmushi yace "kinsan halin d'an gidan naki, Akwaishi da zurfin ciki. Amma ko ya fad'a ko karya fad'a lokacin da muka sanya na biki bazamu janyeba, kuma bazai san dijama matarsa bace sai ranar d'aurin Aurensu a lokacin idan yajiyewa kunnensa an d'aura da shi" Allah Inna na kasa samun suk'uni a duk lokacin da na tuna da Alk'awarin da na d'aukarwa d'an uwana akan auren dijama da Mahmud." Tsohuwa ta girgiza kai tace "haka ne, hakan da kayi shine dai dai, Domin Kuwa idan kafito kanunawa duniya cewa dijama matar mahmud ce zaka haddasa k'iyayya a tsakanin 'ya'yanka musamman idan kayi diba da yanayin Khalil akan dijama, ina lura dashi naga alamar sonta yakeyi, dan ma baya samun goyon baya a wurinmu, Da anfito fili annuna masa dijama matar mahmud ce da ba'asan irin k'iyayyar da zai d'orawa d'an uwansa ba, Irin hakan ne kakejin labarin wa ya kashe k'anensa, Ko k'ane ya kashe wansa, Duk akan abinda suke so." Amma da ace mahmud ya fito ya nuna soyayyarsa gareta a fili da abin xaizo da sauk'i." Mommy tace duk da hakan a yanda nake ganin Khalil sai an zaunar dashi anyi masa bayani yanda zai fahimta, Domin Khalil yana da xafi sosai akan abinda ya keso." Tsohuwa tace "Allah ya kyauta, Insha Allahu abin zaizo da sauk'i." Idan kuma akaga abin zaizo da wani matsala da tashin hankali sai a aurawa Khalil d'in ita, ai da Khalil da mahmud duk d'aya ne. Wata k'ila mahmud d'in kulawar da yake mata da nuna soyayyarsa gareta Duk na 'yan uwantaka ne da zumunci, Ba wai yana sonta ba ne domin ya aureta." Tsohuwa tace "ranar auren tana nan yanda aka sanya ta?" Abba yace "insha Allahu baxamu janyeba, saura sati shidda kenan. Duk Wanda ke da rabo a wnn lokacin tsakanin mahmud da shi Khalil d'in za'a d'aura dashi, ni dai burina d'aya ne na sauke nauyin dake saman kaina na d'an uwana." Sallamarsu dijama ta katse masu hirar da sukeyi, Dijama na ganin tarin kayan lefe a gaban tsohuwa tana kallo, gabanta ya fad'i jikinta yayi sanyi ta dake, Suka shigo da sallama gaba d'ayansu." Fateema tana murmushi ta nufi wurin kayan lefen domin sunyi matuk'ar bata sha'awa ta shiga dubawa tana murmushi, Dijama kuma ta durk'usa ta gaida Abba da mommy da tsohuwa, Suka amsa mata suna murmushi da sakin fuska tare da tambayarsu ya hanya." Tsohuwa tace " dijama kin manta dani idan ba zuwa nayi garin nan ba baxakije ki diboniba, tunda kika bar k'auye kwatakwata zuwanki biyu." Shi kuma mamuda ba'a maganarsa dama kece kike kaishi garin, tunda kuma kika dawo kusa dashi ban kuma k'ara ganin k'eyarsaba bare yanzun da yayi mana nisa." Murmushi tayi tace "yi hak'uri tsohuwa kinsan banda kamarki, makaranta ce kawai take hanani zuwa amma yanzun idan zaki koma k'afata k'afarki a tare zamu tafi" Tsohuwa tayi murmushi ta gutsara goronta tace "Buba yace a gaidaki tare da k'awayenki suwaiba da lantana." Dariya tayi tace Allah sarki Lantana da suwaiba 'ya'yansu nawa yanzun wai?" Tsohuwa tace "uku uku ke garesu, Buba kuma d'an sa biyu matarsa uku yace "yana nan yana jiranki har lokacin da kika kammala makaranta kika dawo snn zaicike ta hud'u dake." Fateema tasaki dariya tace "mutuwa kenan dijama a k'auye." Dijama tace "to meye Dan nayi aure a k'auye a kusa da tsohuwa a can fa naso nayi wayo a can Sam ni bazan tab'a raina k'auyeba." Khalil ya shigo yaci karo da kayan lefe ajiye, Zaro ido yayi yace wad'an nan kayan fa na waye?" Tsohuwa tayi karaf tace "ba'a sani ba tunda babu Wanda ka ajiye a nan da zaka shi go mana d'aki babu ko sammala bare gaisuwa, Dafe kai yayi Dan ya manta kwatakwata baiyi sallama ba, Yace "Allah ya Baki hak'uri tsohuwa Ashe kinxo?" Bansani ba tace had'ida wurga masa harara, Sai da ya koma ya Kuma shigowa da sallama snn aka amsa mashi tare da gaida su, Snn ya samu wuri ya zauna idonsa na kan dijama yana kallonta." Fateema ya kalla yace "FATEEMA wad'an nan kayan waye ko ishaq ne ya kawo maki?" Tace A'a yaya Khalil kayan auren dijama ne sulaiman ya kawo mata, Anan take ya canza fuska ya mik'e tsaye yace "da gaske yakeyi kenan." Ya fita a fusace." Dukansu suka bishi da kallo snn mommy da Abba da tsohuwa suka had'a ido suka kalli junansu." Dijama kuma ta mik'e tsam jiki ba kwari ta nufi d'akinsu, Kai tsaye kan fado ta fad'a ta saki wani kalar kuka." Tana Cikin kukan ne Mahmud ya kira wayarta, domain yaji su sauka lafiya?" Ta d'auki wayar tana shishshikar kuka hankalinsa a ta she ya shiga tambayata abunda yake faruwa." "Tabbas yaya da gaske ne sulaiman ya kawo kayan lefensa, Na gansu da idona gasu can a falo." "Kukanta yakeji har cikin ransa yayi saurin runtse idonsa yace "ki daina kuka na fad'a maki baxaki auri sulaiman ba, Idan Abba ya keb'e shi d'aya kije ki fad'a masa bakyason sulaiman, idan kika fad'a masa daga k'arshe idan nazo garin nasan matakin da zan d'auka." Anan ya shiga kwantar mata da hankali da kalamai masu dad'i har tayi shuru ta fara dariya ta manta da damuwar da take cikinta." ******************* Kwanakin biki sai k'arasowa yakeyi dijama ta kasa tunkarar Abba da magabar bata son sulaiman, Kullum cikin far gaba take bata cin abinci, Duk ta rame kamar ba itaba." Sai ta fito da niyar ta tunkari Abba da maganar saitaji nauyi da kunya Abba yayi Mata Duk kan komai a rayuwa bazata tab'a juya masa baya ba." Babban tashin hankalita d'aya ne duk lokacin da takira wayar Mahmud a kashe take jinta, Wanda hakan ya kuma Sanya ta shiga cikin tashin hankali har ta kwanta ciwo." *************** Mahmud shima hakan takasan ce a garesa, Baya Cikin kwanciyar hankali kullum tunaninsa yana wurin dijama, gashi yanzun baya da lokacin kansa aiki bincike sukeyi a gidan mata." Shine babban a wurin domin ogansu ya lura da mahmud aiki yake a kan gaskia dan haka ya mayar da ragamar binciken gaba d'aya a hannunsa, kullum da zarar anyi sallar a suba yake fita baya dawowa sai 2am, kwata kwata ya manta a Inda ya ajiye wayarsa, Wnn ne ya bawa Yusra da mar hurd'arta da Alhaji Yasir a yanda take so ba wani tsoro a tare da ita." Yau dai sauran sati biyu auren su dijama, Wanda Kowa a gidan ya cika da mamakin rashin zuwan mahmud Kuma da zarar aka kira wayarsa a kashe." Wanda a Ranar jikin dijama ya tsanta sai numfashi take saukewa sama sama tareda dafe zuciya kamar wacce ranta zai fita." Mommy ta shigo d'akin domin ta Kuma duba jikin nata ta sameta a cikin Wnn halin da sauri ta juya ta kira Abba cikin Minti talatin aka nufi asibity da ita, Cikin gaggawa likitoci suka amsheta emergency aka nufa da ita suka shiga bata taimakon gaggawa." Wanda Khalil yana ganin hakan yafito ransa a b'aci ya shiga motarsa ya nufi gidan sulaiman, Horn ya dingayi a k'ofar gidan baji ba gani, Sulaiman dake Zaune a falo tareda yaransa suna cin abinci, Cikin sauri ya mik'e tsaye tare da yiwa fareeda hannu alamar ta jira ya yadawo domin daga jin wnn horn d'in shi ake nema a waje." Da saurin sa ya fito daga gidan yana mamakin wake nemansa haka?" Khalil ya hanga a Cikin mota zaune." Khalil kuma yana ganin fitowar sulaiman yayi saurin fitowa a Mota a fusace, ya tunkare sulaiman gadan gadan cikin hushi yana zuwa ya cacume wuyan rigarshi yaci kwalarsa har sai da idanun sulaiman suka fito waje." Yace "na rantse da Allah Duk kasake dijama ta rasa ranta akanka ka rubuta KA ajiye kai ma saina kasheka da hannunna." Domin na fahimci bata sonka kawaicine kawai Abba yayi ya Baka ita Wanda yin hakan yasa aka k'untatawa tawa rayuwa." to barikaji koda ka aureta, Ka kuma rubata ka ajiye sai dai Kowa ya rasa Dan Kuwa nafika buk'atarta nafika Sonta Dan babu Wanda ya isa yayi rayuwar aure da dijama sai ni." Magana ta k'arshe da zan fad'a maka itace tunkafin rayuka su b'aci kaje asibity a gaban bainar jama'a kafa d'awa Kowa cewa kafasa auren dijama idan ba hakan ba ni kad'ai nasan abinda zanyi maka Wanda sai Kayi Dana Sanin sani a rayuwarka." Ya sakeshi da k'arfi Wanda sai da sulaiman yayi baya baya kamar zai fad'i Allah kawai ya tsareshi bai d'inba." Ya bi Khalil da kallo yana murmushi yana mamaki." Khalil kuma yaja mutarshi a fusace ya nufi asibityn." ******************* Yau mahmud zasu kai hari gidan mata bayan sun kammala duk binciken da sukeyi akan gidan." Sunyi shirinsu Cikin kayansu na sojoji ko wannesu d'auke da bindigarsa, Hakan kawai Mahmud yake jin Kansa Duk a hargitse gabansa fad'uwa, dijama kawai ke fad'o masa a rai." Sai da suka bari misalin k'arfe biyu 2:30 na dare, lokacin da suka tabbatar da Duk wani d'an isaka Wanda ke zuwa wurin ya hallara." Yau kuma Alhaji ATIKu yayi Sabon kamun wata baby kyakkyawa Wanda Alhaji Yasir ya had'ewa miyau ya dinga rik'on Alhaji Atiku akan ya d'an sammashi ya d'ana." Alhaji Atiku yace "Sam ba zai bashi ya d'ana ba, Sai dai shima idan ya Amince ya sammashi ta shi baby Wanda ya dad'e yana had'iye miyau shima ya d'ana." Alhaji yasir yace "Eh ya yarda ya Amince, suka shirya yanda zasu b'atarwa da 'yan matan tunani, Bayan Alhaji yasir ya kammala sarrafa Yusra misalin k'arfe 1:30am ya d'agata ya d'auki rigarsa yasaka Yace tajira shi yadawo kada ta Sanya kayanta zaici gaba ne idan yadawo ya kashe wutar d'akin duhu ya gauraye ko ina yanda ko tafin hannunka baka gani." hakan shima Alhaji Atiku abunda ya cewa babynsa kenan." Suka fito a tare" kasan cewar d'akin da suka kama Jere da na juna." hakan sukayi canjan d'aki Wnn ya fad'a d'akin wnn" Kai tsaye Alhaji Atiku ya fad'awa Yusra ya shiga sarrafata Wanda ita kuma Yusra ta d'auka Alhaji Yasir ne, kasan cewar duhun dake da d'akin Wanda shima Alhaji Atiku bai San 'yarsa bace yusra shalelen sa, Basu ankaraba sai k'arar tashin bindiga suka rik'aji yana tashi, Gaba d'akin da alamar ashigo kame gidan." _labarin Wnn page d'an ya faru da gaske_ [8/17, 20:19] Washa: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _Yar gidan tsohuwa_)😅 Written by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basher_) *61* Gaba d'aya sojoji suka zagaye gidan da bindigoginsu, Aka dinga kama matan banza ana jefasu a mota, Mahmud tareda yaransa suke shiga d'aki d'aki suna fito da karuwai ana zubasu a mota.' Alhaji Atiku da gaba d'aya hankalinsa a tashe yake daya fahimci halin da ake ciki jikinsa ya soma rawa domin yasan k'aryarsa ta k'are sunansa zai b'aci a gari." Hakan ya lalubo rigarsa cikin duhu ya saka batare d yasanya wando ba, Sanya rigarsa yayi dai dai da shigowar Mahmud d'akin d k'arfi ya banka k'ofar tare da kunna wutar d'akin." Alhaji Atiku ya gani tare da Yusra akan gado d'aya ko wannen jikinsa sai rawa yakeyi.' Salati mahmud ya saki ya dafe kai yayi saurin fita daya baya baya a d'akin tare da kaiwa zauna ya ajiye bindigarsa gefe d'aya." Yaransa suka zagayeshi suna fad'in oga lafiya?" Alhaji Atiku duk ya shiga cikin tashin hankali ganin da mahmud masa ya kamashi dumu dumu da macce a gado d'aya kwata kwata bai juya ya kalli fuskar yarinyar ba bare yasan ko wacece." Itama yusra haka saboda tashin hankali bata lura d ko waye a kusa da itaba." Sojoji suka shiga d'akin suka fito da Alhaji Atiku da Yusra waje." Adai dai lokacin da aka fito da Alhaji Yasir da budurwarsa." Sai lokacin Yusra taga Alhaji Yasir anfito dashi daga wani d'akin tayi saurin juyawa ta kalli to waye take tare dashi, Wanda shima Alhaji Atiku juyowar da yayi kenan dan ganin fuskar ko wacece." Ido biyu sukayi da juna a zabure yaja da baya yana nunata cikin tashin hankali, a rud'e yace "Yusra kece kika fito a d'akin nan?" Itama cikin tashin hankali tace Daddy kaine?" Wayyo na shiga uku na lalace." Alhaji Atiku ya d'ora hannu a kai ya kai durk'ushe yana fad'in kaico duniya, nayi dana sani." Ya d'aga kai ya kalli Alhaji Yasir yace "Abokina kuma Amina na ya kad'aice da 'yata kwaya d'aya tilo wacce nafi so akan komai, Nima mahaifinta na kad'aice da ita, nayi ma'amala da ita tamkar matata." Gaba d'aya sojojin wurin suka shiga cikin Al'ajabi suna tsine masa Albarka." Mahmud ya rutse idonsa zuciyarsa na k'una kwata kwata baya son ya bud'e ido ya gansu." Kuka Yusra takeyi sosai tana fad'in "kaico rayuwata ni dai banyi sa'ar uba ba Allah KA k'arb'i rayuwata na mutu na bar duniyar idan ba hakan ba ina zankai wnn abin kunyar." Daddy KA cuceni KA cuci rayuwa, baka bani tarbiya ba, ka sangartani KA koyamun duk abinda nake so zan samu a duniya ka koya mun intaka duk wanda nakeso duk ynda naga dama.' Ga irinta nan ga irin tarbiyar da kabani yau na wAyi gari tare da kai a shinfid'a d'aya munyi ma'ala irin ta dabbobi da akuyoyi d'a yabi uwarsa uba yabi 'yarsa kaico rayuwatah." Alhaji Atiku kuka yakeyi kamar k'aramin yaro yana doka kansa a gini sai gani sukayi ya fad'i k'asa jini yana zuba ta hanci da baki da kunne." Da sauri sojoji suka sanya su Yusra a bayan mota tareda 'yan uwanta 'yan iska, Alhaji yasir shima sai kuka yakeyi gashi Zaune a bayan mota da matsayinshi da komai. Yanaji yana gani aka wuce da shi." Alhaki Atiku kuma cikin wata mota aka sanyashi aka nufi asibity dashi." Sai da aka kammala kamen gaba d'aya duk mutanen dake gidan ankamasu antafi dasu snn mahmud ya tashi daga Inda yake yana Jan k'afa yashiga mota suka tafi." Magana yaransa suke masa amma ina yana cikin tashin hankali mahmud ya zamar masu kurma." Ana shiga asibity da Alhaji Atiku wuyansa ya kare harshensa ya fito yashiga fisge fisge snn rai yayi halinsa." Dafe kai Mahmud yayi yana kalmar shahada, Ji yayi gaba d'aya duniyar tayi masa zafi, Alhaji Atiku ya rasu ya amsa kiran ubangiji." Hakan aka d'auki gawarsa aka nufi gidansa da ita, Kai tsaye mahmud yaje office d'insu inda aka rufe su yusra domin a hukuntasu ya fito da ita batare da yayi mata maganaba bare ya kalleta dan ko son ganinta bayayi ya d'auko ta a motarsa ya nufi gidansu da ita." A bakin k'ofar gidansu ya ajiyeta ya d'auko takarda saki uku ya mik'a mata, ya kalleta da rinanun idanunsa da sukayi jajir yace "Yusra dama bantab'a sonki ba ko da da sau d'aya, bantab'a yimaki kallon macce kirkiba Dibo da yanayin rayuwarki da ta mahaifinki. Hakan na daure cikin rashin son da nake maki na zauna dake ashe kina can kina tarrayya da mahifinki kin zama a kuya kowa binki yakeyi mahaifinki ya biki abokinsa ma ya biki da duk wani wanda yake buk'atarki, Yusra na sakeki saki uku ko a hanya bana fatan Allah ya Kuma gad'ani da ko mai kama dake ne." Ta kai durk'ushe a gabansa tana kuka tana magiya "mahmud ina Sonka baxan tab'a daina Sonka ba, Ina rok'on Allah ya kasheni da sonka a rayuwata." Wani kallo ya wurga Mata mai cike da tsana da kyamata yaja motarsa yayi tafiyarsa." A Daren ranar a yanda yaga dare haka yaga safe, Cikin tashin hankali da tunani Dan shi tunda Allah ya halicceshi bai tab'a ganin Wnn rayuwarba." Sai da aka kira sallar asuba bayan yaje masalaci ya dawo sai a lokacin ya tuna da wayarsa ya lalubota ya kunnata ai kuwa ya dinga ganin sak'onnin dijama kala kala akan yayi Sauri Yazo za'a aura mata sulaiman." Zai kira wayarta kenan sai ga Kiran mommy ya shigo cikin Sauri ya d'auka ya gaida ita cike da ladabi, mommy ta Shiga yimasa fad'a INA ya Shiga kwana biyu ayita Neman wayarsa a kashe, Hakuri ya Shiga bata tare da nasar da ita aikine ya rik'eshi." Mommy tace 'dijama na nerman yafiyarka don Kuwa a yanzun hakan tana kan gadon asibity Cikin mawuyacin hali rai ko mutuwa." kansa ya juya cikin hanzari da tashin hankali yace "mommy meyasa meta?" yaushe ciwon ya kamata?" Ji kawai yayi mommy ta kashe wayar, Da sauri ya mik'e tsaye ya Shiga shirya kayansa ya fito ya shiga motarsa ya d'auki hanyar kano, Sai dai idan ya tafi ya kira oga ya fad'a masa daga baya." Alhaji Atilu anyi masa wanka anshirya shi Cikin suturarsa akayi masa sallah aka kaishi ma kwancensa na gaskiya." Wanda Yusra babu abinda takeyi sai aikin kuka suma Kuwa tayi shi ba iyaka." Hakan mahaifiyarta tun da taji abinda ya faru bata kuma yin magana ba, illah jawai ta dinga bin kowa d ido tana kallonsa." Tana Ganin anfita da gawar Alhaji Atiku ta rafke jiki ta fad'I a nan take ciwon sashe ya kamata." Yusra ta kuma fashewa da kuka ta Kuma shiga Cikin wani tashin hankali Wanda ta gwamma ce mutuwarta da rayuwarta." **************** Khalil sai safa da marwa yakeyi a Cikin asibity, Wanda aka hana Kowa ya shiga cikin d'akin da dijama take saka makon dibata da akeyi." A can ya hango sulaiman ya shigo da motarsa a harabar asibityn, wani jin haushinsa da takaicinsa suka Kuma taso masa domin ganin yakeyi Duk rashin lafiyar da dijama takeyi sulaiman ne ya haddasa mata ita." Wurin sulaiman d'in ya nufa kamar wani zaki ya tunkareshi, sulaima dama yana da haushinsa a yanda ya iskoshi har k'ofar gidansa yayi mashi rashin kunya, Yana zuwa daf dashi yashiga hararar sa, sulaima, kuma Alurar soja ta motsa, ya juya cikin b'acin rai ya kalli Abba da mommy da tsohuwa, Ya damk'i hannun Khalil cikin hushi ya janye shi daga Inda su mommy zasu iya ganinsu, yana rik'e da hannun,sa Khalil sai k'ok'ari yakeyi ya kwace hannunsa amma ina ya kasa, Sai da ya kaishi Inda ba mutane sosai Sulaiman ya kaishi jikin bango ya Sanya k'afarsa d'aya ya take masa k'asa, Still hannunsa yana rik'e da hannunshi ya murd'e shi sosai babu abinda ya ke fita a jikin Khalil sai gumi gashi ya kasa kwace kansa, Sulaima yace " meyasa kake so ka kaini bango ne Khalil?" Na lura da rashin kunyar ka gare ni, ina d'aga maka k'afa ne saboda halaccin Abba da mommy da kuma abokina mahmud kana so kasanya ni nayi butulci garesu." Zanyi maka gargad'i na k'arshe ko hanyar da nabi idan KA kuskura kabi ta wurin Saina Karya maka kafa daya." Khalil ya zaro ido waje zufa sai wanke mata fuska takeyi." Snn kuma bazaka tab'a Auren dijama ba, Domin bata dace da da kaiba ba." Snn idan ka kuma Shiga gonata Saina d'auke maka kai da bindiga kowa ya huta da halinka." sann ya d'aga masa k'afa tare da sakar masa hannu yayi tafiyarsa." ****************** Misalin k'arfe goma mahmud ya isa garin kano. Kai tsaye asibity ya nufa hankalinsa a tashe [8/17, 20:19] Washa: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _Yar gidan tsohuwa_)😅 Written by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basher_) *62* Da sauri yayi parking cikin Hanzari ya bud'e motarsa ya fito, Abba ya hango a bakin k'ofar d'akin wnn ya tabbatar masa a nan d'akin aka kwantar da dijama." Wurin Abba ya nufa ya gaida shi ya kallesa cike da mamaki, yana tambayarsa ya hanya?" Lafiya k'alau yace "hankalinshi ba a kwance ba yana k'ok'arin shiga cikin d'akin." Tura k'ofa Yayi ya shiga da sallama gaba d'aya d'akin cike yake da mutane mommy tsohuwa Khalil sulaiman fateema sai kuma Abba da ya biyo bayansa." Idonsa a rufe suke, Babu abinda yake kallo sai gadon dijama da ya ganta kwance kamar wacce ta mutu, Duk ta rame ta fita hanyacinta ruwa kawai ake k'ara mata, Ya gaida su mommy da tsohuwa cikin tashin hankali ya nufi gadon dijama, A gefen gadon ya zauna ya zuba mata ido cike da tausayi da kuma so da k'auna, "Mommy meyake damun tane?" Mommy tace 'wayasa ni, dijama gata nan dai kullum Cikin tashin hankali take da tinani, daren Jiya suman ta biyu duk a tunaninmu rai yayi halinsa." "Da sauri ya juya ya kuma kallon dijamar saka makon wani juya ido da takeyi Alamar wani suman ne ta kumayi." Gaba d'aya d'akin suka mik'e tsaye sukayo kanta, Abba ya fita da sauri ya tafi kiran likita." Mahmud ya cire robar ruwan da ake k'ara mata ya janyo ta gaba d'aya a jikinsa akan k'afarsa ya kwantar da ita, Yana "fad'in Khalil mik'omun ruwan robar can, Cikin tashin hankali Wanda baya misallatuwa Mahmud ya shiga girgiza dijama yana 'fad'in Kitashi Dijama kadda ki mutu kibar yaya mahmud d'in, ki tashi dijama mahmud yana sonki, Bakinsa ya sanya a cikin bakinta ya shiga hura mata iska da k'arfi, Anan take tayi saurin sauke ajiyar zuciya, Yana ganin hakan ya kuma rungumeta ajikinsa yana fad'in "bud'e idonki ki kalli yaya mahmud d'inki nine a gabanki." Dijama ina sonki, yaya mahmud yana sonki pls kadda ki mutu kibarni." Hakan yayi dai dai da shigowar Abba da likita Mahmud ya kalli Abba yace "Abba ina son dijama KA aura mun dijama, Na dad'e da soyayyar dijama a raina, Dan Allah Abba kada Ku aurawa sulaiman dijama saboda bata son shi ni take so Nima ita nake so Abba kada Kuyi watsi da soyayyar da tun k'uriciya mukeyiwa junanmu ita, Wanda Allah ne kad'ai ya had'ata kuma ya san manufar yin hakan." Turus Abba yaja ya tsaya mommy tacika da farin ciki hakan tsohuwa sulaiman hakan da sai murmushi yakeyi, Khalil kuma sai zufa yake fitarwa akan tashin hankali da gid'e mewa." Dijama suka gani ta bud'e idonta fuskarta d'auke da murmushi ta kuma k'ank'ame Mahmud ta rik'eshi gam alamar kada yatafi ya barta." Mahmud shima ya kuma rungumeta kamar zai maida ita a ciki." Mamaki suka shigayi suka kalli junansu ko wannen da murmushi a fuskarsa." Sulaiman ya matso ya matso kusa dashi ya dafa kafad'arsa yace "Abokina kwantar da halinka a duniya babu abinda bazan iya sadaukar maka dashi ba, Dama abinda muka dad'e muna jira kenan, na bar maka dijama dijama ta zama taka Allah ya Baku zaman lafiya da zuri'a d'ayyaba." Hawaye suka shiga wankewa Khalil fuska wad'anda bai San lokacin da suke fitowaba, Shi dai yasan yana son dijama so mai tsanani amma ya zamar masa dole ya hak'ura ya sadaukarwa da d'an uwansa ita, yana son Mahmud sosai kuma tun tashinsa yaga Mahmud da dijama a tare, A tare ya sansu a tare yake ganinsu duk hotunan da yake gani lik'e a falo mahmud ne da dijama." yayi saurin share hawayen fuskarsa Dan kada Wani ya lura dasu, Mommy tana lura dashi Karo na farko dataji Khalil ya bata tausayi." Ta girgiza kai tayi kamar bata gan shiba." Ya tako yazo wurin mahmud ya Dafa kafard'arsa yace "Tabbas d'an uwana Kaine KA dace da dijama, Domin Kuwa kafi Kowa Sanin abinda take so da Wanda bata so, Dijama tana sonka kaima kana Sonta sai dai muyi maka Addu'a Allah ya baku zaman lafiya a rayuwar aurenku." Gaba d'aya d'akin Kowa yayi shuru zuxiyar Kowa cike da farin ciki, Sai a lokacin tsohuwa tasamu damar bud'e baki tace "idan kowa ya Amince da aurenka da dijama ni ban Amince ba saboda anriga da ankarb'i kayan auren sulaiman." Dijama tayi saurin d'agowa daga kwance da take a kan k'afar mahmud ta kalli tsohuwa" Tsohuwa tace kalleni da kyau marar kunya, Dama ciwon da kikeyi na mahmud ne kwananki biyu baki San Inda kanki yake ba har suma kikeyi kina tashi, Amma yan zun dibeki zuwan Mahmud gaki nan kin tashi har kina iya d'aga ido ki kalleni." Muna funcin banza muna funin wofi, Wazaku nunawa zurfin ciki to kubari kuji saina ga Wanda zai d'aura maku Aure, Sai dai ko wannenku ya had'iye zuciya ya mutu akan soyayya amma baxaku Aure junaba Dan kuwa dijama ta sulaiman ce." Dariya tsohuwa ta basu gaba d'aya d'akin aka sanya dariya, Tsohuwa tace "oh ga mahaukaciya INA magana kuna yimun dariya." Mahmud ya gyarawa dijama kwanciya ya kalli tsohuwa yace "ke dai nasan matsalarki d'aya ce goronki ne ya k'are, kibari idan natafi sayo goron d'aurin aure na zanbiyo maki da naki" Anan Aka Shiga wata sabuwar hira, Abba yace "baxai janye ranar d'aurin aure ba domin Ya riga da yasanya sanarwa, Kuma ya fad'awa mutane, har Iv ya fara rabawa, Dama Alk'awari ya d'auka koda dijama tana saman gadon asibity sai and'aura aurenta illah so idan mutuwar ce ta mutu da igiyar aurenta a kanta." Gaban mahmud ya fad'i jin Abba yace har anbugo invention, Abba yaciro invention a Aljihunsa mai kyau ya mik'awa mahmud kamar yasan abinda mahmud yake fad'i a ransa." Jiki na rawa mahmud ya karb'a ya shiga dubawa abin mamaki sunansa ya gani tareda na dijama ajikin Iv." Murmushin farin ciki ya shigayi yana mamakin ya akayi hakn ta faru?" Dama Abba ya San yana son dijama ne?" Ya karawa dijama Iv ta gani itama murmushin takeyi tana kallonsa cike da farin ciki." Abba ya lura da alamar tambaya a kan fuskar mahmud ya nemi wuri ya zauna ya shiga bud'e masu b'oyayyi yar wasiyar da mahifin dijama ya bari tun ranar da aka Haifeta." Da dalilin da yasa sulaiman ya fito a matsayin masoyinta, Zaune Khalil ya kai ya shiga nadamar rashin kunyar da yayi tayiwa sulaiman sai ma yaji wata sabuwar kunyarsa yakeji." Bayan Abba ya gama fad'a masu Duk wani abinda basu saniba, Snn daga karshe Abba yace "Allah ya sanyawa rayuwar aurenku Albarka ya Baka.ikon yin Adalci atsakanin matanka." Gaban mahmud ya fad'i, Nan take ya canza fuska idonsa yayi ja da ya tuna da Alhaji Atiku da yusra, Mamaki aka shigayi ganin Cikin Minti d'aya idonsa yayi ja ya canza fuska.' Ya shiga fad'awa Abba duk abinda ya faru, har zuwa mutuwar Alhaji Atiku, Salati Kowa yashigayi." Abba yace "nayi Dana Sanin amincewa Alhaji Atiku akan aurenka da 'ayarsa." Sai daga baya nagane d'ana baiyi sa'ar matar aure ba, Mahmud kayafemun domin na San Baka son Yusra biyayya CE kayi mun ka aureta, Kuma kayafewa Alhaji Atiku duk wani abu da yayi maka." Sulaiman yace " k'arshen azzalumi da mazinaci baya kyau, Allah ya yafe masa mudai mun yafe masa." Anan aka shiga hirar biki, da abubuwan da za'ayi, Mahmud yace 'walima kawai zaiyi ya godewa Allah." A wnn yinin dai dijama sauki yasamu dan harda abinci take Wanda mahmud yake bata da kansa cike da so da k'auna." Sai tarairayarta yakeyi yana lallab'ata ita kuma sai k'ara shagwab'a takeyi, Mommy na ganin haka ta tattara kayanta ta tafi gida aka bar tsohuwa, Babu abinda tsohuwa takeyi idan taga rashin kunyar tayi yawa illah ta mere baki☹ tace "Allah ya kyauta zamani ya lalace. Ai dai dole ka hak'ura har akai maka ita gidan ka" Washe gari aka sallami dijama suka koma gida akaci gaba da hidimar biki, Wanda a yanzun tasaki ranta tana walwalarta duk wani motsi nata a kan idon mahmud Dan ma tsohuwa ta sanya masu ido." Gyarasu kawai mommy takeyi da ita da fateema da kayan mata masu kyau 'yan zamfara." ******************** A shanty ta haihu d'a namiji kamarsu d'aya da Khalil." Abin mamaki mahaifinta bai San da cikiba sai dai yaji kukan jariri yana fitowa a d'akinta, Koda yake lek'awa ya ganta gurfane ta haihu a lokacin ba kowa a gidan [8/17, 20:19] Washa: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _Yar gidan tsohuwa_)😅 Written by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basher_) *63* Mamaki ya shigayi da Al'ajabi ya rik'e baki cikin bak'in ciki yace "Aisha kece kika haifar mun d'an shege a gida?" Lallai kuwa zan kasheki na kuma kashe abinda kika haifa, idan har baki fad'a mun wanda yayi maki wnn cikin ba." Yayi kukan kura ya shiga d'akin da niyar ya mak'areta, inna laure ta shigo gidan tadawo daga gidan bikin mak'ota, jin kuka jaririn da taji ne yana fitowa a d'akin Aisha yasa tayi saurin nufar d'akin da saurinta." Mijinta tagani malam Abu yana k'ok'arin shak'e wuyan Ashanty tare da jaririnta." Cikin sauri ta shigo d'akin ta fitar da malam daga d'akin Yana fad'in na rantse da Allah muddun baki fad'a mun uban shegen d'an nan ba sai na sanya wuk'a na yankaki." Inna d'aure ta Shiga salati tana fad'in yau me zan gani a gidan nan?" Aisha kice kika haihu?" dama ciki ke gareki shiyasa kike k'unshewa a hijabi?" Kuka Ashanty ta fashe dashi tace "inna Laure ki taimakeni ki gyara mana jikinmu. inna laure ta tausaya mata ta shiga gyara mata jikinta tare da jaririnta, Abinda yafi d'aurewa inna laure kai shine duk wasu kayan jarirai Ashanty ta saya masu kyau, da tsada, Wato tasan da tana da cikin kenan,?" To meye ribarta da zata bari ta haifi d'an shege?" Bayan inna Laure ta gyara mata d'anta ta karb'eshi ta kure shi da ido yaro sak mahaifinshi Khalil komai nasu iri d'aya, Tayi murmushi tace "nagode inna laure." Inna Laur ta rafka tagumi tace "amma dai Aisha kinbani mamaki, ina ganinki da natsuwa da kamun kai yanzun kece zakiyi cikin shege Kuma kibarshi har ki haifeshi." Idon Ashanty ya kawo kwalla tace "inna laure kaddarace da sherin shed'an da kuma soyayya ta ribace ni har Khalil yayi nasara akaina." Baba ko baice zai yankani ba idan banfad'i Wanda yayi mun cikin nan ba, Dama nayi Alk'awarin da zarar Allah ya saukeni lafiya zanfad'i Wanda yayi mun shi, na kuma d'auki d'ansa na kai masa." Haka ta dinga kuka tana nadama tare da danasi biyewa sharrin zuciya da kuma shed'an." A daren ranar inna laure ta lallashi mijinta ta kwantar masa da hali tareda Nuna masa kaddara ce zata iya fad'awa akan kowa." Har malm Habu ya sauka, Amma yayi Alk'awarin duk yyi ido biyu da yaron da yayi mata cikin sai yayi masa rashin mutumci dan police station kai zata rabasu." ******************* Shirye shiryen biki akeyi a gidansu dijama inda gobe ne ake d'aurin auren dijama da fateema." Wanda dukansu sunsha lallai da k'unshi sai k'amshi suke zubawa da shek'i." Mahmud yayi gaiyatar abokanansa k'asa k'asa tareda abokanan aikinsa, inda sulaiman sune manyan abokanan ango." Khalil ya saki jikinsa ya cire dijama a ransa, Amma kuma idan sau dubu tabi ta gefensa ta wucea sai ya kalleta sau dubu." mahmud yana so ya kad'aice da matarsa abar sonsa amma tsohuwa tayi masa katanga da ita, Wnn abin yana damunsa a ransa." Yauma hakan ta kasance ya d'auki waya yakirata yace "takawo masa abincinsa, Tsohuwa na kusa tana jinsa, dijama zata mik'ewa tsohuwa tace "dawo ki zauna bari ni na kaimasa da kai na, idan kukayi hakuri dake dashi ai gobe iyanzu kuna can a tare." Dijama ta turo baki ta harare tsohuwa tace "naga alamar tsohuwar nan kina Neman ki Raba hanta da jini." Tsohuwa tace "A'a jini da b'argo zan raba, amma bazakije ba." Ta mik'e ta d'auki abincin mahmud ta nufi d'akinsa ta kai masa." Mahmud da yana kwance akan gadonsa yana jiran shigowar dijama domin yana son ya kalli fuskarta mai cike da Annuri." kwakwasar k'ofa yaji anayi, ya kuma gyara kwanciya yana murmushi yace "shigo kawai keda d'akin mijinki." tsohuwa ya gani d'auke da tiren abinci. Had'e fuska yayi tare da wurgawa tsohuwa harara yace "daga ina hakan kuma tsohuwa?" To waya ma fad'a maki yunwa nakeji ina buk'atar abinci? Ni dai gaskiya tsohuwa kinaso ki fara Shiga hurumin da banaki ba a gidan nan." Ki d'auki abincin kawai ki koma dashi, Tsohuwa ta mere baki tace " baka isaba, au dama ba yunwar kakeji ba? To bazan d'aukeba tunda nariga da nako maka." Duk nasan take takenka marasa kunya, Oh bani kaso ganiba shine bazakaci abincin ba, to kada Allah yasa kaci, ta fito d'akin tana ta faman masifa." Yau ne ranar d'aurin aure Kowa a gidan cike yake da farin ciki. Wanda Abba da mahmud da khalil da sulaiman sukayi ankon shadda fara iri d'aya Wanda Abba ya d'unka musu gaba d'ayansu." Babban riga da hula." Abba ne da mommy suke tsaye a harabar gida suna magana, Sai gani sukayi wani mutum dattijo d'auke da jariri 'yarsa tana biye dashi daga baya ya shigo gidan." Kai daga ganin mutumin kasan a fusace yake, Ya tunkaro Abba Wanda shima Abba shi yake kallo cike da mamaki." Dattijon yace yanuna Abba yace "kai ne Alhaji Hassan?" Abba yace "eh nine Allah yasa dai lafiya?" Malam habu yace "inafa lafiya d'anka yayi wa 'yata ciki gashi har ta haifa maka jika, kuma na rantse bazan yarda ba kotu ce kawai zata rabamu." Abba ya cika da mamaki kansa ya d'aure yace "d'ana kuma?" Ina ganin ko dai b'atan hanya kayi ba'ayi maka kwatancen A dai dai ba," Malam Habu ya juya ya kalli Ashanty yace "ke ba nan gidan bane?" Fad'a masa sunan d'an nasa Wanda yayi maki cikin." Ashanty tace "sunansa Khalil Kuma a nan gidan yake." Abba ya zaro ido waje yace "Khalil kuma tare da juyawa ya kalli mommy da take murmushin da yafi kuka ciwo. Tasan Khalil zai aikata hakan ga Irin abinda take gudu Kenan ya faru." Ta mik'a hannu ta k'arb'I jaririn ta bud'e masa fuska, tana kallonsa, Abba ya d'an lek'a idonsa ya kalli fuskar jaririn gabansa ne ya fad'i dayaga sak fuskar Khalil CE a lokacin da yake jariri." Yace "tabbas wnn jinin Khalil ne Tabbas, wnn d'an Khalil ne " Malam Habu yace Alhamdulillahi tunda kuka fahimci hakan yanzun kotuce kawai zatayi mana shari'a daku." Abba yace "kayi hak'uri kazo mushiga daga ciki muyi magana ta fahimta da kai." Snn malam Habu yabi bayan Abba da mommy suka shiga babban Falon sa Inda yake ajiye bak'i." Bayan sun zazzauna Abba ya d'aga waya yakira khalil yace ya same shi a falonsa Wanda yake sauke bak'i." Cikin hanzari Khalil ya shigo Wanda tsohuwa ta biyoshi tana masa magana yayi banza da ita shine tabiyo bayansa." Da sallama yashiga falon Turus ya yaja ya tsaya sakamakon ganin ashanty da yayi zaune a kusa da mommy da jariri rungume a hannun mommy.gabansa ya shiga fad'uwa." Wasu kalar miyau ya had'eye masu d'aci ya shiga zarar ido anan take Cikin minti biyar babban rigarsa ta jik'e da zufa." Ina k'asa ta bud'e ya shige, da ya huta da Wylnn Abun kunyar Tabbas yau ranar tonan asirin sace, Tunkafin ace ya zauna ya nemi wuri ya zauna tare da sunkuyar da kai k'asa, Shigowarsa da yanayin da ya shiga Abba ya Kuma tabbatar wa kansa ya aikata." Tsohuwa tana ganin hakan itama ta nemi wuri ta zauna." Abba ya kalli Khalil ya Nuna masa Ashanty yace "kasan wnn,?" idan ka kuskura kayimun k'arya sai na sab'a maka." "Khalil da sai zufa yake fitarwa ya taso yayi gurfane a Gaban Abba yace "Abba natuba kayafe mun sharrin shed'an ne ba halina bane." Cikin hushi mommy ta mik'awa Abba. Jaririn ta taso ta d'aukeshi da mari tace "ba magana ake makaba KA tsaya kana magiya da Neman yafiya." Ashe duk hud'ubar da nake maka da nasihar da nake maka akan kaji tsoron Allah karka kusanci zina, ta tashi a banza, Ashe abinda kake aikatawa kenan idan KA fita." Ta juya ranta a b'ace idonta yayi ja ta kalli Abba ido cikin ido abinda bata tab'a yimasa ba, Tace "ga irinta nan ga irin abinda na dad'e INA yiwa gudu Kenan ya faru akan khalil, Na dad'e ina fad'a maka irin rayuwar Khalil da halinsa amma sai ka Sanya k'afa katake wani lokacin har laifina kake gani Gani kakeyi nacika Sanya mashi ido da takura." Duk uwa tagari Wanda ta reni d'anta ta bashi tarbiya tasan halin rayuwar d'anta Alhaji kace Kahlil yaro ne bai San abunda duniya take cikin ba bare har ayi masa aure, To ai ga irinta nan yau an wayi gari ankawo maka d'an shege Wanda Khalil yayi cikinsa a waje gashi a hannun ka a rik'e, yanzun ka ganewa idonka cewa namiji baya kad'an, Kuma ka ganewa idonka yanzun Khalil ba yaro bane tunda har ga d'ansa nan ka rik'a da hannunka." Abba yayi shuru domin sai yanzun ya tabbatar da maganar da mommy takeyi akan Khalil gaskiya ne Wanda shi yake Ganin kamar tacika Sanya mashi ido ne." Tsohuwa ta rik'e baki domin ita tama rasa abin fad'a." Abba yayi kyaran Maurya yace "hak'ik'a nayi kuskure babba da ban tsaya na lura da yanayin rayuwar d'ana Khalil ba." Malam Habu Kayi hak'uri kuskurene ya Riga da yA faru, in har ka shirya Aurar da 'yarka, to a yau za'a d'aura mata aure da khalil." Bana buk'atar komai naka tun daga kayan d'aki harzuwa abinda zata buk'ata anan gaba." A razane Khalil yayi saurin d'aga kai ya kalli Abba, . Malam Habu yayi murmushi cike da Jin dad'i yace "a shirye nake." Abba yayi masa godiya snn ya d'aga jaririn yayi masa hud'uba tare da sanya masa suna Abubakàr Sadeeq." A ranar aka d'aura Auren mahmud da Dijama FATEEMA da ishaq Khalil da Ashanty baby😊 D'aurin aure ne Wanda ya tara dubban mutane k'asa k'asa." [8/17, 20:19] Washa: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _Yar gidan tsohuwa_)😅 Written by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basher_) *64* Biki yayi biki anci ansha an wadata mahmud dijama sai murmushi sukeyi suna dariya sai pix kawai ake d'aukarsu, Hakan itama fateema tare da angonta ishaq sai annashawa sukeyi suna dariya." Wanda Khalil yana d'akinsa a kwance yana tunanin abin kunyar da ya aikata, ko dawani idon zai kuma kallon Abba da mommy, idan har ya san kunya to yajita a yau ?" Wato Ashanty dan ubanta bata zubar da cikinba, sai da ta sanyashi ya tuzarta, gashi yanzun an aura masa ita ko ya zaiyi da ita?" Shi sam Ashanty bata d'aya daga cikin tsarin matan da yakeso ya aura har yyi rayuwar aure dasu, amma ya zamar masa dole ya koya mata hankali Wanda ya lura da bata shi.' ************** Misalin k'arfe 8 na dare aka kai amare gidajansu, Hakan aka kai dijama gidan Mahmud hakan shima, khalil aka kai masa Ashanty, Wanda basa da wani nisa da Mahmud, Gaba d'ayansu gidajensu sunyi kyau iya kyau wnn duk tsarin Abba ne." fateema itama ba wani nisa take dashi ba sosai, Wanda itama gidanta yayi kyau mijinta yyi k'ok'ari wurin tsara gidansa." Mahmud da sai zumud'i yakeyi ya fito cikin dakakkiyar shadarsa sai k'amshi yake zubawa yana yiwa su Abba sai da safe, Da murmushi a fuskarsu suke amsa masa "tsohuwa tace "ai kin banza yanzun ta zurfin ciki ta k'are gaka ga dijama a wuri d'aya, kuma kasani duk ka cutamata kayi mata mugunta Allah yana kallonka.' Mahmud yayi dariya yace "kai kuji wnn tsohuwar dani da matata kike neman kiyi mun Allah isa, kina nufin kinfi ni sonta ne ko yaya?" Abba yace "mahmud wuce kayi tafiyarka tun kafin ranka ya b'aci." Tsohuwa tace " A'a kabarshi kawai ya gama yimun rashin kunya idan ban war ware auren nan yanzun ba menake." Mahmud ya saki wata dariya yace "ai aurena da dijama auren zobene ba saki ba yaji mutuwa ce kawai xata rabamu." Ganin Abba yana hararasa yasa yayi saurin fita yana dariya tare da yimasu sai da safe." Tsohuwa tace "ina shi Khalil d'in ai sai ya fito yaje wurin matarsa da d'ansa illaso daren yau sai su cinye kansu." Ai kuwa bata rufe bakiba ta Ganshi yafito sanye da jallabiya yana tafiya kamar Wanda kwai ya fashewa a ciki, Mommy ta wurga masa harara ta kau da kanta, gefe Abba ne kawai ya d'an sakar masa fuska, Tsohuwa tace "kai kuma naka salon kenan kashigarwa Amaryarka da jallabiya kamar wani limami🤔" To Allah ya kyauta." Mu dai atafi sai da safe, Muna gaida Abubakar Sadeeq, wani k'unci ya Kumaji a ransa, bai tankawa tsohuwa ba domin kansa a k'asa yake gaba d'aya kunyar mahaifansa yakeji." Tsohuwa tace "kana wani sun sunkuyar da kai kamar wani na Allah, Nina San har abinda yafi wnn zaka aikata, Tunda ka tashi idonka a tsaitsaiye yake, Hassan ne baiganeba Halinka ba amma ai yanzun KA kawo masa sheda tare da saka mako Ma kyau." Allah ya shirku gaba d'ayanku ya kuma tsareku da shairin shed'an wuce katafi mun sallameka sai da safe." Khalil yafita jiki ba kwari ya yanufi gidansa, Da shigarsa gidan babu abinda yakeji yana tashi sai kukan jariri Abubakar sadeeq Allah yayi masa fitinar kuka ba dare ba rana." Wani dogon tsaki yaja mai cike da jin haushi da takaici yayi shigewarsa d'akinsa, Hakan dai suka kwana Sadeeq ya hanashi bacci saboda bala'in kukan da yakeyi." ******************* Mahmud yana shiga gidansa k'amshi ne yake tashi tako ina a gidan, Murmushi yasaki ya mufi d'akinda yasan nan ne na dijama, Ya tura k'ofar a hankali ya shiga da sallamarsa cikin taushin Murya." A can tsakiyar gado ya hango dijama a zaune ta rufe fuskarta da mayafi, tana murmushi." Shima murmushin yakeyi ya nufita yaje kan gadon ya zauna ya Sanya hannu ya janye mayafin yace 'yar k'anwata kuma Amaryata kunyar yaya mahmud akeji yau." Murmushi tasaki mai cike da farin cikin tace "yaya mahmud sannu da zuwa." Wanda shima "murmushin yakeyi yana kallon fuskarta gani yayi tayi masa wani fitananen kyau, yace "yawwa Nana khadija ta mahmud." Dariya tayi ta rufe idonta, shima murmushin yake yana kallonta wani irin sonta yana fisgarsa." Ya mik'e daga kan gadon ya cire babban rigarsa yaje kitchin ya d'auko plate ya zuba kazar da yazo da ita tareda fresh milk mai sanyi ya ajiye." Snn yaje kan gadon ya cire mata mayafin jikinta ya ruk'o hannunta ya sauko da ita daga kan gadon suka zauna k'asa a kan kafet ya tura mata plate din gabanta tareda tsiyaya mata lemo a cup yace "bisimillah muci k'anwata." Dijama ta saki murmushi ta Sanya hannu ta shiga ci, tana shan fresh milk d'inta hankalinta a kwance tsakaninta yaya mahmud ba jin kunya da cutar kai." Dama yunwa takeji, sai da taci ta k'oshi snn ta janye hannunta tace "Alhamdulillah." Kallonta mahmud yayi cike da burgewa yace har kink'oshi?" Ta d'aga kai tana murmushi." Snn shima ya cire hannunsa tareda yin hamdala, Ya mik'e yanufi hanyar toilet yace taso mutafi muyi Alwala, Tamik'e tsaye tabi bayansa a tare suka yi Alwala suka fito, Yana gaba tana bayansa suka gabatar da sallah raka biyu Wanda Annabi Muhammad (S A W) ya umurce mu da muyi a darenmu na farko." Bayan sun sallame sallah ya dafa goshinta yayi Addu'a suka tofa gaba d'ayansu. Snn ya mik'e tsaye ya rik'o hannunta ya mik'ar da Ita tsaye suka kusanci junansu suna jin saukar numfashin junansu idonsa cikin idonta suna kallon juna, K'amshin turarensu ya gauraye Dana juna, Wani irin so da k'aunar junansu ya shiga ratsasu, A hankali ya matso da kansa daf da nata, suka had'a goshi wuri d'aya dogon hancinsu ya had'e wuri d'aya ya sanya bakinsa ya tallabo leb'on ta na sama ya shiga tsotsa cikin shauk'in so da k'auna." Runtse idanta tayi jikinta ya soma rawa tsoro ya ziyarceta ganin yanda jikin mahmud ya soma rawa k'afafunsa suna Neman kasa d'aukarsa." A hankali ya dinga tafiya da ita bakinsa cikin bakinta har yakaita kan gado ya kwantar da ita ya haye kanta, Ya cire bakinsa cikin bakinta ya tsura mata ido, yana kallonta ya sanya hannu a fuskarta yana mata wani salon tafiya mai rikitarwa idon dijama a rufe tana k'arb'ar sakonnin mahmud." Snn ya d'an hura mata iska a hanci, Wanda ya sanya tayi saurin bud'e idonta cike da kunya, Murmushi Mahmud yayi yace "dijama ina sonki, Bantab'a son wani Abu sama da yanda nakesonki,ba." Bansan ko meye so ba sai a kanki ina rok'on Allah ya kashe ni da sonki a rayuwata." Ya mirgina gefe ya d'aga kanta tare da mikewa tsaye yace "kishiga toilet kiyi wanka kafin na dawo." Ya bud'e wadruf ya d'auko mata wata rigar bacci mai shigen kyau fara mai santsi ya bata yace "idan kika fito daga wankan ki sanya wnn." Snn ya fita tareda janyo mata k'ofa." tana ganin ya fita tasaki murmushi ta bi k'ofa da kallo ta d'auki rigar baccin ta rungume ta lumshe ido tace yaya mahmud INA sonka." Snn ta mik'e ta Shiga toilet tayi wanka ta fito ta d'auko turaren da mommy ta Sako mata a jaka ta Shafa a kowace kusurwa ta jikinta snn ta d'auko rigar baccin ta saka." Gaba d'aya k'irjinta a waje yake, cibiyarta ma a waje sai daga can k'asa akasaki d'an wani net ya rufe mata gabanta da bayanta amma pant d'inta gashi nan a bayane ana gani a Cikin net d'in." Rigar bak'aramin kyau tayi mata ba ta kalli kanta a madubi wani irin kunya taji ta kamata, Tayi saurin juyawa da Sauri domin ta haye kan gado ta lullub'e tunkafin mahmud ya shigo ya ganta a haka." Aikuwa juyawarta kenan saiji tayi ta fad'a a jikin mutum, mahmud ne tund'azun yashigo bata lura dashi ba tsaye yayi a gefe d'aya yana k'arewa Surar jikinta kallo, hankalinsa a tashe, babu abinda ya k'ara rikitashi irin k'irjinta a yanda ya gansu manya manya dasu a tsaitsaye, da Santala Santalan cinyoyinta." Rungumeta yayi ya shiga shunshunar wuyanta zuwa wurin boobs d'inta kansa yasaka a tsakiyar boobs d'inta ya dinga wasa dashi, Snn ya d'auketa ya d'orata a kan gado yayi mata rumfa da jikinsa yasanya harshensa cikin bakinta yashiga wasa dashi Cikin wani salo." ya gangaro zuwa boobs d'inta ya shiga lulayashi da hannu yana wasa da shi idonsa ya rufe da matsananciyar sha'awarta bai San lokacin da ya kai bakinsa a kai ba ya Shiga tsotsa yana wasa dashi." Dijama kuma sai runtse ido takeyi saka makon wani irin zafi da takeji a kan boobs d'inta, yanda yake tsotsarsu kamar yaron goye, cije baki tayi ta na k'ok'arin tureshi amma INA mahmud yayi nisa, Hannu ya Sanya ya cire rigar gaba d'aya yayi wurgi da ita gefe d'aya, ya Sanya hannunsa yashiga shafa jikinta ko ta ina har xuwa pant d'inta, gaba d'aya ya cire pant d'in yayi jifa dashi ya sanya hannunsa ya shiga wasa da wurin, Wani nishi dijama ke saukewa, sama sama hakan shima mahmud, Sai da yaji wurin ya jike da ruwa, Wanda a dai dai Wnn lokacin idonsa ya rufe ya d'age mata k'afa sama ya Sanya Baki ya shiga lasar wurin, Sha'awarsa ta kai k'ololuwar tashi ya cire wandonsa tare da karanto Addu'ar saduwa da iyali ya fara aiki." *Hmmmmmmmmm* *idan ana sallah ba'a magana* 🤸‍♂🤸‍♂🤸‍♂🤸‍♂ [8/17, 20:20] Washa: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _Yar gidan tsohuwa_)😅 Written by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basher_) *Godiya ta musamman gareku Abin Alfaharina bazan tab'a mantawa dakuba* *members of Ummu Safwan Hausa Novels hak'ik'a Wnn GRP nawa ina Alfahari da karamcin K INA sonku gaba d'ayanku har Cikin raina Wanda sunanku baya lissafuwa saboda yawanku* *yawan masoya dad'i garesa sann yawan kulawa k'auna ce, ina godiya d kulawarku gareni* *Aisha A moh'd* *Hauwa Sarki* *Mss Hafsy* *Maman Sadeeq* *Mum Hibbat* *Manshart* *Zeey mairiga* *Sajida* *Munnirà* *ina godiya sosai karku manta Ana tare* *65* Wani irin jijjaga yakeyi jikinsa na rawa kwata kwata baya cikin hanyacinsa aiki kawai yake rabawa dijama, Tun tana kuka da magiya akan ya gyaleta harta fara tureshi amma ina bai masan abinda takeyiba." Sai da ya biya buk'atarsa snn ya sauka a kanta, Wanda a lokacin ta galabaita ko hannunta bata iya d'agawa." Idonta a rufe sai hawaye kawai take fitarwa, Janyota Mahmud yayi a jikinsa ya rungumeta cike da so da k'auna." Jini yagani yana zuba a gabanta cikin tashin hankali yayi saurin tallabarta ya nufi toilet da ita, Ruwan zafi ya zuba masu shiga jiki ya sanyata a ciki amma ina jinin bai tsayaba." Dafe kai yayi hankalinsa a tashe ya d'auketa daga cikin ruwan zafin ya mayar da ita kan gado, Ya d'auko wayarsa yakira likitansa Wanda yake dubasa, tun a waya ya shiga fad'a masa abin da ke faruwa." K'arfe 2:30 na dare doctor ya tsaya da motarsa a kofar gidan Mahmud cikin hanzari Mahmud ya fita harda da d'an gudunsa yaje ya bud'e masa get yashigo." Likita ya shiga d'akin da d'an saurinsa domin ya dubata, a nan ya gano matsalarta ta d'an k'aru ne a saka makon k'arfin da aka Nuna mata." Anan doctor yayi mata d'unki ya bata magani snn ya fito ya samu Mahmud a falo sai safa da marwa yakeyi, Doctor ya dafa kafad'arsa yace "kwantar da hankalinka Ango ciwon da sauki k'aruwa ce tayi saka makon rashin binta hankali da bakayiba." Haba soja kada fa KA manta ba a fagen yak'i bane, Komai d'an a hankali ne, kuma abin nan naka ne ba k'arewa zaiyiba, yana nan a tare da kai, ya kamata KA dinga lallab'a yarinyar mutane, Murmushi mahmud yayi ya d'an sosa kai cike da jin kunya yace "bazaka gane halin da nashiga bane doctor. Yanzun a wane mataki take?" Doctor yayi murmushi yace Yanzun dai nayi mata d'unki ga magani can na rubuta mata gobe idan Allah ya kaimu kaje kasawo mata kabata tasha, insha Allahu zata samu fly." Mahmud yayi masa godiya ya rakashi ya shiga motarsa ya tafi." D'akin yashiga ya tarar da Dijama tasamu yin bacci hawaye a gefen idonta, Ido ya tsora mata yana kallonta cike da tausayi, yanaji lokacin da take Cema sa "yaya mahmud da zafi kayi a hankali kada kajimun ciwo." Amma ya rasa abinda ya hanashi sauka a kanta." Shi dai ya San a lokacin baya cikin hayyacinsa. Wani irin dad'i da d'add'ano wanda yasa gaba d'aya kunnuwansa suka rufe, D'an'd'anon ya fisgeshi ya kasa d'agawa kanta." Dijama ta dabance komai nata da ban yake da sauran mata, ya kaiwa goshinta kiss yace "ina sonki k'anwata komai naki mai kyau ne." Anan ya tashi ya shiga toilet ya tsarkake jikinsa yayi wanka ya d'auro Arwala ya fito ya tayar da sallah godiya ga Allah da yayi masa baiwar macce ta gari." ***************** Kwanan mahaifiyar yusra uku a sibity rai yayi halinsa, Yusra ta Kuma Shiga cikin tashin hankalin da baya misaltuwa, Babu abinda takeyi sai kuka gashi batasan dangin mahaifinta ba, bare na mahaifiyarta, Saboda bata da lokacin su,bata damu da dole sai ta sansuba, mutum d'aya ne tasani k'anin daddy ko shi a k'auye yake idan Yazo wurin Daddy ta dinga hattatarsa Kenan tana kyamatarsa idan ya zauna a kan kujera bazata tab'a kuma zaunawa a kantaba saboda kawai yana rayuwa.a k'auye." Gashi yanzun nemansa takeyi bata San inda Zata ganshiba , duniya tayi mata zafi duk inda ta wuce sai nunata akeyi har ya kai ta daina fita kullum tana cikin gidan sanye da k'atuwar hijabinta da zungureriyar carb'inta." Kwatsam sai ga ma aikatan banki sukazo karb'ar kud'insu a wurin Alhaji Atiku tunda sunji labarin ya rasu." Anan tashiga tarkato masu kadarorinsa ta basu daga ciki harda gidan da take zaune a cikinsa. Ya Shiga." Anan suka bata lokacin da zata Bar gidan, Tana nan zaune cikin k'unci da bak'in ciki, tayi nadama sai a yanzun ta tabbatar da duniya ba'a bakin komai takeba, lallai ba komai ake Nema a duniya a sameshiba." Tana nan tana neman mafita sai ga k'anen daddy yazo, daga k'auye, Yusra ta durk'usa k'asa tashiga bashi hak'uri da magiya akan ya yafe mata duk abinda tayi masa a lokacin baya ya taimaka ya tafi da ita." Shuru yayi yana kallonta ta bashi tausayi ganin yanda ta muzanta tayi bak'i duk ta canza kama kamar ba itaba." Anan dai ya hak'ura yayi wa zumunci kara ya d'auketa tareda kayanta suka shiga cikin akori kura suka nufi k'auyensu." Hmmmm rayuwa kenan." ***************** Hakan dijama take shan tarairaya da kulawa a wurin mahmud, Kwata kwata baya son ganin b'acin ranta Motsi kad'an idan tayi a kan idonsa, yana tambayarta ko akwai abinda yake mata ciwo ne ta girgiza kai alamar "A'a." Sai da sukayi sati d'aya a hakan duk lokacin da yayi tozali da ita sai sha'awarsa ta motsa, Abin yana damunsa ya d'auki waya yakira likita ya tambayeshi wai har yanzun bata warkeba ne?." Likita yasaki dariya yace "mahmud baka da sauk'i, To ta warke kana iya zuwa wurinta amma Dan Allah KA lallab'ata kada KA Nuna mata k'arfinku na sojoji Katina da ba a fagen yak'i kake ba." Mahmud yayi dariya ya kashe wayar cike da Murna da jin dad'i." Daren yauma sai da dijama ta sha wahala harda kukanta da hawayenta amma mahmud bai San tanayiba aikinsa kawai yakeyi." Sai da yasamu natsuwa snn ya shiga lallashinta tareda yi mata Alk'awari kala kala." Mahmud namiji ne mai yawan buk'ata yanada k'arfin sha'awa sosai ko fita yayi tadawo sai ja dijama a d'aki sai sunyi." Dijama tun tana gajiya yanzun har ya kai ta d'an fara sabawa, Kullum Cikin shan wahala take a wurin Mahmud abinda yake damunta d'aya ne mahmud ya din yimata a hankali mana sai dai ya dinga yimata da k'arfi Wanda a kullum sai ta galabaita tayi gashi." Mahmud kuma a ganinsa lallab'ata yakeyi domin ya fahimci tana hak'uri dashi da dauriya." Dan hakan yake kuma jin wani Sabon Sonta da k'aunarta suna ratsa ko wanne b'argo na jikinsa." Ahakan yasa yaji gaba d'aya Abuja tafita rayuwarsa ya nemi transfer yadawo kano da aikinsa Duk dai ogansa baiso hakan ba, Gidansa na Abuja kuma ya mayar dashi makaranta islamiya Allah ya kai lada a k'abarin mahaifan dijama." ****************** Khalil kuma kukan Sadeeq a kullum damunsa yakeyi ya hanashi bacci, yanda yaga dare hakan yake ganin safiya Bak'in ciki ya taru yayi masa yawa, ace k'aramin yaro da shi a dubi shi ace yana da d'a, Idan ya tunkari d'akin A shanty domin yayi mata rashin mutumci Wani kallo take wurga mashi na reni tace "kayi ciki Kuma kace Baka son kukan jariri ai kuwa k'arya kasha, kuma idan KA sake kace zaka cutar damu a gidan nan to zan kira wayar Abba na fad'a masa." Jikin Khalil sai yayi sanyi ya dawo d'akinsa ya kwanta." Saima ya dunga tafiyarsa makaranta baya dawowa sai lokacin da ya so yaga dama. Wata rana ma a can yake kwana saboda Khalil baya iya rayuwa sai da macce. " Daren yau sadeeq ya tashi da matsancin zazzab'i Wanda har suma yakeyi, Ashanty ta d'aga waya ta dinga Kiran khalil yana can tareda 'yan matansa a club. Su uku Mariam Salma Billy, Yana ganin kiranta yak'I d'agawa." Kafin safe sadeeq ya rasu, Kuka Ashanty takeyi takira Abba da mahaifinta, Cikin HanzAri Abba ya k'araso gidan, Ya shiga tambayarta ina shi khalil d'in?" Tana kuka tana fad'a masa ai khalil ya daina kwana a gida." Girgiza kai Abba yayi yaciro wayarsa a Aljihunsa yakira khalil, Khalil yana ganin kiran Abba gabansa ya fad'i Abba yace kazo ka sameni a gidanka ina jiranka." Cikin hanzari khalil ya ture matan da ke kan jikinsa ya fito ya shiga motarsa ya taho gida." Abba bai nuna masa komaiba illah yafad'a masa cewa d'ansa Sadeeq ya rasu" Khalil ya d'an razana da mutur sadeeq wata zuciyar tace masa mutuwarsa ai tafiye maka alheri." Anan take akayi masa sitira suka kaishi makwancinsa." Bayan sundawo daga wajen rufeshi Abba ya shiga tambayar Ashanty ko akwai abinda take buk'ata ta girgiza kai Alamar A'a Abba yayi masu sallama yayi tafiyarsa." Abba Shikad'ai Cikin d'aki yana tunanin rayuwar Khalil tabbas Khalil yaro ne k'arami amma mata sun bud'e masa,ido Tun a can baya bai lura da hakan ba sai yanzun." Yashiga tunanin wata k'ila ko karatun baya tsayawa yayi." Ya girgiza kai yace "nasan matakin da zan d'aukar maka Khalil." Sati d'aya da rasuwar Sadeeq, misalin k'arfe 4:30pm Abba ya shirya ya tafi makarantarsu Khalil, a lokacin sun had'a wani party a Cikin makarantar Khalil shine shugaba." Yana can gefe d'aya tareda 'yan matanshi sunyi kwakwance akan ajikinsa suna shafashi, wurin ya cika da samari da 'yan mata ko wannen da budurwarsa." Abba ya tambayi wasu d'alibai da yagani a zaune suna karatu kwanin sha'awa yace "Dan Allah ko Khalil yashigo makaranta yau." Suka amsa da "eh yashigo amma suna can party sukeyi, Wani d'alibi daga cikinsu yace "ai Khalil aikinsa kenan yatara 'yan mata da samari ayi ta chasu." Gaban Abba ya fad'i hankalinsa ya tashi yanufi wurin da akayi masa kwatancen Inda Khalil d'in ya ke, kid'a kawai kakeji yaketashi a wurin, A can Abba ya hango Khalil tsakar filin rawa yakeyi 'yan matansa sun zagayeshi ya rik'e masu k'ugu suna rawa." Hankalin Abba ya kuma tashi, Ya kasa k'asawa warin." [8/17, 20:20] Washa: 🌹 *DEEJAMAH*🌹 ( _Yar gidan tsohuwa_)😅 Written by *UMMU SAFWAN* ( _Fareeda Basher_) *66* *Alhamdulilla Allah na godema da kabani dama da lafiya na kammala wnn littafi nawa, Alherin dake ciki Allah ya sadani dashi, kuskuren danayi Allah kayafemun*🤲🤲🤲 *Na sadaukar da wann littafin ga 'ya'yana Abin Alfaharina* *SAFWAN ANAS BAWA* *FATEEMA ZAHRA BABANGIDA* *MUHIBBAT & MAMIE* *SADEEQ NURA BABBAFA* *HABIBA NAZIFI LAWAL* *AFFAN* *ALLAH YA RAYAMUN KU YA SANYAWA RAYUWARKU ALBARKA, YARA MANYAN GOBE* *ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH*🤲🤲🤲🤲 🔚🔚🔚🔚🔚🔚 Yayi tsaye yana kallon ikon Allah Khalil sanye da GAJEREN wando da wata riga a jikinsa red colour, sai casunshi kawai yakeyi da 'yan mata." D'aya daga cikin abokanansa suka hango Abba a tsaye, ya lallab'a yaje wurin Khalil ya rad'a masa a kunne." Cikin Khalil ne ya murd'a yaji zawo yana neman kub'uce masa a lokacin da yayi ido biyu da Abba, Ya dinga ture 'yan matansa da suka lallak'a meshi suna kuma shigewa jikinsa, turesu yakeyi sai kuma yin cikinsa sukeyi." Dakyar yasamu ya ficikesu da k'arfi daga jikinsa,YAYI wurgi dasu ya nufi wurin Abba jiki ba kwari kansa a k'asa ya sunkuyar da shi." Abba yana ganin ya tunkaroshi ya juya baya yayi tafiyarsa ransa a b'ace kai tsaye office d'in shugaban makarantar, ya shiga, yanata faman fad'a shugaba sai hak'uri yake bashi." Khalil ya shi go office d'in bayan ya canza kayan jikinsa zuwa manyan kaya, kai tsaye gaban Abba yaje ya durk'usa tareda sunkuyar da kansa k'asa, Yayi nadama iya kunya yajita, yakasa had'a ido da Abba." Abba da sai fad'a yakeyi "ashe khalil ba karatu yakeyi ba yaketa faman kashe kud'insa a banza kuma ace aka kasa samun ko da d'aya daga cikin malaman makaranta su same shi a gida SU fad'a masa ko a b'oyene." Cikin jin haushi da takaici ya sanya k'afa ya shure Khalil dayake durk'ushe a gabanshi ya d'aga hannu ya d'aukeshi da mari." Yace "Khalil kabani mamaki ashe baka da tarbiya?" Ashe haka halinka yake kaketa b'oye mana?" Lallai sai yau na kuma yin nadama tareda danasin maganar da mahaifiyarka tayita fad'a mun akanka akan nayi maka aure tin lokacin da kanuna kanaso." Tashi katafi KA janyo mun 'yan matanda naganka dasu a yanzun idan ba hakanba na rantse ranka sai yafi nawa b'aci." Jiki ba kwari khalil ya mik'e yafita saka makon ganin b'acin ran Abba da yayi Wanda bai tab'a ganiba." Cikin minti goma ya janyo 'yan matansa Mariam da salma da billy, Wad'anda suka sanya hijabi har tanaja a k'asa." Suka durk'usa gaban Abba kamar masu rok'on gafara." Abba yace "kuna son wan can?" Ya nuna khalil Suka d'aga kai gaba d'ayansu, alamar eh Gaban Khalil ya fad'i." "Iyayenku sun shiya yimaku aure yanzun?" Suka had'a baki da "eh." Dukansu ya karb'i number iyayensu ya fita a fusace." Cikin satin nan aka d'aurawa Khalil aure da Mariam da salma da billy." Abba ya canza mashi babban gidan Wanda yake d'aukar macce hud'u aka zuba mashi matanshi gasu nan mallakinsa ne yayi abinda yaga dama dasu yaci har sai ya gaji" Ai kuwa family kowa mamaki yakeyi Khalil da mata hud'u, Mahmud shi abun dariya yake bashi da al'ajabi." ***************** Burin Mahmud na duniya shine Dijama kullum soyayyarta sabuwa take koma masa, Dan haka baya iya awaya biyu a wurin aiki sai yadawo gida yaga lafiyarta. Daga nan ya d'auketa sushige d'aki." Idan yana gida kuma baya barinta ta huta koda yaushe boobs d'inta yana cikin bakinsa yana tsotsa dashi yake kwana a baki." Yau juma'a ta kasance mahmud baya fita aiki, dijama ta kammala kalolin abincita Ta gyara Gidanta ta sanya turaren wuta mai k'amshi ko ina gidan ya d'auke da k'amshi, Tayi kwalliyarta cikin shaddaa ash colour Wanda sukayi anko da mahmud shadda tayi matuk'ar yi mata kyau." Shima mahmud yafito cikin shaddarsa yana sauri ya tafi masallaci ganin irin kyau da dijama tayi har sai daya kai k'ofar fita ya dawo ya tallabo kanta yashiga tsotse janbakin bakinta, Sallamar da sukajine yasa yayi saurin sakinta yafita da sauri dan gudun kada yak'i samun sallah, Yana cewa dijama kiyi shiri idan nadawo zaki karb'i goron juma'a." Fateema ce tashigo tana gaidashi ya amsa yayi tafiyarta." Dijama taji dad'in ganin fateema ta tarbeta da murna da farin ciki, tacika mata gabanta da kayan marmari da abinci." FATEEMA tafaraci tana kallon dijama tace "sis naganki ki k'arayimun kyau da k'iba, meye sirrin ko dai ansamu ne?" Dijama ta mere Baki tace "wane irin k'iba kuma dan bakinsan wahalar da nake shaba ne, Wlh sis yaya mahmud mugune ya cika mugunta da yawa kullum fa Abu d'aya ba dare ba rana a koda yaushe cikin ruwan zafi nake ina gashi, Daren farkonmu sai da akayimun d'inki Dan mugunta. " Kema hakan ishaq yake maki?" Fateema ta tintsire da dariya tace A'a mijina da naki mijin ba d'aya bane, Karki manta mijinki fa soja ne, yasha fafatawa da Arna a wurin yak'i shiyasa yake k'ok'arin ya kashe arnan gidansa." Karki damu da Wnn sis nidai burina d'aya kikuma jurewa ki kama yaya mahmud kireshi da kulawa da tarairaya kada kitab'a Nuna maSA kingaji da Daukar ragamarsa da hakanzaki saba." Suna cikin hirarsu mahmud ya shigo Wanda a gaggauce ya gama sallah yanufo gida Dan a matse yake." Da sallama yashigo falon idonsa yana kan dijama, Ya zauna akan kujerar da take kallonta, Tayi masa sannu da zuwa, Fateema ta gaidashi ya amsa tareda tambayarta ya gidan da mai gidanta?" Dijama ta tsiyayo masa ruwa mai sanyi ta mik'amasa ya karb'a yana kallonta ya sha." Ya ajiye cup d'in bayan ya shanye ruwan yacewa fateema "yaushe zaki koma gida?" Tace "sai zuwa an jima yace zaizo ya d'aukeni." Yace "Allah ya kaimu ya mik'e yayi shigewarsa d'akinsa tareda cewa dijama takawo masa abincinsa." Dijama ta kalli fateema tace "kinga kuma wani Sabon salo yau Kuma kunyar cin abinci yakeji a gabanki." Ta mik'e ta d'auki Tirin abincin ta nufi d'akinshi, Da sallama tashiga ya amsa mata yana kwance akan gado daga shi sai gajeren wando shigowarsa har ya cire kayan jikinsa." A Kusa dashi taje ta ajiye tiren abincin ta zuba mashi Tare da tsiyaya masa lemo mai sanyi." Idonsa akan boobs d'inta daya d'an Tifo a Cikin rigarta, Bata ankaraba saiji tayi ya d'auketa cak ya d'orata akan gado Tare da cire mata rigar jikinta." Ya haye kanta bakinsa cikin bakinta Dan gudan k'orafi, Hankali ya zame bakinsa zuwa kan boobs d'inta ya shiga sarrafasu gaba d'aya suka fita hayyacinsu, Mahmud da dama ya Dade da cire wandonsa ya sabud'e mata pant d'inta tareda ware mata kafafu ya saita yayi shigewarsa ya dinga aikinsa." babu abinda kakeji yana tashi. A d'akin sai sautin nishinsu gaba d'aya sun manta da wata FATEEMA can zaune a falo." Fateema kuma tana ganin shuru dijama bata fitoba tayi murmushi ta d'auki jakarta ta rataya tayi tafiyarta tareda rufo masu k'ofa." ***************** Khalil dai auren da Abba yayi masa ya sanyashi natsuwa da biyayya, hankali ya shigeshi sosai kullum nasihar Abba gareshi itace ya kwatanta Adalci atsanin matansa." Hakan ta kasance baya nuna wariya a tsakaninsu." Ganin yayi Hankali da natsuwa sun shigeshi Abba ya d'orashi a kan kasuwancinsa, sukaci gaba da kular masa da kamfanuninsa tare da sulaiman." ***************** Yusra dai tana can k'auye rayuwa ta canza mata tayi bak'i ta rame idan KA ganta sai KArantse da Allah ba yusrar da kasaniba ce 'yar gaye, Kullum Cikin hijabi take da carbi a hannunta tana istigifari." Anan tasamu wani makocinsu yace yana sonta aka d'aura masu aure matansa biyu itace ta uku." Rayuwa kenan." ************ Agurguje A kwana a tashi ba wuya Cikin dijama ya fito, Inda take shan tarairaya a wurin mahmud da tsohuwa mommy da Kuma Abba." Ranar da suka cika wata Tara da aure a ranar ta haihu ta haifi d'anta namiji mai kama da mahaifinsa.farin ciki a Wnn familyn abun ba'a magana." Ranar suna aka nad'awa yaro suna muhammad inda a kayi shagalin biki fuskokin Kowa cike da farin ciki. Abba da mommy da tsohuwa suna zauna a Cikin rumfa motar Khalil ta shigo ya d'auko matansa ko wacce da k'aton cikinta." Tsohuwa ta rafka salati ta rik'e baki tana kallonsu tace lallai namiji baya kad'an." Kai kuma 'yan hud'u za'a Haifa maka kenan🤔 Shi Wnn wata tara cif ya haihu kamar Wanda yakejira aika masa ita." Ta juya ta kalli fateema tace ke Kuma INA ganin basir ke damun mijinki da sai yanzun kike laulayin cikin." Gaba d'aya suka Sanya dariya suna fad'in tsohuwa problum😂😂😂 Kowa sanyawa ido kikeyi." Alhamdulillah anan nakawo karshen Wnn labari na DEEJAMA YAR GIDAN TSOHUWA KUBIYOMU A LITTAFIMU RANAR D'AURIN AURE NA." godiya gareku masoyana a duk inda kuke UMMU SAFWAN na sonku, ZANYI MISSING D'INKU FRIEND'S D'IN DEEJAMA😭 Copied By HAYATU BABA ZUBAIRU (YAYA HAYAT) (ADMIN OF ADMINS) (admin Hayat hausa novels Hausa novels and fashion Cool novel, makeup and kitchen1⃣ Cool novel, makeup and kitchen2⃣ AND Cool novel, makeup and kitchen3⃣) WHATSAPP NO: 09030159301