DOCUMENT MADE BY ADMIN ABDUL DOMIN MAIDAWA KO HADA MAKU LABARIN KU ZUWA PDF KO DOCUMENTING KO SAKAWA LABARIN KU SECURITY CODE A KIRA 07068808039 HAUSA NOVELS SOKOTO: WHATSAPP NO: 07068808039 WEBSITE: Abdulmkibab.hexat.com 🕌🕋🐄🐄🐄🐄 📝💫Bismillahirahamanirahim***🌳🐄 Mi'wasmiti. Page 1⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🕌🐄🐄🐄🐄🐄 Tafiya take cikin sauri sauri da Dan sassarfa tana tafe tana Dan mita da holo irin Na tsofaffi da sauri Na dan qarisa gunta Na Dan kalleta a nitse a take Na gano tsohur ba fillatace cikin hikima Na gaidata da yaren fillanci cikin Dan sakin fuska ta amsamin ba tare da ta tsayaba a hankali Na bita gami da cemata kakata ina zakije haka da sanyin safiya gashi sai sauri kike kamar wacce jirgi ke shirin tashi ya barta .. Ta Dan juyo ta kalleni tare da ci gaba da tafiyarta tana mai cemin ba doleba nai sauri ai ko faduwa zanyi Na fasa bakina Na zubda haqaran robar sai Na hamzarta .ai shi yafi jirgi shi sama da jirgi yake in ya shirya baya jiran kowa kuma shi jirgi ai yana bada lkci. toshi bai bada lkci shi tamkar hadari yake inya fito tofa ba jira kuma shi kamar guguwane sarkin birkita taro.... Cikin mmk nace keko kakata waye wannan ? kuma a ina yake? Cikin surutunta da mita tace gidan kamannin zani zanyi aikene Dan yau zasu gembu cikin mambila ..da Dan sauri na bita nace gidan kamanni kuma ?su haka sunan gidan yake ? Wannan wacce irin kamace dasu ? Na jera mata tabbayoyin aiko ta fara bani lbri tiryan tiryan🐄🐄🐄 Zuriyar Alhj Muhammad babayo Wanda akafi sani da Mlm babayo kuma sarkin shanu Dan asalin jihar tarabane can cikin mambila. Matansa 2 yayansa 5 maza 4 mace 1 uwar gidan innayi tana da Yaya 3 maza 2 sai mece 1 babban dansu barrister Muhammad Bello Muhammad sai mai binshi doctor Aliyu Muhammad sai qanwarsu Aysha.Muhammad Sai amariyar yayanta 2 duk maza Amadu shine babban danta sai hamisu Duk da kasan cewar mlm babayo ba fillatanine baiyi qasa a guiwaba wajen ilmantar da yayansa ilimin zamaniba sunyi karatu mai zurfi Barrister M.B.M Wanda suke kira baba bello yana da matarsa daya Nenne Aihuwarta 12 Amman yanxu haka yayanta 3 ne kadai sabida aihuwar wabi take Sadiya itace babba bayan aihuwar sadiya sai da tayi aihuwa 5 duk suna komawa sai Na 7 in ta sami da namiji mai suna Ahmad tokoran qaninshi Amadu bayan Ahmad ta kuma aihuwa 4 duk suna rasuwa sai ana 12 ta samu Allah ya barmata shi sunanshi Rabi,u... Sai doctor Aliyu Wanda suke kira Abba da matarsa Ummi yayansu 4 Yusuf shine babban dansu sai Abubakar da Usman sai Autarta Aysha . Sai Goggo Aysha wacce take Aure a Yola tana auren doctor Umar babban Abokin yayanta doctur Aliyu Abba kenan yayanta 3 Adam sai hydar sai Maryam Sai Amadu Wanda suke kira baba matarsa 1 yayansu 2 Abdul sai Amira. Sai baba Hamisu matarsa 1 dansa 1 Sadiq . Kamanni Family zuriyace da ta samu wadata da rahamar ubangiji Allah ya musu baiwa tako ina ga ilimi ga kyau ga arziqi ga zaman lfy da qaunar juna da tsantsar shaquwa da tausayawa Su yayan inna basu karatu sosaiba sai suka Koma makarantar Dan gote baba bello da Abba su suka budemusu wani katafaren filin seye da sayarwa mai suna kamanni family kuma su Amadu da Hamisu suna zaunnene da iyayensu acikin garin mambilan yayinda bb bello da Abba suke cikin taraba da zugar iyalensu sai dai alqawarinsu ne duk weekend suke zuwa gaida iyayensu da qannensu Years en Adam da Yusuf da Ahmad dai daine Sa.annine su randa akayi 40 en Adam a ranan aka aifi Yusuf ran sunan Yusuf kuma aka aifi Ahmad rayuwarsu Ahmad Abin Sha.awane da burgewa rayuwace mai tsafta sun kasance masu qaunar juna ga wani irin kamanni da suke fiye da tunanin mai karatu mutane da dama sukan dauka yan 3 ne sabida zallan kama fararene tas irin farinnan mai daukar hankali gasu kyawawa tamkar larabawa ga tsantsar cikar haiba gashin kansu tamkar indiyawa kamanin su kuma ya samo asaline sabida dukkansu da iyayensu suke kama sukuma iyayen kamane Na haiqan a tsakaninsu Sabanin abinda ke sakaninsu sai hali haqiqa halinsu ya banbanta dana juna kamar yadda wasu al.amura suka banbanta a tsakanin su Adam irin mutanenane da zan iya cemusu fadi garas mgn dai da zaran tazo ransu toh fa zata fito yana da yawan surutu da abin dry gashi da raha Ahmad bawan Allah damo sarkin haquri haka Allah yayishi shi mutumne mai haquri da tawakkali ga sauqin kai ga iya zama da jama,a gashi da fara.a ko yaushe fuskarsa Na dauke da murmushi Sam bai iya fushiba shi.... Ayagi sarkin fada mishkili kafi mahaukaci ban haushi muqu baya dry sai Abu ya baci Yusuf yadda wasu Al,amura Na rayuwarsa yasabawa sauran jama,a hakama halinshi shi Yusuf irin jarirenane da ake aifarsu da kaciya a jikinsu shi da kaciyarsa ya fito duniya tun tashinshi bai da yawan mgn haka kuma baison yawan surutu gashi da ra.ayin riqau ba,a juyashi yana da zuciya ga iya horon yara baison shishshigi da Sa ido ko Kadan madafacine sosai zakayi zaman shekara dashi bazakaga dryarsa ba haka kuma ko shekara 4 zakayi dashi da wuya kaga qwoyar idonshi kuma kab wanan halin bb bello ya gado yayinda shikuma Ahmad ya dauki haqurin Abba danshi Abba tamkar ba mai suna Aliyu bane. Amman duk da fadan Yusuf bayayi da su Adam sun shagu shaguwar da ba adadi tare suka tashi gida 1 daki 1 don dole mahaifin Adam ya haqura ya barshi a taraba tare sukayi marantarsu tun daga primary har xuwa university innada sukayi digiru ensu Na firko a qasar India Yusuf da Adam sun karanci medicine shi kuma Ahmad Abba ya sashi ya karanci business Amnan shi Yusuf yanxu haka yana karatu a jami.atul Madina enda yake qara karantar likitanci a musulunci Sai in sun Dan samu Hutu yake zuwa kamar yanzu tun cikin Ramadan yazo duk ya buwayi qannenshi mu samman Aysha da basa hada inuwa daya tamkar wuta da audiga haka kuma su Usman da Abdul d Rabi,u suma duk ya fara gungurarsu Amira ko dama cewa take suna zuwa bikin sallah bazata dawoba sai ya Koma Dan ita Amira a gaban bb bello take haqiqa kowa najin takaicin yadda Yusuf da Aysha basa shiri qiyeyyace sosai Yusuf yake mata wasu lukutan ji yake kamar ya karyata Ahmad kuma wata soyeyyace mai qarfin gske ke tsakaninsu hakama Adam da Amira Kumuje zuwa dai Ku biyoni a hankali lbr Na can gaba 🐄🐄🐄 ‬: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 MI,WASMITI.....page 2⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Taci gaba da bani lbr su Usman da Rabi,u da Abdul ma Sa,annine hakama Aysha da Amira da Maryam ... Yusuf ya kasance mai zuciya tun yana dan yaronshi sanadin zuciyarshi yanzu haka yana da matsalar ciwon zuciya💔 tun suna primary school yana dan shekara 6 makarantar su da aka shigar dasu yinifom en makarnar dan gajeren wondone da yar riga Amman tunda aka dinka musu kayan Yusuf yake ta faman cin rai shi ala tilas bazai Sa gajeren wondo ba dan shi ya kasance mai kunyar bayyana jikinshi tako wanne bangare ne ba yadda ba,ayi da shiba yaqi Abba yace sai a shigar dashi wata makaratar nanma yaqi yace shi dai inda su Ahmad suke nan zaije dole akayiwa shugaban makarantar bayani da yake abokin bb bello basu samu matsala ba Yusuf ya kasance mai kwarjini agun abokan kara tunshi kowa so yake yarabesa ko dan ilimin da Allah ya bashi Wata rana a makarantar yayi fada da wani yaro Mujaheed aiko suka rinqa gudu dan ya samu ya yarama Amman ya kasa kamo Mujaheed ga mlmansu da suka shiga tsakaninsu shi kuma yace dole sai ya rama da aka hanashi ramawarne ya rinqa kuka cikin xuciya da takaici kuka yake har numfashinshi Na yankewa basuyi auneba ya fadi sumemme Kai tsaye gida suka kawoshi Abba ya dugufa coto rayuwarsa da qyar aka samu ya farfado yana tasowa da kuka ya farka yana wlh ni sai Na rama bazan yardaba abi dai yaci tura dole aka nemo yaro yazo da iyayenshi yana zuwa Yusuf sai cewa yayi yazo gabansa ya duqa zai rama Abban mujaheed ya tura masa shi yana jeka ya rama aiko ya samu tsakiyar bayan shi ya rinqa dakamar duka gami da cemai wlh in baka ban haquriba bazan bar kaba yaro ya juya ya bashi haquri To daga nan suka zama abokai Ta dan zagaita surutun nata ta kalleni anitse tace to abinda yasa kikaga ina saurin Yusuf yazo nasan zai azalzalamusu su tafi ba tare da nakai aikenaba."""" Na danyi dariya a raina nace hajia Zubaida ikon rabbi daga tabbaya daya taban bayanin da ya zarce zatona Tacemin jikata ban sankiba gashi har mun saba daga ina kike haka nadan kalleta a nitse nace ni bakuwace daga jihar Adamawa nake sunana Aysha Ali Garkuwan Fulani kuma dama nazone gun Fulani yan uwana saiko nai Sa,ar cin karo da zuriyar sarkin shanu nima zasu barni Na kaimishi gaisuwar sallah ko? a madadin babana tace sosaima kuwa ai suna son baki ⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Babban gidane Na gani Na fada acikin babban birnin taraba gate en gidan ma kawai abin kallone ga ma aikata tako ina jamin sarone masu tsaron barrister M B M cikin gidan muka nufa kai tsaye wani babban parlor mai kama da dakin taro cike yake da mutanen gidan cikin hikima Na zuba musu ido 👀 dan naga wani abin al,ajabi kamace ta gsky a fuskokinsu gaba dayansu shiga iri daya sukayi galilace mai kyau da tsada bb bello da Abba suna zaune kan kujera daya tamkar tagwaye sai dai Abba ya dan fishi tsawo sai Nenne da Ummi suma suna zaune wuri daya cikin shiga ta alfarma da ka gansu kaga jin dadi da kwanciyar hankili haqiqa Nenne macece mai mutunci da kawaici da tsantsar qawaunar dan wani ga alkunya bata iya gwada son yayanta sama da sauran yaran Ummi Na mutunta ta matuqa Daga can gefe kuma su Usman ne suna dan hiransi. Ahmad kuma da Adam suna tsakiyar porlon kan wani tattausan carpet Sai Amira da take ta zirga zirgan zuwa tadda Aysha wannan zuwanta Na 3 kenan sai ta tashi ta zauna da zaran Amira ta fita sai ta sake nadewa a borgo Muna shigowa ba jimawa Naji wani irin qamshi mai ratsa zuciyar dan Adam nan take parlon ya hargitse da qamshin mai dadin shaqa gaba daya Na maida hankalina kan qofar danafi zaton tanan qamshin ke shigowa Cikin nitsuwa yake tfy da cikar kamala taku yake da salon girma hasken fuskarsa kamar tauraro⭐ komai najikinshi tamkar shi ya tsarawa kanshi kai tsaye gaban bb bello ya dan duqa ya gaidashi ya gaida su Nenne ya dan miqe yana gyara riqon da yayiwa briefcase enshi da woyoyinshi ya miqawa Ahmad hannu suka gaisa Adam ya dan harareshi cikin tsokana yace kai yaro ninefa babba ka fara gaida kanina ya qarishe mgnar yana dry Ya dan kalleshi cikin salon ka isheni da shegen son girma Abdul dake gefe yace good morning Hamma Yusuf a hankali yace morning Usman dake zaune gefen Abdul yace da kyau ba gaisuwaba ai yayi mgninka shi ko gaisuwar baiso dan haka ni bazan wahal da bakinaba Rabi,u ya danyi dry yace ni bari in gwada ya dan kalleshi da kyau yce Hamma Yusuf..... da sauri ya daga mai hannu ya yimai nuni da su taso su tf ya dan kalli bb bello yace baba mu tafiko Sagal kaka ta amshe mgnar tana mai cewa kai Yusufa ni ban kai ka gaisheni bane komeye kana tafe kana yamutsa fuska kai dai har Abadan baza,aga fara Arkaba Rabi,u ya ce toh ma ai Aysha muke jira tun dazu bata fitoba ya dan juya ya qarewa parlon kallo bata gun Amira dake manne jikin Ummi sai yanxu tace Hamma Yusuf ina da sauri ya dakatar da ita gami da cewa cikin mishkilanci da Alamun bacin rai yana mgn da dan fada fada ke tashi kije ki kirata in kuma ba hakaba wlh zan shigo Na babbalata muna fukar yarinya sai baccin tsiya ta iya da sauri ta nufi dakin Kaka kuma taci gaba dacewa Amira kije kicemata jirgin✈ ya iso kuma har ya fara dirin tashi ta dan juyo ta kalleshi kanshi a qasa tace mutum baida aiki sai sababi ni wlh ai wannan turaren daka zubbuda zai sani mura Abu kamar anyi barin motar turaren ta kuma shaqar qamshi tai ajiyar zuciya tace gsky ka tsammin turaren dan wlh yamin dadi ya kalleta cikin murtuqe fuska ya dan tabe baki Adam ya kwashe da dry yace kai kaka sharrinki yafi ta tsohuwar mota yanxufa kikace zai kasheki da turaren zai saki mura sai kuma kice ya baki duk sukayi dry yace Allah biyaye karka bata ta dan harari Adam tace toh dan hassada kada Allah yasa ya banin mana ga mai gidana zai sayamin ta fada tana kallon Ahmad ya danyi murmushi yace zanma dauko miki nashin matar Tai dry cikin jin dadi Usman yace toh yaukuma menene saqon naki? tce kai da Allah tafi daga can mai muryan mata kai sai shegen made Amman dai duk da hakan kafimin yusufa kam ta maida hankalinta kan Ahmad tece Ahmadu in kaje kace innayi ta baka naman raqumi nakeso..... aiko su Rabi,u sun sami abin dry Yusuf ya kalleta yana cewa Aku kawai baki da aiki sai surutu sai shegen kwadayi ke dai nama nama kowa ya gaji da nama Amman banda ke Edin tace nayi surutun so kake naita baqin hali irin naka baki kamar dinkekke andai ji jiki wlh kuma sai kaban turarenan ehe ⭐⭐⭐⭐ Kwance take ko a jikinta kamar ba ita ake jiraba cikin sauri Amira ta daka mata duka ke Aysha toh wlh ga hamma yusuf ya fito Da sauri ta bude ido gami da zazzarosu 😳 ta diro daga kan gadon tana qoqarin cire kayan jikinta gaba daya jikinta bari yake tana shiga toilet tana Na Shiga uku 🙉 dan Allah Amira fitomin da kayana da mayafina da takalmi yau kam Na kade mugu ya samu dan dalilin jibgata By garkuwan Fulani Ku biyoni masu karatu wannan goron sallarkune daga gareni 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 MI,WASMITI.....page 3⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 9:55 PM*12-09-2016 Bayan ta gama yan gyare gyarenta ta fito sab da ita gonin sha,wa Doquwar rigace ajikinta tayi kib da ita cikin sauri ta dauki ribbon enta da dan kwalinta a hannu ta fito parlon tfy take cikin sauri sauri hankalinta gaba daya nagun Ahmad shiyasa bata lura da shi a gunba tana isa ta miqawa Ahmad en ribbon en gami da dan juya bayanta tce ya Ahmad gashi tufkemin gashina ga yan kunnena ma ka samin da sauri kasan yanzu za,aitamin masifa Karba yayi yana murmusawa ya dan matso yana tattara gashin da ya kwanta har kan kafadunta Rabi.u ya dan kalleta cikin jin takaici yace wlh kedai kinji jiki kina mace Amman wai sai maza ke shiryaki....cikin tsiwa tace endin aiba kai nace kaminba ehe Yusuf dake tsaye a gefensu takaici ya gama cikashi yarinya ta bata musu lkci sannan ta fto tana musu rasar kunya cikin jin haushi ya ware tafin hannunshi zai shimfi da mata mari da sauri Ahmad ya dan jata jikinshi ya tura fuskarsa aiko marin ya sauka kan lallausar fusakarsa Adam ya dan juyo dan jin sauqar marin kai biyaye lfyarka kuwa ? a harzuqe Yusuf en yace wlh yau zakici dan banxan duka kaji muna fukar yarinya ya kalli fuskar Ahmad a take tai jawur abinka da farar fata hatta zanen yatsunsa sai da suka bayyana a kuncinshi ita kam tuni ta gudu gun Nenne cikin jin tsanarta ya kalleta ya kadai kai gami da cije lips enshi ya fita a fusashe Amira ta kalleta shike nan Aysha kin kade wlh saikinfi fura kirbuwa agun Hamma Yusuf kika Sa ya mari ya Ahmad ai kinshiga tara..tai rau rau da ido tace dan Allah Ummi ki bashi haquri. Usman ya harareta yace Wlh ya dakakin dai Munafuka ba bakya tsoron kowaba tun yaushe muke jiranki sai kace kece uwarmu gaba daya.. Nenne tace yi shiru abinki bazai dakekiba Bb bello ya miqe hadi da cewa kutaso mu tfi.. Motocin 3 ne a harabar gidan daya Usman ne ke jansu bb bello da Nenne sai Abdul da yake kusa dashi daya kuma Rabi,u ne ke jansu Abba da Ummi suna baya sai Anty Sadiya dake gefenshi a hankali suka fita harabar gidan sai dayar kuma Yusuf ne xaune a ma zaunin driver Adam ya zauna a gefenshi sai Amira da Aysha a baya Ahmad Na daga tsakiyarsu Aysha Na maqale da hannu Ahmad a jikinta duk ta rude Kusan minti 20 da fitarsu bb bello Amman shiru yana zaune sai danne danne yake a lap top enshi tamkar ba masu shirin tfy ba Adam ya dan kalleshi cikin yanayi yadai yace haba biyaye tfy fa zamuyi kuma kai zamanka ai ya kama mu tfi ko shiru kamar badashi akeba sai gyara zamansa yayi ya dan kishin gida da jikin kujera Ahmad ya danyi mirmushi cikin muryar lallashi yace tuba muke yayana aimana afuwa a huce plss mu tf kasan Abba zai ta jiran isowarmu ya juyo ya kalleshi ya maida kanshi a hankali phone enshi ya fara suwa ya balle marfin motar ya fita gindin wata bishiyar manqoro 🌳ya zauna kan wasu kujeru da aka tana dan zaman mgn yakeyi kamar baison ya dan hada fuska yana mai cewa Rashida ni fa bana son fitina ai sauri kikayi aiki ne yamin yawa ko zaman kiranki zanyi cikin muryar gudun matsifarsa da tsantsar qaunarsa tce ayyah Yusuf yau kwana nawa bamuyi mgn ba kai baka kirana saidai in ni Na kiraka sallah guda bazaka kiraniba mu gaisa cikin gajiya da mitarta da surutun nata yace ya isa ya isa haka badai gashi yanxu mun gaisaba ni yanzu ina da abin yi da sauri tace dan Allah kar ka katse kiran Yusuf yaushe zakazo ne ? Barana ya bata amsa a gajarce ya katse kiran cikin jin takaici ta qurawa phone📱 nata ido a fili take cewa ya Allah ka mallakamin zuciyar 💛Yusuf ka juyomin hankalinshi gari Allah ka sassautamin sonsa a raina Rashida yar kano ce kuma tare sukayi karatu dasu Yusuf a India allah ya jarabceta da qaunar Sa a ranta shi kuma mishkilanci da taurin kai da ra,ayi sun hanashi maida hankali kan ko wacce mace A hankali Ahmad ya zauna gefenshi biyaye ya kirashi cikin sanyi muryarsa tashi mu tfi ko ido ya zubawa fuskarsa hannu yasa ya shafa fuskar yace biyaye meyasa meyasa zakasa hannuna ya mari fuskarka Kasan kimar fuskarka gareni kuma kasa Na cutar da zuciyata bana qaunar duk wani abin da zai tabamin gangarjikinka da lfyarka wlh naji tsanar ta araina dan ta sani Na mari dan uwana da hannuna. Cikin sakin fuska Ahmad yayi ajiyar zuciya ya shafa fuskartashi cikin murya mai nuna gskyar abinda yake fada yace biyaye zafin marin a fatata ya tsaya bai shiga cikin 💘 zuciya taba hakazalika komai kamin duk zafinshi bazanjiba Amman da marinnan ya taba fuskar Aysha Na da zuciyata zata soku da dafi 💘ya daura hannushi kan kafadarsa yaci gaba da cewa biyaye komai nakeso a duniya kana tayani son abin ya akayi ka kasa tayani son Ayshana meyasa zuqatanmu suka samu sabani kan Aysha ni duk zuqar numfashin da zanyi a duniya da nauyin qaunar Aysha nake janshi yayinda kai kuma da tsanarta kake Jan naka numfashin meyasa ya tsura mai ido cikin yanayin tabbaya idonsa sunyi jaa shi bai saniba mganganunshi qara samai tsanarta suke a cikin zafin nama da sauri ya nufi gun motar Da garfi ya fixqota waje ya watsa mata mari ciki jin radadi tasa kuka ta dafe quncinta da gudu ta fada qirjin ya Ahmad tace Hamma Yusuf dan Allah kayi haqiri wlh bazan qaraba Amira kam tuni ta rakube jikin glass A hankali Ahmad yace ngd biyaye mu tafi tunda kayi abinda ranka ke so ya jata suka shiga A fusashe ya figi motar ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ MAMBILA Bayan isarsu baba bello da kadan suma suka iso parlon cike yake maqil da zuriyar bappa yaya bayan gaishe gashen da sukayi shidai yusuf su babba Amadu kawai ya gaisar ya koma can gefe ya zauna ya bude lap top enshi yai ta dan danne danneshi Sadiq yazo kusada shi ya zauna suna dan dubawa tare dan haqiqa yana qaunar yaron duk da ba wani mgn dashi yakeyi sosaiba Abba ya kalli Ahmad dake zaune kusadashi yace Ahmad meya tsayda ku ? ya danyi murmushi yace Abba kawaidai mun tafi a hankaline ya jinjina kai yace toh kun kyauta Bappa yaya ya dan kalli Yusuf daya murtuqe fuska yace kai Dudabe har yanxu baka Koma bane ya daqo ya zuba mai harara dan ba abin da ya tsana kamar kiransa da Dudabe da bppa yaya yakeyi yaci gaba da cewa Ahmad shi har yanxu hutun nasu bai qare bane ? Ehh da sauran lkci dai ya bashi amsa Adam yace wai kai menaka da komawarsa ne ko a kanka yake zaune baba bello yace Adam haka naka dama kai inkazo dai toh sai kai ta sokano mana su innayi tamiqe tana nasan yusufa da tea bari Na kawo maka ta dauko flask en da cup ☕ta dire mai a gabanshi tace ga shayinka dan nasanka kananan kamar balarabe ya dan kalleta ya motsa bakinshi a hankali yace sai anjima zan Sha.ko Sadiq dake gefenshi Badon yana kallon bakinshiba da bazai San me yaceba inna ta dan tabe baki tace yayi ai In dai Yusuf ne ya iya gwatsale mutane Bappa Yaya yace Dudabe har baki 3 bai amsaba bai kalleshiba ya danyi dry yace Allah sarki Dudabe am mu muna sonka kamar mu mutu kai kuma kana qinmu kamar ka mutu duk suka danyi dry Adam ko dry yake hard a buga hannu yace madallah biyaye toh Bappa Yaya mu da bakwa son kuma ko zaku kaimu bola😂 haka dai sukai ta hira da nishadi hirar zumunci By Admin ABDUL 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇MI,WASMITI.....page 5⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 A hankali ya direta kan kujera hadi da manna mata kiss a goshi Nenne ta kallesu cikin qauna ta murmusa tace kai Abubakar kamar dama ita kadai kai kewarta da sauri cikin dry ya duga gaban bb bello ya gaidashi da Abban su Ummi farin ciki take sosai tanajin dadin yadda Abubarkar ke mu,amala da qanneshi tamkar abokan watsanshi zafi sosai takeji a ranta in taga yadda Yusuf ke hantarar su da donqofarsu Sam baya zama dasu yayi hira Sam abin bai mata dadi amatsayinsa Na shine babba hira suke sosai tana maqale jikin ya Abubakar ga Ya Ahmad a gefensu Nenne ta kalli Amira tace toh kunyi ta mai hidima yanxu kuma kun xo kuna ta surutu Baku kawo mai abincin ba da sauri ta miqe gami da dauko abincin Yusuf dake gefensu mamaki yakeyi sosai a ransa kome su Ahmad keji da maqalema yara qanana basa ko jin kunyarsu da gudun karsu rainasu abin haushi yake bashi sosai ya sake kallon yadda Abubakar ya ke ta lallaba yarinyar har abin kyamama yake bashi ga uban surutu da suke zubawa kamar parrot ko bakinsu bai gajiya da cokoikoiwa cikin qosawa da surutun nasu ya miqe ya zai tafi a lkcin Kuma Abubakar ya dan ture Aysha a jikinshi yace Auta baki kawomin ruwaba fa ta miqe kenan sukayi ido 2 da dodon nata cikin razana da tsantsar tsoronsa jikinta har bari yake bata San sanda ta furta إنا لله وإنا إليه رجعون،الله‍م اجرني في مصيبتي وأخلف لي خير منه‍ا ya kalleta da kyau yana qoqarin gano me take nufi shine matsifar ko qaqa ai bata bari ya idda tunaninsaba ta juya da gudu tai dakinsu hakanne ya tabbatarmai dashi din take qoffa yayi ya girgiza kashi gami da cije lips enshi ya fita Sukama sukaci gaba da hiransu Ahmad dai ya gano Abinda Yusuf ke nufi Aransa yake mmki wai ace mutane uwa daya uba daya Amman basa taba haduwa gu daya kamar wuta da auduga ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ A hankali take tfy har ta iso qofar gidansu dai dai baking get in taga wasu maza su biyu zasu kai Sa,annin ya Ahmad kanta a kasa tana tfy cikin gaji tana kai gidan kaka sai shegen nisa in bakajeba tai ta mita tazo daidai gunsu da sauri dayan yace yauwa qanwata yaki ta dan kalleshi a nitse ta iso ta gaidasu suka amsa da fara,arsu dayan yace aha qanwata in kin shiga kicewa yayanki Yusuf ya fito mu tafi Ta dan kallesu a yatsine tace ni bani da wani Yaya mai wannan sunan ehe ban sanshiba ta qarishe mgn tana qoqarin tfy da sauri suka kalli juna har suna hada baki wajen cewa ina ke yar gidannane ehh ta basu amsa da mmk sukace kuma kice baki San Yusuf ba ? Ta dan juya ido tace ehh ni yayuna ba Yusuf sai ya Ahmad da ya Adam kuma basannan ta juya da nufin tfy a firgice ta zaro ido 😳ta dan ganinshi a bayanta juyawa tayi da sauri zata Koma inda ta fito cak ta tsaya sabida tsawar da ya watsa mata maza kixo ki wuce gida yarinya sai shegen yawon tsiya zan kamakine ya kada kai suka shiga mota itako tai cikin gida ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Bayan sallan 🕌isha Ahmad ya shigo gida a lokacin tare suka shigo da Abba ya ajiye mar jakarsa ya fito a parlor suka hadu da Aysha su Ummi Na zazzaune ya dan kalketa cikin salon tsantsar qauna ya dan shafa cikinshi yace Aysha yunwa nakeji a kawomin abinci dan Allah toh tace cikin zumudi tace ya Ahmad me zan dafa maka ?hankali cikin murmushi yace matayassara Ummi ta danyi dry tace inbanda abinka Ahmad gani ga Nenne duk baka tabbayemu abincinba sai itta zaka tabbaya ya dan Sosa qeya yace uhum Ummi ai gwara tun wuri ta koyi kula dani dan nasan Abbbana kam ya bani ita sai dai bansan me baba kuma zai ceba ya dan kalli Nenne yace Nenne inason Aysha inasonta a raina bana iya boye sonta a zuciyata💛 da Zahirina cikin wani yanayi Nenne ta kauda kanta daga kallon dan nata abin qaunarta Tanajin Ahmad tamkar bugun zuciyartane ya matso gabanta ya rusuna yace Nenne banason yadda kikemin in namiki mgnar Aurena da Aysha A hankali ta daura hannunta a tsakiyar kanshi tace Allah ya maka albarka kai da sauran yan uwanka baki daya Amin yace cikin jin didi ya juya ya tf part ensu ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ A harabar gidan ya samu Adam da Amira suna hira cikin nishadi SLM kawai ya musu ya wice ciki a parlor ya tadda Yusuf zaune kan kujera ya miqe qafafunsa kan Center table ya daura laptop enshi kan qafafun yana daukar lacturer ta online Jallabiyace a jikinshi ya gyara gashin kanshi gonin Sha,awa Sai qamshi yake kamar fure cikin qaunar juna suka gaisa da Ahmad ya dan kalleshi yace biyaye ina ka tsaya haka sai yanxu tare muke da Abba ya fada yana cire kayan jikinshi yaci gaba da cewa bari naje Na dan watsa ruwa ya tafi bedroom enshi kai tsaye toilet ya wuce ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ A hankali tai SLM gami da dire tiren abincin kan dining ta juyo cikin sanda ta tsaya saitin kanshi duk a tunaninta Ahmad ne dan komai Nasu iri daya hatta gyaran gashinsu Sam bata gane shine a gunba a hankali ta sunkuyo kanshi tasa bakinta daidai kunneshi ta dan hura issaka ta dan tura yatsunta cikin lallausar gashin kanshi mai qamshin gaske cikin rada tace I love u ya Ahmad tana maici gaba da wasa da gashinshi cikin daqiqa daya ya gano itace ya San ba mai haukannan sai ita a take ji wani malulun baqin ci da takaici duk illahirin tsikar jikinshi sai da ta tashi gaba daya ya harxuqo cikin fushi da zafin nama ya juyo kamar walqiya ta ganshi gabanta tunda ya juyo fuskarsa ta saki qara tana baya jikinta bari yake sosai gaba data ta fiddo idanta woje Ahmad dake toilet da sauri ya dauro towel ya fito cikin xafin nama yana ai dama nasani za,Rina sai ya sata kuka Shikuma Yusuf hannushi har rawa yake cikin daga murya yace zonan bakince baki da nitsuba ba dama inada cikinki yau sai Na babbalaki gutsi gutsi ya fada yana gwada yadda xai ballatan ya daga hannushi zai yarfa mata marinshi mai bala,in zafi da Sauri Ahmad ya shiga tsakaninsu yace cikin salon kar ka daketa yace huce a kaina ninace ta kawimin abinci yasa hannushi ya dan balleta a jikinshi yace tf Aysha sai da safe ko aiko a guje tai cikin gida Amira kam dama tunda taji qaranta tai cikin gida cikin Fushi sosai ya kalli Ahmad da Adam wlh kun isheni kun isheni abin yayi yawa ko kunya bakwaji qatti daku Ku liqewa yara qanana salon Ku jamin raini kallekafa biyaye da girmanka ka wani dauro towel a ququ girjinka duk yana woje yanzu da daurin ya kwance shikenanfa ka kade a gaban qanwar qanwar bayanka den tasoka ko ta rainaka Adam yayi dry sosai Yace toh me a ciki ba shikenan ba tasan German abinda zata aura ba 🍌 shi dai Ahmad shiru yayi sosai Yusuf kuma ke fada yayinda Adam ke qara tunzurashi A qufule yace Wlh Ku daina kiramin su nan in bakusan kunyaba Ni inajin kunya bira girma ya fadi Yaya Yaya ase yayun banzane ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Mambila Yau lahadi tun da sassafe suke shirin komawa cikin Tarawa dan sunyi hutunsu Na qarshen sati gaba dayansu daga kan Adam har zuwa kan Aysha suna zaune kan dining suna karyawa yayinda sukma manyan suna tsakiyar Palon sun da tattaunawa Aysha da Amira ke Serving ensu duk sun xubawa kowa suna tunani ya zasuyiwa Yusuf shi ba ,amai gwaninta Ahmad ne ya dan kalli Aysha cikin mgn da ido ya nuna mata shima ta hadamar tea cikin dan jin tsoronshi ta jawo cup ☕ta zuba mai tea duk hankalinta Na kanshi ta ina zaiyi matsifa Koma taji mari cikin tsoron har ta zuba mai gishiri a madadin sugar a cikin tea en Shi kuma tunda ta fara yake kallon farshen dan qaramin yatsar hannuta Na hagu ta barshi wai ita gayu shi kuma kyamar farce yake a rayuwarsa Ya kalli sadiq dake gefenshi yace kai. Sadiq Kawomin scissors enka toh yace gami da miqewa ya lura Sarai gishiri tasa shiyasa ya jawo cup en ya dan kurba dai dai lkcin Sadiq ya mi qamai ✂ ya karba ya tura mata cup en yace gishir a madadin sugar kasheni kike shirin yi ko toh ke zaki shanye yasa hannushi ya kamo dan yatsar ya dan dannan scissors en da niyar yanke farcen aiko ya hada da kan dan yatsar 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 MI,WASMITI.....page 4⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Gaba dayansu suna cike a porlon cikin shirin komawa Sunyi sit dan bppa Yaya zai musu Nasiha da Addu,a kamar yadda yake musu ko yaushe in sunzo komawa i dan da wani mai buqata ko uzuri ko umurni toh duk a wannan lokacen yake bawa yayanshi damarsu Shiru sukayi cikin maida hankali kanshi Sadiq ne yayi slm tare da shigowa da sauri Aysha ta juyo gunshi cikin harara tace Allah Sadiq ka kawomin kayana ko baka dinkaba ni gsky Na gaji Amira tace gsky kam kaya kusan shekara baka dinkasuba Usman dake gefenshi ya kaleshi a yatsine yace gsky dai Sadiq ka shiga tara tunda Sam baka da cika alqawari duk halayen teloli kai ka hada ga shegen son kudi Kaine dinkin yan mata kaine dinkin samari har Na tsofaffi baka bari.... Innayi ta amshe zance da cewa ai Sadiq kam sai a hankali wlh nima tun bayan sallahn bara Na bashi fatarina ya dinkamin aljihu a jikinsa Na samu gun ajiye yan canji da woyata Amman har yau bai baniba Mixxixx Rabi,u ya ja tsaki sai da duk suka juyo gunshi yace kajifa kaji shirmanta ko ana mgnan kaya masu rai kekuma kina mana mgn bujenki Duk sukayi dry Adam yace tab innayi kawai ya batar miki da fatari . Tab tace aiko sai ya biyani shidai Sadiq sai dry yake Abdul ya kalleshi yace ai ba dry kakeba biyan fatari zakayi Ya dan gyada kanshi ya ajiye wata qatuwar leda yace toh kudai ga naku dan wlh dama nasan su Aysha Anty masifa jiya ko bacci banyiba saida Na gama hada muku ya kalli su Usman yace Yaya Usman kuma ga naku. Abba ya danyi gyaran murya yace toh Ku saurara ai mana Addu,a Bappa Yaya ya rinqa musu nasiha da sanya musu albarka daga qarshe ya musu Addu,a ........ Duk suka fito suka shishshiga mota a hankali Yusuf ya yafito Sadiq da hannushi da sauri ya iso gunshi cikin kulawa yace kai Sadiq anya kuwa kana maida hankali kan kara tunka ? Cikin girmamawa yace sosaima Hamma Yusuf nama kusa try Universityn zariya yace ka dai kula dan naga gaba daya so kake ka zama mai dabi,ar mata shiyasa bansoka da dinkin nanba dan mafi akasari telolin mata da masu daukan photo dabi,ar mata suke dauka haka dai ya dan mai nasiha Suka tfy suna kewar juna ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Yau kusan satinsu 3 kenan da zuwa mambila amma Yusuf bai kuma zuwa ba kuma duk weekend sai sun je yau jumma,a bayan sunyi sallan la.asar duk suna hallare a babban palonsu suna ta hira bb bello ya dan gyaran muraya yace toh Yusuf kunsan gobe Saturday ko dan haka duk Ku shiyarya da wuri dan tfyar sassafe nake son muyi.. Ya dan tura hularsa qeya kadan yace hmm baba nifa ina da taya goben Ummi ta dan kalleshi cikin jin haushi tace wai kai kam wanne iron mutum ne kai Sam bakason shiga yan uwanka kowa mararin zuwa yake Amman banda Kai su kullumu basu da mgn sai taku Amman a fili kake nunawa Baka damu da suba Duk baqin haline hakan da mugun mishkilanci wlh bakaji dadin rayuwarka ba..ta qarishe mgnar cikin fada Nenne ta dan kalleshi tace ina zakaje ne Yusuf ?. Ya dan yamutsa fuska yace Yola zamuje dan tunda nazo bamu jeba gashi har klcin komawata ya fara matsowa Goggo jiyama saida ta kirani tana ta fada bamu jeba Adam ya kalleshi da kyau yace wai kai ban ganeba fa kanata xakuje bakujeba kai dasuwa kenan zaku ? Ya dan harareshi ta wutsiyar ido yace toh da dasuwa nake zuwa ? Atoh nikam bazaniba ban saniba wataqil Ahmad zaije Ya kalleshi a yatsine yace wlh sai kaje dole kaje mutum baison jiharsa ta aihuwa ko kadan Ahmad ya danyi murmushi yace toh Abba mu dai gobe Yola zamu Abba da su Nenne su kace toh Allah ya kaimu lfy ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Haka kuwa akayi Adam badon yaso ba suka tfy Adamawa bayan sallah azahar kada suka isa A hankali Ahmad yayi parking a harabar gidan hydar da Maryam dake qoqarin fitowa da sauri suka qarasa gunsu cikin jin dadin ganinsu hydar ya karbi briefcase en Yusuf da miqamar hannu suka gaisa Maryam ko da sauri ta fada jikin Adam tana welcome ya Adam sai yau kuka zo ya dan subbaci goshinta yace ya zafin garinku tai dry dai dai lkcin da ta fada jikin Ahmad ta dan dago kanta ta kalli shi tace kajifa ya Ahmad wai garinmu wato shikam bandashi murmushi kawai ya iyayi yana dan tureta daga jikinshi dan wani mugun Abu yaji yana yawo a jinshi abinda bai tabajiba dan ya runqumi su Amira ga kuma Yusuf dake ta watsa musu harara A hankali ta nufi jikin Yusuf tana Hamma Yusuf yaus..... Da sauri ya katseta ta hanyar daga mata hannu da murtuqe fuskarsa tamkar sojan dake filin daga Atake tasha jinin jikinta *********** Bayan sun gaggaisa gogga ta cika musu abinci a gabansu suna ci suna dan hira ba laifi yau yadan sake Amman dai baici Abinciba har baba Umar ya dawo ya jasu palonshi sukai ta hira yana musu da nasiha ya kallesu da kyau cikin qaunar yaran nasu yace Ahmad kunci abinci kuwa ? Alhamdulillah baba munci mukam Amman biyaye baiciba ya fada yana nuna shi OK yace ya kwallawa Maryam kira yace ta kawo mishi abinci .. da kanshi ya zuba mishi ya bashi yana maza cinye banason dabi,arkannan ta zama da yunwa da gyar ya danci kadan ya kalli Goggo yace Goggo nonofa mai dan sanyi tana dry ta dauko mar mai sanyin gsky toh nanne ya danci Haka sukai ta hira kashe gari suka dan zaga dangin babansu Adam Da a zahar suka kama hanya sai jaligo ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Aysha kam tunda tasan yana dan zaman palon ta daina fita da zaran tasan yana gun bata fita duk da bawai mgnarsa take jiba qamshin turarensa ke fadamata yana palon Dan gudun bala,inshi da duka Yau tunda safe suke ta dan girke girken dan yau babban soja xai diro daga Abuja ya Abubakar kenan sosai take farincikin zuwansa dan yana gwada mata kauna ta haqiqa Qarfe 2 dai dai ya dira a babban palonsu tana tsaye gefen dining area tana ta shirya mai abinci Sam bata lura tare suka shigoba da qarfi tasa dan qara ta fada jikinshi yako tallabota yana dan juyawa da ita a tsakiyar palon sai dry take sosai tana miss U ya Abubakar juyi yake da ita sosai tana maqale a jikinshi Ahmad dake gefensu farinci yake sosai a ransa ganin ayshansa Na cikin happy aduniya duk abinda zai sata farinciki to shima zai sashi farin cikin Muje zuwa masu karatu aiki Na gaba Na Gode da kulawarku da qaunarku gareni Nina kuna raina 😍😘 MI,WASMITI.....Page 6⃣ Na Aysha Ali Garkuwa🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Da garfi ta saki qara gami da fizge hannunta dan azabar da ya ratsata jini kuma a take ya rinqa tsirtowa abinka da farar fata gata da laushi kamar auduga kuka take sosai tana yarfa hannun tana bubbuga qafafunta a qasa Ahmad kam tuni ya kamo ta ya riqo hannu yana matse kan dan yatsar da niyar tsaida jinin amman abin yaqi Adam ya jawo handkerchief en Yusuf dake kan cinyarsa da sauri ya yagi gefen handk en ya kamo hannu ya daure kan dan yatsar Amman ina jinin zuba yake Abubakar kam da Ahmad tamkar a jikinsu jinin ke zuba kuka take sosai jin kukan yasa Ummi da Nenne suka shigo a tare da sauri sukayi gunta tana lafe jikin Ahmad cikin mmki Nenne tace kai Ahmad meya yankata haka shiru yayi yana girgiza kai yana damqe da hannun ba abinda yake furtawa sai sorry Aysha cikin jin takaici da tausayinta a hatsele Ummi ta buga musu tsawa kai ana muku mgn duk kunyi shiru ke Aysha waya miki muguntarnan dan ita tuni tasan mai aikata aikin dan duk suna zagaye da ita suna ta tausarta shiko oga ko a jikinshi ko inda suke bai kai idonsaba kamar baya gun kanshi a sunkuye yana ta danne danne a phone enshi ga cup en coffee a gabanshi yana dan Sha Ummi ta sake daka musu tsawa tace wai kuna jinmu kunyi shiru Rabi,u ya dan kalleshi yaga a sunkuye yake ya maida dubanshi gun su Ummi gamida gyaran murya ya dan dunqule hannushi ya miqar da dan babban yatsarshi ya nuna Yusuf in gamida dan musu alama shine yana gedawa Ummi kai da dan furta haaa Nenne tace toh Koma waye yanzu dai kai Yusuf zoka San yadda zakayi ka tsaida jinin kanshi a qasa yace Nenne ni kuma ? Ummi ta jinjina kai tace a a ba kaiba wani mugun da ban da ya yanketa wlh ka kiyayeni ka fita harka yarinyar nan dan banga me ta tsare maka ba tunda kai zuciyar dutse Allah ya maka baka da qaunar yar uwarka bare tausayi kullum sai mugunta fada sosai takeyi Shiru yayi zuciyarshi najin zafin yarinyar da tsananta a ranshi shi kullum a kanta sai ranshi ya baci cikin jin takaici ya shiga dakin innayi ya fito rike da kwalbar turare da qarfi ya fizqo hannu ya matse ya danna bakin kwalbar fesss ya fesa cikin yankan Da qarfi ta saki qara dan jin yadda azabar zafin ke ratsa jikinta har cikin zuciyarta sosai ta qanqame ya Abubakar tana wayyo Ummi ya qasheni ya Ahmad zafi nakeji gaba daya hannu sai bari yake Ahmad ya zagaya ya kamo hannun yana huramata iskar bakinshi mai sanyi yana dan shafa kanta Abubakar kuma yana dan buga bayanta a haka dai jinnin kam ya tsaya sai ajiyar zuciya take ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Gaba daya porlon sunyi shiru suna sauraron Bappa Yaya A hankali yayi gyaran murya ya dan jinjina kanshi irin Na manyan mutane ya kalli yayan nashi daya bayan daya cikin muryar gsky da gsky ya kalli baba bello yace bello mgnarmu akan yarannan lokaci yayi da ya kamata ace duk mai shirin aure ai masa Sam banji dadin ganinsu a haka kun xuba musu ido suna abinda sukaga dama ya dan yi shiru sannan ya kalli Aliyu yace Aliyu inason mako mai zuwa Umar yazo da qanwarku Aysha dan insha Allah zamu San matakin da zamu dauka akan abin cikin girmamawa yace to Bappa insha Allah zan kirashi Juyawa yayi gunsu Ahmad cikin yanayin tabbaya yace kai Adamu kai ka fidda matar aureko ? Ehh ya bashi amsa yana mai nuna Amira yana ko dai baza ka ban ita bane a a Na isa nine mai badasu oho nasani ko zaka gwada ikonka.. Dudabe ya kira Yusuf ya dago cikin jin haushi yace meye kuma ? Ehh akwai batun aure fatan ka shirya dan bazaka bar qasannanba saida matar aurenka uhum kawai yace dan yasan tsohonnan da iya kalen fitina shi kuma Bappa Yaya cewa yake wlh kunji kunya kune manya kan Abubakar Amman gashi dayin aurensa shekata 2 kenan da da saurin rabo da har an samu qaruwa Ahmad ya danyi murmushi yace toh ai shikenan muma zamuyi yanzu kam cikin kallon Ahmad din yace shiyasa Na yarda da kai Ahmad kai mutum ne sosai Na tabbata bazamu samu matsala da kaiba shisa matarka ta musammance Adam ya dan kalleshi yace mukuma ba mutane bane ko eh ai Ku kam gwara ma kai akan sarkin fadannan kam ya nuna Yusuf haka dai yaitawa zuriyarsa addu,a da fatan Allah ya maidasu lfy har bakin gate ya rekasu ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Tun daga bakin qofa yakejiyo hayaniyarsu duk sun cika gidan da sowa a hankali yayi slm ya shiga pictures suke ta dauka dasu Ahmad da Adam Abubakar kam duk ya gama biye musu sosai suke ta dauka harda kaka da ta zo yanxu Usman shike daukarsu harda nunamusu yadda zasuyi cikin mmki yake klnon yadda yake tawani lonqwosa kamar mace Aysha fake tsaye tsakanin Ahmad da Abbakar duk sun dan sunkuyo Suna kallonta suna murmusawa itako ta dan dago kanta tayi kalan shogoba da sakalci Ahmad yasa hannushi ya dan tallabo fuskarta good Usman yace kunyi kyau ya daukesu ahankali ya karisa tsakiyar palon duk da baya ta bashi qamshi turarenshi ya sheda mata ya shigo dan haka ba tare da sun juyaba sukayi cikin wani parlon da sauri Kaka ta kalleshi cikin tsokana tace toh fa watsa taro duk ka watsasu ya dayamutsa fuska lokacin da yauzauna gefenta Ahmad da Adam suka sashi tsakiya Usman ya kallesu sunyi ras dasu gwanin Sha,awa ya dan kalli Yusuf a marairaice yace plss Hamma Yusuf bari Na daukeku daya wlh kunyi kyau harara ya watsa masa kaka tace Abubakar maza karbi ka daukesu ai shi photo tarihine wataran zaka tuna da dan uwanka Camera ya karba ya rinqa daukarsu duk motsin da sukayi sosai sukayi kyau kamarsu ta fito Sak da Sak suyi tamkar taurari kaka ta kallesu tace toh ko kufa ya dan yamutsa fuska yace kai nifa banson fitina da surutu ke Sam bakya iya shiru eh din nayi surutun bakinka ko nawa haka dai suka wini hira su Nenne Na musu dry Sam shi Yusuf da kaka in sun hadu sai fada ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Yau asabar tun da safe suke ta shirin tafiya mambila su Goggo Aysha kam da su hydar da Maryam da maigidanta baba umar tun jiya jumma'a suka wuce mambila ?🍇🍇 MI,WASMITI.....page 7⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Gaba dayansu kusan a porlon suka wuni sunata hirar zumunci sukuma su bappa Yaya da 'yayashi da surkinshi suna can parlonshi Na mu samman suna ta tattauna mgnarsu ta mu samman Tafe suke bayan sun fito masallaci yin sallan la.asar har sun danyi cikin gida Adam ya kallesu cikin raha yace biyaye muje cikin rafi mana mu dan Duba yanayin wajan Ahmad ya dan kalli Yusuf yce biyaye zamuje ? Kai ya dan gyada mai alamar bazashiba wlh sai kaje mutum kamar mai iska in kai kadaine ai kullum sai kaje amman dayake kaga su Rabi,u ma zasu sai ka wani ce bazaka ba cewar Adam kenan usman ya dan kallisu cikin salonsa Na dan rigima yace toh fili da fadi ai ba saimun zo gunkuba.. Haka dai suka jashi suka tfi ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Rafine babba mai dubbin sirrai da qworamai ga duhuwa da qamshin furanni ga wani sanyi mai sanyaya zuciyar dan Adam ga yanayin shauqi da tsuma zuqatan masoya wurine mai dubbin tarihi tun na iyaye da kakanni suna kiran wurin da funa rafi Suna shiga duk suka watse cikin rafin kowa da abinda yake buqata Yusuf mutum ne mai son yananin sanyi da qamshi wurin Na tsuma zuciyarsa gaban wani qwarama mai ruwan garai garai qarqashin sirran bishiyiyin ayaba ga qatuwar bishiyar bangoro da wata bishiyar kashu da jijiyoyintama cikin tabkin suke ninqaya ga kukan tsuntsaye masu kama da sautin sarewa a hankali ya taka ya qarisa kan daya daga cikin kuyerun da aka jera a wurin masu dan tsawo Wanda sunfi kama Dana kwanciya 🌳 A hankili ya kwanta tare da yin wata sassanyar ajiyar zuciya gamida lumshe idanshi duk Wanda ya ganshi yasan yana cikin nishadi Cikin yanayin tsokana Adam ya dan yafito Ahmad ya nunashi da ido yace shi dai har abada haka yake son kasan cewa ba kowa kusa dashi ya lumshe ido kome yake gani ranine.? sai Allah Ahmad ya bashi amsa yana dan murmusawa cikin shauqi ya fara zagaya wurin yana dan ciren yayan itatuwan cikin zuciyarshi Aysha ce ke yawo phone📱enshi ya zaro gami da kiranta bugu daya ta daga Cikin muryar tsantsar qaunar Ya Ahmad dinta take mgn jin muryarta da shauqi ya jingina jikin bishiyar 🌳 hadi da lumshe ido cikin sanyin murya yace Aysha kina ina ? . Ta dan qara magalewa jikin innayi ta danyi ajiyar zuciya tace Ya Ahmad gani a kan gadon innayi Cikin sanyi ya fesa munfashi yace toh kizo lambu gani ina jiranki Toh tace gamida da cewa ya Ahmad ta wanne gefen kake ? Bakin gwaramannan ya bata amsa Aiko cikin zumudi ta figi mayafinta ko Amira da Maryam bata nemaba ta fita da Sauri sauri ta nufi rafin Ahmad ya nufi gun kenan yaci karo da hydar da sauri ya miqa mai phone enshi yana ya Ahmad Abba Na nemanka tun dazu yake kiranka layinka bai Shiga shine yace Na kawo ma Da sauri ya kara phone en a kunne 📱👂🏻cikin biyeyya ya ke mgn toh Abba ganinan zuwa ehh yanzu zanzo cikin sauri ya katse kiran ya miqawa hydar phone en ya nufi gun su Yusuf fuskarsa dauke da murmushi yace biyaye ni Abba Na kirana ZAmu tf bakin kogi gun dabbabi 🐄🐪 da sauri Adam ya miqe yana muje Nima xani har sundayi nisa Ahmad ya dawo ya dan kalli Yusuf yace biyaye kai bazaka jebane ? Kai ya gyada mai alamar bazashi ba Adam yace kai da Allah zo mu tf ai kasanshi ba zuwa zaiyiba ya fada yana hararanshi shi ko sarkin hali ko idanshi bai budeba da sauri suka tf abinsu ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Tunda ta shigo cikin rafin sanyin iskar da qamshin furannin suke ratsata ta lumshe idanta hadi da ware hannayenta tana tfy cikin rausaya tana shaqar qamshi kai tsaye gun da ya Ahmad dinta ya gayamata ta nufa tana dan ratsewa shuke shuken har ta qarisa wajen duk idanta a rufe cikin nitsuwa take dan tsallaka kujerun a nufinta zataje bakin ruwan ta zauna aiko a hankali qafarta ta dan zame zata antaya cikin ruwan da sauri ta ja qafar baya tana shirin juyowa taji ta afka kan kujerun Yusuf dake kwance a rigingine idanshi a rufe ba abinda yaji sai fadawar mutum a kan faffadan girjinshi cikin mmk da sauri ya ware idanshi gami da dan yunqurawa zai tashi Ita kam tun da ta fadi cikin razana ta yunqura sai tajita jikin mutum da sauri cikin fara.a tace ya Ahmad yau kam Dana karye ta dan saki murmushi gami da dan manna fuskarta kan girjinshi ta zagaya hannuta ta bayanshi duk abinnan da take idanta a rude Shiko cikin takaici da jin haushinta ya ware manyan idanunshi kan fuskarta cikin fushi da takaici ya danna mata tsawa keeee Baki da hankali ko jin muryar dodonta cikin tsoro ta bude idanta dan tsawace mai rikita mutum ya sakarmata har sai da cikin rafin ya dauki sautishin da sauri ta yunqura dan ta tashi bata gama firgicin tsawarba taji wani irin axabebben mari daya yarfa mata cikin jin zafi tasaki qara aiko ya miqe cikin zafin nama ya rinqa zuba mata Maruka tun tana tsaye har ta fadi qasa nanko yasa qafarsa ya rinqa bol da ita tana kuka tana wayyo Hamma Yusuf dan Allah kayi haqri wlh ban saniba ne plss Na tuba su hydar dake can gefen bishiyoyin goiba da sauri suka nufi gun amman suna zuwa ganin Hamma Yusuf ne ke tabkarta yasa gaba daya suka tsaya hydar ya kallesu cikn jin takaicin Yusuf yace wai me ya tsaiya daku ? Rabi,u yace tab wazai qarisa wannan mugun yahada dashi shi dama in dai baiyi dukaba baya jin dadi cikin jin tausayin ta ya Shiga tsakaninsu ya sunkuya ya dagota ya dan juyo badan ya soba sai dan kar Yusuf yace ya rainashi yace dan Allah kayi haquri Hamma Yusuf Cikin fushi da murtuqe fuska yace maza Ku bacemin da ganan aiko da sauri ya jata suka tf ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Abinka da farar fata tuni fuskarta ta kumbura tayi jawur ga wani azabebben zazzabi daya rufeta tun kafinnsu isa gida jikinta sai bari yake tab aiko Ummi kam ta hatsala fada take tamkar zata aro baki har zuwa bayan maggariba fada take sosai Nenne sai bata haquri take amma ina fada take har su Abba da Ahmad suka shigo gida yayinda bba bello da Yusuf ke binsu a baya . Yan uwana musulmai ina barar addu,arku ga dan uwana ya Abubakar Wanda Allah ya mai rasuwa ya Allah ya jiqanshi da rahama 👏🏻😭😭😭 🍇🍇🍇 MI,WASMITI.....page 9 Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 🙏🏻Bayan ya bude taron da addu,a ya dan yi gyaran murya ya jinjina kanshi jikin kushin ya dan kalli illahirin Family enshi din haqiqa shi da kanshi yanajin nauyin furicin da zaiyi zuciyarshi Na samun rauni idan ya kalli idanu jikokin nashi yana samun fargaba sosai yanajin tsoron kar yau ta kasance ranar nadama ko ranar baqin ciki ko ranar daukewar farin cikin wani sashi daga cikin sashikan zuriyar tasa jikin jinjina kai ya dan dago kanshi Ya dan zuba musu ido gaba daya a hankali ya danyi gyaran murya ya bude baki cikin sanyin lafazi da taushin baki yace Bello da kai da sauran qannan ka da matanku da qanwarku da maigidanta da dan uwana da iyayenku mata Yau gashi mu dukkanmu Allah ya kawomu wannan rana da muke fatan isar da wani alqawari da muka dauka idan Allah ya nufa yai shiru ya dan zuba musu ido sukuma yara daga kan Adam har xuwa kan Aysha ido suka zuba musu cikin yanayi tabbayar wanne alqawarine wannan Ahmad tun wayewar garin bugun zuciyarsa ta zarce tunaninshi sai yanxu yaji abin Na sauqa shiko Adam kallon kakan nasu yayi cikin dan zaquwa yace gsky mu bama son Jan rai kana mgn kana jinkirtawa da sauri baba Umar ya daga mai hannu alamar ba batun wasa ganin haka yasa gaba daya sukayi shiru sai yusuf shi dama baiyi mgn ba asalima kanshi a sunkuye yake Aysha da ke dan manne jikin innayi ta maida kanta tai lamo yayinda Amira ke gefen Adam maryam kuma Na jikin Nenne duk suka maida hankalinsu kan Bappa yayan a hankali yaci gaba da cewa Ahmad Bai Amsaba sai ido daya zuba mai bugun zuciyarsa Na tsananta 💗Ahmad ya kuma kiransa da gyar ya iya amsawa Na,am jin yadda sautin muryar Ahmad din ta fito yasa Yusuf da Aysha dagowa a tare suna klonshi sai yanxu su duka sukaji wani baqon yanayi ya darsu kan zuqatansu sautin muryar kakan Nasu ya katse musu Al,amarin yana mai cewa Ahmad A kullum duk zuriyarmu tana alfahari da kai haqiqa Na tabbata kai mutum ne mai cikir haiba da nazartan hilin da ake ciki Ahmad ina alfahari da kai a zuriya ta Na tabbata kai dayane mai fahimtar kalemen mutum duk kaushinsu da dacinsu Tun kana yaro baka taba kaucewa Umurnin iyayenka ba ko yaushe kai mai biyeyyane a garemu Baki daya shiru ya dan kumayi yayinda duk parlon sukayi sit Yanayin Ahmad kuma yafi kama da wanda tsoro ya cika zuciyarsa sukuma iyayensu gaba daya sada kansu qasa sukayi Cikin qarfin hali yaci gaba da cewa Ahmad a yau Alfarmanka nake nema kuma da yafiyarka dani da iyayenku baki daya Ahmad muna masu tausar zuciyarka muna kuma buqatar haquri daga gareka Cikin rashin fahimta yace bappa yaya ni kuma muryarsa har rawa take yaci gaba da cewa ya isa tunda tun forko kace iyayena toh mgna ta kare ba wani neman alfarma tsakaninmu a hankili ya daga kanshi ya kalli qanin mahaifinshi yace Abba ni dai ni din Abba me kuke buqata a gareni da har kuke ban haquri ni Ahmad danku meye rage da baku minba a duniyarnan 🌍 ya maida dubanshi gun mahaifinshi da mahaifi yarshi yace baba da Nenne kun gama min komai Nenne am Na Dade ina Neman abin da kike buqata in miki a duniyar nan da kema zakiji bakiyi asarar yaranki da suka rasuba cikin 'yaya 12 da kika aifa sai mu 3 Allah ya bar miki Nenne ni Ahmad ki gayamin meye buqatarku yaku iyayena ya qarishe mgnar Yana mai zubda qwallah😭 ya dan kalli kakanshi yace bappa Yaya gayamin meye buqatarku ko zanji sauqin abinda ka dauramin haqiqa zuciyata ta soku 💘in dai bazaku sani Abu kai tsayeba sai kunce kuna Neman alfarma Ahankili Abba ya daura hannushi kan tsakiyar kanshi cikin wata iriyar murya yace Ahmad Allah yamaka albarka ubangiji ya jibanci Al,amuranka Cikin muryar kuka nenne tace Amin yusuf kam tuni zuciyarsa ta fara tafasa ganin hawayen biyayenshi Aysha ko kuka takeyi sosai innayi Na tausarta Gyaran murya yayi yace Ahmad alfarman da muke nema a gareka batun Aurenka da Aysha sai kuna ya sunkuyar da kanshi ganin yadda gaba dayansu jikokin nasa suka zuba mai ido Haqiqa yusuf yasan wannan zaman kalen fitinane shiyasa ya dago kai fuska a murtuqe yace dan Allah kai mgn kana gasamin zuciya da maganganunka da suke Sa dan uwana zubda qwallah Ayijar zuciya ya danyi Yace Ahmad batun aurenka da Aysha babushi dan ita Aysha tana da mijin 😳😳😳 Cikin razana da fargaba da bugawar zuciya ya katse shi da meyasa ? Waye mijin tadin ? A ina yake ? Hannunshi Na dafe da qirjinshi yake wadannan tabbayoyin a take sukar zuciyarsa ta tsananta wani nauyi ya danni maqoshinsa Zufa ta fara ketomai tsoro mai tsanani ya rufeshi har cikin hanjinshi yake jin sanyi Na ratsashi Itako Aysha tunda taja wani numfashi sai ta zama mutum mutumi a zaune sai barin da jikinta keyi cikin mmk abin yusuf yace ai wannan mgnar hogice wayeshi da za,a hana dan uwana farin cikinshi akan wani can banxa tun tana qarama yake wahala da ita wlh ni dinnan a matsayina Na yayanta ni zan aurar da ita ga dan uwana Adam ya dan kalli Bappa Yaya a fakaice yace cikin yanayin kaji tsohonnan da zance shirme ai wanan ba huruminka bane sai ka bari iayenmu suyi ikonsu a kanmu Allah sarki Ahmad duk sun rikice sabida bidar farin cikinsa dama Ku hausawa kunce nagari Na kowa Su Usman ma duk sunyi zurui Abdul mai saurin kuka shikam da Sadiq kuka suke sosai Rabi,u kuma sai kada kanshi yake a hankali yace (nayeku Na ko jibare ) tsufa ko rikicewa ne Baba bello ne ya dan rinqa musu fada cikin qarfin hali yana sabida me zaku samu a gaba kuna kuka ko ance muku mutuwa akayi da gyar dai suka dan tsaqaita sai yanxu Bappa Yaya yaci gaba yace Ahmad tabbayoyinka harsunmin yawa duk da dai zan amsa ma ka su yanxu wasu kuma sai wataran zakuji amsar sai batun aurenka da Aysha babu shi domin kuwa ita tana da miji Amman duk da haka ba hanaka sure za,ayiba tunda an dakatar dakai kan Aysha haka nan kuma an mayarma ka da yar uwarka Maryam a madadinta Sai yaxu Usman yace toh wai waye ne wannan da za,abashi Aysha a hana ya Ahmad ita ? Yusuf ne shine mijinta shine Abokin rayuwarta shine tsohon alqawarin zuriyar nan ya basu amsa daram duumm ras ras zuqatansu suka rinqa amsawa cikin firgici da razana ta dago kanta a take zufa ta keto mata bakinta har rawa yake tana waye kace? dan uwanki yusuf nake nufi Adam ido ya zazzaro waje cikin dimuwa yace (hey ado andi ko a yeccata bo) kai Kasan abinda kace kuwa shiru yayi bai bashi amsaba 😭💗😱 Cikin dimuwa da fargaba Ahmad ya dan ja guiwarsa ya qarisa gun Abba hannushi ya daura kan guiwowinshi ya dago kanshi ya zuba mai ido cikin wani can ji da muryarsa tasamu yace Abba gskanta min furucin mahaifinku shin zancenci gsky ne ya kuma batun haramcin auren nasu Abba ko ya mantane Aysha da yusuf uwa daya uba dayane ? Abba matuqar ka gskan tamin toh nayi alqari koda zan rasa raina nane Da sauri yusuf ya qarisa gunda yake yasa tafin hannushi ya rufe bakinshi Toh masu karatu Ku biyoni muji wannan wanne irin rikitaccen Al,amarine wannan sarqakiya ya zata kaya 🍇🍇 MI,WASMITI.....page 8⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Da sauri Ahmad ya qarisa kan kujerar da take zaune zama yayi daf da ita yana klon fuskarta cikin yanayin damuwa da tabbaya hannushi daya yasa yana shafa fuskarta da tayi jawur yayinda ta dan manne jikinta da nashi tasa hannuta daya ta sankalo hannushi ta daura dayan kuma kan hanun nashi ta dan ranqwafar da kanta kan damtsenshi Cikin zaquwa yace Ummi meya sameta ? Cikin fushi da jin haushi Ummi ta nuna Yusuf dake zaune can gefe kan dining table ai kasani Ahmad ba mai salon muguntar nan sai shi din shugaban mugaye ko yaushe mutum bai da aiki sai cin zali nan taci gaba da fadan kamar forko qara matsowa kusa dashi tayi cikin fada tace wlh ina gaya maka ka fita harkar yaranan idan duka kake son yi toh dole sai ka haqura sai randa ka haifi naka 'yayan amma bamu zaka yi ta dakawa yaraba daga yau sai yau ko mugun klo ka kuma yiwa yarannan ranka zai baci Sosai Ummi take mai fada gaba daya shi kam ya gama cika yadda take mai tsababi a gaban qannenshi kanshi ya. Sunkuyar duk da hali irin Na Yusuf baison bacin ran iyayenshi baison yaga ransu Na baci a kanshi cikin yanayinshi dayafi kama da baya son mgnan ya kalli Ummi a hankali ya bude bakinshi yace dan Allah kiyi haquri Ummi daga nan bai kuma mgn ba Ahmad kuma dake klonsu duk ya fahinci abinda ya fada da kuma abinda ke zuciyar sa💛ya tabbata tsanar Aysha fadannan ya qara mai shiyasa bai fiye son ana mai fada a kan lmrin taba Hankilin shi ya mayar kan Abba da yayi shiru ya zuba mai ido cikin ta kaici ya bude baki kamar maiyin fada sai kuma yace Yusuf am Allah ya shir yeka ya tausasa maka zcyar ka 💛 yasa maka qaunar yan uwanka Allah sarki Abba shi bai iya fada da mugun baki ba a rayuwarsa shiyasa komai lamarinsa yafi tfya da Ahmad Borkono 🌶sai Baba bello gaba daya halin Yusuf halin wan mahaifinshi ya dauka bba bello shiyasa duk bala insu da masifarsu su suna shiri da juna lkta da dama ganin Abba da Ahmad suke a matsayin su kamar basu damu da raini ko wani abu ma kamanci shiba Shiyasa kuma ba komai Yusuf keyiba bba bello zai fadaba sai dai ya zuba musu ido yana dan fara,a Bayan sun kam mala cin abinci kamar yadda suka saba in sunzo mambila duk haduwa suke a parlon aita hira Yanzuma duk suna ta hira sai Yusuf da Adam da suka fita yayinda Ahmad kuma yau jinya yake tuquru duk ya susuce a kan abar qaunarsa itako sai zuba shogoba da sakalci take tun dazu yake ta faman lallaba mata koda tea ne ta dan Sha taqi ya dan kalleta cikin jin tausayin ta yace plss Aysha tashi ki dan Sha ko kadanne a hankali ta qara male hannushi tai rau rau da ido cikin sanyi mirya tace ya Ahmad ni ya isheni bana jin yunwa hannushi daya ta kamo ta daura kan wuyanta tace kaji jikina fa zazzabi nakeji Jikin kam yayi zafi sosai shiyasa da sauri ya miqe ya dan debo ruwa a dan roba da dan qaramin towel a hannishi ya dawo gun ya zauna ya dan kamo hannuta ya zaunar Daidai lkcin su Adam suka shigo Adam ya kallesu da kyau yace sannu da qoqari biyaye Usman dake gefensu tun dazu yake binsu da ido ya dan ja tsaki ya juya kanshi yana wlh ya Ahmad yarinyar nan tama rainaka kai kuma sai wani biye mata kake Rabi.u ya dan harareta yace ai ni nafijin haushin me biye matan ai wlh ba mgnin ta sai Hamma Yusuf Bki ta dan tura gami da dan hararsu tace ehdin Da sauri ya dan juyo gunta gami da watsa mata harara cikin murtuqe fuska yace (hey Ummuh hado moi on qworgima hado de a tonta ta amin ) ke tashi daga nan waye Sa,anki anan da kike bamu amsa Cikin dan jin haushi da tsanarsa ta miqe tana klon Ahmad hannuta ya kamo ya ranqwafar da ita yace biyaye (anon on wari tawi amin hado mai ko ?) Ku kukaxo kuka samemi a nan din ko ?_toh dan haka kuyi gaba .. Dry Adam yayi yaja hannun Yusuf yace (en dillu) mu tafi suka tafi suma su Usman tfya part ensu sukayi Shiko sai da ya samu ta danyi bacci ya zame hannushi ya dan gyara mata gashin kanta ya dan shafa kan kuncinta da yasha maruka yayi jawur ya dan kalli Ummi da Nenne da suke dan hirarsu qasa qasa yace Ummi tayi bacci ya dan qarisa gun Nenne yace Nenne am (sai fajira ) good Night Nenne Na ya juya ya tf Murmushi tayi tana jin dadin yadda dan nata gudan jininta yake gwada mata qauna sosai ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Yau Sunday kuma yaune zasu Koma cikin taraba su baba Umar kuma gobe zasu nufi Yola tun wayewar garin ranan Bappa Yaya da yaranshi da matanshi da qaninshi gaba dayansu suke babban parlonshi suna ta tattaunawa Su Nenne kuma Suna ta shirinsu yayinda su hydar da Usman suka tfi cikin rafi Adam kuma da Amira gidan kawun amiran suka tf sai Ahmad dake kula da Aysha Suna parlon su Ummi nata xirga zirgansu a hankili ta kirashi Ya Ahmad cikin kulawa yace Na,am Aysha meke faruwa ? Ta da sunkuyar da kanta tace ya Ahmad wai pisa bilillahi me nayiwa Hamma Yusuf ne ya tsaneni haka ?har baya iya boye qiyeyyata kowa Na sona Amman bandashi meyasa ne Murmushi ya danyi mai dan sauti yace Aysha ina kika tabajin dan uwa ya tsani yar uwansa biyaye yana sonki shi dai kawai haka halinshi yake yana da mishkilanci kuma baison raini Da sauri ta kallishi gamida sake hannishi ya Ahmad kenan ni Na rainashi ne ? Dry ya danyi ta kuma dan kauda kanta ta dan tura baki tace wlh ai dama Na ganeka ya Ahmad wlh kafi son Hamma Yusuf a kaina kai akan kowama ko yayi laifi baka gani kuma ka sani sarai ( o kallu do ) shi mugune bai da tausayi Shirun da taji yayine yasa ta dago ta kalleshi ita ya zubawa ido cikin wani yanayi duk yanayinshi ya sauya a hankali yake dan girgiza kanshi ya maida bayanshi ya jingina jikin kjra ya dan lumshe idanunshi da sukayi jaa cikin sanyin murya yace Yusuf da Ahmad da Adam wasu abune guda 3 da Allah ya halitta wadanda suka kasance tamkar hanta da jini a jikin juna farin cikin daya cikin mu 3 dinnan ya wada cemu yayinda bakin cikin daya zai mana illah a zuqatan mu 💘 baki daya rayuwarmu zata kasance ne tamkar taurarin nan guda 3 da suke nuna alamun lkci Aysha ina son yan uwana bana taba jurar baqar mgn a kansu haqiqa ina son yusuf amma duk da hakan shi yafi sona yusuf da Adam jinina ne ya dan tsaya ya bude idanshi ya zuba matasu itama din gaba daya shi ta warema NATA idan da sukafi kama Dana maijin bacci a zahiri ta ga gskyar abin da yake fada a kwayar idanshi a hankili ta nuna kanta tace ya Ahmad harni bankai Hamma Yusuf a zuciyar kaba ? kai ya girgiza yaci gaba da cewa shi Yusuf da Adam jininane su ke kuma bugugun zuciya tace 💗💘 tabbas in babuke toh ba Ahmad cikn wani irin sauti yace Aeeeshahhh ni da kaina bansan wane irin so nake miki ba Aysha sonki a zuciyata babban sukane 💘 Na tabba ta in ance babu ke a a cikinta to bani a duniya 🌍 jawota yayi ya manna kanta kan girjinshi yace kinji bugun zcyta toh duk numfashin da zan shaqa a duniya da qaunarki nake shqarsa a hankali tayi sassanyar ajiyar zucya tace ya Ahmad har abada ZAMU kasance tare A haka sukayi ta jaddawa juna son da qaunat da sukewa junansu har su yusuf da Adam dasu hydar suka dawo ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Banyan sunyi sallan LA,asar duk suka hallara a parlon da shirinsu Na tfy kamar yadda suka saba komai Na zuriyarsu a daidai wanan lkcin suke tsara komai da duk wani hukunci ko umurni da zasu bayar a zuriyar tasu toh hakama yanxu duk sun nitsu dan jin ta bakin Bappa yayan Nima kaina Aysha Ali Garkuwa Na nitsu sosai dan Na tabbata yanxune ZAmU ciga cikin lbr ?🍇 MI,WASMITI....page 🔟 Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Hannushi Na kan bakinshi ya dago kanshi ya rinqa girgiza mai kai da zuba mai manyan idanunshi da suka qanqance sukayi jawur Shi kuma sai dafe hannushi yayi a qahon qrjinshi a hankali ya ciro hannushi daya ya zame hannun yusuf daga rufe mai baki da yayi ido yusuf din ya zuba mai cikin jin ta kaici yace haba biyaye meye amfanin furucinnan ina tunanin ka ya tfi me amfanin yarintarka shin kai yarda kayi da ( talol ) tasuniyar Bappa Yaya ya za ayi kwanyarka Na aiki kake bin shirmen qoqolwar tsohon da ya gama birkicewa kai ka gaskanta zancenshi ya dan dakata ya dan kalli iyayenshi cikin yanayin bada shawara da dan rusuna kai yace bba bello tun tini nake CE muku ku rinqa kula da yanayin zantu kan mahaifinku amma sai kuke ganin Sherri nake mishi to ai yau kunji kun kuma gani kuma ya muku ta yadda dole ku yarda tabbas ni nasan tsufa ta birkita tunaninshi zancen gsky ku kaishi likitan sakatiri ya dubashi............ Baba Hamisu ya daga mai hannu da sauri yayinda yake mai donqolo yace kai yusuf ya isa haka mahaifin namu a gabanmu kake cewa ya zauce Kai ya daga ya kalli baba bello ya kirashi cikin Neman qarin bayani yace wai baba ku kun yarda lfyarsa lau kun kuwa ji abinda yace ko a lbrin films da novels kun taba jin inda yan uwa uwa daya uba daya sukayi aure kun tabaji ? Ya qarishe mgn cikin tabbaya yaci gaba da cewa toh haqiqa wannan al.amari yana Neman wani duhu da zai kawo cikin wannan zuriya tamu Abba ne ya dakatar dashi da cewa ba kai muke sauraro ba kuma ba hukuncinka muke jiraba dole tsarin mahaifinmu xamu bi Cikin sauri Usman yace Abba koda ya sabawa sheriyarmu ta musulunci ? Baba bello ne ya katseshi ba tare da ya bari Abba ya bashi amsaba Shikam Ahmad tamkar robot ya zama Cikin yanayin jimami Abba ya dafa kafadar Ahmad ya dan sun kuyo ya kalleshi cikin sanyin jiki da murya yace eh Ahmad Aysha tana da miji kuma yusuf shine mijinta kai kuma a madadin family enmu gaba daya ina mai baka hqri ha kazalika ni Na zabarma matar aurenka Ahmad Na zabama Maryam yar uwarka mu kuma yar qanwarmu Ido kawai ya zuba musu sai duk mai mgn ya bishi da ido ya rasa me qoqolwarsa ke tunawa ya manta meye farin cikin rayuwa ga wani azabebben nauyi da ya tokari qahon qirjinshi da maqoshisa tunani yake ko mafarkine abba ne ya kuma katseshi da kiranshi cikin yanayin Neman alfarma Ahmad ya zuba mai ido ba tare daya amsaba yaci gaba da cewa Ahmad ka amince zaka Auri yar uwarka Maryam ka amince ka haqura da Aysha ido ya qurawa Bappa Yaya a zahirin ranshi baya qaunar Maryam kuma furucin yake da niyar furtawa kai Bappa Yaya ya gyada mai cikin yanayin kayi mgn A hankali baba Umar ya kalli Ahmad cikin taushin lafazi yace Ahmad ba dole in baka son Maryam ka fada insha Allahu bazan bari a hadama zafi biyuba rashin abin sonka da kuma samuwar Abinda baka so idonshi ya sake maidawa kan goggo Aysha nauyin furicin ya sauqa kan harshenshi taya zai kalli qanwar mahaifinshi da baba Umar sannan qanwar biyayenshi Adam yace bai qaunarta bazan iyaba ya bawa kanshi amsa Yusuf kuma da Aysha dama illahirin mutanen porlon shi suka zubawa kunne da ido👂🏻👀 dan jin mai zaice yusuf hatta jijiyoyin hannushi motsi suke dan tsabar bala,I gashi ba daman yin matsifar jin tsanar kakan nasu yake sosai duk da shi a badirinshi baima ji mgnarba bare ya yarda da ita. Ka Abba qanin bappa yaye kenan shi ya katse shirun da cewa gsky ne Ahmad kana da damar da zaka auri duk wacce kakeso tunda baka sami zabinka Na forko ba cikin Yanayin jin haushi yusuf ya kalleshi yace wlh ni ban son jin zancenka da Na dan uwanka zanceku zai sai zuciya mai rauni da ciwo irin tawa zuciyar 💗 ta buga Shi kam baba Amadu mahaifin Amira sai yanxu ya danyi mgn cikin sanyi yace ba komai yusuf komai Alkhairi ne. Alkhairi kuma ? ya tabba yeshi ehh alkhairine yusuf mitarka ta fara isata kar ka hatsalomin da fushi Na baba bello ke bashi amsa kanshi ya sunkuyar cikin qunar rai Cikin taushin lafazi Hydar da Abdul har suna hada baki suke cewa Baba bello wai ina mgnar nan ta dosane aure tsakanin Hamma Yusuf da Aysha cikin tausasa lfzi Rabi,u yace karfa garin yiwa iyaye biyeyya mu aikata haramci a zuriyar mu Kai Nenne take girgizawa cikin qunar rai da gyar tace ya isa kun ishemu da tabba yoyinku marasa amsa A hankali bappa Yaya ya danyi gyaran murya ya dago kanshi yabi dukkanin illahirin zuriyar tasa da ido yusuf yake kallo sosai yayinda ya fahimci zuciyar Sa Na dab da fara tuna mai shin to a cikinsu waye binqelawo kai ya jinjina ya maida dubanshi kan Adam daketa murtuqe fuska tamkar sojan da aka bugawa tabbarin yaki idosa cikin idinsa ya sauqa da sauri cikin birki tecciyar murya da mgn kuma ta gsky da gsky da kaga yadda yake mgn kasan har cikin ransa hakane yace kai Bappa yaya ..... ?🍇🍇🍇 MI,WASMITI....page 1⃣1⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Kai Bappa Yaya wlh ka daina klna cire idon 👀 ka a kaina Sam ni bana wani qaunar ka kalleni Duk suka juyo suna klnonsa cikin mmk shi kuma da iya gsky Sa yake mgnar ya kalli baba bello yana Abba gsky ni ku gayawa tsohonnan ya daina zuramin ido danni wlh banaso ya maida hankalinshi kaina Tunda Na riga Na gane cewa kwanyarsa ta toshe tunaninshi ya koma hada auren mu harraman juna Ya juyo ya kslleshi cikin harara yace ( mi do yecce fa accu larugo am mi yida hala bema ) ina gayama fa ka daina klna dan bana son mgn da kai Dan ba mmki yanzu kace ni ma din ka fasa ni zan auri Maryam tunda abin naka ya Koma wa da qanwa tsufarka ta baka shawaran hadawa ya Ya kuma murtuqe fuska ya girgiza kai ya cije lips enshi yace tam ni dai wlh mutum bashi ya haifeniba kuma bai isa ya sarrafamin tunanina ba eh kayi ikonka iya kan yayan ka Yusuf dake qufule yace a barshi ai shi ji yake duk shi ya aifemu Baba Umar ne ya kalli dan nashi cikin hada fuska yace kai Adam ya isheka haka kafa kiyayeni Kai ya sunkuyar ba tare da yakuma mgn ba A hankali Abba ya kalli Ahmad yace Ahmad ka yarda da auren Maryam ? Cikin nitsuwa ya qarewa iyayen nashi kallo ya tabbatar da gsky mgnarsu a qowayar idansu 👀 cikin sanyin murya Yace Abba Na Amince zan auri Maryam ina sonta tunda ku iyayena ita kuka zabamin Na yarda Na kuma Haqura da Auren Ayshaaa Zanci gaba da klonta a matsayinta Na qanwata ta jini cikin dimaucecciyar murya yaci gaba da cewa Duk da tarin tabbayoyin da suke tare a zuciyata wadanda banda amsarsu bani da kuma mai ban amsarsu sai ku Kukuma kun wuce matsayin da zaku sani Abu intsaya bincike akan isarku a kaina Abba ngd da zabinku a hankali ya rufe bakinshi yayinda yayi qasa da kanshi Abba ya dafa kanshi ya rinqa jero mai Addu,oi Ahmad Allah yama albarka yasa ka gama da duniya lfy kaima Allah ya baka Yaya masu yimaka biyeyya fiye da yadda kake mana Allah ya jibanci Al,amuranka 👏🏻 Gaba daya suka amsa da Amin ya rabbi Aysha dake zaune tayi mutuwar zaune sai yanxu ta samu kuka ya kwofce mata 😭 cikin kuka take mgn Ya Ahmad me kake nufi kace ka Amince kana nufin kafi son a rabamu anya kuma kalaman Na baya gsky ne Da rarrafe ta qarisa gaban Ummi ta riqo hannuta ta fashe da kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro Jin kukanta yasa nauyin dake zuciyar 💗 Ahmad karuwa da hannu bibbiyu ya dafe girjin dan azabar da yake jin Yusuf ko gaba daya qoqolwarsa ta hargitse ta birkice yama rasa me yake tunawa ga sautin kukan ta da yakeji kamar sauqar aradu duk ya gama cika yayi tab fashewa kawai ya rage yayi kuma ba hali gasu Abba Juyawa yayi ya kalli Ahmad a daidai lkcin da ya yunqura ya miqe a lkcin kuma woyoyinshi dake kan cinyarsa suku zube a tsakiyar parlon Duk suka tarwatse a gun sabida haduwarsu da tayis qafarshi yasa ya cure. Laptop enshi dake gabanshi Ya nuna Ahmad a lkcin da fitar numfashinshi ya fara korar juna cikin wata iriyar murya yace ( a hafdi biyaye am ) ka keuta dan uwana Kana ganin wai jarumta kayi kenan to mu ka naqasawa rayuwa ya juya a fusace zai fita Cikin fada Abba yace kai yusuf dawo nan Da sauri Bappa Yaya yace barshi gwara ya fita dan tuni numfashinshi ya fara birkicewa ka sanshi da zuciya tunda ba samun yadda yake son zaiyiba in ya zaunama sai zuciyar tasa ta buga jarabebben yaro Kawai Haka sukayi Addu,a Suka watse Taronsu Shi kam yana fita ya figi motarsa ya nufi taraba ikon Allah ne kadai ya kaishi Sukuma suka dawo a tare ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ HALIN RAYUWA Yanayin zaman kamanni family ya canja rayuwa ta juya musu farin ciki ya musu qaura duk wani hayaniya da zaman parlo aita hira ya canza Yau kusan kwanansu 4 da dawowarsu Amman har yau dinnan Aysha bata kuma ganin ya Ahmad ba hakama yusuf duk da dai shi kam dama bai fiye shigowaba Adam ma tunda suka dawo bai shiga ba Zaune take kan kujera ta duqunqune ta tura kanta cikin cinyarta tana sana ar tata a hankali Amira ta dafa kafadarta ta zauna gefenta Cikin sanyin murya tace Ayyah Aysha ki tausayawa kanki ki tausayawa umminki mana baki ga duk damuwarki ta kama zuciyarta ba ta danyi shiru ganin Ummin a gefensu cikin damuwa hannuta dauke da cup en nono ta zauna gefenta cikin rarrashi tace Aysha karbi ko da nononne ki Sha kinji ko Kanta ta dago ta zuba musu jajayen idanunta cikin takaicin rayuwa tace Ummi ni banjin yunwa Na qoshi Haba Aysha yaufa kwana 5. Bakici abinciba so kike kijawa kanki cuta ne Kanta ta manna jikin Ummi ta fashe da kuka cikin kukan tace Ummi wai da gskne mgnar aurena da Hamma yusuf Ummi kuma da gaske bani ba ya Ahmad Ta dan zuba mata ido tace Ummi Amman bakya sona ko girgiza mata kai tayi cikin sanyi tace Aysha ina kika taba ganin uwa taqi yarta nima wannan abin ba a son raina za ayishiba Amman bari in gaya miki gskyan Al,amarin ...............👂🏻👀 duk ta zuba mata ido dakunne danjin meye gskyar abin ?🍇🍇🍇 MI,WASMITI...page 1⃣2⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Cikin lallashi taci gaba da cewa Aysha nima kaina wannan abin yafi qarfi nane shiyasa banda iko ko damar hanawa shiyasa wlh da ina da iko da Na hana ko dan farin cikin Ahmad inajin quna a raina sabida halin da Ahmad ya kasance a ciki ina jin tausayin mahaifiyarshi da Abbanku dan duk duniya sune Na forkon shiga matsala in damuwa ta dameshi Ta daura hannuta a kanta tana shafa gashin ta cikin taushin lfzi tace Aysha kiyi hqri da gddarar ubangiji ki daure kiyiwa iyayenki biyeyya kibi umurninsu Kuka sosai ta saki cikin jin zafi tace Ummi shikenan ni kam bani da wani sauran farin ciki ko ? Kina dashi Aysha am me zai hanaki ai rayuwa juyawa take wata ran sai lbr rayuwa zata kawo miki farin ciki zuciyarki ta Koma tamkar bata taba riskar takaiciba Haka dai taita bata baki Amman duk da hakan taqi cin abinci sai kuka da ta sake suna zaune a haka har bacci yaci qarfinta tai baccin Gudun kar a tadda ita taci gaba daga Inda ta tsaya dole Amira ta dawo parlon suka kwana tare ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Yau 10 days kekan da jin wannan sabon salon rayuwar da suke ciki damuwa da kuka su suka zama abincin Aysha yayinda Ahmad da yusuf sukayi wuyar ganuwa Adam dai yakan dan chigo kadan kadan Misalin qarfe 9 Na dare Abba da ummi ke zaune a parlon Abban suna dan tattauna wa cikin damuwa Abba Ya dan kalli Ummi yana mai cewa Ahmad fa kwana 3 kenan ni ban ganshiba kuma yawanci a kwanakin zai kirani da safe muna gaisawa zai katse kiran kuma ko Na sake kiranshi sam layukan nashi basa shiga abinfa Na damuna sosai ya qarisa mgnar cikin damuwa Ummi ta danyi ajiyar zuciya cikin sanyi tace wlh ni kam ma yau kwana goma kenan Ban ganshi da idona ba sai dai kullum zai kirani mu gaisa kam Haka kuma shima yusuf bai shiga kuma dukkansu ko abinci yadda aka kai musu haka za,a dauko Kanshi ya jinjina gami da zaro wayarsa number Usman ya kira yana dagawa ko gaisuwarsa bai amsaba yace (hey Usman ya 'youni nam ya Ahmad Mon) kai Usman je ka kiramin ya Ahmad enku Toh ya amsa da sauri gamida katse kiran Ya kalli Nenne da suke parlonta suna ta dan hira yace Nenne ya Ahmad fa ? Abba ke nemansa kai ta dan kada tace wata qil yana dakinshi A dakin ya sameshi kan sallahya yana kwance yayi rigigine hannushi ruggume da Al,QURA,ANI mai girma Amman kuma idonsa a lumshe yana ta rera karatun cikin narkekkiyar sauti baki 2 yana mai mgn bai jiba saida ya qarisa gun ya zare AL,QURA,ANIN Da sauri ya bude idonsa Shima din shi ya zubawa ido cikin yanayin tuhuma dan ganin yadda ya koma tam kar ma jinyaci yace ya Ahmad (dume hebima) meya sameka Kai ya dan gyada mai cikin qarfin hali ya dan murmusa yace kai ba komai lfy ta lau ya fada a lkcin da ya miqe tsaye Ba dan ya yardaba yace toh masha Allah tunda lfy kaje Abba Na kiranka Da sauri ya kallishi yace yana ina Yana parlonshi ya bashi amsa lkcin da ya juya ya fita ⭐⭐⭐⭐ A hankali cikin nitsuwa yayi slm Abba ya amsa mai Shigo ya cemai Ya shigo cikin girmamawa ya zauna inda Abba ya nuna mai kusa dashi a kan carpet yayinda Abban kuma ke kan kujera Cikin mmk suka zuba mai ido Ummi ce ta fara mgn cikin kaduwa tace Ahmad baka da lfy ne ? a,a. Ya bata amsa a taqaice Cikin damu tace doctor kallifa yadda yaronnan ya zama cikin dimuwar Abba ya xuba mai ido ya dafa kanshi Yace Ahmad meyasa baka cin abinci gafa yadda yunwa da damuwa da tunani suka galabaitar da kai Ya dago kanshi ya kalli shi cikin qarfin hali da murmushi a fuskarsa yace Abba inafa cin abinci Kanshi ya dan kawar ya kalli Ummi yace Fatima kawo min abincina Toh tace ta juya da sauri ta nupi kan dining dan dauko abincin Kanshi a gefe ya kirashi cikin taushi yace Ahmad tsoronmu kakeji ko? shiyasa kke buya kar mu sake zaluntarka Da sauri ya daura kanshi kan cinyar Abban ya dafeshi da hannu Bibibbiyu yace cikin rawar murya A,a. Abbana baku zalunceni ba bare naji tsoron kar Ku kuma Mun zalunce ka mana Ahmad am banda yadda zanyine shiyasa Ahmad qaddara ta rigayi fata ka gafarcemu hqqa mun zama masu tauye haqqi a gareka dana Ummi ya kalla a lkcinda ta dire tiren abincin a gabansu gamida dan sunkuyar da kanshi yace ummi ki tunawa Abbana matsayinsu a guna mana in yana fadar haka zafi nakeji sai inga kamar ganisuke basu isa daniba Ummi kam sai hawaye cikin muyar kuka tace ga abincin ta dan zuba mishi ta miqa mai Abbane ya karbi pilet en ya zame qasa kusa dashi Tuqeqqen tuwon shinkafane da miyar taushe sai qamshin man shanu yake Sa hannu kaci kaji ko Ahmad ba musu ya danci abincin badon yanajin dadinshi ba Sai dan ya faran tawa Qanin mahaifinshi Bayan ya dan mishi nasiha da qarfafa mai guiwa da sanya mai albarka Sukayi sai da safe har bakin part ensu Abban ya rakashi A bin mmk a palonsu ya samu .......... ?🍇🍇 MI,WASMITI...page 1⃣3⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Yusuf Ne zaune yana riqe da cup din black tea yana dan Sha gefenshi yaje ya zauna cikin yanayin happy ya dan murmusa ya kalleshi yana kai biyaye yaufa kusan kwana 5 ban gankaba Klonshi yayi cikin harara ya miqa mai cup en yana gashi karbi kasha karba yayi ba musu yana Sha ya dan tsaya zaiyi mgn da sauri ya dan daga mai hannu yace gama shan tukun sai kayi farfa gandan naka kar kayi ka qware Ajiye cup din yayi ya kalleshi da kyau yace biyaye farfaganda kuma ni din Yes ya bashi amsa kai din dai ba waniba ya dan girgiza kanshi da dan gyada kan cikin yanayin muryar da tafi kama da zaka qwaremu yace Biyaye bazan iya fushi da kaiba bazan iya rayuwa cikin happy bayan kai taka rayuwar ta cabe ba Hannushi ya dan daura kan qirjinshi yace kana son soya zuqa tanmu da biyeyyarka mara amfani a wannan karon cikin jin takaici yace nifa banda matsala dan banma ji zancen tsohonan ba bare Na wani yarda da tsarinsa Na gaibu ni kwannan zan barmusu qasar Amman damuwata nasan zasu yimaka daurin kazar kuku Dry ya danyi yace tab guduwa zakayi kenan ? ehh ya bashi amsa tunda ban da mafita iyayena sun Sa baki kan zancen zauceccen tsohonga ai dole Na bar qasan Zan fadawa Abba murmushin takaici yayi yace Na tabbata bazaka iyaba shiyasa Na fadama Haka suka danyi ta tattaunawa har zuwa qarfe 11 sukayi shirin kwanciya Dama shi yusuf tunda suka dawa da yake bai son kayan takaici injishi da fada sai yakan wuni gidan kaka Zubaida sarkin surutu sui fada su shirya ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Yau kusan 2 weeks kenan da dawowarsu mambila amman har yau Aysha batasa ya Ahmad dinta a qwoyar idantaba Duk da fama da take da azabebben ciwon girji Sam bata iya cin abici sosai qirjinta ke suqa kuma dai dai kan dukiyar fulaninta har taji tamkar zasu tsage Kwance take a dakin Nenne dan ta dawo nan dan fakon ya Ahmad din Can cikin bacci taji sautin muryarsa cikin sanyi yana dan mgn da Nenne shi bakin qofa tazo ta tsaya ta dan yaye lblen kadan yadda zata hanqoshi da kyau a hankali ta zuba mai ido duk ya canza ya wani rame fuskarsa tai sakau ya bar dan sajenshi ya dan baje ya qara fadi sabanin da dayake siriri yanayin shi gaba daya ya sauya zaune yake qasan carpet yayinda Nenne ke kan kujera ya dan miqar da hannushi kan kujerar ya kwantar da fuskasa kan damshe hannushi inda ya kasance kamar wurin baccin Aysha Cikin sanyi Nenne Ta kallishi gami da cewa Ahmad tashi kaci abinci kar yayi sanyi Kai ya dan qara kwantarwa ya lumshe idansa a hankali ya motsa lips enshi yace Nenne naci abinci da Abba banjin yunwa Kanshi ta dan dafe tace Ahmad ka dawo da wolwolarka mana tashi yayi yadan qara matsota ya daura kanshi kan cinyarta yace Nenne am bazan iyaba Na rasa farincikina dole wolwolata ta bace ya dan damqo hannuta yace Nenne wazan gayawa in as on Aysha har abadan in ba keba kullum nauyin zuciyata qaruwa yake suka mai zafi nakeji A hankali Aysha taji kukan da take dannewa ya kwafce mata cikin sauri da kuka ta qarisa gunshi Ganinta yasa ya miqe cikin wata iriyar radadi zai fita da sauri ta bishi ta fada bayanshi ta runqumoshi jikinta ta manna kanta tsakiyar bayanshi dumin hawayenta naratsashi da gyar ta iya budan baki ta juyo gabanshi cikin sautin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro tace ya Ahmad... ?🍇🍇🍇 MI,WASMITI...page 1⃣4⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Murya Na rawa tace ya Ahmad guduna kake? meyasa ? Baka son ganina ko ? Cikin kuka mai tsuma rai tace ni dai har Abadan xan kasance mai yarda da zancen zuciyarka ce ta daura hannuta kan qirjinshi tasa daya hannunta kan fuskarshi ta ware yan yatsunta A hankali ya lumshe qwayar idansa zafi Na ziyartar qoqon zuciyarsa da qyar yake fidda numfashi taci gaba da cewa zance fuskarka ba zahiri bane kai kace Aysha bugun zuciyarkace 💗 A.yanxu kuma sai ka shimfida ja rumtanka kan fuskarka Dan kawai kayiwa Kakanmu biyeyya kan abinda bashi da iko a kai Da qarfi ta riqe kafafunshi tana jijjigawa tana kuka Ya Ahmad haqurinka zai cutar da rayuwarmu Tuni jikinshi yayi sanyi sonta da yake dannewa qasan qoqon ransa da ruhinsa suka rinqa tsirgowa rauni sosai ya ziyarci zahirinsa Hannunshi yasa ya runqumota tako manna kanta cikin qirjinshi tana sakin ajiyar zuciya hannunshi yasa yana share mata qwallar idanta sosai suke sauqe ajiyar zuciya Nenne kam tuni tabar porlon Can kuma zuciyarsa ta darso zancen gskyar da aka rigada aka fada mai bashi ba ita kamar cikin razana ya balleta a jikinshi ya Dan tureta zai fita ta sake kamo hannunshi Juyowa yayi cikin sanyin murya yace Auta Abba Na kirana ya janye hannunshi ya fita ranshi Na soyuwa ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ A hankali ya shiga parlon ya kwanta kan tattausan kujerar kaka ya harda qafafunshi ya daura laptop enshi kan ruwan cikinshi phone enshi kuma ya ajiye kan hannun kushin din ya lumshe idansa Maganganun kakansu ke masa yawo a kai a ranshi yake gskanta jibewar Bappa Yaya numfashi ya furzar a hankali yaci gaba da cire abin a ransa Kaka dake kitchen tana girke girkenta Na tsofoffi duk ta cika gidan da qamshin man shanu girki take tana ta zirga zirga kuma sai mita take ita kadai Missxx ya Dan ja gajeren tsaki ita dai wannan tsohurwa bakinta bai iya shiru Tazo parlon kusan sau 3 Amman bata ganshiba sai yazu da ta shigo riqe da akoshi sai qamshi yake Tana ni bana son iyayi in zaki fito kici abinci ki fito irinku nawa akayi daga baya a dawo kamar za a hadiye juna... Tsaiwa tayi da sauri ta kalleshi cikin da tsorita tace kai Dudabe yaushe kazo ban saniba ? Ai saikasa nai ihu mutum ko slm bazaiyiba Shiru bai kulata ba ta sake ta kalleshi tana kai hannuta kan qafarshi da yake ta kadawa tace kai da Allah banson isa ehe Dan kai kazo ka sameni har gidana kuma inama mgn kamin banza Duk dai bai kulataba ta juya ta ajiye akoshin kan santer table ta Dan matso tana ai nasani ba bacci kakeyi ba mutum sai baqin hali ni yau har ina murna bazaka zoba jarabatu kawai😏ta ja dogon tsaki ta juya zata tafi da Dan sauri ya kamo hannunta ba tare da ya bude idonshiba cikin rashin son surutun Yace Dan Allah ki nitsu mana shin ke bakya iya Abu a hankaline Ya tashi ya zauna ya jawota gefenshi yana gsky ni Yau ba fada zamuyiba mgnar gsky nakeson muyi dake kaka ta Dan harareshi tace kar kawani min zaqin baki ban da masaniya kan tabbayoyin da kakemin kullum batun aurene dai ba fashi kuma dolenka ita zaka aura Ya Dan kauda kanshi daga gareta Dan yasan zai harareta kuma yana son ta Dan bashi wani qarin hske kan batun birkiceccen auren da suke ta tunanin zai yiwu Hakan yasa ya kalleta a daqile yace wai ke gani kike zakumin dolene ni zancen yayanki kamar tatsuniya nake ganinshi wlh kin San bashi ya haifeniba bare ya wani haqiqance a kainaba Tace aiko tunda ya haifi ubanka zance ya qare Da sauri yace (hey oyani handebo hala mai habe kudina) ke hajia yau kuma abin naki harda zagine Edin ai naga kaima zagemin Yaya kake da niyar yi A a Na isa Na zageshi gaban qanwarsa Da yafima kam ta bashi amsa Kaka ya kirata cikin tausarta yaci gaba da cewa mgnar gsky ni dai yayanki bai isa ya Sani abinda bana soba Dan bashine ubanaba Amman matsalata Dan uwana sun cusa tarin damuwa a rayuwar Dan uwana klonta yake cikin neman mafita yace ni shawara nake nema a gunki Dan ni kam kwanannan zan Koma gun karatuna Amman nafison sai Na tabbata Na bawa Dan uwana farin cikinsa cikin raunin murya yace wlh kaka komai zai iya faruwa da Ahmad Ku tausaya mai tunda shi mai biyeyyene a gareku Duk yanayinshi ya sauya azahiri ake gane tausayin Dan uwanshi dake cikin ransa Kai ta Dan jinjina tace Dudabe ( no mi watta be alkawal be wadi daga dubi cabfande tati e tati ) ya zanyi da alqawarin da akayi 33 years da suka gaba ta bazan iya hana komai ba Kallonta yayi cikin jin haushi yace ke kullum abi daya kike gayamin bakya tuna haramcin auren da kuke cewa za,ayishi Yarinyar da muka fito ciki daya da ita insha nono in barmata da yake duk kun jibe shine kuke ta babatu a kai toh wlh zan shiriya zanje Yola gun baba Umar da iyayen Ummi Na tunda kunfi son sai wasu sunji barnar da kuku tutiyar aika tawa zanje nace baba Umar ni banaso kar a kuma hada koda sunana da wannar mayyar yarinyar ni Na tsani koda ganintane ban ko qaunar tunata ya qarisa mgnar yana tattara phone enshi cikin klon yarinta da take mai tace Dudabe kar kaje zafa kaji kunya wata ran harara ya watsa mata yace dudabo Wlh in baki daina kirana hakaba bazan sake zuwa gidankiba ai dama bani Na kiraka ba tabashi amsa Aysha dake jin duk hirar da sukeyi tana tsaye qofar shigowa dama tunda safe tazo kafin ya shigone taje gun matar mai gadin gidan kakartasu itama kanta kaka bata San bata nanba tsaye tayi idanta tab hawaye bata lura dashiba sai jin da tayi ya yarfa mata mari yasa loptop enshi ya hanka deta ta fada qasa shiko yayi wucewarsa 🍇🍇🍇🍇 MI,WASMITI...page1⃣5⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Tunda ya fita taje ta kwanta kan cinyar kaka tanata kuka mai shiga rai da gyar taita lallashinta Cikin kuka tace ba gashiba ai kuna gani da idonku kaka wlh kun Sani sarai mugune 😡bai qaunata kuma shine kuke wani cewa zaku qullamai ni kaka gajiya dani kukayi shine kuke Neman Mae kasheni ko ??? a,a Aysha insha Allah bazai kashekiba da yardar Allah zaki zama Zahra ⭐a gareshi Tashi tayi ta gyara mayafin jikinta ta tura Dan bakinta tace Sam kaka buku duba haram ko halal kan batun aurenan shiyasa ba amfanin sauraronku Cikin kunar zuciya tace Ni ya riqada zuciyata ta bushe zan daina tsoron Hamma Yusuf koda ko kasheni zaiyi ta juya tai tfyarta kaka Na kizo Aysha tace anqi zuwan ⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐⭐ Yau jumma,a kuma yaune baba bello da ya Abubakar suka dawo daga qasa mai tsari daga aikin umrah da sukaje gaba daya suna cike a babba parlon suna ta Dan hira Adam ma dayaje Yola jiya ya dawo Shiyasa suke cike a parlon sunata hira sai Aysha ne da take dakin su tayi shiru cikin tunanin. Ko meyasa ya Ahmad ke gudunta Idanta a lumshe hawaye Na bin gefen fuskarta a hankali Abubakar ya Sa hannunshi ya share mata qollar cikin lallashi ya dagota yana gyara mata gashin kanta daya Dan baje cikin tausarta yace ayyah autan Ummi meyasa kike kebe kanki daga cikin mu banajin dadi Sam nafison ganinki kina raha da walwalah Aysha ki yarda da qaddara ki jure zafin da kikeji duk abinda kikeji baikai abinda ya Ahmad ke jiba baki ga yadda ya dawoba Amman A hakan yake bawa iyayenmu qarfin quiwar yiwa nasu iyayen biyeyyeh Kanta ta manna a jikinshi taci gaba da sheshsheqar kuka tana ya Abbukar kafasan waye Hamma Yusuf kasan baida wani buri a duniya daya wuce yasani baqinciki ya Abubakar ko ka manta uwa daya uba daya muke a ina aka taba irin aurenan Kai ya jinjina ya jawo hannuta suka nufi palon yana Aysha kada ki tsananta bincike Ni zuciyata tsinkewa take sabida bansan meye a qasaba banson jin wani mugun qulli shiyasa banason binciken haka ya jata suka tfi ******* suna shiga tana maqale da hannuta cikin hannu Abubakar suka zauna ta daura kanta kan damtsen hannunshi Ahmad dake sunkuye da kanshi sai yanxu ya dago ido cikin ido sukayi da qarfi yaji zuciyarsa Na duka Tara Tara Cikin qarfin hali ya miqe ya Dan kalli Yusuf dake murtuqe da fuska yace (biyaye in dulliko) mu tafiko kai ya Dan girgiza mai bazaka tafi ba eh yace yaci gaba da latsa phone enshi shi kuma cikin hikima ya zame ya bar gun Dakin shi ya tafi Duk abinda yake binshi da kallo kawai take bayan fitarsa kadan ta Dan saki hannun Abubakar ta miqe tayi woje A hankali ta murda qofar dakin ta shiga can ta hangoshi kwance kan gadonshi yayi ruf da ciki matsowa tayi ciken sanda tasa hannuta ta zare picture enta daya kifu a kai idansa ya rumtse gamida cije lips enshi cikin Dan dakewar murya tace bude idonka budesu ka kalleni ka gayamin meye a zuciyarka shin xaka gskanta zancenka Na baya ko zaka qaryata kanka da kanka Kai ya rinqa juyawa cikin disashewar murya yake ta maimaita a,a Hannu tasa ta dafa kafa dunshi tace ya Ahmad wlh kashemu kake son yi kallifa yadda ka dawo da rayuwarmu A hankali yace Aysha nine da laifi meyasa kike qara azabtar da zuciyata? Ehh kaine da laifi Ashe dama yaudara gsky ce maza nayi sannan kai sai ka rasa wacce zaka yaudara saini qanwarka kasan dama ba aurena zakayiba meyasa ka cutar da zuciyata💔 Ya Ahmad ka cucemu ta fada cikin kuka kan qirjinshi ta fada tana kuka 😭 Sosai tana Dan bugaga girjinshi tana dama baka sona ashe zancenka qaryane dakace Aysha ce bugun zuciyarka 💗 A hankali zaciyarsa keta cushewa zancenta ke ratsashi idanshi ya fara budewa bakinshi ya fara motsawa zafi da yakeji ya fara bunqasa cikin rauni ya kamo hannuta ya daura kan qirjinshi Yace kinjin har Abadan bazan miki qaryaba haqiqa ke Aysha kece buguzucita💗 Na gayamiki duk numfashin da zan zuqa da sonki nake zuqarsa wlh ina mai sheidamiki rayuwar Ahmad sauran kadan tunda aka tirsasawa zuyata fidda qaunarki Ayshaaa ki sani wlh duk randa Na gama cireki a raina toh tabbas a ranar zan barduniya🌍 Cikin sanantar kukan tace OK zaka ciren a ranka kenan ? Eh Aysha ya zama dole naiwa iyayenmu biyeyyah da qarfi ya danna hannuta kan qahon zuciyarsa yace kiji har abada zan mutu da qaunarki hannushi 2 ya hada yace plxx Aysha( burtinam ha sudu am usenifu ta loru waru ha am) Fitamin a dakina ina riqonki karki qara zuwa guna Klonchi tai sosai cikin zubda qollah tace fitar numfashinka shi zai yanke nawa numfashin yayinda muka mutun zuciyar Dan uwanka dakafiso zata buga Dan rashinka ta sake kallonci tai murmushin takaici tace Allah sarki duniya su Abba zasuga tarin qawarwaki wataqil rashinka yasa Abba na barin duniya ayyah baba bello zai qunci takaici da dacin rayuwa A hankali ta matsoshi tace yau zanyi ban kwana da kai kiss taimai kan kumatunshi yayinda shi kuma ya lumshe ido a hankali ya manna kanta kan qirjinshi can kuma ya Dan daqota ya manna mata kiss a goshinta ta kalleshi cikin yin murmushi takaici ta sake shi tafi tana suyar zuciya 🍇🍇🍇 MI,WASMITI...page 1⃣6⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 ---------------------------------- Haka dai rayuwa taci gaba da juyawa cikin quncin rayuwa Yau jumma,a Bayan an sauqo daga sallan jummaa Duk sukayi gida Cike suke a parlon Sai Yusuf da Ahmad da basa gun Baba bello ne ya dan kalli Usma dasu Rabi,u ya danyi gyaran murya yace kai Abdul tashi kuje parlona ku fitomin da kayayyakin dake ciki To suka amsa gami da miqewa sukayi part inshi din Aysha ya kalla a dan fizge gamida dan yafi tota da hannu a hankali ta dan saki hannun ya Abbakar ta miqe taje gabanshi ta dan duqa Wani dan leda mai sheqin gaske ya miqa mata yana gashi ki kaiwa Yusuf kuma kice ina kiranshi dum zuciyarta ta Nada wani sauti 😳😳😳ido ta zaro cikin firgici tace baba ni kuma ? Eh ya bata amsa gami da gyada mata kai Cikin firgici da razana da bugun zuciyarta da ya tsananta 💓 da gyar ta miqe dakin Ummi ta nufa riqe da laidar Kaka da tazo bikonsu su duk sun daina zuwa gunta Ta kalleta cikin wasa tace ke figi ruga yau ba mgn ne Baki ta dan zunbura ta zauna gefen Umminta tana rau rau da idanta tace ayyah Ummi dan Allah ki ajiye wannan in Hamma Yusuf yazo ki bashi wai inji baba Kai ta dan girgiza mata A a ni ban isaba ko ni ya aika dole nakai aiken ba wani nawa den ke kiwani ce sai ni zan bayar Kaka tayi caraf ta karbe da cewa ai wannan ma rashin kunya ce Kallonta tayi a lkcin da tamiqe tasa bayan hannunta tana goge qollah tana wlh Na Sani sai ya zageni kun sanshi sarai mugune 😡 banje inda yake bama Yaya ke kaka badai burinki ke da dan uwanki ku naqasamin rayuwa ba kusani kunci da takaici Da sauri Ummi ta dan yimata don qolo Kaka tai dry tace Barta Fatima ai randa zatayi alfahari da hadinmu nanan tafe Ita dai fita tayi tana dan qunquni Zaune yake a dakinshi a qasa kan carpet jikinshi sanye da 3 qtr sai dan riga mai hade da hula ya Daga dukkan alamu woya yake Ita kuma a tsakiyar parlon ta dan tsaya tana tunanin ya zatayi tayi slm shiru toh ko bayananne ta tabbayi kanta sabida tayi SLM yafi a qirga shirun da taji yasa Ta danyi tinanin shiga dakinshi ta ajiye mai kawai Cikin nitsuwa kanta a sunkuye tayi cikin dakin ba tare da tunanin ko yana cikiba sai xuciyarta dake bugawa Bugun zuciyar ya tsananta a lkcin da ta shiga dakin kanta a qasa tana nufin ajiye mai kan gadonshi sai ji tayi tayi tuntube da qafarsa aiko tai taga taga ta fada kan kirjinshi Da sauri cikin mmk da jin ta kaici ya hanka data duk da bai gama gano wayeba sabida duhun dake dakin Itako tuni hancinta ya sheida mata shine qamshin turarensa yasa ta ganoshi shiyasa cikin sauri ta miqe gami da miqa mai aiken jikinta har bari yake cikin tsoro da rawar murya ta miqa mai ledar tace (da Hamma baba on vi mi waddine ) gashi Yaya baba ne yace in kawo ma Fuska a murtuqe ya zaro ido ya buga mata tsawa yana ( salu vurti nam hado ) wuce ki ficemin daga nan Tsoron sawar da masifarsa yasa ta dan saki laidar Wasu yan takardu masu kyan gani suka watse a gun har kan qafarsa Iskar pankar dake kadawa ya rinqa watsa su Mmk sosai ya bayyana a fuskarsu su dukka cikin al ajabi da dimuwa yasa hannu ya dauko daya yana dubawa da fargaba sosai cikin minti 2 kamanninsa suka qara sauyawa bugun zuciyarsa ya tsananta numfashinsa ya fara dabur cewa idansa ya sauya daga yan qanana farare suka koma manya jajaye hatta jijiyoyin kanshi dana hannushi suka taso sama da wani irin yanayi ya tako ya nufi inda take Cikin tsoron da take ta Sa hannu ta toshe bakinta da hancinta🙊 da nufin hana kukanta fita sai hawayen daketa kwaranya a hakali ta rinqa takawa tana baya baya shi kuma yana binta har suka pito parlon Ganin zatayi waje yayi saurin fizgota har saida ta fada jikinsa By Hausa novels sokoto Whatsapp: 07068808039 🍇🍇 Mi,WASMITI..page 1⃣7⃣to2⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Cikin takaici ya rinqa sakar mata maruka Zuwa yanxu tsoro ko gudun dukan ya fita a ranta firgicin ganin i,v din Auren sun da suka gani yafi komai bada tsoro a gareta jikinta da zuciyarta duk sun qageshe Zafi sosai Yusuf keji a ransa ya gama makancewa da bacin rai shiyasa baiji bai gani yaketa bugarta kallonta yake ido cikin ido a fili yake cewa badai ke kince taurin kaiba ba tsayuwa kikayi kina tsuramin shegun idanunki 👀 kamar Na matsafaba toh wlh kanki zakici mayya fitinenniya ya kuma hambararta tai baya 2 ta fadi bakin qofa a dai 2 lkcin Ahmad da Adam suka shigo parlon Da sauri Ahmad ya sunkuyo ya dagota yayinda Adam ya nufi gun Yusuf din yana fadin Haba biyaye me hakan anya kana cikin hankalinka kuwa ko dai ka fara shaye 2 ne A harzuqe yayi kan Adam yana zazzaro ido woje yana eh giya nasha Adam ko kana da maganin buguwarnan tawane cikin mmk Adam yake klonsa kamar dai a bigen yake kam da sauri ya dakatar dashi hannushi ya jawo ya ajiyeshi kan kujera Goran Faro mai sanyi ya ballo ya miqamai karban Goran yayi ya cillata kan Aysha da sauri Ahmad yasa hannushi zai tare Goran cikin qeqashewar zuciya ta ture hannun ta kalleshi ido a bushe cikin yana yin dacin rayuwa tace barshi barshi ya Ahmad wlh ni a yanxu nafi buqatar azabar Hamma Yusuf ina dai sau daya ake mutuwa toh kubarshi ya kasheni ko duk ma huta wlh nafi buqatar zalumcin Hamma Yusuf din Don gwara nashi ai Ku naku boyeyyen zalumci kukemin wanda zai iya fasa zuciyata ta qareshi mgnar tana mai zubda qollah😭 Cikin sanyin jiki Ahmad ya kamota ya rugumota ya mannata a girjinshi yana Dan shafa kanta yana bubbuga bayan ta A hankali ta rinqa sheshsheqan kuka mai tsuma rai Yusuf da yake ta numfashi kamar zaki Dan zabar bala,i da zuciya cikin daga murya yace wlh kar nazo Na sameki a nan Dan wlh sai na lahira ya fiki jikin dadi Da jin haka Ahmad ya jata sukayi cikin gida Adam ne ya rinqa yiwa Yusuf din nasiha kan ya tausasa zuciyarsa Haba biyaye shin a duniyarnan akwai mai wuce qaddararsane ?shin muke tsarawa kanmu rayuwa ne ko mahaliccinmu? haba Yusuf rayuwafa komai asannu mutum zai bishi matuqar kana son cin ribar rayuwar..... Cikin sauqe ajiyar zuciya ya kalli Adam din cikin rawar murya da hardewar harshe yace Adam ya zanyi ya zanyi da burin Dan uwanmu Ahmad nafi jin makomar rayuwar Ahmad ya kamo hannushi yaci gaba da cewa shin kai baka tunanin yadda Ahmad ke son yarinyar nanne biyaye haqiqa kakanmu ya kasance mai zalumci a kan jikanshi Ahmad da yafi mu dukamu haquri da biyeyya a garesu cikin rawar murya yace Adam wlh so suke su kashe rayuwarmu da bakinciki Adam ya zanyi Plx biyaye ka tayani samawa Dan uwanmu Ahmad farin cikin Sa Sosai jikin Adam yayi sanyi ya kalleshi cikin sanyi yace insha Allahu yau dinnan zamu samu mafita Yusuf zamuyi tunani daga yanxu xuwa dare gobe da safe sai mu isar da manufarmu a haka ya samu ya Dan lafar da fushin A cikin gida kuwa Ahmad ne a gaban Nenne bayan ya samu Aysha ta lafa da kukan ya barta tare da Abubakar yana ci gaba da tausarta zaune yake a gaban nenneshi ya daura kanshi kan cinyarta sai fidda wani nannauyan numfashi yakeyi cikin zuciyarsa sai tafasa takeyi da ka ganshi kaga tashin hankali Allah sarki uwa da dan ta sai rabbi tuni Nenne ta gano yanayin da gudan jinin nata ke ciki a hankali tasa hannuta cikin sumar kanshi mai tashi da sheqi ta rinqa shafa kan nashi tana Dan shafa kumatunsa da daya hannun nata dai 2 kain kuncinshi taji damshi alamun hawaye😭 da sauri ta dago kanshi ta zuba mai ido shima itan yake kallo ya Sa hannayenshi 2 y daurasu kan nata da ta tallabe mai fuska 😭cikin zubda hawaye da muryar kuka bakinshi har yana rawa kamar maijin sanyi Yace Nenne Na kingako nikuma kinga yadda rayuwa ta juyamin ya zanyi Nenne inason Aysha kuma Bappa Yaya ya hanani ita Nenne ke kadai zan gayawa naji sanyi ya kuma kamo hannuta yaci gaba da cewa wlh inasonta tana sona kuma an rabamu Nenne duk duniya bayanke da Abba ba Wanda nakeji kamarta Itama hawayen takeyi cikin salon ni nacuceka ya kai Dana tace Ahmad ba laifinka bane ba laifin kowa bane laifi nane Nina kawo wannan irikitaccan al,amari Amman ka gafarceni D'ana da Sauri ya katseta da cewa ni baki min komai ba ni zan nemi gafararku a haka baba bello ya shigo ya samesu suka hadu sukayi ta bashi baki da samai albarka Da slm marsa da shigansa duk kusan a tare yayisu kuma duk batajiba har saida ya zauna gefenta daga dukkan alamu yanxu ta Idar da sallah A Dan firgice tace kai me hakan wlh dudabe sai nakai qararka gun Aliyu Dan ka isheni ji yadda ka shigomin a fijajam bako slm cikin harzuqa yace ancemiki ni alulkitab ne da zanshiga wuri ba slm toh ai nidai banjiba Hmm toh nidai nayi slm bakadai yi da qarfiba kam toh ni maroqine da Zan kama ihu a gari oho dai tace masa ai tunda kin ga nine shikenan ga baki ga tsoro harara ta cillamai shi kuma yaci gaba da cemata dama baki ya Dan tabe ya kalleta a cukushe yace ke ni dama zuwa nayi ki...da sauri ta katseshi in baka lbrin ko toh nima bansan komai ba kan batun aurenku da akeson hadawa Cikin qulewa yace keda Allah fadi ba,tambayaba ai duk surutn siya kin iya Amman da yake kinga INA roqonki shine kiketa wani jirgani toh ni bashixan tabbayeki ba zuwa nayi ki rakani mambila yanxu kafin manqqariba mun dawo baba bellone ya Aiken aiko dajin haka ta miqe tana yauwa Dama inason zuwa toh mutafi Hajia a yawe Oho dai sainaje Dan baqin ciki murmushin mugunta yayi aranshi yake cewa kedai komai fada A hanya kaka sai bala,I take dan ganin hanyar Yola suka kama fada take ase Dama baka da mutunci INA zaka kaini ? Sama zan kaiki ya bata amsa fuskarsa Na kan titi yanata tsula gudu mita kam da masifa ya shashi Amman dayake mishkiline kafi mahaukashi ban haushi ko a jikinsa 5:00 pm suna cikin porlon baba Umar ?🍇🍇🍇 MI,WASMITI...page2⃣1⃣to2⃣5⃣......Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Bayan yan gaishe gaishe da sukayi sai suka Dan tsagaita Kakace tace kai Dudabe ka bada aike Dan dere yanayi. toh yace mata gami da Dan kallon baba Umar cikin yanayinshi Na rashin surutu ya Dan sunkiyar da kai gami da Dan sake dagowa ya kalleshi ido cikin ido yace Baba dama zuwa nayi kamin taimako ka Duba Al,amarinmu ni da yan uwana sai kuma ya danyi shiru Dr Umar ya Dan jinjina kai yace fada min ba komai gayamin menene matsalar Ya Dan kalleshi gami da cewa baba Dama ni batun Auren nan ne sai kuma ya kurawa kaka ido Dan jin wani uban salati da ta dago haydar ma idon ya zuba mata ta kalleshi a yatsine tace wlh Allah ko Yusufa (a wasmitan ) zakafa yi nadama ka kama bakinka Dan gaba wlh kana dab da jin kunya zakayi nadama gabafa wlh ka iye bakinka..... Ke da Allah wayasa bakinki cikin zancen nan me hadinki dani bafa cewa nayi kirekoni kimin gatsali a zancena ba kuma wlh ki kama bakinki ni da wadanda suka isadani nake mgn badake karere ba ya qarisa mgnar yana mai watsa mata harara da zazzaro idansa woje Dr Umar yadan murmusa Dan Sani dama haka zata iya faruwa shi mmk mayayi sosai dayaga wai Yusuf ne da kaka a mota daya kuma tafiya mai nisa gashi ba Dan rabiyar fada a tsakaninsu Yusuf ne ya katsemai tunanin nashi yana mai fadin baba Wlh tallahi kaji nayi rantsuwar musulmi ko baba bana son Aysha wlh Na tsaneta ko ganin ta bana son yi Sam banjinta a raina baba wlh Auren da kukeson hadawa wlh masiface baba ni wlh Na yarda ko mahakaciya Ku samo Ku hadani da ita matuqar zan tsira ban Aure Aysha ba Kaka kam baki ta sake tana ware ido tana fadin wataran zakaji kunya wlh sai kunya ta hanaka ganin abinda ke gaban ka ni kam baza,ayi tijarar nan daniba barima ka gani woje zanyi Hydar da shima Sam bai farinciki da Auren da suke son hadawan ya harareta yace kifi ruwa tafiya ya koma ya kalli mahaifin nashi yace gsky baba niba banason wannan hadin naku nafison ya Ahmad ne ya auri Aysha Goggo Aysha dake gefe najin muhawararsu ta bisu da ido tana mai cewa Yusuf ai banan ya kamaceka kazo ka furta qiyeyyar da kake yiwa Aysha ba gun Umminka zakaje ka fada ido ya Dan zaro yace wlh tace duk randa Na kuma furta mata wani zance akai zata tsinemin cikin kaduwa Dr Umar yace Subahanallahi Meyayi zafi haka insha Allahu bazata tsinema ba Cikin yanayin lallashi ya dafa kafadarsa yace Yusuf kayi haquri Qaddara ta rigayi Fata Bani da wani zabi bayan Na Bappa Yaya Yusuf nima cikin qarqashin ikonsa nake Kayi haquri ka ruggumi qaddara Kayi biyeyya ga iyayenka zakaga sakayya mai kyau Wlh bani da ikon watsa Auren ka da Aysha da ina da iko da tuni Na watsashi Ya kuma dafa kafadanshi yace abinda baka saniba Yusuf ya rigada an Dade da daura aurenku kai da Aysha Tun Aysha nada shekara 8 aka daura aurenku Cikin firgici da mmk tsosai haydar kam dake zaune kan hannu kujera bai san lkcin da ya zameba Yusuf kuwa baki ya bude kawai yana binshi da kallo a rensa yake cewa wadannanfa sun Dade da kamu da cutar haukannan bamu kula da wuriba muryar hydar ce Ta kuma bashi wani sabon tsoro Hamma Yusuf toh ai Abu yazo da sauqi yoh ba sai ka saketa ba kawai Cikin kaduwa ya kalli hydar cikin murmushin takaici yace yoh in banda abinka Hydar ai Auren da ya halatta ayishi shi ake iya sakarsa toh kai ka yadda Auren ya daurune? Kai ya jinji yace haka nefa Hamma Yusuf Dr Umar ne ya kallesu cikin Solon yaro mankaza Ya kalli hydar yace haba Aliyu ase kaima kna da baqin tinani wannan wacce iriyar shawara kabaiwa Dan uwanka Ali ban sanka da haka ba ya kuma maida dubansa kan Yusuf yace wlh Yusuf ina jiyemaka tsoro fushin iyayenka kaji tsoron Allah kayiwa iyayenka biyeyya shin kai bazaka yi koyi da Ahmad ba ka ganifa shi aka gwara Amman ba Wanda zaice ga qorafin ko furuci mara dadi dayayi kayi koyi da Dan uwanka Haka dai yaita musu nasiha Daga bisani suka kama hanyar taraba a motako yasha mita gun kaka ------------------------------------------------------------------- 8:27 pm ya sauqi kaka a qofar gidan ta kai tsaye gidan Anuty Sadiya ya wuce A Can kuma gidan Anuty sadiyan tun bayan isha Ahmad yazo yana shiga bayan slmar da yayi bai kuma mgn ba Ikram yarta tai gudu ta shiga bedroom tana mami ga uncle Ahmad yazo Tare suka fito da ikram tana zuwa kan cinyarshi ta dale tana uncle xamuje gidan zoo ko kai ya Dan gyada mata ba tare da ya bude idoba A hankali Sadiya ta kalli Dan uwan NATA cikin sanyin murya tace Ahmad ka rinqa mai maita innalillahi ka yawaita hamdala kaji Dan uwana ? toh yace muryayarsa Na rawa hawayen da yake boyewa suka samu damar zubowa Allah sarki Ahmad duk jarumta irin tashi ga so Na maidashi rego ko yaushe idansa bai bushewa da qollah😭 haqurinshi ya fara gazawa cikin sanyi ya zame daga kan kujerar ya komai gefen Anuty Sadiya ya riqo hannuta ya daura kan qahon zuciyarsa yana mai Jan numfashi da qarfin yace Anuty numfashina tafiya yaketi kiji qahon zuciyata kamar zata stage ina tausayawa rayuwarta INA taushayawa biyaye a INA kuma tausayawa Maryam Dan zan aureta ne kawai Amman ba batun so kam gashi matsalar Aysha ko tafi komai damuna a duniya wlh Anuty da mutuwa nayi da yafi min da wannan rayuwar gomin ko nasani Nanda Dan wani lkci zan mace Na barku ya daura hannushi kan jinyarta yana mai cigaba da cewa Ayyah Anutyna zan mutum Na barki nabar Aysha zan barki da Yusuf da Adam Na tabbatar duk abinda zan miki zasu miki toh Amman Anuty duk duniya ba mai yiwa Aysha abinda zan mata biyaye baya Sonta bare ya riqemin amanart Anuty zanbar Amanar Aysha a gunki keda ummina ku kadai ne zaku iya riqemin amanrta bazan ba Yusuf amanar Aysha naba Dan nasan bazai riqemin ba Niko banason abin da zai gasamin Dan uwa Kuka Sosai sukayi cikin kuka mai tsuma Sadiya take fadin bazaka mutuba Dan uwana zakarayu zamu rayuwa tare zamu zamewa Nenne mu 3 tamkar da 30 Ahmad banda qawa ko aminiya kune kawayena kai dasu Yusuf Ahmad ni INA gidan miji in kamutu zakabar Nenne mu da kewa Rabi,u bazai iya mata kula da biyeyyar da kake matanba Da Sauri yace Anuty banso Rabi,u ya kasance mai irin halina gashi ni yanxu hiyayyarce ke shirin rabani da duniya Bazaka mutuba Cewar Abba cikin mmk Sadiya ta kalleshi tana Abba yaushe ka zo ? Tun dazu nazo Sadiya duk naji hirarku Sadiya Yusuf Na Haifa Amman Ahmad shine jigona insha Allahu Ahmad bazai mutuba Shi daya da nake gani naji sanyi Abba kuka yakeyi harda hawaye Ahmad ya kalleshi cikin dauriya yace Abba dama kana zuwa gidan Anuty Sadiya ne ehh gashi kuma ka gani aini yawanci Abba kanxo muyita hirarmu Amman Sam baba shi baya zuwa ko kadan suka danyi dariya Abba yace toh ai dama ni ya kamata Nazo bashi ba tunda shi yanaga gidan surkine ni kuwa gidan ma,aikacin asibitinane kuma mijin y'ata Haka dai sukayi SLM suka tafi suna fita daga layin Yusuf kuma Na shiga Amman basuga junaba da yake akwai cikowar ababen hawa Cikin tsoro da firgici Yusuf yayi kan Anuty Sadiya jikinshi har bari yake ganin halinda take ciki Kuyi haquri masoyan wannan littafin insha Allahu zan Duba qorafinku nason Na yawaita Sa fillanci a ciki haka kuma INA Baku haquri da jinkirin da kuka gani I love all makaranta wannan littafin Fasaha Writers INA gaidaku Auntys din kamaluuuu 😝 ?🍇🍇🍇 MI,WASMITI...page2⃣6⃣to3⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Cikin kaduwa yace Anuty meke faruwa? ya Na ganki haka kiga yadda fuskarki ta kumbura ?meya sameki ? Haka ya jero mata tabbayoyin Cikin qoqarin boye damuwarta tace Kai Yusuf me haka ka firgice gaba daya kawai ciwon idone ke damuna kuma yanzuma Abba ya kawomin mgni Hannuta ya kamo suka zauna kan kujera ya kalleta da kyau ya Dan kauda fuskarsa gami da yamutsa fuska Cikin kula tace Yusuf meke damunka Lips din shi ya Dan ciza gamida Dan kamo Na kasan yana tsotsa Yusuf meke faruwa ne ka gayamin mana Qara matsar lips din yayi yace Aunty Na tsani Aysha Na tsani Auren Anuty Aysha fa burin Ahmad ce Eh ita burin Ahmad ce Amman kuma zabin iyayenmu ne da suka zaba maka ita Cikin takaici yace Anuty hardake bakya tuna makomarmu ba komai Yusuf insha Allahu ba wani Abu Hmmm Anuty ba haka naso ji daga garekiba Amman naga kema layinki daya da tsofaffinan Cikin sanyi ta rinqa mai nasihar da shidai lebenta kawai yake ganin yana motsawa alamar mgn take Can dai yace ni zan tafi har baking gate ta rakashi yaja mota ya tafi Allah sarki yau kusan duk ba wanda yayi bacci Abba gaba daya ya karaya Nenne kuma kan sallahya ta kwana tanayiwa gudan jinin nata addu,a Yusuf kam abin ba,a cewa komai a jikin shi yakejin alamun ciwon zuciyarsa ke shirin dawowa Adam shima cikin tunani ya kwana shiko Ahmad ciwon da yakeji a zuciyarsa ne ke qaruwa kullum dare Anuty Sadiya kam kusan kuka ta kwana yiwa Dr Bashir mijinta kenan Dr Umar ma lamarin ya dameshi Ummi kuma tabbas tanaga an cutar da Ahmad haka dai kowa ya kwana zuciya a quntace *************"*"""****** Yau Monday bayan maqqariba duk suna tare a parlor kowa da abinda yakeyi su Abba ma duk suna nan lami mai aikice keta kacaniyar ta a kitchen Abba ne ya kalli Usman yace je ka kiramin Ahmad toh yace gamida miqewa ya fita,,,,,,,, Tare suka shigo kai tsaye gaban Abba yaje ya zauna baba bello Na cemai Ahmad Yusuf fa ? Yana wonka ne baba. toh yayi kyau Cikin gyaran murya Abba ya kalli duk kan mutanen parlor ya zaro wasu document dinsa daga cikin jakarsa Ahmad ya miqawa yace ingo duk inda kaga za,asa hannu ka saka cikin mmk ya kalli abban yace toh Abba bari Na jira biyayena Ido ya Dan qura mai gami da cewa kai nasaka ba shiba Ahmad bai iya musuba ko da abokaima bare da iyaye Duk ya shiga budewa yanasa hanu daya bayan daya ya gamasu tas ya dagasu ya hada ya miqawa Abba Cikin tsantsar qaunar Dan Dan uwan nashi yace toh mutanen parlon nan ku zama shaida bayan shaidawar Allah ☝🏻ni Aliyu Muhammad Aliyu Na baiwa Dana Ahmad company Na dake birnin Abuja Na bashi halak malak Na kuma malla kamai gidana da yake anquwar fada nanan cikin taraba Gaba dayansu farincikine ya cika fuskokinsu ba abin da suke fadi sai Masha Allah kai Abu yayi kyau Abba Allah ya qara budi Nenne kam kukan farinciki takeyi sosai baba bello kuma fada ya kama haba Ali kasan abinda kakeyi kuwa ? Da Saudi Abba ya katseshi da cewa Dan nayiwa danka kyauta shine laifin Cikin jin kunya baba bello yace a a wlh ba haka bane Ali Ahmad ai dankane Aliyu . Toh inko kasan da haka barunka kasa albarka kawai haka kuwa akayi Ahmad kam da ya zama mutum mutumi sai yanxu yaji bakinsa Na furta Jzkllahu bil jannah👏🏻 Abba ubangiji ya jibanci lamuranka gamida yin sujjadah yayiwa rabbi godiya murya Na rawa ya miqa mahaifinshi yace baba ganifa kyautat da Abba yamin Abba Na ya gamamin komai a duniya gaban Abubakar yaje yana kalli Sadip Na gani ya fada gamida cewa ya Ahmad ka wuce haka a gun abbanka runqumarsa yayi sukayi ta farin ciki kowa yaji dadin wannan kyautar Usman kuma cewa yayi ya Ahmad tukuicina mata nakeso Ka samu Usman key din motarsa ya cilla mai gamida cewa ga tukui cinka Wow Rabi,u da Abdul ke fadi usmanko rawar choki ya kama harda juyi Dai2 lkcin Yusuf ya shigo da Sauri Ahmad ya runqumasa gamida nunamai kyautar da ya samu gsky farin cikin Yusuf tamkar yamafi Na Ahmad Adam kuma cewa yayi dole ayi walima a gongoje Wunin ranar dai farin ciki ya dawo cikin family din saka makon farin cikin Ahmad din sun shirya kan cewa ran jumma zasuyi waliman shiri sukeyi sosai sun gayato manya manyan mlmanmu Dr Ibrahim jalo jaligo dasu alaramma malam Sulaiman gasu shehk Kabir Gombe su isa Aliyu fantami duk dai anata shiri Gaba daya shirin walimar yadan kauda damuwarsu kasan su Bappa Yaya tuni anxo Dr Umar ma da iyalansa abokan Abba Dana baba bello da dai dukkan yan uwa musulmai Qaqa qara qaqa Taro yayi taro gaba daya duk girma irin Na farfajiyar qofar gidan kamanni family ya kasa daukar jama,ar dole wasu har bakin laying anquwar 2:12 pm kowa dake cikin anquwar ya shaida daurin Auren Maryam Umar ardo da Ahmad Muhammad Aliyu saikuma Adam Umar ardo da Amira Ahmad Muhammad Aliyu 😳😳wasu fuskarsu mmk yake nunawa wasu kuma figicine sosai aurenda ansa sai nan gaba 1 month shine yanxu lkci daya a hargitse Abu cikin tsananin firgita Yusuf ya nufi gun Ahmad Cak ya tsaya jin ana cewa ayi addu,a ga ma auratan asaka da Aysha Aliyu Muhammad Aliyu da kuma Yusuf Aliyu Muhammad Aliyu Toh fa gaba daya kowa da abinda take fadi Wanda bai sansu bama jin sunan su ya kansa mutum 🤔 Bugawan 💗qirjin Ahmad kuma da Yusuf ba,a magana dukkansu ko qwaqwaran motsi sun kasa A cikin gida kuma jin wannan lbrin yasa Aysha dake shirin Shan ruwan ta qware takoyi muguwar gwara a take a gun ta fadi ba.. Sokoto Hausa Novels 🍇🍇🍇🍇🍇🍇 MI,WASMITI..page 3⃣1⃣to3⃣5⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Jiki Ba Qwari ta zame ta zube kan gado ta fara rera Kuka mai tsuma ran mai sauraro Su Nenne dasu Ummi da mama matar baba Ahmadu mahaifiyar Amira kenan dasu kaka da wasu qannen Ummi cikin su ko harda innah mahaifiyar lamido on top Dan Baban lamidon yayane ga Ummi mahaifiyar su Yusuf din Gaba daya lallashinta sukayi Nenne ce ta jawota kan cinyarta tana shafa kanta Aysha ki bar kukan nan haka dan Allah ko so kike muma ki samu kukan kinga Ummin ki kam tunda gari ya waye kukan itama take ki daure Aysha am kowa inya yaga kin sake muma duk zamuji dama dama 2 Sheshsheqa takeyi har kamar zata shide ganin haka yasa Ummi kam juyawa ta fita tana cige lebenta da zubda qollah😭 a ido Cikin hatsala kaka tace Ke 👈🏻Aysha zakici kanki nace wlh kanki zakici (Minin kam ha alari amin do ha doddo a accata amin) Mukam inda kika ganmunnan an an zaki barmu ehe 😡😏 (anon bikkoi jotta saro enmon be fotai bemon ) ku yaran zamani wai iyayenku basu isa dakuba) Wlh ina gaya miki matuqar dai baki gyara halin kin nan Na taurin kaiba toh wlh zakisa baqin ciki cikin rayuwarki. Bayan hannuta tasa ta goge gwallar dake bin fuskarta cikin rawan murya da disashewar voice dinta tace kaka ni kuma wanne farin cikene ya regemin a rayuwata ai bani da wani sauran haske sai duhu ta dago ta kalli Nenne tace Nenne insha Allahu bazan sake saku kukaba kuyi tamin addu,a Allah ya dauki raina kowa ya huta da sauri Innah tace kul👈🏻 Aysha kar ki kuma irin wannan furucin Anuty Sadiya Ce ta zauna gefensu taci gaba da bata baki a haka dai suka samu ta Dan tsagaita kukan 🔆🔆🔆 Bayan an gama daurin Auren Sai akaci gaba da gudanar da liyafar da aka shirya Daga nan kuma akayi sallan LA,asar Sannan manyan malamai suka rinqa bada tasu gudumowar a inda suka rinqa bada shawar wari ga angwayen da amaren Sune ba ,a tashi a walimarba sai goshin maqqariba nan kuma akayi sallah akaci abinci aka kumayo ishaa daga bisani Fagan ya zama Na alaramma malam Sulaiman ne ya hau ya rinqa rera karatun alqura,ani mai girma inda sautinshi mai dadin sauraro ya rinqa rasa cikin anguwar tako ina 9:25 pm Yusuf Na kwance a parlon shi kadai abin duniya duk ya isheshi Amman kuma yana qoqarin nemawa kanshi da biyayenshi mafita ne kuma a tsarinshi ya samo musu ma fitan Adam da Ahmad kuma suna can suna fama da abokansu da suka samu hallaruwa wajen bikin Daga nesa yakejin surutunsu alamar nan part din shi suke zuwa Dan gajeren tsaki ya ja gamida juya kanshi ya lumshe idansa kamar maiyin bacci Iska ya Dan furzar cikin ransa yake cewa Ko waye ya gayyato min wadannan parrots din mutane bakinsu baya iya shiru nasan kuma ba aikin kowa bane sai Adam duk Yanxu zasuzo su matsawa rayuwata Ya kuma Jan tsaki dai2 lkcin suka is a tsakiyar parlon Mmk nayi sosai ganin wadanda suka zo din Su LAmido on top ne Na ruwan kashe gobara Gefen shi kuma kamal ne anqon yusra Dalibina Daga daya gefen kuma Modibbo ne angon Bilkisu meke faruwa Bayan shi kuma Yaya habeeb ne nida Yaya habeeb can kuma gefen jalal ne Na jalaluddin Abin mmk sai ga wasu masu kama sak 🤔lah Na gane su ase Hassan da Hussain ne na littafin yar Fulani Na Aysha Ali Garkuwa Cikin gajiya suka zazzauna lamido ne ya zauna gefen Yusuf ya Dan harareshi yana wlh kadai ji jiki mutum sai baqin halin.... Kai kuma sai shegen surutun siya eh anyi din bakinka ko nawa Nan kuma ya juya gun kamal ya Dan yi daryar tsokana yace kai kamaluuuuu dama ase kana iya barin asran taka kazo wani woje 😜 Kai dai lamido Dan duniya ne toh duk nacina Na kaiku ne kai da modibbo cewar kamal kenan gaba daya sukayi dry Cikin qasaita modibbo ya hararesu wlh kundai kunji jiki yara qanana daku sai baqin jaraba hararanshi lamido yayi yana Nikam nafi qarfin yaro sai dai ko en kamal ne yaran Dan wlh ni kam Na wuce yaro Hussain ne ya karbe zancen da cewa ai wlh kamal kam da lamido da modibbo layinku daya Habeeb ne yace kamal ai shi ba daga qafa Harara kamal din ya watsa masa yana aiko wlh ni kam Na daqa qafa kusan shekarun biyu ina haquri lamido ne yace toh shiyasa kaso ka cinye baking yar mutane tsabar kiss ne harda kumbura mata lips 😀yoh da an barka cinye bakin zakayi ko kamaluuu 😝😀 Adam ne yace kaifa on top layinku daya da kamal Dan wlh Baku da sauqi Yusuf ne ya kalli hasaan yace yane sarki hasaan kayi shiru ko daya ke nasan kai ba irinsu akukkuturunan bane iyayen jaraba basu da aiki sai Na zance mata lamido ne ya watsa mai harara yanxu kai kuma Yusuf har kana da bakin mgn ne duk jara barmu mun kaima ne dry sosai sukayi kamal yace har kai da modibbo bai kai kuba jalal ne yace ji Dan iska kamal kai ware kanka kake a cikin jara babbun ai Ku duk mota data CE ta deboku Lamido ne yace kunsan Allah mu ture batu zoleya kawai dai mu jarabarmu ake gani da yake mu bama iya boyewa ko daurewa ya Nuna hassan da Yusuf yace wlh kunga wadannan muna fukan masu qiffqifta idanu sun fimu Yusuf ya kai mai bugu ya kauce da sauri Jalal Na kai lamido abin kuma harda yar Sherri ne Da sauri ya kalli Yusuf yana nuna lips enshi yace ka Ganshi ko wlh zabar fitinarsa CE tasa baya taba bude idansa ya woresu ya kalli gari dan da zaran yaga mace yake daburcewa yai ta rawan sanyi Cikin dry Habeeb yace kai lamido dama rawan sanyi da Yusuf ke yawan yi lkuta da dama ase abin ne ke motsowa? Sosaima kuwa kaga yan qananan inda nunshin nan da baya budewa ya ga gari ko toh wlh Sha,awarsa Na tashi zakaga sun fiffito sunyi woye a take zakaga idan yayi jazawur leben bakinsa jajayennan sai kaga suna ta rawa kamar mai jin sanyi sai ya wani kamo lebenshi Na qasan ya rinqa tsotsa sai sunyi fari tas ya wani Sa hannushi ya damqe mararsa ya rinqa mammatse cinya yana hanata tasowa😝🙈ya rinqa rawar sanyi gaba dayansa ya rinka yiwa mutane barin baki sai kaji shi yana wani shiiiiiiiiiiii hahhhsh Jara bebbe kawai wai a hakan kuke cewa Yusuf Nada dauriya Duka Yusuf din ya kai mai tare da miqewa yana qoqarin shiga bedroom yana miqa yana mammah Mujahedin da yanxu ya shigo yace wlh zancen ka gsky ne Dan yanxu miqar nan da yake abinne yake motsawa Dan an kira sunan mata kawai yanxu haka mgni zaije ya Sha. Duk sukayi dry suna tafawa Ido lamido ya kashewa Yusuf yana kadai San ba qariya muke makaba ko😉 Hassan ne yace komai dai menene ai muna iya control din Sha awarmu bama danne yayana mutane kam 😡 Kamal ne yace aiko kwa kashe kanku wataran Habeeb yace bar yan rainin wayo ai shikam Hassan yasan azabar daya Sha da yar Fulani ta qauracemai Jalal yayi dry yace kasan wai su sun iya fulaku Kamal yace wayace ma ana fulaku kan abinnan😉 Hussain ya kalli Ahmad yace wannan kuma da ya wani tsamure zai iya tsinana wani abin kirkin ko dai sai mun kawo kafi doki mun baka kasha duk suka kece da dry Cikin sanyin yanayinshi yace kai dai Mayya kawo idanka kaina ni ko Na gazama qanwatace zatayi haquri dani kamal yace ka banu gwara ka miqe Dan wlh mata basa son lusarin namiji😝 Yusuf ne ya katse musu dry da suke tayi Dan ceqiyanci Kai biyaye INA mgnina ? Adam yace tab yoh ni nasan inda ka ajiye abinka cikin hada fuska yace ka Sani kam kasani sarai ai dama Kaine kullum kake kwashemin abinna kana zubar Dry sosai modibbo yakeyi yana nuna idan Yusuf da suka firfito sai zaresu yakeyi sai wani sheqi sukeyi da qwalla tab aciki kamar mai shirin yin kuka Kamal yace Abun ya motso kenan Lamido yace in ka masu in dauki maka amariyar ka dan mu kam baqin sauqine zamu Baku fili😜😀😀😉haka dai sukayi ta yiwa juna Tsiya Bayan an gama biki duk baqi sun kokkoma sai yan kadan da suka rege 🍇🍇🍇🍇🍇 NAYI NADAMA Mi,WASMITI page 3⃣6⃣to4⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Gidan Adam A hankali yayi SLM tare da shiga cikin bedroom din nasu Cikin nishadi yayi ajiyar hrt Dan wani sanyi da qamshi da yaji yana ratsa gabban jikinsa Daki kam ya hadu iya haduwa Amariya Amira ce ke zaune kan gadon tana sanye da kaya Na alfarma sai qelli goshi takeyi cikin takun shauqi Ya isa gareta Hannu ya miqa mata alamar ta kamashi zai jawota ta sauqo Cikin jin kunyar da bata tabajin tana yiwa Dan uwannata ba yayanta kuma mijinta a yau Cikin Yanayin mmk yace meerah yau kuma kunyata kikeji ya Dan ronqofo ya jawota tsaye suna fuskantar juna ya Sa hannushi ya tallabo fuskarta ya Dan zuba mata ido cikin wata iriyar muryan da bata tabajin ya Adam din nata dashi ba sai yau Yace Plx meerah kar kibari wata baquwar kunya ta cutadar damu Shiru dai tayi Dan haka kawai ta sinci kanta da jin kunyarshi Kinji ko meerah ? Kai ta gyada alamar eh Hannuta ya jaa ya kaita bakin qofar toilet Yace shiga kiyi alwala Toh tacemai gamida shigewa ciki Shima alwalan yaje yayi a gefenshi Yana shiga Ya sameta a zaune Darduwa ya shimfi da musu Sukayi nafila raka,a 2 Bayan yayita jero musu addu,oi Suka shafa Zata tashi ya jawota ta zauna lader da ya shigo da ita ya bude Gaseshiyar kazace mai Dan romo 2 sai juice kala 2 masu sanyi kai tsaye shi ya rinqa bata a baki cikin kuya take karba haka dai sukaci sukasha 11:15 pm Adam ya jawo amariyarsa cikinsa gami da kashe hasken dakin Cikin Dan jin tsoro ta fara Dan tureshi A hankali ya kai bakinshi dai 2 kan kunneta Yana furta mata zantuka masu kama da darasi mai wuyar fahimta nan Kuma hannushi ya fara isar da saqonshi gareta Sosai ta tsorita jin yadda yayan nata ya rikice mata a yau din Hannushi ya zira cikin rigar jikinta har ixuwa qirjinta Firgita tayi sosai jin yada yake sarrafata Cikin muryar tsoro da qoqarin yin kuka ta kamo hannushi tana kayi haquri Wlh tsoro nakeji ya Adam Na tuba Kai ya rinqa girgiza mata yana mgn cikin wuya da tsananin buqatuwa Kiyi haquri meerah bazan iyaba Wlh bazan iya jure wannan Daren ya kau cemin ba a haka dai cikin hikima ya rabata da budurcinta Garfe 3 dai 2 Adam ya samu nitsuwa yayinda itako Amira tasha Kukanta shiko yayi ta faman lallashi da gyar ya samu Ya lallabata tayi wonka bayan ya Dan gasa mata jikin ta Anan suka samu sukayi bacci mai dadi da nishadi Gidan Ahmad Tinda ya shigo gidan ya wuce dakinshi Kan gado ya fada cikin Kunci zuciya da zafin Rayuwa A hankali yake furta Ase dama haka rayuwa zata kasan cemin ase wannan Daren da nake tayiwa tanadi da shiryawa da burin Mallakar Aysha ase hakan bazai kasan cemin ba Sannan qaddara ta hadani da Maryam yar uwata a matsayin mata Wani daci yaji yana tuqarsa daga cikin maqoshinsa Cikin murya mai rauni yace Am so sorry My Aysha Ki gafarceni qanwata Dana San bazan aurekiba da bazan dasa miki sona a ziciyarki ba Wlh da nasani da nabar abin a zuciyata ni Kadai Da ko ba komai ban cutar da keba Cikin zafin rayuwa Da tajuya mai baya Yake ta fadin Wlh da inada yadda zanyi In sawa biyaye Na sonki a ranshi da Na saka mishi Dan da koba komai zai kulammin dake Amman ban da damar Sa so ko qiyeyyah a zuciyar Dan Adam Zogi sosai zuciyarsa ke yi hannushi ya saka ya danni kan qahon zuciyarsa Yadda gaba daya jikin shi ya dauki bari ga wani zufa da yake ta keto mai tako ina Sosai yake jin azabar ciwon zuciya cikin rawan baki ya rinqa surutai masu ban tausayi kusan a haka ya kwana sai sunan Aysha da yaketa kira yana ki gafarceni Amariya Maryam kuma dama tayi zaton haka Dan tunda aka hadata da ya Ahmad Wanda tasan ba itace burin ranshiba tabbas ta sawa ranta wannan Abu zai iya faruwa Shiyasa tunda taga 12 yayi bata ganshiba ga soron da takeji gida shiru sai ita kafai a haka ta fito parlor cak ta tsaya Jin sautin kukan da Ahmad din keyi da sabbatun da yakeyi cikin raunin murya da halin quncin rayuwa A hankali ta qarisa baking qofar Lkci daya kuma tausayin Dan uwan NATA kuma mijinta ya rinqa ratsa qahon zuciryata Nan ta zame a wurin ta rinqa kuka mai tsuma rai a haka suka kwana shi yana ciki yana nashi kukan itako tana baqin qofarsa A haka kuma rayuwa taci gaba da Tafiya agaresu Yau kwana 7 kenan da yin bikin Kuma lamido shi basu komaba Shiyasa Yusuf ke Dan jin dama2 tabbas yaji kewar yam uwana Amman lamido Na debe mai kewa sosai Suma kuma su Ahmad sukan xo suyita hira Adam ne ma bai cika zuwaba da yake shi rayuwar aurenshi dadine ke tafiya Yau asabar kuma yau su lamido zasu komai Yola shi da innarshi Tafiyar yamma zasuyi Shiyasa basu tfi ba har yanzu Bayan sunyi sallan azafarne suna dawowa gida Lamido ya kalli Yusuf yace kai bazanfa koma banje gidan su Ahmad ba Toh me nawa da kake gaya min zan hanaka zuwa ne ? Banson iskancifa Yusuf ai dai ka Sani tare zamuje kam ko A a ni kam bazaniba Haba Yusuf gidan su Ahmad din kake cewa bazaka jeba ka tunafa kasan ko suwaye Ahmad dinka nefa biyayenka da Adam dinka yan uwanka abokanka aminan ka shin ko ka manta matsayinsune a gareka Yusuf ko zarginsu Ahmad kake da laifin da ba nasu ba Hannun shi ya kamo cikin tuna sarwa yace Yusuf ka dawo cikin hayyacinka .. Kai ya jinjina gami da cije lips enshi ya kalli lamidon yace Hakalina tashi yakeyi ako da yaushe in naga halin da Ahmad ke ciki kaga fa lkci daya yadda biyayena ya fita hayyacinsa gaba daya ya birkice farin ciki ya bar rayuwarsa Toh in banda abinda Yusuf ai yanxu ya kamata ka nunawa Dan uwanka kulawa Kai ya dan jinjina yace Toh shi kenan mutafi Gidan Adam suka fara zuwa A parlo suka samesu Adam Na zaune kan 3str Amira ko Na konce tayi pillow da cinyarsa suna hira jin SLM marsu yasa Adam miqewa Da sauri ya bude musu qofa suna ganin juna Adam ya miqawa Lamidi hannu cikin wasa suka tafa lamido ya kalleshi da kyau yace kaji Dan duniya kana Sha,aninka shiyasa ka wani sheremu yau kwana nawa bakaje gidaba Kai on top banson Sherri shekaran jiyan cammafa naje ko biyaye ai ka tuna ya fada yana kallon fuskar Yusuf din harara Yusuf din ya watsa masa gamida cewa toh ni dai ka kama kanka Dan wlh naga alama zaka jamana raini gun yarinyar nan Yoh raini kuma Na nawa tunda ta ga gadon baccinsa ta kuma yiwa mararsa kallon tsaf ai raini ya qare anan cewar lamido Kenan Adam yace bar Dan iska shima zai worene wannan wuri in kasan dadin da ya qunsa ai bakayi taurin kaiba dry sosai lamido yayi Shi kuma cikin ta kaici yace wallah tallahi kunji Na muku rantsuwar musulmi ko toh wlh ni kam har a bad a bani ba Aysha kam kodako mata sun qare a duniya koda zan rasa rai nane Adam ya kalleshi cikin mmk yace ni kuma Na tabbatar kana tare da wahala wotarana Dai2 lkcin suka zazzauna kan kujera cikin jin kunya Amira ta kawo musu dirings masu sanyi ta gaidasu ganin yadda hamma Yusuf din ya murtuqe fuska yasa ta wuce kitchen dinta taci gaba da aikinta Basu dade ba Yusuf ya miqe yace su tafi gidan Ahmad A baking gate sukayi qaro dashi yana kokarin shiga mota cikin tsoro da firgici da tsananin kaduwa suka isa gun shi da sauri Yusuf ya kamo hannushi....... FAHIMTARWA Da yawa suna min qorafin basa fahimtar me sunan littafinnan yake nufi sabida ganin sunan da yaren fullancine ana yawan cemin menene ma,anar MI,WASMITI toh Manar mi wasmiti dai yana nufin NAYI NADAMA Fatan masu karatu kun gane sunan novel din nayi Nadama Kuma insha Allahu zanci gaba da hada sunan da hausan Ina godiya da kulawarku KINA RAINA UMMI Garkuwa marubuciyar Jennifer fatan alkhairi a gareni Gaisuwa ga dukkan marubutanmu inai mana fatan alkhairi NAYI NADANA MI,WASMITI page 4⃣1⃣to4⃣3⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Hannunsa Ya riqe cikin mmk da kdma da tsabar firgici cikin kaduwa yace Biyaye meke damunka ? Baka da lfy ko? Shiyasa yau kwana 2 bakaje gidaba ko ? Shiru dai baiyi mgn ba Cikin damuwa yace Haba Ahmad ya ina mgn kayi shiru Ji yadda gaba daya ka rame Ase dama shiyasa kake yawan Sa manyan kaya Dan ka boye yadda ka sauyane ? Cikin yanayin shi Na sanyin hali da kawaici da haquri yayi murmushi Garfin hali da qoqarin boye halin da yake ciki Yace Ni wlh matsala ta da kai kenan saurin rudewa jifa yadda ka wani gigice kana ta jeromin Tabbayoyi Toh wacce tabbaya daya nasan Zan amsa maka Adam ne yace ka gaya mana gsky ya fada cikin son gane me Ahmad din ke son boyewa musu Dry yayi cikin qarfin hali yace Bani da wata matsala ni kam Cikin kura masa ido Yusuf yace ka tabbata? Yes bani da matsala ya fada yana kamo hannun lamido Yace on top mu isa kunzo kun tsaidashi a woje Yusuf ne ya kirashe biyaye Na,am ya amsa masa Yace juyo ka kalleni Cikin dryar tausayawa Kansu da Kansu yace anqi juyo wan Da sauri Yusuf ya Sha gaban shi yace nace ka kalli qoyar idana ka cemin baka da matsala Cikin sauri yayi gasa da kanshi Dan yasan muddin ya bar idon Yusuf cikin nasa toh zai gano halin da yake ciki Dan su tun suna yara sukan laqanci halin da Dan uwansu yake ta cikin qwayar idan juna koda ko ya boye a fuskarsa Part dinshi ya nufa riqe da hannun lamido Cikin karaya da yanayin cushewar tunani Yusuf ya kalli Adam cikin rawar murya yace biyaye inajin tsoro Wlh tsoro nakeji Adam kalli yadda Ahmad ya dawo Adam kasani Na Sani iyayenmu sun Sani su Kansu su Bappa Yaya Sun San cewa Ahmad Aysha yakeso Itace burin ranshi Sun kuwa San zai iya zaucewa in aka hanashi ita Adam meyasa Suke son Sabautamin rayur Dan uwana Kanshi yake ta jijjigawa da juya idan shi yasa lips enshi Na qasa a baki ya ciza da qarfi Hawayen da suka cuko a idonsa yakeson su kwaranyo ko zai dainajin nauyin da ya danni qirjinshi Amman ina abin yaqi Da qarfi ya riqe hannu Adam yace Biyaye ni Banajin kaina banajin Aysha Dan uwana nakeji Adam ni Yanxu Na gama tsara komai Na komawa cshool Ba Wanda zan gayawa sai kai da Ahmad Dan banson su Abba su San zan tafi nafiso sai naje Na kirasu Na gaya musu Amman Adam kaga halin da Ahmad yake ciki Adam ko dai Na fasa tafiyar Nanne Adam in natafi Na bar biyaye da kai kadai zaka iya kula dashi Cikin rawan murya Adam Yace kaje insha Allahu ba komai yadda zaka barmu lfy haka zaka dawo ka samemu lfy Duk kulan da kake tunanin zaka bawa Ahmad zan hada da nawa Cikin murmushi takaici yace Ya ja hannushi suka bi bayan su a parlo suka yada zaggo suna ta Dan taba hira Har aka kira sallan LA asar Adam ne ya fara shiga yaje yayi alwala sai lamido yana fita yace Yusuf kuyi saurifa kunsan innah tanan ca tana jirana kuga dare yanayi Tare suka miqe Ahmad dinne ya fara shiga yayi alwalan sai Yusuf din ya shiga sauri sauri yayi ya fito Har yazo baking qofar fita Sai kuma ya dawo da sauri ganin abin mmk Da sauri ya fito parlon ya kira Ahmad din hannushi ya jawo har gaban gado ya kalleshi cikin Tuhuma yace Biyaye jinin menene wannan a kan shimfidarka har kan pillows dinka ? Shiru yayi Cikin kaduwa yace Ahmad tabbayarka fa nakeyi Cikin inda inda ya kama cewa A.a Ai dama Damafa Biyaye ka Dane inda inda ka gayamin gsky Lamido ne ya katseshi da cewa wlh kai dai bakaji Dadiba Yusuf Ka fiye bincike da qididdigar mutane Kazo gidan sabbin amare Dan kaga jini a makwancinsu ka tsaya dogon bincike kai Amman dai anyi surkin banxa Cikin jin dadin zance Ahmad yace qyaleshi dai duk suka fita suna dry Amman banda Yusuf Dan shi ya zargu da jinnan da ya gani Har zasu fita Adam yace bamufa ga qauwar tamuba Ras Ahmad yaji gabansa ya fadi har sai da ya fafe qirjinshi danshi har ga Allah mantawa yakeyi da wata a cikin gidan Lkci daya kuma yaji kunya ta rufeshi ko ba komai Maryam bata cenceci haka daga gareshiba Dan ba laifinta bane Muryar tane ta katseshi da tunanin da yakeyi Cikin Dan sakin fuska tace laa ya Adam Hamma Yusuf ya lamido sannuku da zuwa Da sauri ta nufi kitchen tana bari Na kawo muku abinci Yaya Ta fada tana kallon fuskarAhmad din shi kuwa da sauri ya kauda ganinshi daga gareta Dan kunyarta yaji sosa Yusuf ne yace a a Alhamdulillah mun gaisheku wucewa masallaci zamuyi Cikin Dan tsoro tace Ayyah Hamma Yusuf da sauri haka Ko ruwan Baku shaba Toh mubar sallan kenan ya fada fuska a daure 😡 A ranshi kuma yace ba gashi ba har sun fara tsare mutane da raini Cikin sanyin murya tace A,a Toh Ku gaida su Ummi Harara ya kuma watsa mata yace suwayen yan Aiken naki mu zaki aika Kai ta girgiza gudun kar ta kuma mgn ya zama laifi A ranta tace shi kenan Aysha am ke kam kin kade zama da wannan masifeffen Tare suka fita Ahmad Na bayan su Har yazo baking qofar sai ya kuma komawa yazo dab da ita ya Sa hannushi ya tallabo fuskarta cikin rauni da sanyin murya yace Maryama kiyi haquri ki gafarceni Rau rau tayi da ido alamar kuka da sauri ya zaunar da ita kan kujera yace ki yafemin ba nufina kenan Na cuxguna miki ba kimin afuwa yake yar uwata Cikin sanyin murya tace Ni baka min komaiba ya Ahmad kuma ko ka minima Na yafe Cikin farin ciki ya subbaci goshinta ya fita yana cewa rabbi ya miki albarka Amin tace cikin jin dadin addu,arshi gareta 3:30 pm su inna sukayi sallama da su Ummi suka kama hanyar Yola sun tafi suna kewan juna Yau saura kwana 2 Yusuf ya bar Nigeria Da yamma su Abba da baba bello Na zaune a harabar gidan nasu Yusuf ne yashi cikin nitsuwa ya isa gunsu Cikin biyeyya yace sannuku da hutawa baba Abba yanxu naje hospital baka can anata nemenka kawai suna ganina suka tsareni Baba bello yace a to kace yau ka Sha aiki kenan ehh wlh baba har C,S nayiwa wata mata Ayyah me aka cire ? Da namiji Masha Allah rabbi ya raya amin yace Ya Dan kalli baba bello yace baba Yanxu zan wuce mambila Dan Na kwana biyu bamu hadu da Bappa Yaya ba toh yayi kyau ka gai dasu yaushe zaka dawo ?insha Allahu Gobe zan dawo Abba yace (Allah yare jam wartira on jam) Allah ya kaika lafya ya dawo da ku lfy Ameen ya rabbi yace gamida miqewa ya je ya sallami su Ummi ya kama hanyarshi shi kadai 🚗 Gembu Mambilah Garfe 6 dai2 ya isa farfajiyar gidan ba kowa sai Dan hirarsu da yake juyowa daga cikin parlon baki ya Dan table gaida cewa badu da aiki sai surutu cikin gajiyar hanya Ya bude Qofar kenan ita kuma tazo da Dan gudu gudun ta kawai sai ji yayi ta fada cikin girjinshi a take yaji jinin jikin shi ya dauke duk yaji tsikar jikishi Na tashi qoqolwar shi tayi dip duk network dinshi ya dauke Cikin qarfin halin ya sunkuyar da kanshi Dan ganin wacce wannan dai dai ya tabbatar ko bai ga wayeba yasan macece Dan yaji suka guda biyu a qirjinsa alamun qirjin macece ya have da NASA Ido ya zaro woje Dan mmk da ganin.... ?🍇🍇🍇 NAYI NADAMA MI,WASMITI page 4⃣4⃣to4⃣5⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Yarinyar da ya tsana kamar yadda ya tsani abinda zai cutar da biyayenshi Da sauri cikin jin haushin ta ya yarfa mata mari Cikin jin zafi da sauri cikin raxana ta dago Sosai ta qara tsorita ganin fuskar da bata qaunar gani da sauri ta juya dafe da fuska Cikin zafi nama ya miqo hannu zai cabkota ya dirka mata Na jaki Sadiq dake gaban ta Yace kin banu Aysha kauce Da sauri ta ruga A guje bata tsaya ko inaba sai cikin dakin innayi kan gadon mai rumfanta ta dale tana mai kukan takaici A parlor kuma zama yayi bai kula kowa ba sai faman murtuqe fuska yake da huci Bappa Yaya ne ya Dan kalleshi da kyau a ransa yake mmkin halin irin Na Yusuf shi har abada ba,a gane far in cikinsa da baking cikinsa ko yaushe fuska ba walwalah Cikin kula yace Kai Dudabe meke damunka kaketa huci Anyi din Toh yau kuma da bala,i kazo kenan? Ehh da bala,i nazo yanxu kai kuma kana da bakin mgn ne Bala,I da fitina ya wuce wanda ka janyo mana An janyo din nace an janyo ko Aikin kawai Dan kaga ina binka ina sonka Shine kake son ka samin hawan jini Ka sawa kanka dai Innace ta kalleshi cikin tsokana tace ayagi sarkin fada ka iso har ka fara daga shiga Da dukan matarka kayi slm Sannan ka sauqo kan Bappa an da kuma kanwa zaka kuma hawa Kanki zan hau nai ta surface miki bala,i matuqar kika qara kiran waccar yar yarinyar kuma muna fuka a matsayin matata Innayi ce tace toh dibino gwara muyi axumin mgn in ba so muke a hanamu baccin dare da sababiba Oho dai can ta matse muku ya fada gami da daga kafada Bappa Yaya ne yace Toh tashi mu tfi Masallahci Dudabe am Bazan je da kaiba haka kawai kai ta wani kirana 'Dudabe Nacema bana so Amman taurin kai da son ka konamin rai ya hana ka bari 😡 A haka dai sukaje sukayi sallah Basu dawoba sai da sukayi insha A parlor suke ta Dan hira yanxu ya Dan sauqo Cikin kula ya kalli kakan nashi Yace Bappa Yaya jibi in Allah ya kaimu zan koma wurin karatuna Dan an nememu kwanannan Cikin Dan jin sanyi yace Ayyah dudabe zaka tafi kuma sai mai Nisan kwana Ko zaka dawo ka samemu ko kuma shike nan an rabu Duk da halin irin Na Yusuf yana qaunar kakannishi sosai a ranshi yana sonsu fiye da zaton mutum Cikin qarfin hali yace ba komai kakana zan dawo Na samemu lfy Innayi tace hmm Yusuf am ai dolene watara kam ka dawo ka samu bamu kan doron qasa 😱 hannun ta ya kama ya hada Dana inna yace insha Allah ba komai Suna cikin hiran Bappa Yaya ya miqawa Yusuf din phone dinshi yace hingo kamo min babanku Da sauri ya kalleshi cikin tuhuma yace Me zaka cemai Kafasan ni bansan gulma Dan basu San jibi zan komaba Na kuwa sanka da barin zance yanxu zaka shafa musu zancen Cikin mmk da Al,ajab yake kallonshi A ranshi yake cewa wato so yake ya zulle ya bar matar shi a nan toh lallaiko yaro shirinka yayi nitsa A daqile yace Ina mgn kayi banza dani A Dan fir ya dawo daga nunanin da ya tfi Dry yayi irin ta yaro man kaza kenan A fili kuma cewa yayi toh Na FASA kiranma ba shike nanba? ehh gwara kam Ya fadi tare da miqewa ya nufi dakin innayi yana innayi zo kiban tea Toh tace gamida bin bayan shi Suna shiga ya hau kan mairumfanta ya kishin qida yana kallon rumfar gadon da yasha kolliya a ranshi yake cewa tabbas wannan gado yayi a rayuwarta kuma insha Allah sai Na shigarda gadonnan cikin tarihin rayuwa Haka kawai shi kam yake son gadon kakar tasa haka kawai yake jin nishadi in ya hau gadon da farin ciki Innayi CE ta katsemai 🤔da yakeyi tana toh ga shayin ko a kan gadon zakasha ne? A a zan sauqo mana Amman ajiyeshi ya Dan huce Toh tace gami da dire cup din a qasa Itako Aysha tunda ta shigo ta.kwanta kan gadon tana kukan marinta da yayi a.haka bacci ya saceta Baccinta take cikin jin dadin gadon Shiko Sam bai lura da ita a kan gadonba Shiyasa yayi kwanciyarsa Can cikin bacci ta Dan fara juyi a hankali ta daqo hannuta daya cikin sanyin baccin ta dire hannun kan qirjinshi Lkci daya kuma ta mirgino da qafarta ta daura kan ququnshi cikin sekon 10 duk ta kanainayeshi Cikin firgita ya bude idan shi da sauri ya tashi ya zauna har jikin shi Na bari Cikin takaicin gani wacece ya Daga hannushi sai da ya dubu kan fuskarta ya watsa mata maruka har 3 ajere cikin kidima da firgici ta saki kuka mai qarfin gami da bin bayan shi ta diro daga kan gadon Cikin kuka dataje baking qofar ta juyo ta kalleshi cikin tsana tace mugu azzalumi Allah ya isana wlh bazan yafe maka ba ko qabarinka naci da wuta 😳😡ya zaro mata cikin zafin nama ya diro daga kan gadon yana fadin ke 👉🏻ni kike zagi ? Ehh din an zageka azzalumi Aiko cikin zalumcin ya nufi kanta Dan yana iya babbalata in ya kamata ganin yadda ya nufuta kamar wani ma yunwacin zaki yasa ta arta a guje 🏃🏻‍♀cikin Zafin nama ya rufamata baya bata tsaya ko inaba sai cikin dakin Bappa Yaya Da sauri ya riqota yana ke Ayshatu lfy kuwa ke da waye Ita dai ihu take da.iya qarfinta tana Hamma Yusuf ne Bappa Yaya wlh ka tare shi ka Sani baida imani zai kasheni Toh me kika masa Wlh.ni ban masa komaiba shine ya sameni INA baccina kawai yakama dirkata Shi dai Yusuf huci kawai yake Yayea qoqarin fixgota Cikin tsawa kakan nasu ya jawata ya turata bayanshi yace je kiyi zamanki kai kuma ficemin a daki ko yanxunnan Na kira ubanka nace kazo dukana 😡👉🏻baki ya ciza gamida kada kai yace wlh zaki shiga hannu Na kuma zaki gane kurenki yayi woje yanata huci Bayan fitashi ne ya miqowa Aysha woya yace kamo min bello Karba tayi ta ki rasa sai da ya daga sannnan ta miqa mai ta shige toilet bayan sun gaisa Cikin rada rada yace kai bello kasan Dudabe nata shirin tfy jibi jibinnan ko Ehh yace mai Na Sani Amman shi yana tsamman ban saniba Adam ya zo ya gayamin Toh batun matarsa fa ? Ehh ai tare zasu tfi ko baya so Dan yanxu haka Na gama mata shirin tafiyarta kab Dry yayi cikin jin dadi yace yauwa Allah ya muku albarka daku da zuryarku baki daya Amin ya rabbi ya fada cikin jin dadi Sannan yace toh ka kirashi gobe da safe kace ya taho da ita Dan in Nina fada bazai yardaba Toh shi kenan Bappa A haka sukayi SLM ya kashe woya yana dryar cin nasara Da safe bayan ya gama shirinsa ya shigo ya ya rinqa binsu innayi ko wace har dakinta yana basu kudi da yi musu slm yana ce musu Allah ya sadamu da alkhairi Duk sai yaji ba dadi A farfajiyar gidan yaga Sadiq ya bude but din motarshi yana zuba kaya Ga Aysha kuma a bayan Bappa Yaya tana kuka Cikin tsoro take cewa wlh zai dakeni ni bazan tafi da shiba Cikin mmk da take baki yace ke da Allah can ki rufe mana baki nima motata ba ta daukar mahaukata bane Kai Sadiq Rufemin mota Wanda ya kawoki yazo ya maidake ai ni ba bawan kubane Cikin isa Bappa Yaya yace toh ai bani nace Ku tafi taraba ubankune ya fada kuma tunda kace kai kafi qarfi bari Na gaya mishi Miqawa Sadiq woyar yayi yana maza kamomin bello karba yayi ya kirashi bugu daya ya daga ko slmarsa bai amsaba yace toh bello ga isheshshen Dan naku yace bazai taho da itaba Dry ya danyi Dan yasan anacan ana shan rgima tsakaninmu Yusuf da mutanen gidan baki daya. katse kiran yayi ya kira Yusuf din Bugu daya ya daga cikin takaici Dan yasan mgnar da zai mai Toh kawai yace Ya fito cikin motar woyar Na kunneshi daga dukkan alamu mgn yake mishi har yanxu Da garfi ya fizgo hannuta da ita da jakar tata gaba daya ya cillasu a gaban motar gamida maida marfin gib ya rufe cikin fushi ya shiga ma zaunin direba ya figi motar da qarfin duk abinnan da yake baba bello Na jadda da mai Yusuf karfa kasa yarinyar nan kuka cikin takaicin ansashi daukar ta a dole yace Ni ba ruwan Na da itafa baba,,,,,,,, cikin mota ko a zuciye ya dago,,,,,,,, Ina gaida dukkan ma karanta novel dinnan inai mana fatan alkhairi 🍇🍇🍇🍇 NAYI NADAMA MI,WASMITI page 4⃣6⃣to4⃣8⃣Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Jakarta ya danna mata kan cinyarta cikin mugunta Daga nan bai sake kallon ko gefen da taken ba Titi ya zubawa ido Yanata sharara gudu Kafin 9:11 Am Sun isa Kashe gari Tun da safe Aysha ke kuka wuy wuy da hawaye da suka kasa tsayuwa Saka makon bayanin da Abba ya mata Na tafiyarta tare da Hamma Yusuf din Kuka take sosai tana pita parlorn Abban nata kitchen ta nufa Ummi dake qoqarin hada musu breakfast ta fito da sauri gami da kama hannuta cikin tausaya mata da cikar takaici Dan Sam Ummi bata son abin da zai taba mata autar tannan Daki ta wuce da ita kan gado ta zauna gamida jawota Cikin kuka ita kuma ta zame ta zuba guiwowinta a kasa ta kifa kanta kan cinyar umminta cikin tsananin kuka tace Shi kenan Ummi nikam Na shiga ukuna Ummina cikin Neman alfarma tacigaba da cewa Dan Allah Ummi Ku gafarceni Na tuba kumin afuwa dan son Annabinmu Dan Allah kar kubari ace tare zamu tafi da Hamma Yusuf wlh tsoronshi nakeji Ummi zai kashe miki nifa Haka tai ta kuka tana surutai Ummi ta dago fuskarta tace kalleni nan Aysha Na miki alqawari Indai Na isa Da Hamma ku To insha Allah bazai cutar da keba Kisa ido kigani ni nasan iya koki da dokokin da zan bashi a kanki Haka dai tai ta bata baki da kontar matada hankali Dama tuni an qarisa mata shirinta Ahmad kuma da Adam tun da sukayi sallan asuba suka taho gida Dan yiwa biyayensu rakiya zuwa airport Suna tare a farfajiyar yar gidan bayan an gama dura jakukkunansu a but Cikin nitsuwa Yusuf yaje gaban baba bello ya Dan duqa gamida cire hular kansa cikin sanyin murya yace toh baba zan tafi fatan Allah ya qaddara saduwarmu kan alkhairi ya Dan yi shiru kadan ya Dan kuma dago kanshi cikin rawan murya yace Ku gafarceni baba in akwai abin da Na muku cikin rashin Sani A hankali baba bello ya dafa kanshi cikin son Dan Dan uwanbnashi yace baka mana komai ba Yusuf Allah ya maka albarka Yusuf mu iyayenku xuqatanmu baza su iya yin fushi da kuba duk da kaso ka boye min tafiyar Amman ya zama dole nasan duk woni motsinaka shiyasa tun jiya Na sanar da kai munSan da batun tafiyar taka Dan kar da safe ka shirya ka tafi ba tare da ka nemi afuwar iyayenka da sanya albarkan suba Allah yayima albarka Hannun shi ya Sara kan hannu baba bello da ke cikin sumar kanshi yace Amin ya rabbi A hankali ya taka yaje Gaba mahaifinshi Cikin biyeyya ya duqa gaban shi ya dago ya kalli ma haifin nashi yace Abba ka gafarceni ka San yamin albarka ko zan samu sauqi cikin rayuwata Ya kuma Dan duqar da kanshi Yagi gaba da cewa yau zan tafi ina mana fatan saduwa cikin alkhairi Kai Abban ya jinjina yace ba komai Yusuf Allah ya muku albarka baki dayanku da kai da yan uwanka INA maka fatan alkhairi cikin karatun ka Amin yace cikin jin dadi Haka yaje gaban Nenne ita ta samai albarka A gaban Ummi ya tsaya cikin mmk ganin tana riqe da hannun Aysha ita kuma sai kuka take fuskarnan duk tayi jazur da ita Ba tare da ya qara kallon inda Ayshan takeba yace toh Ummi ni kam zan tafi sai kuma Allah ya gaddara saduwarmu Toh Allah ya kaiku lfy ya kuma dawo daku lfy Amin yace cikin rashin gane me zancen Ummi yake nufi Allah ya kaimu lfy to shi da waye kenan Cikin ransa kuma yace toh me ruwanka kai da zaka bar musu qasar Cikin Dan sassarfa ya qarisa gun Adam rungume juna sukayi cikin qaunar juna Adam ya Dan kai bakinshi dai2 kunneshi cikin sanyin jiki yace Zamuyi missing dinka biyaye A hankali yace insha Allah kamar yau zan dawo muci gaba da rayuwar mu mu 3 dinmu Har yanxu suna ruqqume da juna cikin jadda dawa Yusuf ya Dan bubbugi bayan Adam yace Adam nabar amanar Ahmad dinmu a hannuka Dan Allah ka kukan mana dashi ka Samar mai farinciki insha Allah nima inna isa zan aiwatar da aikin ummra zan roqi mahaliccinmu da ya cikawa Dan uwanmu farin cikinsa Cikin qarfin hali Adam yace Na karbi wannan amanar A haka ya sakeshi tare suka nufi gun da Ahmad din yake tsaye yana jingine da jikin mota Anuty Sadiya Na gefebshi wanda yanxu kenan isowarta Ya Isa gaban shi kenan Abba ya iso riqe da hannu Aysha cikin muryar umurni ya kamo hannu Yusuf din ya damqa mai annum Aysha cikin nasa ya hada ya rumtsesu Cikin mmk ya dago ya zubawa Abba Ido cikin Ido sukayi Cikin kaduwa ya bude baki zaiyi mgn Da sauri Abba ya dakatar dashi dacewa Bana son jin komai daga gareka Yusuf a yanxu haka umurni nake baka kai tsaye ka kama hannun matarka tare zaku tafi wannan umurnine kuma kab mun gama yanke wannan hukuncin Cikin razani da kidima ya maida dubanshi kan baba bello da alamun tabbaya Kai ya jinjina mai cikin alamun yes umurnine Ummi ya kuma kallah cikin daure fuska tamai nuni da amanace Cikin tsananin bugawar qirji ya maida dubanshi ga Ahmad dake gaban shi da ya zama tamkar an dasashi Girjinshi ke duka 3 3 a take zufa ta fara keti mai tabbas yasan da tfyar Yusuf Amman baiyi tunanin za a hadashi da Aysha ba Cikin sauri ya dawo kanshi ya kalli fuskar Aysha Ido cikin Ido sukayi cikin wata iriyar narkekkiyar murya ta saki kuka mai tsuma xuciyar mai sauraro Kuka take tana wayyo ya Ahmad dina shike nan kun rabani da ya Ahmad dina Cikin azama ta fizge hannuta daga cikin hannu Yusuf din da ya zama tamkar ruwan ya cinyeshi Da qarfin ta fada qirjin Ahmad din ta Sa hannuta ta qaqumishi ta mannashi da qirjinta tamkar zasu chige cikin juna Gaba daya shiki kam ya zama tamkar takarda jinshi yake a tsakiya shi ba sama ba shi ba qasaba tabbas badan a jingine yake da jikin motoba da tuni sun kai qasa Bugun zuciyarsa kuwa tamkar zata balla girjinsa ta fito woje qoqol warsa ko gaba daya ta cushe mai ji yake kamar zai zauce Allah sarki Ahmad damo sarkin haquri A hakan yayi murmushin qarfin hali yasa hannushi ya dagota cikin ciccijewar voice yace Aysha ai tafi ya ba mutuwa bace koba Dade ko banjima zaki damo ki samemu Kuma muma zamuna kawo muku ziyara Ita dai kuka take harkamar zata shide Hannuta ya kamo ya miqawa Yusuf cikin qarfin hali da juriya yayi Dan murmushi yace Biyaye ko zaka iya riqe wannan amanar da zan baka cikin takun jarumta ya matso gareshi yace Yusuf bazan taba gane kana so naba sai ka tayani son abinda nakeso fiye da kaina Dry ya danyi kuma cikin dacin rayuwa yace INA nufin Aysha kuma INA nufin so Na Dan uwanta ka Cikin mmk Yusuf ya zuba mai I do shi tunda suke da Ahmad bai taba kiran shi da woni sunan da ya wuce biyayeba Amman yau ya kirashi da yusuf kenan yana nufin amanar dai yake bashi da gsk Da qarfi ya jawoshi ya fada jikin shi runqume juna sukayi kamar zasu shige jikin juna Cikin rada yace Ahmad nayima alqawari zan dawoma da farin cikinka Cikin juya kai yace Na yarda Amman in kasa Aysha farin ciki ne koda INA cikin qabarina zanyi farin ciki biyaye am Da sauri cikin razani😱 Yusuf yasa hannu ya rufe mai baki cikin firgici ya rinqa ja da baya yana fadin a a A a kam Ahmad zamu rayuwa tare kuma Zamu mutum tare Shiko Ahmad Abba ne yazo ya jashi sukayi cikin gida yana juyawa yana kallon Yusuf dinncikin sanyi ya daga mai hannu tare da furta mai zanyi kewarka Dan uwana Usman ko da Rabi,u gaba daya jikin su yayi sanyi Abdul ka mai saurin kuka tuni yake ta sharbar kuka Baba bello da Adam ne kadai suka yi masu rekeyi Basu dawoba har saida jirginsu ya tashi Allah sarki Ahmad ko ya rayuwa zata kasan CE mai ne ? Abinda masu karatu suka rinqa kirana suna tabbaya ta kenan ko ya Yusuf zai yi da amanar da aka bashi ? Duk dai am soshinku Na gaba kunbiyoni dai a hankali Fatan alkhairi ga dukkan daukacin alummar musulmai Inai mana barka da jumma,a Dan jin ra ayinku masu karatu qofar a bude take da shawarwarinku ina alfahari daku NAYI NADAMA MI,WASMITI.. page 4⃣9⃣to5⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Maryam kam tun ran dasu Hamma Yusuf suka zo musu ziyara Suka fita tare da ya Ahmad har yau bata kuma sashi a idonta ba Haka kuwa rayuwa ke tafiyar musu kullum dare Ahmad zaiyi ta kukan zuci da zantuka cikin tsananin quncin rayuwa Haka kuwa sukaci gaba da rayuwa Sai dai al,amarin Na yau din ya firgita Maryam sosai Misalin Garfe 8:30 Pm Maryam Na cikin kitchen tana Dan tafasa indomi Dan tunda gari ya waye batasa komai a bakinta ba Daga cikin kitchen din taji sautin da ta saba ji matuqar dare yayi Cikin fargaba da tausayawa Dan uwan nata Ta fito ta nufu qofar dakinshi A hankali ta zame a baking qofar Cikin fitar hayyaci take jin zantukan da ya Ahmad din yakeyi Cikin kuka yake ta nanata innalillahi wa,inna ilaahi raji,un Cikin muryar kuka sosai kamar yaro Yake cewa ya Ubungijina ka kawo min mafita Allah Na ka dubeni da idon Rahama rabbi ka bani ikon cinye wannan jarrabawar da ka jarab ceni da ita yaci gaba da fadin Woyyo Allah Wayyo yar uwata Aysha ko cikin wanne hali zaki kasance Allah sarki Dan uwana biyaye Na kamin adalci ka luranmi da burin raina Ki gafarceni Yar uwata Na cutar da zuciyarki Cikin tsananin kuka yaci gaba da cewa Ya Allah menayi gareka ka hukuntani da wannan baqin cikin rayuwa ya ugaban gijina kowa Na cikin farin ciki sai ni zuciyata ke suyuwa Ya Allah ka jibanci lamuranna Kukan da yakeyi ya sata kuka sosai tun tanayi qasa 2 cikin sheshsheqa har kukan yaci qarfin ta ya kufce mata Can cikin kukan tajishi cikin rawar murya yana Astaqafirillah Astaqafirilah Haka yayi ta Nana tawa har zuwa woni Dan lokaci can kuma tajishi cikin kuka mai tsananin da alamar toshewar numfashi Yana fadin ya Allah kai kaso ka ganni a haka ya ubangijina kai kafini sanin matsala ta ya Allah ka karemin imanina ya Allah ka kawo min sauqi tako wacce hanya Cikin Jan numfashi yace koda ajalinane matuqar dai shine waraka ga rayuwata Allah ka bani Sa,ar tafiya kawai Ya Allah ka gafar tamin kura kuraina Allah ka bani ikon sauqi haqqin matata maryama da ya rataya a wuyana Yana cikin haka Wani irin tari mai garfi ya sarqa fe mai wuya Trin yake yana fadin ase dama bazan rayu dakeba Aysha Ayyah yar uwata ko zaki gafar tamin nan kuma tari ya rufeshi mgnar ta tsaya sai tarin da yakeyi cikin jin daukewar numfashi ya rinqa zagaya cikin dakin kamar mai yin dawafi Cikin tsananin kuka da firgita da fitar hankali Maryam ta zame a baking qofar ta konta kuka takeyi sosai Kukan takeyi irin kukan da Dan Adam zai iya suma da kaji kukan kasan bata cikin hayyacinta Qofar take bugawa da qarfin cikin rawar murya Take ta kwada mai kira tana Ya Ahmad Zo ka bude min qofar ya Ahmad Ka budemin wayyo Allah Na Dan uwana wayyo Abba Na wayyo Nenne na kuka take sosai tana buge buge kamar ta bebbiya tana ya Ahmad ka bude dan Allah kazo ka budemin qofar Cikin rike cewar ya rinqa salati yana lalabu qofar Dan Sam idonshi bai gani da gyar yake furta Ina kike Maryama ban gankiba Na rasa qofar Ita dai kukan takeyi tana buga qofar da iya qarfin ta Da gyar ya samu ya lalubo qofar ya bude Yana budewa yaji ta konce a qasa tanata kuka mai qona zuciya Da sauri ya durqusa guywa bibbiyu hannushi ya Sa ya kamata Yana fadin Maryama kiyi shiru kiyi haquri zo ki fadamin waya taba min ke ita dai kukan take da cure cure tana tuttureshi gashi da iya qarfin ta take kukan a nata tunanin tanayi da qarfine Dan a kawo mata dauki Da gyar ya tattaro iya sauran qarfin shi ya matseta a cikin qirjinshi Amman Sam ta kasa tsaida kukan nata Cikin tausayi yace maryama ban so cutar dakeba ya yar uwata idan laifin nawa ne kimin afuwa banson Na mutum da nauyin cutar da ke a zuciyata kanta ya qara mannawa kan qahon xuciyarsa cikin karaya yace Maryama kiji bugun xuciya tako maryama ba zanyi tsawon rayuwa ba shiyasa gwara Na nemi gafararki Zancenshn ya qara ingizata ta qara rushewa da kuka tana qamqameshi cikin tsoro tana fadin bazaka mutuba ya Ahmad insha Allahu zamu rayuwa tare mu mutum tare ya Ahmad in ka mutum nima zan mutum Ganin ta rude sai surutai takeyi duk yayi iya yinshi ta kasa barin kukan Shiyasa cikin Hikima Ya tallabo Fuskarta Cikin tausayawa Kansu da Kansu ya tsurawa bakinta Ido yadda take kuka baji ba gani A hankali qoqolwarsa ta rinqa bashi umurni Cikin sanyi ya manna bikinshi da nata Da dabara ya samu ya zira harshenshi cikin bakinta A hankali yaji jikinshi Ya fara sakewa tako ina yaji kamar ana watsa mai ruwan zafi a take idanshi ya fara canzawa Cikin zafin nama ya samu ya cabko harshenta ya rinqa tsotsan harshen cikin wani yanayi ya fara sarrafata Itako gaba daya jikin ta ya Debi bari da firgici jin irin karatun da yayan nata yake qoqarin biya mata nanda nan ta fara tureshi cikin tsoro da son zaro bakinta daga nashi Amman Ina ta kasa A hankali ya zare bakinshi daga Nata ya nufi kan gado ya zube sai faman maida numfashi da mishi yake tayi Da hamzarita ta sake miqewa a karo Na 3 ta samu ta miqe din bata fadiba ta nufi kan gadon Zama tayi a gefen kanshi tana Ya Ahmad tashi mu tafi asbiti Hannushi yasa ya kamata ya kontar da ita a gefenshi cikin Rada yace maryama bani haqqina ko zan samu sauqin zogin da nakeji Zuba mai indo kawai tayi tana zubda qollah😭 A hankali ya ronqofo kanta cikin hikima ya zare rigar jikin ta ya rinqa sauqe mata salo kala kala A hankali naji sautin kuka guda biyu Na tashi Ita kuka take Na tunanin irin shirin da Aysha take yiwa derennan ga ya Ahmad din ase abin zai canza ya dawo gareta Shiko kuka yake yana ya Allah ka zama sheidana Na sauqi haqqin maryama da ya rataya a wuyana rabbi ka bani ladan biyeyya da nayiwa iyayena Bayan sun gama dawowa haiyacinsu Ya tashi ya hada mata ruwan zafi ta Dan gasa jikinta tayi wonka ta fito ta kinga gefen shi shima wonkan yaje yayi gamida yin alwala yazo yayi ta nafilfili Sai da akayi kiran salah ya tasheta shi kuma ya nufi masallaci Bayan ya dawo daga masallacin ya samu bata nan Cikin mutuwar jiki ya konta Zuciyarsa Na bugawa a ranshi yaji bai yiwa maryama tashi Adalciba a fili yace da Aysha ce da bazan mata hakab da zan bataba kulawa t sosai Da gwarin guywa ya nufi dakinta tun da tazo gidan bai taba shi gaba sai yau Sosai yayi mmkin ganin ta konce hawayen Na bin fuskarta da sauri ya qarasa gunta cikin Dan kula ya tallabota ya daurata kan cinyarsa Maryama ni nasaki kuka ko ki gafar ceni kar kijamin Allah ya isa Kai ta rinqa juyawa tana zubda qollah😭 cikin sanyin murya tace ya Ahmad ba kamin komai ba kuma ko kamin ma Na yafe Toh meyasa saki Kuka Kaine ya Ahmad Da sauri yace kuma kince ban mki komai ba Ehh bani kake yiwaba Toh me NAYI gayamin yake yar wuta Na baki haquri Cikin kuka tace ya Ahmad meyasa bazaka Sa haquri a rankaba ya Ahmad ka ruqwumi qaddara mana ka dena azabtar da zuciyarka da ta maso yanka da halin da kake ciki Cikin cije lebe yace maryama ba yin kaina bane bani da yadda zanyi Cikin kula tace ayyah ya Ahmad duk da nasan ba sona kakeyiba Amman zan roqeka alfarma ka daina rufe qofar ka gareni Da sauri ya katseta da cewa waya CE miki ban sonki kin tabajin inda Dan uwa yaqi yar uwarsa Cikin kukan tace Ya za ayi in yarda kana sona Cikin qarfin hali da qoqarin ganin ya fatan ta mata yace zo zonannki gani Bakinshi ya hade dannata ya rinqa tsotsar harshenta sai da yaji tayi nuqui ya zare bakinshi ya dan nunata yace Maryama zabin Allah kece zabin da Allah ya min kuma bazanngi zabin mahaliccina ba cikin Dan jin sanyi tayi ajiyar hrt tace I love U so much my dear Broz Me 2 Yace mata gamida fita ya nufi dakinsa Kai tsaye toilet ya nufa Dan amai yakeji mai bala,in zafi yake jin yana tuqarsa daga qahon zuciyarshi Sosai yaketa kakari ga wani zazzabi mai zafi da ya rufeshi a take Cikin tsinkewar zuciya da frigata da tsantsar azaba ya zubawa a man da yake kwara wan ido 😳 NAYI NADAMA MI, WASMITI page5⃣1⃣to5⃣3⃣ Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Jini ne guda2 baqiqqirin dashi aman yayi sosai Cikin wahala da dimuwa ya koma cikin dakin kan gadon shi ya fada Cikin maida numfashi a hawale cikin tausa yawa kanshi yake qoqe qollahr😭da ta cicciko mai ido A ranshi yake tunanin wannan karo Na biyu kenan yana aman jininnan ran da Maryam ta tare da yau kuma Cikin tunanin da azabar da yakejin baccin wahala ya saceshi Dan wannan lkcin ya kasance kamar shine dare a gareshi daran kuma yakan zame mai tamkar rana da wuta a cikin zuciyarsa Tin daga wannan rana Maryam take shigewa rayuwar Ahmad sosai Dan qoqarin qanin ta debe mai kewa ta Dan kawar mai da matsalolinshi Ba laifi kuma iya dai dai gorgodo ya sake Yana boye damu warshi Dan ganin Maryama manshi Na shiga ciki. Damu sosai Sai dai banan gizo ke saqanba Ase a hankali ciwon zuciya ya gama raraka qarkuwar jikin Ahmad Wata rana da aman ya sashi a agaba Dole ya shirya cikin sirri yaje hospital gojin forko da akayi aka gano zuciyar Sa ta samu mugun raunin dr Jabir ne ya kalleshi cikin kula da tausa yawa yace Ahmad dole sai anma dashen zuciya Kai ya sunkuyar cikin siyayar da qollah😭 ya Dan kuma daqowa yace Dan Allah doctor ina Neman alfarmanka plx wannan mgn ta zama sirri tsakani Na da kai karka gayawa Abba Na Cikin mmk Dr yace Ahmad me kake nufi zaka boye musu abinda ke damunka ne shin sai ciwon ya kasheka ne kakeson su Sani Ko nufinka bazaka nemi mgni ba Na gayama dole ayi dashen zuciya kuma mu anan ba,ayi dole zamu fidda kai India ne Dan acan muke da qorarrun likitocin zuciya Zan nemi mgn Dr kuma zan fidda kaina India a bincikeni in takama ajene ma Na tabbatar zaka tsaya min a mddin Abba Na Toh meya baka son shi din ya Sani ? Sabida zai cutu nikuma ban son abinda zai cutarmin dashi In yaji shima zai iya kamuwa da ciwon Na tabbatar Abba zaisamu matsala matuqar yaji cutar dake jikina kaima da kanka kasan rayuwara ta azgara ai shiyasa nafi son sai nasamu sauqi Ko kuma sabanin n hakan inyaso a gaya mai daga baya Cikin sanyin jiki Dr yace haba dai Ahmad aishi cuta ba mutuwa bane zafin ciwo bai kawo qarshen numfashi Haka dai yai ta kontar mai da hankali Cikin wota 2 suka kammala shirye shiryen tfyar cikin sirri ba Tate da kowa ya saniba Kullum Yusuf sai ya kira Ahmad da Adam dama wannan Al,adarsu kenan ko basa tare sai sun Kirayi juna da safe Dan jin lfyar juna da dare suyi sai da safe Sosai Ahmad ke qarfin halinsa kan baya son kowa ya gane ciwon dake tare dashi Lkta da dama in yaje gida yakan zauna yasa Nenne shi a gaba yana tuna wanne irin hali zata shiga ran da babu shi sautari in yaji haka yakan fita kawai ya komai part dinsu da a yanxu ya zama nasu Usman yai ta kuka Wata rana da yamma yana zaune a parlon shida Maryam Na konce a gefebshi tayi pillow da cinyarsa A hankali cikin hikima ya tura hannushi cikin rigarta cikin tafiyar tsutsa y sauqe hannun akan qirjinta Ya rinqa shafawa A hankali ta lumshe idanta gamida sauqe gajiyar hrt Kanshi ya Dan ronqofo saitin kunnetan yace maryama tawa shin tsaka Nina da ke waye rego ya fada yana shafa mararta A Dan kunyace tace Ya.Ahmad me mukayi na raqunta Biki ya Dan ciza yace yoh har yanxu ban samu Na baki rain on Magaji naba INA tsorofa kar bazan samu mai min addu,a ba Da sauri ta tashi ta zauna kan cinyarsa tana fuskantarshi tace nacema bansan iri zancen nan naka ko Toh nayi shiru Masoyiyata maryama Cikin jin dadi ta sanqalo wuyarsa ta hada bakinsu wuri daya ta rinqa bashi keutar kis masu zafi Cikin bugatuwa yace Maryam mutafi daki A kuyance tace Kai ya Ahmad me zamuyi a daki kuma Bakinshi ya kai saitin Kunneta yace farauta zamiyi Na farauto baby's A kunyace tayi cikin daki cikin fatan Allah yasa ta samu ciki a yau dinnan ko zai samu mgji Dan yau saura 1 week su tafi shi da Dr Bayan komai ya LFA sun dawo hayya cinsu yana shafamararta yana Allah ka inqatamin A hankali woyarsa ta fara suwa da sauri ya daga ganin Abba Na a rubuce a fuskar woyar Toh ganin zuwa Abba yamxuma kuwa Sauri sauri yayi wonka ya nufi gida Cikin sanyi sanyi yayi slm gami da shiga parlon abban Baya ya zauna gefenshi kadan daga qasa kan carpet A hankali yace abba barka da gida Barkadai Ahmad Abba gani Cikin wani irin yanayi Abba ya dauki duk takardun binciken lfyar Ahmad din ya ajiye mai a gaban shi Cikin mmk ya daqo kanshi ya zubawa abban Ido Shi kuwa Abba komawa yayi ya zauna gamida dafe qirjinshi cikin cijewar voice yace Ahmad me wanna Ahmad ase a duniyan zaka iya boye min wata matsala taka Cikin salqewar qarshe yace Tun yaushe kake tare da wannan mugun ciwon ni dai Ahmad ka boye mun cutar dake jikinka Cikin zubar qollah😭 ya kontar da kanshi kan cinyar Abba ya rinqa zubda qollah😭 cikin jin zafi azuciyarshi ya kalli abban yace Abba toh ya zamuyi ya rigada rayuwa ta zo qarshe dole Kunasona INA sonku dole mutuwa zata rabamu zan tafi Na bar Yusuf da Adam cikin kadaicina Abba zakayi rashina dole da nasan wannan ciwon bazai barniba Ina tausa yawa nennena ko ya zatayi ran da taga gawata a miwe a gabanta Nan kuka yaci qarfin su su duka biyu aka rasamai bawa woni haquri a cikin su Can dai Abba ya rinqa shafa kanshi cikin kontar da hankali yace Ahmad cuta bata kawo mutuwa ba mmk yanzu wanda ke da lfy ya mace Allah ya barmana kai din Tun randa kukayi mgn da Dr jabeer bai bariya qara koda kwana dayaba har gida yazo ya gayamin matsalar taka kuma duk shirin tafiyar nan da akeyi dani akeyinta tare zamu tafi insha Allahu zamu dawo cikin nasara Ka kontarda hankalinka Haka dai sukayi mgnarsu su biyu suka rufe Yakarbi takardu ya tafi dasu Part din Nenne shi ya nufa yayi SLM bata parlon Dan haka kai tsaye ya wuce cikin bedroom Tana konce gefen gado cikin fara ta amsa slmar gami da nuna mai gefen ta a hankali yazo ya durqusa a gabanta ya manna kanshi kan cikin ta Razana sosai Nenne tayi Dan wani irin sanyi da taji cikin cikin ta irin sanyi da taji a kwana kin da mahaifinta zai rasu hannuta ta Dora a kanshi hannu har bari yake tace Ahmad baka da lfy ne meke faruwa da Kaine ya kai Dana cikin qarfin hali yace ba komai Shiru sukayi Na Dan wani lkci can dai ta dago kanta ta leqa fuskar dan nata Cikin razani da mmk ta taso zaune 😳🙉😱😰 Ku biyoni a sannudai yanxu zamu fara ninqaya cikin lbrin A gsky INA Alfa hari daku Tabital Fulaku group ban manta da kuba novels group Dan gyaran kanmu INA jin dadinku😍😘😍😘 🍇🍇🍇🍇🍇 NAYI NADAMA MI WASMITI page5⃣4⃣to5⃣5⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Cikin mmk tace kai Ahmad yanxu muna mgna yanxu kuma kayi bacci a take Murmushi ya danyi gamida miqewa yace wlh baccin yaci qarfinane shiyasa Nenne am Toh koma gidan ka kayi baccin ka Toh yace gamida yi mata slm ya fita ya tafi Yau Monday kuma yaune da yamma su Ahmad da Abba zasu tafi Tin safe Maryam take Dan harhada damai kayanshi adan ma daidaiciyar jakarsa🎒 Ta Dan bude zip din bayan jakar kenan da nufin zata samai turarenshi a ciki taji takardu a ciki A hankali ta jawosu Dan gyara shirin zamansu Cikin mmk da zare ido ta nufi parlon Da sauri ta qarisa gun shi cikin tuhuma Tace ya Ahmad Me wannan me nake gani ya Ahmad ciwon zuciya ase dama abinda zai kaika India kenan Sai hawaye da yake bin fuskarta cikin kukan tce ya Ahmad meyasa kayi shiru A hankali ya daqo Cikin sanyin jiki yace Toh maryama in Na gaya miki ma mai muka iya bawai Na boye miki Dan wani abu bane Kawai dai banson kowa ya sanine Dan gudun kar a gayawa Nenne Na Cikin muryar kuka tayi dakinta Da sauri ya bita Tana shiga ta rufe qofar kan gado ta fada ta rinqa kuka mai zafi cikin firgici A bakin kofa ya tsaya yana kiranta cikin salon lallashi da waqa waqa ina kikene masoyiya ta Na duba gabas ban gankiba Na Duba yamma ban gankiba naje a arewa banga ya tamkarkiba 😜😝 naga yammata kala kala bbanga kamarkiba maryama tawa pito kixo gareni Cikin kuka da Dan gudu gudu ta zo ta bude qofar hannu ya bude mata cikin goge qollah😭 ta fada cikin girjinshi Ajiyar hrt yayi gamida meda hannushi ya matseta cikin jikin shi yana sauqe numfashi cikin raunin muryar tace ya Ahmad tare zamu tafi ko ? Ido ya lumshe gamida dagota yana kallonta a hankali ya rinqa shafa fuskarta hannushi daya kuma Na kan qirjinta yana Dan canza salon zance a hankali ya rada mata kiyi haquri ba Dadewa zamuyiba kuma kinga tare da Abba zamuje Cikin zuba mata ido ya manna bakinshi da nata ya rinqa tsotsar lips dinta saida yaji gaba daya ta sake Tana ta qoqarin kaisu qasa Cikin qarfin hali Ya Dan zame bakinshi daga nata ya jata suka koma daki kan gado suka zube cikin dabur cewar murya da buqatuwa yace Maryama Na roqeki kar ki gayawa Nenne batun ciwona kinjiko kimin alfarmannan yake matata Cikin sanyin jiki tace nayi alqawari bazan fadawa kowaba Cikin ji. Dadi ya jawota cikin jikishi daga nan kuma suka shiga fagen yaqi suka rinqa kaiwa arna hari suna kashesu😜😝 A ranar jirginsu ✈ya daga sun isa lfy har an fara binceken lfyar Ahmad din.. Gasar saudiya 🕋 Cikin birin madinatul Munauwarah Yau kusan 3 weeks kenan da dawowar Yusuf da Ciggam dinshi injishi da fada daga zuwa Nigeria Hutu aka manna mai ita Duk sawon kwana kinnan Tun randa sukazo bata qara Sa Yusuf a idantaba Tinda suka isa cikin gidan ta zauna a parlon cikin gajiya da yunwa Tunda ya shiga part dinshi bata sake yin motsinshiba Har aka kira sallan maqqariba Sosai takejin kiran sallan da akeyi daga cikin masallancin Madina Dan gidansu ba nisa da masallacin zakaji duk abinda akeyi radau Hatta hasken fitulun masalacin ana gani ras Cikin tsoro da jin Dan jimamin gidan Ta nufi cikin dakin komai nanan ras dakin tsaf anyi mai gyara sai qamshi yakeyi Lkci daya kuma tunanin gida ya fado mata sai kuka Cikin kuka take fadin shike nan haka zan rayu ni kadai duk an rabani da yan uwana ba uwa ba uba ba yayu ba qanne kuka sosai ya kofcemata duk da zuwa yanxu hawayen ta ya fara qafewa Cikin kukan taje tayi alwala tazo ta gabatar da sllahn maqqariba bata tashi a wurin ba har aka kira isha Sallan kawai tayi ta kuma ci gaba da Kukanta Haka ta zauna ba ci ba Sha sai tunani da tsoro da firgici da suka isheta Koda qari ya waye bata fito ko parlon ba haka ta wuni cikin tsoro da kadaici Haka ta wuni ba abinda ke daga ta kan carpet din sllahnan nata sai alwala Haka ta rayu tsawon kwana 3 in banda ruwan da takesha ba abinda takeci Duk tagala bata hatta jikinta in ta tashi tsaye sai taji tana bari kamar zata fadi ga Dan banzan yunwa da jiri da takeji Dole ganin tana qoqarin rasa ranta a rana 4 ta fito parlon cikin tafiyar gala baita ta nufi wani Dan steep Wanda daga dukkan alamu kitchen ne A hankali cikin jin yunwa ta zubawa kitchen din I do komai Na buqatar rayuwa akwai can Gefe ta hango firij da sauri ta qarisa gun cikin tasan hannu ta bude Da sauri ta rinqa ballot inabin ciki masu sanyi ta rinqa ci sai da taji haqwaranta sun mace da sanyi a hankali ta rinqa sauqe ajiyar zuciya A wurin ta zame ta konta Dan jin cikinta Na murdawa konciya tayi cikin sheshsheqar kuka tana fadin ko mutuwa zanyi ba ruwan Hamma Yusuf mugu azzalumi ya ajiyeni a gida kamar karya ni kadai Cikin qunci tace da ya Ahmad da sai gata ya isheni Can kuma ta rinqa sake numfashi bacci mai dadi ya kwasheta a gun Itace bata farkaba sai kiran sallah da ya tada ita Cikin Dan jin qarfin ta dabi inabin da tufa ta fito takaishi dakinta ta dawo parlon ta Debi kayanta ta shigar Dakinta Tun daga ranan haka take rayuwarta sai tayi kwana 3 ana 4 ta fito ta danci fruits tun yana mata dadi har ya dena mata dadin sai dai taci kawai Dan kar yunwa ta kashe ta Tuni kuma yuwwar ta shiga jikin ta duk ta Dan jeme Kuma ga rashin qarfin ko wonka tayi sai tayita haki shiko Yusuf zuwa yanxu yana ma man tawa da wata halitta a cikin gidan duk da kullum yayi woya da mutananen gida sai sun tabbayeshi ita Haka zai ta musu kone kone ko yace yana cikin makaranta ko gani yanxu Na fita gida ko kuma wlh INA cikin masallaci In ance woyartafa sai yace ai ita tace bata buqatar woyar tawama ta ishemu Haka dai rayuwa tayi ta juyawa Ranar wata jumma,a tun da safe Yusuf yayi wonka cikin shiga ta alfarma irin shigar larabawan Riga da wondone masu taushi bugun pakistan yayi rasa ya fito cikin haiba ya Dan kifa yar pulannar da suke sawa gashinshi mai laushi da bakinan sai sheqi yakeyi Ya fesaturare mai qamshi gaba daya ya debi qamshi fa sheqi ya fito cin nitsuwa ya nufi masallahci Dan wannan dabi,ar shi kenan duk ran jumma,a a masallacin yake wuni Ita kuma Aysha tun safiyar ta tashi da wani irin ciwon mara mai tsananin Wanda ko motsi mai qarfin tayi sai taji kamar marar zata balle ga azabebben ciwon kai da zazzabi mai zafi Cikin jikinta takejin sanyi Na ratsa hanjin ta Haka tayi ta rawar sanyi cikin kuka Haka ta wuni cikin azaba ko sallah bata samu ta tashi ta tayiba Qarfe 3:00 pm Na Nigeria Wanda yayi dai dai da 5:00 pm Na saudiya A hankali woyar yusuf ta fara suwa kamar bazai dagaba sai ya kuma daga yaga Ummi CE ke kiran shi Cikin sauri sauri ya fita cikin harabar masallacin Cikin mmk yake kallon sararin samaniyar hadarine baqiqqirin ya hado ga iska mai sanyi ta fara kadawa alamar forkon damina Gaba daya ya zaman sararin samaniyar ta canca kala iskamai dadi keta kadawa yana sauqe nishadi cikin zucuyar duk wata halitta dake rayuwa a wurin Suwar woyar ne ya kuma katseshi cikin duniya nishadin da ya tafi Da sauri ya daga gami da yin sallama cikin biyeyya yace yi haquri Ummi bana kusane Hmm tace gamida cewa ka bawa Aysha woya Cikin Dan yin Jim yace Ayyah Ummi ai bana gida Kana ina? Kinsan yau jumna,a INA masallaci Cikin Dan fada fada tace kai kaga shiga hankalinka rainin wayon ya isa haka ka kama kanka Kullum nakira ka hadani da yarinya sai kai tamin kauce kauce Ina gayama yanxunnan nakeso ka kaimata woya Cikin Dan yamutsa fuska yace Kiyi haquri Ummi in NAYI sallar maqqariba da insha zan kai mata Ka kaimata kawai dai yau dinnan kam nace Toh yace gamida katse kiran Bayan an idar da sallan insha ya fito ya nufi gida cikin nishadi dajin dadin iskar dake kadawa idanshi ya lumshi gami da yin ajiyar zuciya sosai yanayin ke sashi nishadi aduk lkcin da yaji irin yanayinnan shi kadai yasan yadda yakeji a ciki jikin shi jininshi kan carke ruwan kanshi Na sinkewa ta yadda yake sauqar mai da Sha,wa mai qarfin da fiddashi hayyacinsa Cikin tsotsar lips dinshi da Dan rawar sanyi ya qarisa gidan...... Fatan alkhairi a gareku masoyana INA jin dadin irin😍😘 kulawar da kuke bani ℍᗅႮՏᗅ ℕᝪᏉℰℒՏ ՏᝪKᝪᝨᝪ ᗯℍᗅᝨՏᗅℙℙ ℕᝪ: 07068808039 ᗯℰℬՏⅈᝨℰ : ᗅℬⅅႮℒℳKⅈℬᗅℬ.ℍℰᝣᗅᝨ.ℂᝪℳ ?🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 NAYI NADAMA MI WASMITI page 5⃣6⃣to5⃣8⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Cikin takun mishkilanci ya qarisa cikin parlon Ido ya Dan wore gami da qarewa parlon kallo Cikin Dan mmk Yace kamar ba Wani bani Adam dake Rayuwa a ciki parlon Baki ya kuma tabewa gamida Dan buda hannu da Dan daga ka fada alamar ko oho shi dai bai shafeshi ba Kai tsaye Bakin qofar bedroom dinta Ya nufa A hankali ya rinqa Dan buga qofar Har zuwa Dan woni lkci baiji motsinta ba Gashi sai wolqiya da iska dake kadawa tako INA Cikin fara harzuqa ya murda marfin qofar gamida turawa da qarfi Tsayuwa yayi can a tsakiyar dakin Yana yan dube dube A ranshi yake cewa toh ina ta shiga Yarinya sai shegen kadifiri Kofar mashigar toilet nata ya nufa Da sauri ya tsaya gamida qara zubawa gefen gadon ido Can ya hanqota a kasa konce kan carpet ta wani duqunqube sai karkarwa takeyi Da Dan sauri ya isa gun cikin Dan mugunta yayi murmushi gamida Sa qafarsa ya cureta Taba tan da yayi da qafarsa hakan yayi dai2. Haskawar wata iriyar walqiya mai tsananin haske a take kuma tsawa mai qarfin ta ratsa dukkan illahirin fadin garin Ruwan kuma mai qarfin kamar da bakin qoriya ya kece Abin yayiwa Aysha yawa ga firgici zazzabi ga tsoron kadaici ga abin da take tsoro kamar mutuwarta tsawa yana firgitate fiye da zaton mai karatu Shiyasa cikin Tsananin firgita Ta miqe Da qarfi ta fada jikin Yusuf din Tasa hannuta bibbiyu ta qaqumo bayan shi qirjinta ta manna kan nashi qirjin cikin kidima gamida tura kanta cikin wuyan shi Cikin wani irin baqon yanayi Yusuf ya nemi qarfinsa da kuzarinsa ya rasa gaba day sassan jikinsa sun mace ba wani abinda ya rege a jikinsa maiyin aiki sai zuciyarsa Hatta numfashin Sa da jinin jikinsa sun dauke Na Dan woni lkci So yake ya taqarqara ya samu ya hanka data Amman ba qarfin yin hakan Cikin yanayi da ya hade mai Ga yanayi Na sauqan ruwan dama yanayin da yafi komai tayar mai da Sha,awa Ga qirjin mace da yake ji cikin NASA qirjin A take ya fara fita haiyacin sa Lkci guda ya fara rawan sanyi lips dinsa suka rinqa motsawa a hankali Cikin kidi memmeyar Sha,awa Ya kamo lips dinshi Na qasa ya rinqa tsotsa cikin fitar haiyaci A hankali yaji sautin numfashinta Na sauqi kan wuyanshi Dumin jikinta ya rinqa ratsashi Kamar A mafarki Ya tuna wacece a jikinsa Cikin tsananin jarumta Ya tatara gaba Daya sauran qarfin shi ya hanka data kan gado Cikin juya mata baya Dan gudun kar ta gano halin da yake ciki Ya fara surfa mata masifa Can kuma ya juyo yana nunata da Dan yatsa cikin hada fuska 😡yana fadin Waike wacce irin fiti nenniyar yarinya CE Shin baki da hankaline Dan tsabar raini zaki woni shaqoni Da gangan ko so kike ki kasheni ne Toh wlh ki bude idanki da kyau ki ga waye a gaban ki Ni Yusuf nake Ba Ahmad bane ma rainin wayonku da zakuyi ta cakudashi Ita kam tunda taji ya hanka data ta dawo cikin haiyacinta ta kifa kanta kan guiwowinta ta rinqa sheshsheqar kuka A hatsale ya matso gab da ita dai lokacin da kiran Ummi ya shigo woyarsa Cikin nuna mata yatsa yace Ki rufewa mutane baki kinsa Sam ni bansan muna furci kekuma kince ke uwar muna furci CE wlh kika kuskura kikamin ba dai dai ba babbalaki zanyi ko a jikina Nan dai ba Nigeria bane bare kina da masu goyon bayanki Woyar ya miqa mata gamida Cewa (Da jabu leqquru do Ummi on yidi volugo be ma lutti a wanna am nafi kaku ) Ingo karbi phone dinnan Ummi ce ke son yin mgn dake saura kuma kimin muna furci Hannuta har rawa yakeyi ta karba gamida karawa a kunneta Cikin kewar juna suka kira sunan juna Na,am Ummi Aysha tace Sai kuma kawai ta saki kuka mai cin rai ciki kuka Tace Ummi Banda lfy Ummi zan mutuwa Ummi kince wa Hamma Yusuf Ya dawo dani gida ni Na gaji Cikin lallashi tace kiyi haquri Aysha ki nitsu ki saurareni mana ki daina kukan . Toh tace gamida da bayahannuta ta qoqe fuskarta da ta cika da qollah😭 Kina jina ko Aysha in dai zakinayin kukan in an kirki to ba mai kiranki Dan nima yanxu haka a boye Na kiraki Dan Bappa yaya yace kada aita kiranku Dan zaki rinqa yiwa mutane korafe korafe . Cikin shan majina tace Shike nan Ummi yanxu ni kam haka Zanyi ta rayuwa ni kadai cikin uquba😭 Dan Allah Ummi ki taimaka kamin kince a dawo Dani Cikin jin dadin zanceta yace nima den Na huta wlh in sun yarda a satinnan zai maida musu kayansu Ko nima Na samu Na huta da jarabar tsiya duk anbi an matsamin da kiraye kiraye Kowa sai yace min fatan dai tana lfy wato ni kam ko oho in naga dama Na muuu bai da mesuba Mayya kawai Ya fadi a fili dai2/ lkcin da ya fizgi woyar Cikin hikima yace Ummi Kinji abinda naketa fama dashi ko ni kullum cikin lallashinta Ko karatun ban samun inyishi yadda nake so wlh da kun yarda na maido muku da abunku in yaso in Na kammala karatun sai kuyi yadda kukace din Cikin qosawa da zancen nasa tace Kai saurara Toh yace Kana jina ko Ehh ya fadi da Dan yamutsa fuska Dan yasan kwanan zance Cikin umurni tace INA gayama ka kula da yarinyar nan Toh yace gamida cemata toh Ummi sai da safe Allah ya bamu alkhairi tace mai Amin ya fadi tare da katse kiran Yusuf da Ahmad yawanci suna woya kullum amman kwana biyunnsn Sam ko ya kirashi Abba ke daqawa Yusuf yasan suna India Amman Ahmad cemai yayi sunje har kar business din sune A CAN INDIA Kuma kwana biyu kenan anata Duba lfyar Ahmad anyi nasarar gano zuciyarka ce ta stage sakamakon yawan damuwa da tunani da cushewar qoqolwa da numfashi an kuma dora shi kan mgni duk da cutar tamai mugun kamu ta yadda dole cikin biyu za ayi daya ko ya rayu ko a rasa shi Saka makon binciken da ake ta mai dinne yasa ko Yusuf ya kira dole sai Abba ke daqawa Abin ya Sa Yusuf a tunani ga yawan mafarkin da uwan nashi da yaketa damunshi sai dai in bai konta bacci ba Yau alhamis Tun da gari ya waye Yusuf ya tashi da wani irin kasala ga tsinkewar zuciya a kai akai Gaba daya jikin shi ya sake shiyasa ko fita bai yiba Yana konce Kan 3 str dagashi sai Dan 3 qtr da yar farar sheet A hankali yaji phone dinshi nata Neman a gaji a karo Na 7 kenan ta yanke bai dagaba Duk lkcin da kiran ya shiga sai yaji wani irin tsinkewar zuciya A karo Na 8 Ya Sa hannu cikin kasala ya daga woyar mujahedin ya gani cikin dan jin tsinkewar zuciya ya daga..........abinda mujahedin ya gaya mai shi yafi komai qara kashe Ina Alfahari daku masu karatu NAYI NADAMA MI WASMITI page 5⃣9⃣to6⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Mutuwar jiki Cikin tsoro Ya katse kiran Baba bello ya kira cikin rudani Yace baba meke damun Ahmad Baba meyasa Baku gaya min ba Baba ya za ayiku boye Min abin da ke damun Ahmad Cikin mmk Baba bello ya tsaidashi yana Fadin kai Yusuf ka nitsi ka tsaya Wai shin waye ba lfy Kuma waya gayama Ni nasan lfy lau Abban Ku ya tafi da Ahmad Cikin tsoro yace baba boyema sukayi ko Kaine kake son boye min Cikin Dan rudewa yace waya gayama ? Mujahedinne ya kirani yanxu yace min ya qansu a asibitin jinyar zuciya kuma yace yaga an shigar da Ahmad dakin aiki Shi yaushe yaje India ? Shima kwanan nan yaje ya kai mahaifinshi . Cikin Kon tarmai da hankali yace toh Bari Na bincika Naji Da sauri ya kira Adam bayan ya katse kiran baba bellon Ko slmar Adam bai amsaba Yace Adam Ina Ahmad? Cikin da Jim yace Yoh Ai basu dawoba Tukun . Toh me suka je yi a can ? Dan tsaki yaja gamida jawo Amira dake konce a gefensa Yana shafa mararta yace kai Miraah kinyi yar lukutafa ji yadda kikayi nauyi Cikin salon motsa love ta Dan shafa nashi marar har zuwa Dan qasa Da qarfi ya matsota gamida sakin yar qara wash miraah zaki zauta yayanki fa Yusuf dake jin duk abin da sukayi ya hatsala iya hatsala Cikin ta kaici Da tsawa yace Kai biyaye ban son halin akuyanci fa kaji Dan iska Na kiraka zamuyi mgnar kirki ka woni tsayawa kana bunsuranci a gun yarinya qarama Dan iska Na mamajo kawai ka gayamin me Ahmad yaje yi a India Cikin muryar Sha,awa ya lumshe ido yace Sam wlh kai banzane biyaye kai ka takura rayuwarka muma zaka takuramu Cikin muryar gsky da gsky yace Adam ko kasan Ahmad bai da lfy ne ko kasan ciwon zuciya Ahmad ke fama dashi Cikin muryar karaya yace Adam ina amanar da Na baka Cikin zaro ido da tsoro Adam ya ture Amira ya tashi tsaye yanata fadin innalillahi wa inna ilaihi raji un Gaba daya jikinsa rawa yakeyi Cikin tsoro yace Biyaye waya gayama ? Cikin Dan fada yace ban saniba Cikin tsoro ya koma ya zauna kan kujerar Ahmad din ya kira Kiran forko bai dagaba sai ana 3 ya daga Cikin fargaba yace Biyaye Na,am ya amsa Cikin qarfin hali Ahmad Kaine ? Ehh nine mana Da qarfi yayi ajiyar zuciya Kamar yana ganin shi yace Ahmad ka kalleni ka gayamin meke damunka ? Cikin qarfin hali da qoqarin danne tarin da yake son taso mai yace Ni ban da matsalar komai Kai sai yawan tuhumar mutum ko yaushe ai shiyasa INA ganin kiran ka nake qin dagawa Kai ya rinqa girgizawa kamar yana gaban shi yace Ba gsky ka fadamin ba Biyaye qrya kake min Na tabbaya matuqar muna Raye kuma muna halin lfy duk tsananin laifin da Na maka Na tabbaya zaka daga kirana Ahmad meyasa kake son boye min muguwar cutar da take tare da kai Gaba daya muryarsa ta rinqa carkewa Ahmad ciwon zuciya ko Ahmad an gayamin fa Sai kuma ya kasa ci gaba Ahmad dake konce kan gado Abba Na gefenshi Hannu yasa ya kamo hannu abbansu ya rinqa kuka kamar yaro Kukan yake yana fadin Abba Yusuf yaji banda lfy Abba meyasa batun ciwona ya isa kunnen Dan uwana Abba INA tsoron halin da Yusuf zai shiga Cikin ajiyar zuciya Yaci gaba da cewa Abba Na INA sonku kuma Kuna sona Amman dole zaku rasani Abba kamin alqawari zaka bawa Yusuf da Aysha da Adam ga maryama kulawa ta mu samman da zata dauke musu quncin rashina Abba shima kuka yakeyi sosai Yana zaka rayu Ahmad am Zafin ciwo ba shine mutuwa ba Cikin alamar tabbaya yace toh Abba ko Na rayuwa yanxu ai gaba dole zan mutun ko ? Hannushi ya kama cikin kuka yace eh Ahmad mutuwa dolece Amman muna roqon Allah ya rufa mana asiri mu gaba ceku Girgiza kai yayi cikin Roqo yace Dan Allah Abba Na Mu koma qasarmu ta aihuwa Abba tun yaushe aka sallan memu Amman kace sai mun qara ganin wani doctor Abba kayi haquri ba taurin kai nayi ma ba Abba Na mukoma qasarmu Na mutum acan a gabanka a gaban mahaifiyata a gaban baba Na Abba kamin alqawarin muna komawa Zaka kira Yusuf da Aysha suzo in musu kallon qarshe Abba INA son Yusuf da Adam su kasance sune masu Sani cikin makoncina Kuka sosai abban keyi cikin kukan yace nama alqawari insha Allahu jibi jibinnan zamu koma kuma zan hadaka da yan uwanka Can kusan 9:00 pm Yusuf ya kira Abba cikin rawan murya yace Abba insha Allahu jibi zan taho gunku Dan Allah Abba kar kace zaka hanani zanzo naga Dan uwana Cikin sanyin jiki yace Yusuf bazan hanaku ganin junaba Amman muna jibin zamu dawo Kawai ka taho Nigeria mu hadu a can Abba meyasa zaku koma ya samu sauqi ne ? Eh Yusuf jikinfa da sauqi Amman dai kazo tare da Aysha. To yace cikin cushewar tunani Yana katsewa Adam ya kira ya sheida mai yadda sukayi da Abba dan dama suyi zasu hadu a can 🌏🌏🌏🌏🌏🌏 KASHE GARI Tun da safe Yusuf komai yake cikin sikewar zuciya yakeyi komai a hankali ya fito cikin mutuwar jiki ya shiga mota da niyan tafiya airport Dan kammala shirya shuryen tfyar tasu Cikin sanyi jiki Ya fito cikin motar cikin gidan ya komai cikin woni irin sanyi da yakeji a jikinsa Kai tsaye dakin Aysha ya shiga Jikin qofar ya jingina ya zuba mata ido cikin ta kaici Zaune take kan gado sai kuka take kamar wacce aka yiwa rasuwa Masifa yakeson yi mata a ranshi Amman bai da garfin haka bare kuzari Cikin ta kaici ya isa gaban ta Hannu yasa ya dago kanta Da sauri cikin razana ta wore idanta cikin ci gaba dakukun Rai a jagule ya nunata da Dan yatsa Gami da cewa Wlh kina ban tsoro ke ko yaushe kina cikin kuka toh insha Allahu zakici kanki banga me ake mikiba banga da me Na regeki ba Ido ta tsura mai cikin sake Sakin kuka A kufule yace mayya Ni ki tashi ki bani passport dinki banza mayya gobe dai insha Allahu Iwar haka kina can Gun su Ummi kiyita masifar kukanki Cikin sauri ta miqe jikinta har rawa yakeyi Beed side din dake gefen ta ta jawo miqa mai passport din tayi da sauran takar dunta gaba daya Cikin harara ya karba gamida tsince wadanda yake da buwata ya watsa mata sauran Kafin azahar kab ya kammala musu shirin tafi yarsu jirginsu zai tashi shida Na safe Suma su Abba duk sun gama shirinsu tsafa suma tashin asuba zasuyi Yusuf kam tunda ya fita bai dawoba sai 9:12 pm ya shigo kai tsaye dakinshi ya nufa shirin shi yayi cikin sanyin jiki bayan ya gama hada komai ne Ya Dan shiga toilet ya Dan watsa ruwan Yana fitowa ya zauna a bakin gado Cikin jin yiwa ya shafa cikinsa yunwar yakeji kamar zata kashe shi Amman kuma bazai iya cin komai ba duk da kuwa tun shekaran jiya da dere rebonshi da cin wani abu Cikin sanyin jiki ya daga woyarsa Ahmad ya kira a wunin yau wannan shine kirashi na 23 da ya kirashi Dan jin ya jikin shi Abba ne ya daga woyar cikin Dan fada fada yace haba Yusuf Baccinma bazaka barmu muyi bane? Cikin sanyi yace kayi haquri Abba ajiyar zuciya Abban yayi gamida katse kiran Da sauri ya kamo Ahmad dake ta tari da amai cikin azaba ya kamo hannushi yace Abba meyasa kake yiwa biyaye Na fada? Kai ya jinjina yace Haba Ahmad shi Yusuf ya fiye nacin tsiya ne wlh Cikin Tari yace Ayyah Dan uwana ya zamuyi abinda muke tsoro shi zai faru Zama Abba yayi a gefenshi cikin dauriya ya rinqa mai nasiha kan ya daina irin zantu kannan Murmushi kawai yayi gamida konciya A firgice cikin razani da rudani Yusuf ya farka daga mugun mafarkin da yayi Addu ya rinqa yi da Neman tsari da wannan mugun mafarkin A hankali ya rinqa jin sautin kukan Aysha daga dakinta kuka takeyi sosai harda sheshsheqa Da jin haushi ya nufi dakin nata Abin mmk duk kukan nan da takeyi cikin bacci take yinshi Da sauri ya qarisa gunta Ke ke Ke ki tashi sokuwar banza kin konta bakiyi addu,a ba gashi kinzo kina ta mafarkin kina ta yiwa mutane hihu a gari Ko motsi bata yiba kuma bata bar kukan ba Da qarfi ya ware yatsun shi ya zuba mata mari a fuska Cikin razana ta miqe gamida sakin kuka mai tsuma rai Wanda har muryar ta ta fara dashewa Sai tirje tirje take a kan gadon tana wayyo ya Ahmad dina Ya Ahmad kar ka tafi ya Ahmad ka dawo Sosai take sabbatu da sauri yayi kanta cikin kamata Amman Ina sai zullewa take Tana ya Ahmad Cikin mmk yace menene hakan ? Meya samu ya Ahmad din ? hannushi ta riqe da qarfi tana bubuga qafa ya Ahmad ya rasu Hamma Yusuf ya Ahmad dina zai tafi ya barni ya Ahmad dina ya mutum A kidime da zafin nama ya rinqa zuba mata maruka yana fadin ke ki dawo hayya cinki ki bude idanki kiSan abinda kike fada kuma ? Ahmad yana Raye duk shedanin da ya raya miki ya mutum to yayi qarya Abin ya bashi mmk Dan duk da marukan da tasha Sam bata dawo hayyacin taba sai faman qaqumoshi takeyi tana kuka tana rirriqeshi Da qarfin take jijigashi shi ko gaba daya jikinshi ya mutum tsoro ya rufeshi dan shima irin mafarkin da yayi kenan Da qarfin ta kuma janyoshi tana wlh Hamma Yusuf an cemin ya Ahmad ya mutu Cikin qarfin hali ya jawota jikin shi ya matseta cikin qir Jinshi Cikin qarfin itama ta runqumishi tana mai ci gaba da kuka Bakinshi yasa dai dai kunneta ya rinqa mai maita mata innalillahi wa inna ilaihi raji un Sosai take qara shiga jikinsa hannuta ta daura kan qirjinshi tana ta Dan bugawa A hankali ya farajin sanyi Na ratsashi lips dinshi suka rinqa bari A hankali ya jawo blanket ........ NAYI NADAMA 👇🏻 MI WASMITI page 6⃣1⃣to6⃣3⃣Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Blanket din ya jawo Ya rufe su iya qirjinshi Hannu shi ya Sa ya jawota jikin shi Cikin hikima ya dago kanta ya daura kan qirjinshi kanshi Na daidai saman kanta yana shaqar kam shin kanta Cikin wani baqon yanayi ya daura hannushi daya kan Kuma tunta yana Dan shafawa Gaba daya jikinsa Kuma Sai rawa yakeyi Sai wani irin sautin numfashi yake ta fesarwa Bugun zuciyarshi Kuma gaba daya ta angizo Ita kam Aysha batama San me ake cikiba Kukan takeyi tana ta kiran ya Ahmad din nata Kukan Na ratsa kunneshi a zahiri shi Yusuf ya tsani kuka a rayuwarsa Cikin. Sakin ajiyar hrt ya Dan tura mata yasarsa Cikin bakinta da niyar danne harshenta ta bar kukan Amman wani yanayi da yaji tana yi da yatsar tasa yasa shi jin jijiyoyin jikin shi tamkar ana binsu ana tsistinkasu ne Yatsar ta kama Cikin qoqarin yin baci ta rinqa tsotsar yasar tashi tana lasarsa a haka bacci ya kwasheta Shi kam Yusuf rawan sanyi yake sosai gaba daya jikin shi Sai Bari yake ya kame Dan lips dinshi yana hucewa a kai tsotsor lips dinshi din yake sosai yana mai damqe mararsa gaba daya idanunshi sunyi wuqi wuqi Sai fam matse cinyarsa yakeyi Cikin Wahalan ya rinqa zaro yatsar Ita Kuma Sai faman tsotsar yatsar take A haka suka Dan dauki tsawon lkci Sai can ya Dan samu bugun ziciyarsa ta fargar dashi da qarfin ya zare yatsar tashi Dakinshi ya nufa Yana jan tsaki A ranshi yake cewa ba ga irin ta ba A wani hadaka da yarinyar qarama ta zamarwa mutum damuwa ta wani maqalemin yatsa Tana ta tsotsa kamar wata sabuwar mayya Hannushi ya Sa ya Dan shafi kanshi gamida shafar hamtsar wondonshi Tsaki ya kuma ja Aikin ban za yace Cikin quluwa ya nufi toilet dinshi yana fadin Ji sokuwar yarinya tasa gaba daya Na jiqe 😝😉 lol su Yusuf anji harshe me taushi nanma harshen kadai akaji tukun😝🙈😂 NIGERIA Qarfe 3 daidai Su Yusuf suka dira a tsakiyar gidan su Abubakar da ya dauko su yana riqe da jakar yayanshi Ita Kuma Aysha tana maqele da hannushi a haka suka isa parlon Gidan a cike yake Cikin tab zuriyarsu su Dr Umar Ardo ma sunzo Suna shi ga parlon Aysha ta saki hannu ya Abubakar din nata cikin kukan ta fada kan umminta Sai kuma ta saki kuka su Amira da maryam kam sai murna suke yi suna ruggume da ita usman ne ya harareta ke da allah can ke bakya girma da kuka kaka ta kalleta cikin yatsina baki tace barta dai mutum kullum kuka kamar wanda aka hada da baqin cikin rayuwa cikin kukan tace eh ni ba ruwana da ku dama ai kekam kaka nasan matsayi na a gunki ta dan juyo ta kalli Nenne a hankali tace Nenne INA ya Ahmad ? Suna hanya Aysha suma sun iso tintini Adam ya tafi dauko su ne da yake su a Yola suka sauqa Yusuf kam zama yayi can gefen su bayan gaida su Ummi da yayi bai Kuma mgn ba kaka ta kalleshi a yamutsa tace (wairego Na wailego ) Shi dai bai kula taba Sai table baki da yayi a ranshi yace ai nasan so kike nayi mgn ki samu abin fadi Mutum bakinsa bai iya shiru Ehh din yaji tace eh din ba zanyi shirunba Cikin Dan mmk ya kalleta yace kekuma ke da waye ? Da kai mana ta bashi amsa Niko me namiki ? Ai nasan abinda kake fada a ranka Toh kin koma Allan musuru kenan? Oho koma dai me zakace ka fada. Zaiyi mgn kenan su Abba sukayi slm suka shigo Gaba daya parlon suka miqe Cikin tsananin mmk da kaduwa ganin yadda Ahmad din ya rame gaba daya ya can za Sai wani fari da kyau da ya qara yi Adam ne ke dafe dashi suna tafiya a hankali hannushi daya Na kan qirjinshi Abba da baba bello Kuma Na biye dasu a baya Cikin sauri da razana Yusuf ya nufi gunsu yana zuwa Ahmad din ya bude mai hannu haka Adam din su duka 3 suka ruqqumi juna A hankali Ahmad ya rinqa ayin ajiyar zuciya yana wani irin wahalellen numfashi Yusuf ne ya tallabo fuskar Ahmad Cikin rawan murya yace biyaye Meyasa meyasa zaka boyewa zuciyata halin da taka zuciyar ta ke ciki hannushi ya kamo suka taka a hankali Adam Na riqe dashi ta gefen shima Yusuf yana riqe dashi ta daya gefen gaban Abba suka je suka zauna Da sauri Nenne tazo kusa da Dan NATA ta zauna Cikin tsoro tace Ahmad meyasa ka boye min abin da ke damuna Wai kana gudun kar hankalina yatashine Ahmad? Kai ya geda.mata alamar ehh Cikin tausayin Dan nata tace toh in banda abinka Ahmad wane tashin hankali ne ya wuce wannan ga yadda ka dawo Cikin qarfin hali ya Dan ja quiwarsa ya qarisa gun Nenne tashi a hankali ya daura kanshi kan cinyarta gami da Sa hannushi ya riqo NATA Cikin murmushin qarfin hali yace Nenne ke dai ki kasance mai min addu ,a har ranar da zaki zo ki taddani Dum zuciyar Yusuf ta buga jin irin furucin da biyayenshi ke furtawa Itako Nenne bata fahimci komai ba Sai shafa kanshi ta rin qayi tana insha Allahu zan rinqa maka addu Kuma dama kullum Cikin yimaka ita muke Maryam ce ta dauko abincin da suka shir ya musu ta rinqa jerawa a gaban su A hankali ta matso kusa da Ahmad din Cikin sanyi tace ya Ahmad ya jikin Hannushi yasa ya jawo nata kanta ya daura kan qirjinshi Yace maryama tawa kinga Allah ya nufa alqawarin da Na miki ya cika ko Cikin jin kunya tace ehh ya Ahmad Amman yazu dai tashi kaci abinci Yusuf ne ya matso kusa dashi shi ya zuba mai abinci ya matsoshi Sai faman tura mai abincin yake kamar yaro qara mi Da gyara ya danci loma 4 Sai kuma ya fara nishi yana ture hannu Yusuf Yace ya isheni haka banafa iya cin abinci ko kadan biyaye Amman kaga yau da ka bani abinci da hannuka Cikin qaunar Dan uwan taka gashi naci Aysha dake maqale a hannu ya Abubakar ta Sa hannuta 2 ta sanqalo nashi ta daura hannuta kan damtsen hannushi Cikin mmk da qaunar zuciya ta fashe da kuka Gaba daya hankalinsu ya koma kanta Cikin Harara Yusuf ya buga mata tsawa yace Wlh ko ki rufe mana baki ko nazo Na takamiki wuya Banza kawai mai kama da mayya Dan iskanci ki tasamu a gaba kina ihu Munafuk... Bai qarisa zancen nashiba yayi shiru gamida sunkuyar da kai Dan jin furucin Ahmad Cikin zuba mai ido da alamun tuhuma Yace Biyaye amanar kenan ? Hannu ya miqa mata Cikin lallashi yace autan Ummi zo nan ki gayamin waya tabaki Cikin kukan ta fada kan girjin shi Sai da yayi wani irin ajiyar hrt Cikin kukan Tace ya Ahmad tunda ka dawo baka kula ni ba Ka tabbayi kowa ni baka tabba yeni ba A hankali ya ronqofo kan kunneta Cikin Rada Yace ai Ke Aysha matuqar INA Raye a duniya toh INA tare dake ba sai Na tabbayi woni ba Amman kuma A yanxu lkci ya qarato mana Rabuwar Na gaba towa Da sauri ta daqo Cikin mmk ta zuba mai ido Cikin alamun eh gsky nake fada miki Yace gatar da nakeso ki min bayan rabuwar itace addu,a Cikin sanyi ya kuma kalli Yusuf yace biyaye Haka mukayi da kai Meyasa ka kasa cika min burina Meyasa kake yiwa Aysha tsawa har yau baka bar hantararta ba Cikin sanyin jiki yace Ahmad yanxu wannan ba shine matsala ta ba Ni kuwa itace matsalata Hannushi ya riqo Cikin kula ya kalli Abba yace Abba meyasa kuka dawo? bayan jikin Ahmad har yanxu na ciwo? Cikin nitsuwa Abban yace Yusuf Ahmad dinne ya matsa da Sai mun dawo Gida Toh a satinnan zamu koma ya fada yana mai kallon Ahmad din Kai ya geda mai Cikin cewa toh Allah ya kaimu lkcin Amin suka amsa baki dayansu Baba bello ne ya miqe gami da cewa toh duk Ku fito mu tafi masallacin maqqariba tayi A hankali Cikin hikima Ahmad ya rinqa qoqarin tashi Amman INA abin yaki Cikin sauri Adam ya kamo shi ya miqar dashi Fuskar Yusuf ko fal tsoro ya kalleshi Cikin tabbaya yace bakama iya tashi da kanka ne biyaye Sai in an dagaka?. Dry yayi wace tafi wuta ciwo a ranshi yace a ni kam INA tashi wlh kai matsalar ka kenan Sa ido Kai ya jinjina Dan gani quru quru Ahmad ke nunawa shi lfyarsa lau Daki Nenne suka shiga Cikin davara ya kalli Yusuf yace kai turomin maryama kaima jekayi taka al walar A a muje dai in samaka ruwan Kai ya Dan juya yace nave zan iya Malam turomin matata ita nakeson gani kafa San INA hannu kusan wata 3 fa ban jitaba bata jiniba gwara kai taka matar tana katararka Kallon shi yayi a gyatsine yace toh Ayu uwar jaraba bari Na turoma ita ni ban nemi dogon zanceba ka dai tuna a dakin Nenne kake . Eh ai nasani anan din nakeso Na sama mata jika da zai zame mata madadina kai Kuma ka samu abin gani a matsayina Cikin mmk irin mgn ganun Ahmad Yusuf din ya juyo yana kallonshi Ya bude baki Zaiyi mgn kenan Maryam ta shigo Cikin farin ciki Ahmad din yace yauwa maryama tawa zo nan zo yayanki yaji dumin jikinki Cikin qaunar mijin nata ta fada qirjinshi Hannu bibbiyu yasa ya ruggu mota yana sauqe numfashi Ita kam Maryam tama manta da wani Hamma Yusuf a wurin Shiyasa Cikin shogoba ta maqalo wuyanshi gami da furta mai I miss u so much my dear broz Cikin tau saya musu yace Allah ko? ehh mana ta fadi gamida narkewa a jikin shi Cikin Dan murmushi yace toh daqo daqo kanki ki gani ...... Yusuf kam dake tsaye yana kallon su ganin halin da Ahmad din ke ciki😳 yasa shi fita Cikin sauri har yana qoqarin faruwa.... Kuyi haquri masu karatu INA jin qorafe qirafenku kan batun Ahmad Dan Allah kukam kiyi haquri kawai Ku biyoni a hankali zakuga Yadda abin yake 👇🏻 MI WASMITI. page 6⃣4⃣to6⃣5⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Ganin da sauri Ahmad ya hada bakinshi da Na Maryam yana mata wani irin kidi memmen kiss Yasa Yusuf ficewa Da sauri A ranshi yake cewa kome su Ahmad sukeji a jikin yara qanan nan ne Oho musu A daki kuwa tabbas Ahmad yayi missing din maryama haka Kuma ya nuna mata hakan a aikace Sosai yake ta kissing dinta tako ina Itama biye mai tayi Gaba daya sun mance da cewa a dakin Nenne suke Cikin buqa tuwa Ahmad yaja hannuta suka fada kan gadon Wasa yakeyi da iya son ransa Cikin zaquwa ya fara qoqarin zuge zip dinta Da sauri tace ya Ahmad a dakin Nenne fa Na Sani maryama Na San a inda nake Kiyi haquri yau kawai daga yanxu fashike nan Gaba daya ya birkice mata ala dole ya samu ya biya buqatar Sa Bayan komai ya lafa ne ya daddafe ya shiga toilet wonkan tsarki yayi yayi yishi Kuma suffatul kamal so hade da alwalarsa ya fito Tin da ya watsa ruwan a jikin shi yaji woni irin sanyi ya ziyarceshi gaba daya jikin shi Kuma yaji kamar an rufe shi da danyen fata A take jikin shi ya fara rawan sanyi Yana fita rigarsa ya dauka yana zurawa a jikin shi gaba daya jikin shi rawa yakeyi A Dan firgice Maryam ta matsoshi tana fadin ya Ahmad sanyi kake jine ? ko zazzabi ne ke damunka? Kai ya rinqa juyawa Cikin cijewar voice yace shim fidamin darduma Zanyi sallah a gida bazan i iya iya iya zuwa masallacin ba gaba daya muryar shi Sai fizga takeyi Da sauri ta shimfi da mai Yana tada kabbara Cikin ikon rabbi duk ya nemi sanyin ya rasa Ganin ya daina rawar yasa itama tafada toilet din tayi nata wonka Shi Kuma Ahmad yana idar da sallan gaba daya Yaji jikin shi ya sake A hankali ya rinqa jin suqar zuciyarsa Na tsananta Lkci daya zazzabi mai qarfin ya rufe shi ga tari Yana Cikin haka Maryam ta fito Da sauri ta nufi gunshi Dai 2 lkcin da ta isa a dai dai lkcin ya fara wani irin amai jinine yake amayarwa guda guda 😳😩😭😱 da qarfin ta riqoshi Cikin ki dimewa ta rinqa kiran shi ya Ahmad ka tashi tashi mu tafi asibitin Nenne Nenne kuzo wayyo Allah Na ya Ahmad Gaba daya ta rude Cikin tsoron Taji yana kiranta da qarfin Cikin fizgar mgn Yace Maryama je ki kiramin Nenne Na da Yusuf da Adam kiyi sauri kice Abba Na da baba bello su zo Cikin tsoron da kidima tafita a guje babban parlon ta nufa Gaba daya suna zaune shi gowarsu kenan Tana zuwa hannu Abba taje ta kamo Cikin Kasa mgn Sai nuna mai hanyar dakin Nenne take Cikin firgita Yusuf yace Maryam INA biyaye Na Ba mgn Sai komawa tayi ta kamo hannu Yusuf din tana ja Da qer tasamu ta iya bude baki tace Hamma Yusuf Ya Ahmad zai zai Bai tsaya ya qarisa jin zancen ta ba ya nufi dakin a guje Gaba daya suma suka rufa mai baya Yana shiga ya hanqoshi konce Cikin galabaita Yana ganin Yusuf din ya miqa mai hannushi yana mgn da qar yace biyaye Na zo zo gareni zo inji dumin jikinka Na qarshe Da sauri ya qarisa gunshi tallaboshi yayi ya ruqqumeshi a girjinshi Cikin kidima yace Baba bello mu tafi hospital Ya yunquro zai tashi dashi Kenan Yayi mgn da Dan qarfin yace biyaye barni barni a gida barni Na cika a dakin mahaifiyata a gaban idanta Hannu ya miqawa Adam Wanda tuni yaketa sharar qollah😭 Riqe hannun juna sukayi Cikin tsananin firgita Shi Kuma Yusuf ruqqumeshi yayi da qarfin kamar mai tsoron kar a kwaceshi kai kawai yake juyawa yana A a a a ba inda zaka Tafi biyaye muna tare Aysha ko riqe da hannushi daya Sai kuka take kamar ranta zai fita Cikin qarfin hali yace Abba Ku gafarceni ya kuma kallon Nenne da ta fara zama mai daqushewar tunani yace Nenne da sauri ta matsoshi Yace shin ba INA gaya miki cewar Allah da ya bakini ya fiki sona ba Nenne ya nake ga alamar kareya a idonki da qarfin ta riqo hannushi tace Na yarda Ahmad Na San Wanda ya bani kai ya fini sonka . Toh Nenne inko hakane addu,arku kawai nakeso Dan Allah kar ki bin da kuka Ina ita kam a NEnne tuni ta fashe da kuka A hankali ya juya kanshi gun baba belle mahaifinshi kenan Cikin murmushin qarfin hali yace Baba Na zan tafi Na barka Ga Nenne Na ka kulanmin da ita hannushi ya kuma riwewa Baba ka gafarceni idan Na taba yima wani laifin Cikin qarfin hali baba belli ya daga kanshi yace Ahmad baka min komai ba Kuma koda kamin Na yafe maka duniya da lahira Ahmad Allah ya bada Sa,an tafiya Cikin sanyi yakira Abba Abba Na kuka kake min ? Ya tabba yeshi Kai Abban ya jinjina Cikin kuka tsosai yace a a Ahmad kaina nake yiwa kuka Ahmad kaina nake kokawa Da qer ya daga hannushi ya goge qollah😭 da ke bin fuskar Abban yanan murmushi Cikin sanyi yace Abba Dan Allah INA da tabbayoyin da zan muku A yau dinnan Ku daure Ku bani amsar su Kai ya geda yace INA jinka Ahmad tabba yeni matuqar Na sani to zan gaya maka Cikin gajiyar hrt yace Abba meyasa kuka hanani Auren Aysha? Meyasa kukace Aure ya haramta a tsakanin mu? Abba meyasa kuka hadata da Yusuf bayan shi uwa daya uba daya suke da ita ? Kuma yaushe aka daura Auren Aysha da Yusuf? A hankali ya kamo hannushi yace wadannan sune tabbayo yin ka ? Ehh Abba Cikin sanyi yace toh Ahmad zan amsa makasu kamar yadda ka buqata Da forko dai Aysha yatace amman ba ta cikina ba cikin gsky da gsky ya nuna Dr Umar Ardo yace wannan shine mahaifin Aysha ma haifiyarta Kuma itace qanwata khadeeja wacce ta rasu Da sauri Adam yace Abba me kake cewa? Eh abinda dai kaji Na fada ya bashi amsa Cikin dimuwa yace kenan Aysha qanwa tace uwa daya uba daya Ehh sosai ma kuwa Nan ya fara basu amsoshin tabba yartasu Kamar yadda kuka Sani khadeeja qanwa tace uwa daya uba daya dama a cikin mu mu 6 ne maza 4 mata 2 a gurin maHaifi yarmu mu 3 ne bello Sai ni Aliyu Sai Khadija Itama inna yayan ta 3 Maza 2mace 1Ahmadu takwaran Ahmad kenan Sai hamisu Sai Aysha Khadija qanwata ita aka fara aurawa abokina Dr Umar Ardo bayan sunyi Aure Allah ya azur tasu da namiji shine Adam Sai hydar kamar yadda kuka Sani ana tare kuka girma da Adam Daga kan hydar bata Kuma aihuwa ba kamar yadda kuka Sani khadeeja Na matuqar qaunar Yusuf a ranta shiyasa tayi alqawari duk ran da ta haifi ya mace to matar Yusuf CE ta bashi duniya da lahira Ku Kuma bayan kunngama primary school dinki Sai aka sama muku makaran ta a bauchi Inda kukaje kun Sani sai hutu ke dawo daku hutun ma Sai shekara shekara Kuna js 1 khadeeja ta samu Cikin Aysha Cikin ikon rabbi ta goya cikinta lfy ta aihu lfy Tana aihuwa ta kira mahaifinmu tace ta aihu Kuma ta samu ya mace tace Kuma yarinyar yar nan matar Yusuf CE Na bashi duniya da lahira Bayan awa daya da ahuwar jini ya yanke mata a take kafin minti 30 tace ga garinku A haka mukayi kuka muka haqura bayan wata biyu aka aurawa Dr Umar Ardo goggonku Aysha tana zuwa da shekara data ta haifi Maryam Inda itama Kuma tace ta bawa Ahmad ita amatsa yin mata Dama a lkcin Kuma da aka haifi Aysha Nenne Ku ta aihu yaro ba rai tsaka ninsu sati 3 Shiyasa Sai ta karbi Aysha ta shayar da ita kaji dalilin da Aure ya haramta tsaka Ninka da Aysha kunsha nono daya mahaifiyar kace ta Sha yar da ita har tsawon shekara daya da woya 6 kafin ta yayeta Batun daura Auren Aysha da Yusuf Kuma a lkcin kuna India a inda kuke hada digri dinki Na forko A lkcin Aysha Nada shekara 13 Bappa Yaya yayi woni irin ciwon da ya firgita mu Gaba data muka karaya to a nanne yake cemana batun daurin Auren Aysha da Yusuf a lkcin yasa aka daura Auren a tunanin Sa kar ya mutum bai hada Auren ba mu zo muqi cikawa khadeeja wasiyar da ta bashi Tarin da ya sarqafe Ahmad ne ya tsaida Abba daga lbrin da yake basu Da sauri Yusuf ya talla boshi Cikin azaba ga aman jini da yaketa kwarawa Murya Na rawa yace Yusuf kaji ko kaji abin da nake gaya maka Na tabbata Su Abba bazasu hada haram taccen aureba Cikin sanyi da daukewar numfashi ga wani zufa da yake ta keti mai Yadamqo hannu Aysha ya kamo Na Yusuf ya hada su wuri daya ya tura hannu Aysha Cikin Na Yusuf din da qer Cikin wahala da fixgar numfashi yace... .. Gaisuwata gareki Hajiya Ramatu Allah ya jiqan mahaifinku da rahama👏🏻 ?🍇🍇🍇 NAYI NADAMA 👇🏻👇🏻👇🏻 MI,WASMITI page 6⃣6⃣to7⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Cikin carkewar murya yace Biyaye Ga amanar da zan bar maka. Sai kuma tari ya Dan carkeshi Hannushi Yusuf ya riqe da qarfi ya kai kan qirjinshi .. Tarin yayi sosai kafin ya da lfa gaba daya jikin shi ya sake idansa duk sun fiffito kan goshinshi Sai zufa ke tsatsafo a take fuskarsa ta dauki sheqi da qelli A wahalce yaci Gba da cewa Ban saniba Yusuf ko zaka iya karbar amanata ?ban saniba ko zaka iya riqemin amanar tawa ? Ban saniba ko zaka iya Sa farin ciki a rayuwar Aysha ? Yusuf kam tamkar icce ya zama a wurin ya kasa koda qifta idan shi Sai zuciyarshi dake bugawa Da qollah😭 da ke bin fuskarsa A hankali ya daqo hannushi ya shere hawayen dake bin fuskar Yusuf din ya kamo hannu Aysha ya jawota kanta ya daura dai2 kan qahon zuciyarshi Cikin rawan murya yace Aysha kiji bugun zuciyata da zanyi Na qarshe a duniya Ki ji lkcin da sonki a matsayin matar Aure zai bar jikina kiji lkcin da numfashi zai rabu da gangar jikina A yau zaki gsknta cewar kece bugun zuciyata Kanta ta daura kan qirjinshi ta Saki kuka mai ban tausayi Tana ya Ahmad bazaka mutuba numfashi ka bazai bar gaggar jikin ka ba Toh ya zanyi dole zan tafi Na barku Hannushi ya daqo ya kalli inda Maryam ke Durkushe Sai Kuka take jikinta duk bari yakeyi Cikin qarfin hali da kawaici da haquri da jarumta irin Na Ahmad Ya miqa mata hannu Cikin sautin qarfamata zuciya yace Maryama zo Maryama zo Maryama zo masoyi yata cikin kuka ta tsura mai ido tana kallon yadda yake fizgo numfashi Amman wai a hakan yake qoqarin sata farinciki Hannu ta Sa ta kamo nasa Cikin sakin wani irin numfashi ya jawota ya daura kanta kan daya gefen qirjinshi A hankali yace Maryama tawa kin zamani Na zamake Komai zanyi in babuke bazan ji dadiba Maryama kontar da kanki a jikina inji dumin jikinki Na qarshe Maryama matso gareni ki ga fitar raina a take Sai ga wani irin tari mai qarfin ya turkeshi numfashin ya fara fizqa in ya shaqa baya fitarwa da qarfin yasa hannu daya ya qara damqe hannu Yusuf da Aysha da ya hada wuri daya Ya Sa daya hannu Kuma ya damqi hannu Adam Wanda tuni yake kuka kamar mace Kuka 😭😭😭😭😱sosai Maryam da Aysha keyi Nenne ko miqewa tayi Cikin dimuwa kamar wacce hankali ya bar jikinta zata fita Da qarfin Cikin tarin yace Nenne kiyi haquri zaki rabu dani Nenne ki kalli Rabi,u a madadina Baba bello ne ya matsoshi Cikin qarfin hali da jarumta irin ta maza Sai kai yake juyawa yana cije lebe Yace Ahmad Na yafema duniya da lahira ubangiji ya maka raya Allah ya sadaka da Mala ikun rahama Ahmadu Cikin cijewar voice ya rinqa maimaita mai LA ila haillah muhammadura sulillah s a w Cikin sanyi ya karbi Kalmar shahadar da maifinshi ke mai Abba da yake ruqqume dashi kanshi a kan cinyarsa Da qarfin ya ruqqumeshi gami da rumtse idanshi Yana fadin innalillahi wa ibailaihi raji um A hankali Yusuf yaji hannun Ahmad ya saki nashi Cikin zaro ido ya kalli fuskar Ido Cikin ido Sukayi Murmushi Ahmad din yayi Cikin sanyi yace Biyaye ga amanar Aysha Sai kuma ya daura da Kalmar Shahada Idanshi suka koma suka kafe murmushin da yayi yana kan fuskarsa Dr Umar ardo ne ya rinqa mai mata kullu nafsin za ikatul maut Nenne dake gefe cikin gigita tace shike nan Ahmad kaima kabi yan uwanka Ahmad Na rabu da kai Sai kuma ta saki wani irin kuka mai ban tausayi Gaba daya dakin ya rude Hatta Abba kuka yake sosai ringume da gawar Ahmad din Adam kam Tuni ya fada kan Yusuf Cikin riqe hannushi Yana Shike nan Yusuf Ahmad ya tafi ya barmu Yusuf mun rasa Ahmad Sh kenan yanxu dagani Sai kai Yusuf Ahmad ya tafi ya barmu Maryam kam da Aysha qaqqame qawar sukayi Cikin firgici da rudani Suke kuka kamar ransu zai fita Baba bello ne da Dr Umar ardo sune suka samu Dan qarfin jikin miqewa baba bello kam Nenne ya kamo ya ruggume Cikin rawar murya yace haba ruqayyatu kar kibi Ahmad da kuka mana shin baki ga Rahamar da Allah ya mishi ba cikawafa yayi da kalmar shahada Allah sarki Nenne Sai fafawa tayi jikin mijinta ta rinqa kuka mai ban tausayi Cikin kuka Abubakar ya riqo hannu marya da Aysha da nufin ya jasu su fita Da qarfin Maryam ta fada qirjin shi Cikin n kuka tace ya Abubakar da gaske ya Ahmad ya rasu Na rasa ya Ahmad Kai ya rinqa juya mata yana zubda qollah😭ya jata suka fita Ummi CE ta matso Cikin kuka tasa hannu ta rufe mai idanshi Su Usman da Rabi,u kam da abdul dama tuni suka koma parlon kuka suke kamar yara Ummi CE ta miqe gami da kamo hannu Aysha da nufi su fita Tana janta Sai gani tayi tayi yuu Sai fadawa kan Yusuf tayi a sume cikin firgita Ummi ta rinqa kiranta tana jijjiga ta Amman ina Goggo Aysha CE tayi tunanin debo ruwan ana Dan shafa mata a fuska Amman INA ko matsi bata yiba 😱😫dimuwa. Da firgici da tsoro mai matuqar tsananin su suka sauqa kan rayuwar Yusuf inda ya zama tamkar mai Ciwon mantuwa Lallai kuka ma Rahama ne Shi kam Yusuf yau yake buqatar kuka a rayuwarsa Kuma a yau kuka ya mai tsada Zuciyarshi ta kasa tuno komai qoqol warsa Kuma gaba daya ta tsaya bata aiki kanshi da jikin shi duk jinsu a juye suke🙃 Ido kawai Yusuf ke binsu dashi Sai hannushi da yasa ya damqi hannu Ahmad din Su Ummi yake klo Cikin zare idon fuskar Aysha yabi da idonshi Cikin yanayin rashin sanin abin da akeyi Hydar ne ya zo ya ciccibi Aysha yayi dakin Ummi da ita kamar gawa Yusuf kam yana zaune a gun riqe da hannun gawar Dr Umar ya ja Abba ska fita tare Fuskar Ahmad din ya zubawa ido Sai ya juya ya kalli Adam dake durqushe a gefen shi yana ta kuka A haka har zuwa tsawon wani lkci Allahu Akbar Lbrin rasuwar Ahmad Ta kasance tam kar sauqan aradune a zuqatan yan uwa da abokan arziqi Lbrin ya zama tamkar sauqan qanqarane ne a jikin mutane Kafin wani lkci gida ya cika tab da yan uwa da maqota da abokansu Baba Ahmadu ne da Dr Umar Suka shigo Daukar gawar Dan Aje ayiwa gawar wonka ayi mata sutura a kaita makoncin ta Cikin tsoro baba Ahmadu ya daqo yana kallon yadda dr Umar ke ta yin qoqarin cire hannu Ahmad Cikin Na Yusuf Amman ....... Allah sarki rayuwa Dan Adam Dan mutuwa nima kaina Aysha Ali Garkuwa rasuwar Ahmad ta zame min fami a zuciya ta ta famimin rasuwar yan uwana shiyasa wlh bazan iya ci gaba da typing ba har Sai zuwa gobe 😭😭😭 ?🍇🍇🍇 NAYI NADAMA 👇🏻👇🏻👇🏻 MI,WASMITI page 7⃣1⃣to7⃣3⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Amman gsky Baku kyautamin ba masu karatu ya kamata ace tsakaninmu Marubuta da ma karanta a ringa yiwa juna uzuri Daga jin Ahmad ya rasu Sai wasu suka rinqa qananan maganganu wasu harda kirana a woya Wai meyasa zan kashe Ahmad ai wanna NAYI rashin imani Haba masu karatu kukam kuyi Haquri maNa Ku Biyoni A hankali ai zakuga yadda zan tsara mana abin masu bina ta prvt chart kowa da irin qorafin da yake min Dan Allah mu rinqa yiwa juna uzuri Wasu harda cewa ai gwara akashe Yusuf😫 Ina Baku haquri wasu nace Na sasu kuka sosai karku damu zakuyi dry a gaba fiye da yadda kukayi dry a baya zaku Sha nishadi fiye da zatonku Ku dai Ku hira Yusuf ya shigo hannu😍😘🍌🙈😝 Jan hannu Yusuf din yakeyi yana qoqarin rabewa a na Ahmad din shiku ma Yusuf Sai damage hannu da yayi yana mai zuba musu ido Kamar zaucecce a hankali Dr Umar ya zauna kusa dashi Cikin tausasa zuciyarshi yace Yusuf saki hannu Ahmad Kaji sakeshi a yanxu ba wani gata ko Alfarma da zamuyi mishi sama da mu kaishi Cikin qabarinshi Baiyi mgn ba bai Kuma sakiba Sai zuciyarsa da ta rinqa bugawa da qarfin qarfi Hannu nashi ya jawo ya dawowa kan qawar yasa yatsunshi ya rinqa bude tafin hannu da Yusuf do ya damqe Shi kam Yusuf kallon shi kawai yakeyi So ya yake yaji shi shima a mace ko zaiji wani a bu a ranshi ji yake dama haukacewa yayi A hankali zuciyarsa ta fara tuno mai abinda kalaman baba Umar ke nufi a take Kuma Sai jikin shi ya rinqa karkarwa A haka suka samu suka dauke gawar Cikin kuka Adam yabi bayansu Shi kam Yusuf a wurin ya zauna kamar dasashi akayi Acan Kuma akayiwa gawar duk abin da ya kamata kafin ma gari ya waye anyi komai an gama Washe gari da safe wannan lbrin ya iski Anuty Sadiya Duk da mijinta ta ya ji dashi akayi komai Amman ya rasa ta INA zai fara kawo mata wannan zance Sai da safen yace ta shirya suje gida Su gaidasu A mota ta kalli mijinta Cikin sanyi tace Abban Yumin. Na,am ya amsa mata Cikin sanyi Sai kuma tayi shiru gamida dafe qirjinta Hannushi yasa ya kamo nata yace Kin kirani kin Kuma yi shiru Kai ta daqo ta kalleshi Cikin rawar murya da alamar kuka zatayi Tace Abban Yumin Zuciyata Na tsinkewa tsoro nakeji ban San meyasa ba tun jiya nakejin faduwar gaba A hankali ya jawota ya manna ta a jikin shi cikin fargaba yace ki rinqa addu,a ki Kuma kasance mai yarda da gaddara Dai dai nan yayi parking a farfajiyar gidan nasu A hankali ta zame jikinta ta fito Cikin tsoro da firgita ta bude idanta da kyau ganin gaba daya harabar gidan a cike yake da mutane a take qafarta ta fara rawa Cikin tsoro ta juyo gareshi tana Abban Yumin me ya faru me kake boye min Hannushi ta riqe tana jijji gawa da qarfi tana ka fada min INA Abba ban ganshi anan ba Allah sarki ita Sam bata kai tunanin ta kan qaninta ta rasa ba Rabi,u dake gefe ne yayi saurin isowa gareta durqushe wa yayi a gaban ta Cikin kuka yace Anuty Sadiya ya Ahmad ya tafi ya Ahmad ya tafi ya barmu Ido ta zaro Cikin tsoro Sai kuma tayi Cikin gida kai tsaye dakin Nenne ta nufa Can ta hango Ummi da sauri taje gaban ta ta fada Cikin kuka tace Ummi Me nakeji Ummi meya samu Dan uwana wayyo Allah wayyo Dan uwana wayyo Nenne Na wayyo cikina Ummi shike nan Na rasa Dan uwa Adam ne ya kamo hannuta Cikin kuka yace Anuty Sadiya mun rasa Ahmad Anuty Sadiya Ahmad ya tafi ya barmu Gaba daya suka ruda parlon kakace ta tashi itama Cikin kuka ta kamo hannu Sadiya Da Adam tayi Cikin daki dasu Suna shiga Sadiya ta hango Yusuf Wanda tun jiyan bai tashi a wurin ba sai sallan asuba da ya tashi yayi da taimakon hydar Tana hoggo shi ga Nenne a gefenshi Tana riqe da hannushi tana fadin Haba Yusuf kayi mgn mana Yusuf katashi kaje qun baqin da sukazo yi maka gaisuwa Haba Yusuf fushi kakeyi da yin ubangiji ne Shin ase bazaka rungumi qaddara ba Yusufa mufa musul Maine Shi kam Yusuf ido ya zubawa Anuty Sadiya Ita Kuma gabanshi tazo ta durqusa ta kamo hannushi ta kifa kanta kan cinyarsa ta saki wani kuka mai ban tausayi Tana kuka tana fadin Yusuf ya zamuyi Allah shi yabamu Ahmad Kuma shi ya dauke shi Dama kullum haka Ahmad ke gayamin ai Wanda ya Baku ni yaga fiku sona Anuty Sadiya ki dena damuwa da halin da nake ciki ase Ahmad duk maganganu da yakejin wasiyace A hankali ya daura nashi kan kan kafadarta Yasa hannushi ya riqe nata Sai ya kuma kura mata ido Yana jujjuya kai A hankali tace Yusuf kayi min mgn ma ko zanji sanyi a raina dama kullum Ahmad cemin yake ko ya mutum kar Na damu gaka ga Adam da Abubakar duk abin da nake so zaku min Kai ta juya cikin kuka tace Ummi INA Abba Ummi a wane hali Abba yake ? Cikin duseshewar murya tace Sadiya Abba tun a Daren jiya ya tafi Abuja shida Hydar Kuma yau dinnan zasu wuce India A Dan tsorace tace Ummi Abba ne ba lfy ko ehh Sadiya abbanku baya Cikin hayya cin sa Hawan jinisa ne ya tashi Sai hawayen ke bin fuskar ta Adam ne ya kalleta Cikin sanyi yace anty sadiya ko zakizo kije dakin Ummi ki zauna da su Maryam da Aysha da Amira suna can Sai kuka sukayi ba mai lallashin wani Cikin sanyin jiki ta nufi dakin Ummin Ayyah Maryam da aysha suna zaune tun jiya da Aysha ta farfado suke ta kuka abin tausayi Aysha abin ya hadu mata jiya tasan ba ummi bace mahaifiyar ta kuma a jiya ta rasa ya Ahmad dinta Kuma a jiya tasan mahaifiyata ta rasu a lkcin aihuwarta Ganin Sadiya yasa ta fada jikinta tai ta wani sabon kuka Ta ruggumi meta nan sukayi ta kukansu Da dyar dai suka samu suka tsagaita Da kukan Rayuwar gidan ya canja musu gidan ya koma tamkar ba kowa Sai masu zuwa gaisu da zaran bakin suntafi kuma to shike nan gidan yayi shiru Rayuwar Yusuf ta sauya ta koma abin tausayi baya mgn da kowa komai za acemai da kai ko ido yake bada amasa duk masifar Na ta Yusuf da bala,I da mishkilanci yanxu babu su Ya koma abin tausayi Baya iya mgn 5 lafiyeyyu Komai ya rigada ya gama sauyawa Aysha kam ko yaushe Sai ta shiga toilet tayi ta kukanta Sai fuska ta kumbura Maryam Kuma yanxu bata iya kukan ya rigada zuciyata ta bushe Yau ne akayi sadakan 7 gaba daya baqi sun waste su Bappa Yaya ne kadai suka rege basu tafi ba Yau kwana 10 da rasuwar Kuma yaune su Bappa Yaya ya zasu koma Shiyasa da safe ya Tara zuriyar tasa Bayan ya gama musu nasiha Ya kalli Yusuf da Adam yace Dudabe Na,am ya amsa cikin sanyi Ido ya zuba mai cikin tausayawa yace Yanxu me kakeyi a qasarnan ? Kai ya sunkuyar gami da cije lips enshi yace me zanyi Kuma a qasarnan bani da abin da zanyi Toh ka shirya kaida matarka Ku koma kaje kaci gaba da kara tunka Aysha dake takure a jikin Nenne Cikin kuka tace Dan Allah Bappa Yaya Ku barni ni bana son komawa can To me zaki zauna kiyi a nandin ? Ni dai banson komawa canne Ta bashi amsa Cikin kuka Shi dai Yusuf shiru yayi Dan yanxu qoqolwarsa bata fiye gane me ake yiba Haka kuwa akayi randa akayi kwana 15 da rasuwar a ranar baba bello ya kamma lawa su Yusuf shirin tafiyar su A Kuma ranar ✈ jirginsu zai tashi A hankali suke fitowa daga parlon suna zuwa harabar gidan Bayan su Rabi,u sun gama Sa musu kayansu a but Cikin sanyi Yusuf yaje ya durqusa gaban baba bello murya Na rawa yace baba zan tafi Kanshi ya dafe Cikin qarfafa mai guiwa yace Allah ya kaiku lfy Yusuf amin yace Gami da miqewa yaje gaban Nenne itama ta mai addu,a A hankali ya qarisa gaban umminshi Ya durqusa guiwa bibbiyu yace Ummi zan tafi Amman bazan sake zuwa qasarnan da wuriba Cikin ajiyar hrt Ta kamo shi ta tsaida shi A hankali taja hannu Aysha ta samai Cikin nasa tace to ga amanar da Dan uwanka ya baka Yana Cikin qabarinshi mu kuwa mune masu ganin irin yadda zaka riqe amanar da ya baka a dai dai lkcin da ransa yake fita a jikin shi Hannu yasa ya kamo Na Ayshan ya juya Cikin Rashin sanin me zaiyi Ya jata Suka qarisa gaban Adam ya ruggume juna sukayi musabaha Ya kalleshi Cikin sanyi yace biyaye Allah ta sadamu kan alkhairi Amin yace dai 2 lkcin da suka shiga mota Usmanne da Rabi,u suka kaisu airport 3:37 pm jirginsu ya tashi ?🍇🍇 NAYI NADAMA 👇🏻👇🏻👇🏻 MI,WASMITI page 7⃣4⃣to7⃣5⃣ Na Aysha s Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Allah sarki rayuwa mai juyawa A cikin jirgi Yusuf ya zauna kan kuje rarsa ta number 24 yayinda Aysha Kuma nata number 23 ne Nata kujerar itace kusa da window jirgin A hankali Yusuf yake takawa har ya isa wurin zaman nasu Jiki a sanyaye ya zauna Gamida yin taqumi da hannushi daya ya Sada kanshi qasa Bai tuno komai Sai ran da suka dawo India a lokcin da suka kamma la kara tunsu A wannan jirgin suka dawo a wadannan kujerun suka zauna inda ya ke zaune anan ya zauna a wancan lkcin Na gefenshi Kuma biyayenshi ne A hankali ya zubawa sit din ido Zuciyarsa Na suya Sai cije lebenshi yakeyi sabida kuka yake son yi Amman kuma ya kasa samun kukan Yana Cikin wannan halin Yaji abi Na diga kan wuyanshi Hannushi yasa ya shafo wurin kamar ruwa yaji Kai ya dago ya zubawa Aysha dake tsaye a gefenshi dafe da kan kuje ranshi Hawaye wannan Na koran wancan Kallonta yayi Cikin shawa,a A ranshi yake cewa Kinji dadi da kika samu kina kuka kina zubda qollah😭 nasan koba komai zakiji sauqi a ranki Sanarwan da akeyi Na koma ya koma gun zamansa jirgi zai tashi shine ya dawo dashi daga tunanin da yakeyi Ido ya sake zuba mata A hankali ya daqo Hannushi ya kamo nata Ya jawota Gami da Dan Jan qafafunshi Dan ta samu gun wucewa Kan sit din gefenshi ya yaja hannuta ya zaunar da ita Ita kam Aysha ido cike da qollah😭 ta bi fuskar shi da kallo Lkci guda Kuma ta tuno Lkcin da zasu tafi wancan karon Da ta tsaya a kanshi haka tana kuka Cikin masifa ya rinqa surface mata bala,I harda yarfa mata mari yana mayya kawai kin wani tasa mutane a gaba kina kuka toh kanki zakici ai tunda kikayi kuskuren yadda kika biyoni toh wlh baqin jaki Sai ya fiki jin dadi Cikin tsawa ya jawota ya tura a wancan lkcin Tana Cikin tunanin taji jishi Cikin wani irin voice yace Kija bel dinnan ki saka Kai ta sunkuyar Cikin zubar qollah😭 A hankali Jirgin ya rinqa Qugi da Dan diri Cikin tafiya a hankali ya rinqa Dan tashi sama A hankali Yusuf ya maida kanshi jikin sit din ya lumshe idansa jikin jin wani irin azaba a karo Na forko da yaji yana qaunar barin qasarsa ta aihuwa A karo Na forko da yaji ya qagu ya daina shaqar iskar qasar A ranshi yakeji to me y rege masa a qasar nan Babu ya fada a bayyane Gami da bude idanshi da jin zafi a ransa Ita kam Aysha ta window take yiwa qasar ta wani irin kallo da jirgin ya gama tashi sama Ta kifa kanta jikin window ta saki kuka mai ban tausayi Ido ya zuba mata gami da jinjina kai A ranshi Kuma cewa yayi kuka ma Rahama ne bazan hanaki ba A haka Cikin kukan bacci ya debeta Yayinda shi Kuma Sai ajiyar hrt da yake tayi 9:00 Am agogon Nigeria Dai2 da 11:00Am saudiya Jirginsu ✈yayi landing Cikin birnin Madina A hankali fasinjoji suka rinqa fita Ido Yusuf ya rufe a sannu Kuma ya budesu Kan fuskar amanar Ahmad dinshi Cikin sanyin murya yace Ke Ke tashi mun iso Kamar a mafarki taji muryar shi Sai kuma taji tsoro Dan tuna wancan Zuwan nasu inda ya rinqa zuba mata mari Cikin fushi yace ko ki taso ko Na tafi Na barki Bira alaqaqai kawai Banza mayya..a wancan lkcin A hankali ya katse mata tunani da takeyi Muryar shi ta kumaji Cikin Dan kauri yace Ke INA mgn kinyi shiru A hankali ta miqe Tabi bayan shi Har inda aka ta naji motici Dan ma tafiya wani ma aikaci Na biye dasu riqe da jakarsu Har zuwa gun motar Suka shiga suka tafi A dai dai harabar wani qaton gida mai kama da ma aikata part part sun kusa 7 Abakin qofar su direban ya tsaya dai2 bakin qofar shiga Suna fita Yaja motarsa ya tafi Jakar ta ya zubawa ido Cikin ranshi yasan bazata iya dagawa ba Amman kuma shima ga nashi Sai kuma ya kalli inda take ta tsaya Sai rawan sanyi take Dan daga dukkan alamu anyi ruwan samane ya dauke Sai walqiya akeyi da iska mai sanyi da take kadawa Hannu yasa ya dauki jakar tata yasa qafa ya tura mata nasa Ya juya yayi gaba a hankali tabi bayan shi A parlo ya ajiye mata nata ya karbi tasa ya juya yabi Cikin Dan koridon da zai Sa dashi da parlon shi Yana shiga ya fada kan 3 str Cikin Yanayin shi da yafi kama da maraya Ido ya lumshe ba tare da yayi bacci ba zafi yakeji sasoi a rayuwarsa A hankali ya daqo phone dinshi Nenne ya kira Tana dagawa tace Yusuf kun isako ? ehh yace mata Gamida cewa ki gaida baba Sai da safe Toh Allah ya bamu alkhairi tace dashi gamida katse woyar Shi kuwa a nashi gefen kashe phone din nashi yayi gaba daya Ita kuwa Aysha da qyer taja jikinta ta tafi bedroom dinta Kan gado ta fada Cikin kuka a haka a ranan ta kwana kuka Shi kuwa Yusuf kukan ya nema ya rasa shiya sa ya tashi Cikin rawan jiki yaje yayi alwala yazo ya rinqa nafilfili Idan yayi sujjada ba abin da yakeyi Sai nemawa Dan uwan shi gafara Washe gari da safe Abokan Yusuf laraba suka rinqa zuwa mai taziya da dama daga cikinsa sun San Ahmad Wasu sunsu Kuma insun zo kuka sukayi kamar zasu suma Akwai wasu abo kansu su 2 Sulaiman da Bashir Wanda tare sukayi karatu a inda Kuma suma yanxu suna Jami,atul madinan ne suna kara ilimi Bashir Dan Katsina ne Kuma tare da matarsa sukazo Mai suna Zakiya Tunda sukazo Sulaiman yake kuka kamar mace dan shi ya shaqu da Ahmad sosai kusan halin su iri daya Bashirne ya rinqa Dan bashi baki yayinda dashi ma yake ta sharar qollah😭 Shi kam Yusuf Sai cije lebe da yakeyi Cikin daburcewar murya yace Zakiya ki isa gun qaunar Ahmad tana ciki Ku gaisa Toh tace mai gami da miqewa Tayi candin A hankali tayi SLM Cikin parlon ba kowa Ido ta Dan bude Cikin zubar hawaye tana kallon parlon a shirya yake tsafta ba datti ko kadan komai Na parlon farine da jaa gashi labulayen suna sasake shiyasa Sai parlon yayi dubu kamar dare SLM ta kumayi gamida zuwa jikin gini ta kunna wutan tsakiyar parlon Ba kowa har ta juya zata fita Sai kuma taji sautin kukan a cin bedroom din Juyawa tayi ta shiga dakin Kan gado ta hangota tayi rufa da ciki Sai kuka takeyi tana Ayyah ya Ahmad yanxu mun rabu kenan bazan Kuma ganin ka ba Zuwa tayi ta zauna gefen ta Cikin sanyin murya Da qoqarin danne nata kukan tace Kiyi haquri Aysha ki daina bin Dan uwanka da kuka kiyi ta masa addu ,a shi yafi buqata a gareku ba hawayen ki ba Dagowa tayi tana kallonta Cikin rashin Sani Fahimtar hakan da Zakiya tayi shiyasa ta kamo hannuta Tace Ni suna Zakiya ni matar abokin Yusuf ne sunan mijinta Bashir Muma muna qasar nan Kuma tare muke da mijina yana can gun Yusuf dinne . Allah sarki Aysha rashin Dan uwa shiyasa a take taji zaki tamkar Maryam da Amira Cikin hawayen tace kinsan ya Ahmad dinako ? Eh Na sanshi Aysha ! Ayyah to shinefa ya rasu. ehh Na Sani Aysha Kibar kukan Dan Allah Wlh nima zaki Sani kuka Kai ta jinji na gami da share hawayen ta tace Ni ma banson yi mishi kukan kasawa nake in banyi kukan ba ji nake kamar zan mutu Cikin tausa yawa tace ki rinqa addu,a kinji ko Aysha Toh tace Cikin goge qollah😭 Haka dai Zakiya tayi ta lallashinta Har ta samu ta jawota suka shiga kitchen Suka danti girki mai Dan sauki Dan dama ba abin da babu a cikin kitchen din Ita ta dauka ta kaiwa su Yusuf T juya zata tafi Bashir yace in kin gama kizo mu tafi Toh tace Cikin sanyi Dan tanajin tausayin yadda Yusuf da Aysha zasu kasance su kadai A Parlon ta zuba abinci ta matso ayshi cin lallashi tace Ayyah Aysha ki matso kici abinci kinji ko Kai ta girgiza tace bazan iyaba bakina daci nakeji Ta Dan sunkuyar d kai tace Aysha bakya son nazo gobe ko ? Da sauri tace a a wlh inaso To kici abinci Ayyah Zakiya nima ina son ci bazan iya bane shi yasa Miqewa tayi gamida yin Cikin kitchen din furts ta dauko ta kawo mata tace gashi ki daure kici koda inabinnan da Dan dabino ga Apple Karba tayi ta danci Sannan sukayi sallan insha A parlon Yusuf Kuma shi da sulamai sun kasa cinnkomai shima Bashir sai dan tea ya Dan Sha Bashir dinne ya miqe gami da kallon Yusuf Cikin sanyi yace Yusuf zamu tafi Sai gobe in Allah ya kaimu insha Allah zamuzo Amman dan Allah Yusuf ka rinqa Sa dauriya a ranka Yusuf ka rege tunani Dan Allah kar ya maka illa Kasan kana da matsalan zuciya Kai ya sunkuyar Cikin ceje lips dinshi da gaba daya yanxu sun kubbura sunyi jazur sabida rashin kukan da bai samu yayinba Sai yayi ta cizon lips din nashi Haka dai Bashir ya rinqa bashi baki Sannan suka wuce parlon Aysha Sulaiman kam yana ganin ta Sai hawaye Dan shi yasan irin son da Ahmad yake mata Kuma itama tasan Sulaimanu Durqusawa tayi a gabanshi tana zubda qollah😭 Cikin rawan murya yace Sannu Aysha sannu da rashi Allah ya jiqanshi da Rahama Amin ya rabbi ta fada Cikin kuka shima Bashir ya gaida ta sannan suka fita suka tafi Shi kam Yusuf parlon shi ya koma Cikin kuncin zuciya Yadda ya kwana jiya hakama ya kwana yau Washe gari da safe Bashir da Sulaiman sukazo Zakiya kuwa sai da ta tsaya tayi musu girki sannan ta taho Daga ranan haka sukayi tayi Sai randa suka cika kwana 7 da dawowa sannan suka daina zuwa Su wuni Sai dai duk da haka kullum zakiya ke musu girki ta bawa Bashir ya kawo musu duk da baci sukayi ba yadda Bashir ke kawo shi haka yake zuwa ya dau keshi Sannu a hankali yau watansu daya da dawowa Rayuwa ta juya ta canxa Yusuf Dan qolisan nan gaba daya ya zama abin tausayi banda wonka ba abinda yakeyi ko mai bai shafawa A hankali Dan sirinrin sajenshi Na ya rinqa qaruwa yana yawa yana bajewa ga wani irin rama da yayi duk ya canxa sai dai kyau kam kamar qara mai akeyi kullum da safe yana dawowa masallaci Sai ya leqa gun Aysha a cewarsa amanarsa CE ita Duk da ita kam bata ganin shi Wata ranar jummah da daddare misalin qarfe 2 Na dare Aysha dake parlo Wanda a yanxu parlon ya zama dakin kwananta Dan Da zaran tayi bacci a bedroom sai mafarkin ya Ahmad dinta ke bibiyarta Shiyasa ta dawo parlon Inda zata kwana kuka yayinda zata kwana jin sautin karatun Yusuf Kuma a parlon shi Sai dai abin tsoro da firgici jin a yau ba sautin karatun Yusuf din take jiba Cikin firgita ta tashi da sauri ta nufi parlon bashi..... Tsoron ta ya qaru ganin abinda Yusuf din keyi ta kidime ta rude ta kidime da sauri tayi kanshi.......... I love you all my frns😘😍😘 Allah ya barmu tare ?🍇🍇 NAYI NADAMA 👇🏻👇🏻👇🏻 MI,WASMITI page 7⃣6⃣to7⃣7⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Kina raina Asma,u Adam admin din zauren guzurin gobe alqiyama😘😍 I love you all my frns😘😍 Kuka yakeyi cikin fitar hankali kuka mai ban tausayi gaba daya ya fita hayyacinsa Jikinsa kab zuface ke tsatsafo mai tako ina Ya zaune kan sallayah runqqume da qur,ani mai girma a jikinsa ga qaton photo su su 4 Shi da Ahmad din da Adam da Abubakar Hannushi yasa ya dafe kanshi da hannu bibbiyu Cikin kuka Da ya samu rabbi ya sauqo mai dashi a yau Cikin dashewar murya yaketa nanata wayyo Allah Na Wayyo Allah Ya rabbi ka bani ikon cin jarra bawar da ka jarab ceni da ita ya ubangiji kayiwa bawan ka Ahmad Rahama rabbi ka haskaka mai qabarinshi Kanshi ya dafe da hannushi daya gaba daya jijiyoyin kan nashi sunyi rudu rudu Hannushi daya Kuma qirjinshi ya dafe da qarfi Gaba daya jikin shi rawa yakeyi Sai zamewa yakeyi a kan carpet din Cikin wahala ya rinqa kiran Ahmad shi kenan mun rabu Ayyah biyayena Bani da wani masoyi kamar ka bani da mai gayamin gsky kamar ka bani da Wanda nakeji a jikina kamar ka Kaine maisani farin ciki Tsoro sosai ta ring a ji ganin yadda ya fita hankalinsa Da sauri itama Cikin Kukan taje Gaban shi ta zare qura,anin a jikin shi A hankali ta zo gaban shi ta durqusa Cikin kukan Ta rinqa kirashi Hamma Yusuf kayi shiru Dan Allah ka daina kuka Meyasa bazaka yiwa ya Ahmad addu,a ba Wayyo Ummi Na ya zanyi kuka ta kamayi sosai Cikin kidiman Ya jawota jikin shi A yau yanaji bai da kowa a duniya Sai Ita tunda itace ke kusa dashi Gani yake ba Wanda zai San irin zafin da yakeji Sai ita Shiyasa Ya matseta da qarfi a jikin shi Kukan yakeyi kamar yaro Itama kukan takeyi kamar zata zauce Cikin kukan tace Wayyo Ummi Na Wayyo rayuwa ta mana dubu Wayyo Hamma Yusuf ni dai ka maida ni Gida Kanta ya manna kan qirjinshi Yana nima Sai dai su Ummi suzo suga gawata zuciyata zata fashe ban San ya zanyi ba Kanta ta daqo ta zuba mai ido lkci daya Kuma numfashin shi ya fara daukewa Cikin tsoro ta miqe tana tsakiyar parlon tana bubbuga qafa Tana kuka sosai ganin gaba daya kamar mutuwa shima zaiyi Gaba daya ya fara murdewa kanshi Sai juyawa yakeyi da sauri ta zauna gami da Dora kanshi kan cinyarta Gami da sakin kuka Woyar ta ta laluba a wurin Zakiyi ta kira Kiran forko har ya tsinke bata dagaba Sai a nabiyu Kiran Na shiga Bashir da yanxu ya fito wonka bayan ya gama shanawa da matarsa ita Kuma yana shiga tayi Bacci Shisa har kiran ya tsinke bata dagaba Kiran Na qoqarin katsewa Bashir ya daga Woyar Cikin Kuka tace Hello zakiyi Zakiya Hamma Yusuf ki gayawa Bashir Hamma Yusuf bai da lfy Na rasa yadda zanyi Da sauri Bashir yace Aysha Kuna INA meke damun Yusuf din Cikin kuka tace Bashir kazo Dan Allah kazo kawai Toh yace gamida katse kiran Da sauri sauri ya zura Riga hannu kawai yasa ya daqo zakiya Cikin tsoro ta miqe tana lfy honey ? Tashi tashi kisa kayanki Yusuf ba lfy A tsorace ta shirya suka fito Suka nufi anquwarsu Yusuf din mai suna Ibrahim Khalil Wanda Ya kasance yana Dan kusa da masallacin Annabi Shiyasa anquwar ba kewa darene kamar rana Suna shiga Aysha ta juyo Cikin zubda qollah😭 tace Bashir kalli kalli yadda yakeyi Da sauri bashir Ya zauna gami da kamo shi Kanshi ya rinqa shafawa wani Dan farin mgni gamida zaro wata yar allura qarama ya zira mai A take Sai ya kuma rinqa mimmiqewa kamar Wanda ranshi zai bar jikin shi Sai daddamge hannushi yakeyi Yana juyawa Ganin haka yasa Aysha qara rudewa Cikin kuka ta durqusa a gaban shi tana hama Yusuf ka tashi katashi bari in kirana mana su Abba su zo su dauke mu Phone dinta ta Kuma karba a hannun zakiya Baba bello ta kira Cikin Mmkin wake Neman shi a Daren nan Da sauri yayi pikin ganin Aysha CE Cikin kuka tamai bayanin a bindake faruwa Sosai yaji zuciyarsa ya tsinke A ranshi yace ya Allah ka rufa mana asiri Allah ka hanamu sake ganin wani duhun a wannan rayuwar A fili Kuma Da sauri yace Yanxu ina Bashir din Gashi nan ta fada gami da miqa mai phone din A tsorace yace hello Bashir waimeke faruwa ne Ina Yusuf dinne A hankali yace Baba ga shi yana konce yanxu ya Dan samu ya fara lafawa Na kuma yimai alluran banci yanxu ya samu yana Dan lfwa Toh Wai Bashir meke damunshi ne ? Wlh baba Yusuf damuwa CE ta mai yawa ga kadaci Yusuf yana buqatar kulawa baba wlh rayuwar Yusuf Na Cikin hadari gwara a dauki mataki tun wuri kasan Dama yana da hrt problem Cikin firgita da baya nan Bashir din Yace Insha Allahu bashir a satinnan zan shirya mana zamu taho zamuzo mu ga halin da yake ciki Toh bba Allah ya kawoku lfy Amin ya amsa gamida cewa ka bashi duk kulawar da ta kamata Ba komai baba insha Allahu zai samu sauqi Allah yasa yace gami da katse kiran A hankali ya fara nitsuwa Cikin sanyi ya fara lumshe idon shi Bacci mai qarfi ya debeshi Lkci daya ya fara sauqe numfashi mai nauyi Cikin ajiyar zuciya Aysha ta matso gefenshi tana gyara mai konciyar tasa Zama tayi a gefen tana Dan mai kallon tausayi Bashir Kuma shima gefen ya koma gamida rungume matarsa A haka bacci ya debesu Ita kam Aysha gani take tana rufe idanta zai mutum shiyasa ta zauna Sai zubda qollah😭 da takeyi Sune basu tashiba Sai 5:00 Am A hankali Yusuf ya fara bude idanshi Cikin dan sauran mayen allurar baccin Ido ya qura mata Yayinda qollah😭 ke bin fuskarta A hankali ya tashi ya zauna Ya jingina da jikin 1 str A dan Firgici ta miqe tana Bashir ya tashi tashi ka gani Da sauri shima ya miqe gefenshi ya zauna Cikin sanyin murya yace Yusuf ya jikin dai ? Kai ya jinjina gamida Dan motsa lips dinshi yace da sauqi bash Masha Allah To Aysha kinga Dan uwanka ya miqe Sai hankali ya konta a daina kuka Ita dai Sai hawayen ta kalleshi tace ai baba yace zai zo a satin nan Kuma tare zai koma damu Ido ya qura mata Cikin mmk yace waya gayawa baba banda lfy? bashir ne yace yo wannan ai kasan mai fada Zakiya ta kalli mijinta cikin kulawa tace ai gwara da ta fada nimafa jiya naji tsoro sosai Juyawa yayi ya zuba mata ido A hankali ya sauqe idanshi kan qirjinta Rigar bacci CE a jikinta mai taushi Sai dai doguwace har qasa Amman gaba daya ta koma ta manne a jikinta Ido ya sake lumshwa ganin girjin nata yayi wani cur a tsaye Lkci daya idanshi ya fara worewa suna Dan yin jaa Kanshi ya sunkuyar Cikin kamo lips dinshi na qasa ya fara tsotsa a hankali Bashir ne ya Dan kalleshi a fakaice Baki ya taba a ranshi yace kaji Dan banza mai idon ganin mata mutum kamar maye A fili Kuma miqewa yayi gamida kamo hannu zakiya yace Toh mu kam zamu wuce gida Sai anjima Zan zo Na qarisa ma allurar taka Kai ya geda mai alamar toh Bayan sun fitane ya Dan sunkuyar da kanshi Cikin sanyi yace Kinyi sallan ne ? Kai ta girgi zamai Cikin zubda qollah😭 Kallonta ya kuma yi Cikin rauni yace toh tashi kije kiyi sallan Bata dai tashi ba shima Kuma ya kasa tashi Dan baijin qarfi sosai A karo Na forko ya Sa hannushi ya damage mararsa lips dinshi yake son ciza ko zasu bar barin da suka farayi Amman ina a take gaba daya tsikar jijinshi ya fra tashi Sanyin jarabar tasa ya fara ka dashi Har haworansa Na dukan juna kat kat Cikin qarfin hali ya miqe ya fada toilet Ruwan ya sakarwa kansa Cikin ajiyar hrt ya rinqa murza jikinsa da samulu Sai da ya watsa ruwa sannan yayi alwala ya fiti Yana fita ya samu bata parlon sallah yayi Cikin Kushu,I ya rinqa jero addu,oin nemawa Dan uwanshi gafara Bayan ya idar da sallan ne ya zame kan carpet din ya konta Idanshi a rufe Yaji ta shigo dakin Gaban shi tazo ta durqusa Cikin sanyin murya tace Hamma Yusuf ya jikin baiyi mgn ba bai Kuma bude idanshi ba Phone dinta ta miqa mai Tana fadin gashi baba nason mgn da kai Kuma yace layukanka basayi Tsaki yaja da qarfi gamida bude idanshi da tashi zaune Hannushi yasa ya fizgota da qarfi har Sai da ta fada jikin shi cikin sauri Kuma ya tureta Cikin masifa ya daqo hannushi zai yarfa mata mari Sai kuma ya tsaya da sauri saka makon abinda yaji take fur tawa ?🍇🍇 NAYI NADAMA 👇🏻👇🏻👇🏻 MI,WASMITI page 8⃣1⃣to8⃣3⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Wayyo Allah Na Da sauri yasa tafin hannushi mai laushi Ya rufe bakinta Ido ta zazzaro Cikin qoqarin kauda kanta Tana baya baya Cikin mishkilanci Ya rinqa daga qafarsa yana takawa a hankali yana qara matsota ita Kuma tana qara yin baya2 Har saida taji ta jikin Garu Ido ya tsura mata Cikin hada fuska Ya dago hannushi ya kamo kunneta ya matse Da qarfi Da qarfi tayi qara Amman sautin bai fitoba sabida tafin hannushi da yasa ya to she bakin nata Qara matse kunne yayi Cikin yanayin gargadi Yace Kin San Allah ki kiyaye ni In kuwa ba hakaba wlh zan babbalaki Kaji yarinya da rainin wayo wato har kin samu damar murgudamin baki ko😏 toh wlh Allah ki rufawa kanki asiri in ba hakaba kuwa Hmmm ya fada gamida jinjina kanshi alamun zaki daku 😡 Sake matse kunne yayi yana kinji ko bakijiba? Kai ta gyeda alamun taji Qara matsota yayi Gami da manna girjinshi a jikin nata Sake nauyin shi yayi kan qirjinta Gami da matseta ya hadata da jikin ganin idon ta rumtse Cikin wahala jin yadda ya hadata da gini Hannu bibbiyu tasa kan qirjinshi tana Dan tureshi Kanshi ya sunkuyar Cikin boye halin da ya fara shiga Lips dinshi ya kamo ya matse da Dan qarfi Cikin dauriya Yace kina jina ko? Uhum ta fada Cikin Neman iska Dan gaba daya ya matseta Qafarshi ya daga gamida taka nata qafan Cikin mugunta Yaci gaba da cewa Wlh karki ga Su baba sunzo Kice zaki kasa min Rashin Kunya Kin sanni sarai Wlh ko sunanan dakaki zan Barema ai kin Sani sarai Tafiya zasuyi su barki Tare dani Ita dai Sai zaro Ido 😳 Take hannushi ya daga Daga kan bakinta yace Muna fuka Da manyan idan nunki a wurin Na rashin kunya Ita dai numfashi ta rinqa sauqe a hankali Ta sunkuya ta dauke robar madarar Har takai Bakin qofar Yace ke Tsayawa tayi ba tare da ta juyoba Cikin tsurawa gugunta Ido yace In Kuma kika yarda kikamin halin munafurci Kinsan abinda zai biyo baya Kinjini kam ko Ehh tace Cikin jin haushi Toh me kika tsaya yi anan maza kauce daga nan Da sassarfa ta fice Tana Allah ya isana mugu kawai 10:00 pm Suna parlo gaba dayansu suna ta hira Yusuf Na zaune gefen baba suna ta dan hirarsu Usman Kuma yana zaune tsananin Sadiya da Aysha suna ta hira yana nunawa Aysha pictures din Maryam da Amira da dai sauran mutanen gida Cikin mmk ta kalli Usman tace kai Ya Usman Ga yadda Maryam ta qara fari yanxufa ta kaini fari Sai dai Kuma ta rame Sadiya CE ta dan kalleta Cikin Dan jin bacci tace Aysha Maryam ai dole ta rame Cikin yana wahal da ita sosai Kai ta daqo cikin rashin fahimta Tace Anuty Sadiya wake da ciki? Da Dan fara tace yoh Cikin abin tsoro ne naga kin wani zazzaro ido Yusuf dake gefen Sai a yanxu ya Dan kalli inda suke Cikin murtuqe fuska ya harareta da salon ai ita kam Sai zaro idan ta iya Baki ta tura Cikin maida kanta gun Nenne Tace Nenne Wai da gsk Maryam Nada ciki Fuska dauke da murmushi tace Ehh Aysha da gsk Maryam Nada ciki ? Cikin fara,a ta koma jikin Usman tace yes Muma mun kusa mu zama iyaye wayyo Allah Na wayaga Maryam da baby Da sauri ta Kuma tashi taje Gaban baba bello Cikin farin ciki tace Baba Tare zamu koma ko kaga kar ayi suna Bana can Dan kasan dole ni zanje Na rauni da ko yar ya Ahmad Usman ne ya kalleta Cikin mmk yace da Allah can a reni muje biki ni mijiba baya fada Bafa cemiki akayi ta aihu ba Cikinda gaba daya watanshi 2 da sati 3 Mutum Sai shegen son yawo Ehdin ANSo yawon Ai ba kai Na tabbaya ba ehe Gun baba takuma maida dubanta Cikin Neman alfarma Tace Dan Allah baba kar a hanani Zuwa Kai ya geda gamida kallonta Cikin Tuno Dan nashi Yace Insha Allahu zakije Aysha Amman Sai Maryam din ta aihu kinga kafin satin suna Sai kuje Kai ya juya gun Yusuf Dake sauqe numshi a hankali Dan furucin Aysha ya famomai ciwon rashin da uwan shi Yusuf Baba ya kirashi Cikin bada umurni Yace Yusuf in Allah ya sauqi Maryam lfy To ka tabbatar Aysha taje Kai ya jinjina Cikin jin daci Murya Na rawa yace Baba in ban jeba wa zaije Baba A yanxu Dan Ahmad ai baida wani uba da ya wuceni Baba wannan ai dama nauyi nane Na jibanci dukkan lamuran rayuwar wannan Da Baba me zance da ubangijina Ya dauke min Ahmad Sai ya kuma amsar addur Ahmad da yayi aloka cin da baifi awa 2. Baya bar duniya A wannan rana ya roki Allah ya bashi da da zai zama madadin shi a gareni a wancan lkcin INA daukan zance Ahmad a matsayin wasa ase dgske Zai tafi ya barni Sai kuma muryarsa ta carke Yai shiru yanata cijjije lebe Aysha kam tun i Sai hawayen Cikin kuka tace baba har Sai ta aihu kafin inje? Ehh Sai ta aihu kafin kije a nan din ma Sai inki min alqawari Zaki daina yiwa Dan uwanka Kuka ki Kuma yi qoqarin Sa Dan uwanshi Yusuf y daina damuwa Den Na tabbaya koda Ahmad Na makoncinsa toh zanyi alfahari daku Cikin share hawayen tace Na bari baba bazan sakeba inason ya Ahmad yai alfahari dani Cikin jin dad yace Aha haka nakeson ji Allah ya muku albarka baki dayanku Amin suka amsa gaba dayansu Haka sukayi ta hira Har zuwa 1:00 Am Baba ne ya mike Cikin tattara phone dinshi yace toh ni kam zan chiga Sai da safe Shima Yusuf miqewa yayi Cikin kallon Usman yace kai tashi muje mu shiga Baba ne ya juyo ya kalleshi Cikin Dan jin bacci yace a a Yusuf Usman yazo tare zamu kwana Kai ya Dan daqo yace to baba muje mu kwana tare kawai mana A a yace kai dai jeka kawai kai Usman tashi mu tafi Wannan dakin ya ishemu ya nuna dakin daya da yake gefen dakin Aysha wanda da toiler a ciki yace ku kuma Sai Ku shiga nan din ya nuna dakin aysha Toh su Nenne sukace gamida shigewa dakin Ayshan Itama tana biye dasu a baya riqe da laptop din Usman Dan tace a dole zai bar mata har Sai in sunzo komawa Shi kam yusuf a parlon shi ya yada zongo Kan 3 str ya zauna Cikin Dan jin bacci a yau ya danji sanyi a ransa Dan ko ba komai yan uwan shi sun Dan debe mai kewa duk da shi ba hiran yakeyi ba yana dai jinsu kawai A dakin Aysha kuwa Suna shiga Anuty Sadiya ta fada toilet ruwa ta dan watsa a gaggauce Tana fitowa tace Aysha ga ruwan dumi Na hada miki maza jeki danyi Wonka Cikin jin dadi tace yauwa Anuty Na Allah ya bar manake Amin tace Cikin dry Ke dama Aysha son ruwane dake kamar kifi Amman kuma tsoron ruwan sama Kuma kike Kome yasane oho Tana shiga toilet din gamida cewa wlh Anuty ni tsoron tsawa da walqiya da iska nakeji shiyasa Amman in badon suba inason yanayin damuna Dry tayi gamida konci tana to maza jekiyi ki fito Tana fitowa humra tamurza mai balain qamshi gashinta ta Dan saki Dan in ta tubkeshi zai hanata jin dadin konciya rigar bacci ta Ta zira a jikinta mai Dan siririn hannu iya kan gugunta ya tsaya Sai Dan wondonshi Dan madaidaici Shi Kuma iya kacinsa Guywarta Kan gado ta nufa tana fadin Anuty kinyi bacci ne? A a idona 2inaga yadda kike ta wani shan qamshine Kai Anuty Wai gamshi Eh mana tace Cikin CE mata to Sai da safe Ki jamana qofar Toh tace Cikin rashin gano zancen Qofar ta jawo gamida dawowa zata konta a tsakiyarsu Da sauri Sadiya ta mike Cikin mmk tace ke Aysha me haka a INA zaki konta maza tashi ki tafi gun mijinki 😳ido ta zaro Cikin kaduwa tace kai Anuty Dan Allah me haka nifa gsky Ku daina wani cemai mijina Ni ba ruwan dashi Kuma ban zuwa dakinshi nake yiba bare ma wannan mugun banje inda yake bama yana cin zalinah bare Kuma ace INA zuwa inda yake Tashi tayi ta zauna Cikin kamo hannuta parlo ta fito da ita Cikin hada fuska tace maza tafi gun mijinki Aysha ase anamki kallon mai wayo ase babu Sam Auto indai irin wannan zaman kukeyi tofa dole kuita zama Cikin kunci haka Kuma bazaku taba man tawa da Ahmad ba in Kuma kunyi haka to Baku kyauta masaba Ita dai Sai tura baki take tana Ni wlh baruwa bat dashi Fuska a hade tajawo hannuta Sai da ta kaita bakin qofar ta tura ta bude qofar Hannu tasa ta tura bayanta tayi ciki ita Kuma ta juya ta koma tayi konciyarta Shi kuwa jin an bude qofarne ya sashi ya dago kanshi da sauri Dan ganin mai shigowar.... Barka da jumma,ah Masu karatu inafa jiran barka da jumma,ar😀😍😘 H̴A̴U̴S̴A̴ N̴O̴V̴E̴L̴S̴ S̴O̴K̴O̴T̴O̴ W̴H̴A̴T̴S̴A̴P̴P̴ N̴O̴: 07068808039 W̴E̴B̴S̴I̴T̴E̴ : A̴B̴D̴U̴L̴M̴K̴I̴B̴A̴B̴.H̴E̴X̴A̴T̴.C̴O̴M̴ 🍇🍇🍇🍇 NAYI NADAMA 👇🏻👇🏻👇 MI,WASMITI page 7⃣8⃣to8⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 A hankali ya sauqe hannushi Ido ya tsurawa fuskarta Mmk yake Yadda ta wani Rumtse idan nata gamida qaqqame jikinta Dan qara min bakinta Ya kuma zubawa ido Cikin sautin tsoro Take fadin wayyo Allah Na wayyo ya Ahmad Zai dakani Jin sunan Biyayenshi da ta kira ya sauqe mai sanyin jiki A hankali ya Sada kanshi qasa fuska a daure Yace toh Menene me Kuma akayi miki kike ta ihu Ni wlh kinsan banson ife ifenki Na banza nan Dan Allah Ki barni inji da abinda ke damuna Ido ta Dan bude a hankali Da sauri ta Kuma kawar da kanta ganin yadda ya qura mata ido fuskar nan a murtuqe Phone dinta ta miqa mai Tare da cewa Anuty Sadiya CE take son yin mgn da kai Shiru tajishi bai karba bai Kuma mgn ba Sake juyowa tayi Tana kallon shi Hannu ya miqa kamar mai karban phone din Sai kuma kawai taji ya kama kunneta Ya Dan matse Da Dan qarfi ta saki qara Cikin Dan fada fada yace Ke Wai wacce iriyar sokuwace Ke baki San abinda kikeyiba Waya CE miki banda lfy da zaki rinqa bazani a duniya ban da lfy ki kira wannan ki kira wancan Kina tace musu ban da lft Sam ke hankalinki baya jikin ki Ji yadda kike tafiya Ko tsari babu ya fada yana mai qoqarin kauda idanshi daga kan qirjinta Gami da miqewa yana can da Allah tafi can da shirmenki Jiki a sanyaye ta miqe tana fita tana qunquni Mugu kawai azzalumi danma kaga INA jin tausayin ka ne shiyasa ka mutuma in kaga dama Da sauri yace ke me kikace ? Baki ta Dan turo tace a ni cewa nayi Allah ya baka lfy OK insa zaton ai Qunquni kikeyi min A haka ta fita Ta tafi Da rana Bashir ya qara dawowa ya dubashi gami da bashi Magunguna Shi kuwa Yusuf tun daga wannan ranar Ya kamu da ciwon kai Dare nayi Bacci zai qaura cemai ciwon kai mai tsananin zai rufe shi Da zazzabi haka zai ta fama ga tsananin tunanin Dan uwan shi A Nigeria kuwa Tun randa Aysha ta kira baba bello ta shei da mai halin da Yusuf ke ciki . Gari Na wayewa Ya karbi Passport din Nenne Da Na Sadiya Dana Usman ya hada da nashi Yayi ta musu shirin tafiya a cikin satin komai Ya kammala Ran da zasu tafi Nenne ta maida maryama gun Ummi Dan kula da ita Gashi tana fama da laulayin ciki Allah sarki duniya Randa Ahmad zai rasu a ranan rabbi ya albarka cesu da samun Cikin Maryam kam takanyi kuka sosai gaba daya ta jeme Sai Dan fari da hancinta da ya qara fitowa Su Nenne sun Insa lfy Randa suka iso murna a gun Aysha kam ba,a mgn Dan basu gaya musu sun tasoba Kawai Da yamma tana zaune A parlo Yayinda Yusuf ke Cikin daki Yana konce ne Amman hankali shi baya jikin shi Konce yake yayi rigingine idanshi a lumshe Hawayen ne ke ta bin gefen fuskarsa Ba abinda yake tunawa Sai rayuwarsu ta baya Kamar mafarki ya rinqa maimaita shi kenan yanxu Ahmad ba kai a doron qasa yanxu bazan kuma ganin kaba Bazan Kuma jinka ba Yanxu dagani Sai Adam A take ya rinqa jin daci Na tokareshi a maqoshi Yana Cikin wannan Halin yaji Ihun Aysha dake parlo Tsalle takeyi kamar qaramar yarinyar tana maqale da Sadiya Jin tana ya Usman ase Dana kaima zaka zo Ayyah inasu ya Rabi,u Da Dan mmk A fuskarsa ya fito jiki a sanyaye Yana Shiga parlon yaga baba bello a zaune kan 1 str Nenne da Sadiya suna kan 3 str Aysha Kuma Na maqale dasu a tsakiyansu Usman Kuma Na shigo da kayansu Da sauri yaje gaban Baba Cikin Dan jin dadin gani su Ya zauna a gefenshi Cikin sanyi murya yace baba Dama yau zakuzo Ni ban saniba. Ehh ya CE gamida daura Hannusha a kanshi Cikin qashinshi ya tura yatsunshi Daya hannushi Kuma fuskar shi ya shafa gamida shafa har kan sajenshi Ido Ya zuba mai Cikin kulawa Yace Haba Yusuf Wannan wacce iriyar rayuwa kakeyi Ne Yusuf kaga yadda ka maida kanka Fa Kanshi ya kontar kan cinyarsa Gami da rumtse idanshi Murya Na rawa Yace Baba ya zanyi Ya zanyi ne Baba bazan iya manta Ahmad ba Baba mutuwar Ahmad bazata wuce A rainaba Nenne dake gefen tuni ita ma ta fara zubda qollah😭 Aysha CE ta fada kan cinyarta gamida sakin wani Irin kuka mai cin rai Sadiya CE ta dagota Cikin zuba mata ido Tace Aysha Kuka zai dawo da Ahmad ne A a tace Cikin kuka Toh kukan zai mana mgnin zafin rashin shi da muke cikine a a tace Cikin share qollah😭 Murmushi tayi mai zafi tace toh mu daina yiwa Ahmad kuka muyi mishi addu,a Ba gata ko so da zamu nuna mishi Sai addu,a Usman dake gefen Yusuf yace wannan gsky ne Anuty a man kinga fa yadda Hamma Yusuf ya maida kanshi Baba bello ne ya miqe gamida cewa Yusuf maza tashi mu tafi muje a gyara maka gashin kankan nan da fuskar nan taka Jiki ba qarfi ya kalli baba yace baba Bari a yi muku Othern abinci Sadiyace tai maza tace A a Aysha zata tashi zamu shiga kitchen zamuyi duk abin da ya kamata Toh shike nan ma kajiko Suna fita basu tsaya ko inaba Sai wurin gyaran kai Shi kam Yusuf ido kawai ya wore yana kallon yadda ake ta gyara mai kai badon yana soba Dan shi komi yafi son yayiwa kanshi Gyaran akayi mai sosai Gashin nan Sai sheqi yakeyi dama gashi da yawa da sulbi tamkar valarabe Sajennan yayi luv a sufkarsa Gashin girarsa da suke kusan a hadewa Suma sunyi ras sun qara qawata fuskar tashi Lkci daya yayi rasa haibarsa ta fito gonin Sha ,awa Daga nan suka wuce masallacin Aysha kam yau tana Cikin gata Girkinma Usman ne da a Sadiya sukayi Itako tana jikin Nennen ta Sai faman cin inabi takeyi tana ta zuba surutun ta da rakadinta daya bayan daya take ta tabbatar kowa Bayan sun gama girkinne Sadiya ta shigo itama suka zauna sukaci gaba da hirarsu Usman Kuma ya dage Wai zai hada musu kunnun aya Yanata kiciniyar tace marka den ayar ne Su Yusuf suka shigo Bayan sunyi sallan insha Cikin mmk Yusuf ya kalleshi a gyetsine yace toh Usman abin naka Kuma har ka kai nanne Kana namiji ka wani zage Wai girji kakeyi Dry ya danyi yace kai hamm Yusuf nifa ba girki nakeyi ba kunun aya nake hada mana Kai da Allah tafi can kai dai dabi,ar mata duk ka iya ya fada tare da zama kusa da Baba belloN Sadiya CE tace yoh to ba dole muyi girkiba tunda matar gidan bata Ma San ta yadda zatayi wani abinba Dan gani NAYI gas dinkun nan ko sau daya tema ba ayi Amfani da shiba Baki ya tabe Cikin gyatsina fuska yace Wannan me taiya in banda kuka da ihu Dan tsabar iskanci Girkinma Wai bazata yiba sai dai zakiya ke aiko mata Baki ta Dan tura Cikin fakaice idansu ta watsa mai hara da murguda mai baki😏 Ido ya Dan zaro mata Cikin tsawa yace ke waye kikeyiwa harara🙄 Oho tace mai ai ni ba da kai nakeba ehe😏 Ya gane sarai yasan shi tayiwa hakan Shiyasa Cikin Dabara ya miqe Gamida juyowa ya kalleta Yace zo ki dauko Madara ki kawo wa baba baki ta tura Cikin shigoba tace Toh Ba ga Yaya Usman ba ya dauko mana .. Tab lallaima yarinya kin rainani toh Dan nazo gidanku Sai aka cemiki ni Dan aikenku ne Cewar Usman kema ya fada yana gyara koncinyarsa kan 2 str Nenne CE tace ke Aysha ai wannan aikin kine mu kam baqin ne ai Tashi ki dauko Toh tace gamida miqewa ta nufi kitchen Tana tafiya tana leqa fuskar Yusuf din Dan tasan dai tayi mai abin da ya tsana shiyasa da sauri sauri ta dauko madarar Tana uhm gwara nayi sauri ( ta Lamido kallube do wara tawa am hado) Kar sarki mugayen Nana yazo ya sameni anan juyowa tayi da sauqi Dan fita kitchen fin Gim taji ta fada jikin mutum har saida robar ta fadi Da sauri ta daqo Ido ta zaro Cikin tsoro murya Na Dan rawa tace .... ?🍇🍇🍇 NAYI NADAMA 👇🏻👇🏻👇🏻 MI,WASMITI.page 8⃣4⃣to8⃣5⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Idanshi ya qara budewa A take yaji yarrr gaba daya gashin jikinsa Na tashi Kanshi ya kawar da sauri Ita Kuma tsayuwa tayi jingine da qofar Phone dinshi ya jawo Yana Dan daddan nawa Amman Sam hankalisa baya jikin shi Tsawon wani lkci bai Kuma kallontaba bai Kuma yi mata mgn ba Itako tana tsaye a haka har bacci ya fara fizgarta Sai tayi Yuu kamar zata fadi Sai ta Kuma miqewa Shiko Yusuf bai qaunar ya sake daqo idanshi ya qara ganin abinda Zai zame mai fitina ya hanashi bacci Kai ya mayar jikin Kujerar gami da lumshe idanshi Tsaki yaja Tare da miqewa ya nufi daki Koncita Yake sonyi. Amman ya kasa samun nitsuwa Tuni ya Dan Fara tsotsan Lips dinshi Yana Dan tsurawa garu ido Itako Aysha yana tashi ta dawo kan.3 str tai konci yarta A haka tai baccin ta Cikin konciyar hankali Shi kam Yusuf acewarsa yayi baqin gani garin gane ganensa ya tado da azabebbiyar Sha,awarsa gashi Tbs dinshi sun qare Haka ya kwana Cikin Matsi Tun daga ranar Aysha a parlon shi take shi kuma yana cikin dakinshi In gari ya waye ko zasu Dan zauna a parlon Aysha ayi ta Dan hira duk da ma shi Sai ido kawai yake binsu dashi ita kuwa harara ke Hada su A haka har sukayi Kwana 8 Yau jumma Dabi,ar Yusuf tun da safe ya shirya Dan tafi masallacin da wuri Yasa Usman ma ya shirya Dan shi kam baba tun da yaje sallan asuba bai dawo ba yana can 8:00 Am Yusuf ya fito cikin shigar larabawan Yayi ras dashi gonin Sha,awa ga yar qibarsa ta fara Dawowa Dan yanxu yana Dan samun konciyar hankali Dan yanxu Aysha bata ife ifentan nan Kuma ko zatayima shi baruwanshi sannan yana samun kula ta gefen abinci ga baba da yake ta yawan shige mai Dan debe mai kewar Dan uwan shi Fuskarsa cike. Da haiba Yayi luu da idan nushi Cikin shafa sajenshi Ya kalli Usman yace kai tashifa mu tafi lkci Na tafiya Sadiya dake gefe ta kalleshi a fakaice tace Ha Yusuf Toh batun zuwa Hilton dinfa Kadai San ban gama sayeyya taba Kuma gashi gobe zamu wuce Makka Gashi duk mun shirya kai muke jira Kai ya jinjina Cikin gyatsina fuska yace Haba dai Anuty ni gsky kin San ban fiye son yaeon nanba Kuma ma haka kawai Sa kuyita duruwa Cikin garadai Wai zakuyi tsaraba Toh Yusuf ai dolece sayan wani abin Kai ya juya yace toh gsky yau dai frayed ne Kuma ni banson banje masallacin da wuriba Toh kaje mana in ka dawo Sai muje Da yafi kam ya fadi Cikin ransa kuwa cewa yyin in kin ganniba Har zai fita Aysha tace wlh Anuty Sadiya inya tafi yanxu Sai dere. Allah ko tace tare da zura hijabinta Tana toh wlh kawai ka tsaya mu tafi tare in yaso Sai mu dawo da wuri Kai ya juyo Cikin watsa mata harara yana kada kai Gaba daya su Anuty Sadiya kam an nitse Cikin Hilton Sai debo koya suke kamar ba gobe Aysha kam qananan kaya tayi ta jida da dogayen riguna masu Shep Ga su da taushi da sulbi Shi kuwa Yusuf gefe dayaya koma ya zauna ma aikatan ciki da suka saba Sai hira suke tayi Cikin larabci Har zuwa Dan wani lkci Ya kira Usman yace kcefa su fito Dan wlh xan tafi Na barsu A gaggauce suka gama hada kayan Usman yayi gaba da wani itama Anuty Sadiya ta dibi wosu Aysha ko bakos guda biyu Cike da kaya ta dauko ruggume dasu a qirjinta tazo ta wuce ta gaban shi inda yake tsaye yana biyan kudin kayan nasu Kanshi ya kawar Cikin jin hau shin sun bata mai lkci Tana fita yana binta a baya Su Usman kuwa tuni sun fita suna Cikin mota A hankali take tafiya kanta a qasa Dai2 lkcin wani Bature ya fito Cikin motarsa Da woni karensa qato mai jikin kura Karen yana Fitowa kai tsaye gun Aysha ya nufa Ita Sam bata luraba Sai kawai ganin abin da take tsoro kamar mutuwarta tayi a gabanta Cikin tsoro da razani da firgici Ta watsa kayan dake hannuta Ta cillara ihu mai ban tsoro idanta ta rumtse gamida ware hannuta Duka biyu Gaba daya jikin Sai bari yake Shi mai karen dry ma ta Mashi shi Karen Wai hakan gaisuwa ne ihun da takeyi Kuma shi a gunshi wasane Gaba daya hankali mutane ya komo kanta ihun takeyi a firgice Yusuf dake binta a baya da fari Cewa yayi da kyau Karen ya yayyagu sheki dai ba son yawoba Sai kuma yaga gaba daya ta firgice ihu take da iya qarfin ta ta tsaya a wurin Kuma kamar wacce aka dasa A take ya tuna wata rana da irin haka ya faru Ahmad har kamar zaiyi kuka saida ya kai qaran masu Karen Kamar a kunneshi yaji ana rada mai amanar Dan uwanka nefa Cikin sauri ya tsinci kanshi da qarasawa Gunta Qirjinshi ya manna a bayan ta Tare da bude hanna yenshi ya zagayota dasu ya matseta a jikin shi Itama jin mutum a jikinta yasa da sauri ta sauqe hanna yenta da ta bude Ta daura kan nashi Ta qaqqameshi Tanata goga jikinta a nashin A hankali ya Dan sunkuyo Ya manna wuyanshi Cikin tsakanin nata wuyan da kafadarta Gemunshi Na kan kafadarta Bakinshi ya saka dai2 kunneta Cikin rada rada da sanyin jiki Yace Ke da Allah kina Tara mana jama,a Ke baki iya addu,a bane Sai ihu Kinitsu ko nace ki bude idanki Karene fa ba kuraba A hankali ta bude idan Kai ta sunkuyar Sai kuma ta Kuma qaqqameshi Dan ganin Karen Na shinshina qafarta Qara matseta yayi a jikin shi gami da dan daga ta ya tsalla kar da ita daga gaban Karen Yasa qafa ya ture Karen Da sauri mai Karen ya matso yana bawa Yusuf din haquri Ba tare da ya kalleshi ba yaceba komai Aysha kam quluwa tayi sosai Abu Na Neman kasheta Amman Wai shi cewa ma yakeyi ba komai Baki ta tura Cikin zubda qollah😭 ta qarisa gun motar shiga tayi ta zauna tana ta kubbura baki Usman kam dry Yakeyi Sosai harda riqe ciki Yana ke zo zo kinga yadda kika rinqa zunduma ihu har kina watsa musu tattabarun su Phone dinshi ya miqawa anty Sadiya yana Anuty ki gani duk motsin da tayi Na dauketa Dan inason inje in nunawa su Rabi,u kai nama fasa yau dinan zan tura musu ta WhatsApp Anuty Sadiya kam dry takeson amman ta sani tanayi Zata kama kuka shiyasa tayi shiru Sai murmushi Kaway kyau sukayi sosai a pictures din Yadda sukayi abin tamkar masoya ga wani kyau da sukayi kamar larabawa Bayansu ga tattabarun da sukayi musu rumfa Yana isa kuwa ya shiga mota ya ja suka tafi A cikin mota ko Sai tsaki yake tayi Yana faman danna mata harara Suna isa gida Usman ya kalleshi Cikin girmamawa yace Hamma Yusuf ai ba sai mun shigaba kawai mu juya mu tafi masallacin ko Bai kulashiba Sai wani dogon tsaki da yaja Gami da fita Kai tsaye dakinshi ya nufa Yana shiga Ya fara zare kayan jikinsa Toilet ya shiga Cikin jin haushi yayi wonka tare da alwala ya fito ya sake wani sabon shirin Kai ya rinqa jinjinawa a fili kuwa Sai Jan tsaki yakeyi Yana fadin wannan yarinyar Sai kace mayya ga shegen naci da iya maqalewa a jikin mutane Munafuka fitinenniya bata San irin fitinar da take Sa mutun a cikiba Amman Bari zanyi mg ninta A haka ya fito ya nufi masallacin shi da Usman Sune basu dawoba Sai bayan insha Suna dawowa suka samu suna ta hada kayansu Ita kam Aysha Sai faman zubda qollah😭 take tana ayyah yanxu gobe i war haka bakwanan Ni kam ma Na gata kaina tunda aka kwasoni aka kawoni Nan Ayyan Nenne Dan Allah kice baba ya barmu mu tafi tare Cikin lallashi Nenne tace toh ki tabbayi mijinki mana in dai ya barki to shike nan Sai mu tafi taren Baki ta tura Cikin fushi tace Wlh ni ni ban da wani mai hanani kawai dai bakwa son na koma ne Toh bisu mana Dan Allah tashi ki tafi yanzuma Jeki kije kfi ruwa tafiya Wato kinga zasu tafi zaki dawo da iskan cinki Na ife ifen nanko Toh wlh ki kiyeni Banza kawai sokuwa Aiko haka ta faru Dan tun jiya taqi cin abinci sannan yau Kuma ta fara kuka Haka ta kwana kuka da safe ma da kukan ta tashi Taqi cin komai Har Zuwa yanxu da suke Gun da motocin su baba zasu debesu su tafi Cikin makka Kuma daga can zasu dawo Nageria Sosai baba yayiwa Yusuf fada da nasiha kan ya riqe amanar Dan uwanshi sannan yasan shi Aure ba wasaba Hakama Nenne tai tamai nasiha Sadiya Kuma dama tunda sukazo take ta faman nusar da Ayshan 9:30 Am Moticin suka gama shirin su Su Nenne duk suka rinqa miqawa Aysha hannu suna musabaha ta Sai mun hadu Kuma A hankali Sadiya ta rugumota Cikin sanyin jiki da rawar murya tace Aysha Sai wata rana fatan Allah ya hadamu kan alkhairi Dan Allah Aysha am Ku daina yiwa Ahmad kuka Kinji ko ? Lkci daya Kuma Kukan da take dannewa ne ya kufce mata Itama Aysha Sai kukan takeyi Da gyara ta saketa suka shiga mota Gun Usman ta Kuma komawa Fa dawa tayi jikin shi tana Kuka tana ayyah ya Usman Sai kuma yaushe ne Kukan kunji dadi zaku koma Cikin danginku gatanku ni kuwa bani da kowa a nan Sai Allah na Shima Usman sosai yaji kewar qanwarshi abokiyar fadanshi Dan da yake kamar ita ke binshi shiyasa ta rai nashi Cikin lallashi yace haba dai Aysha kina da kowa mana tunda ga Hamma Yusuf kiyi haquri wataran Zakizo A haka ya saketa ya shiga mota suka tafi suna daga musu hannu Allah sarki Aysha a wurin ta tsuguna gami da sakin kuka Cikin kewar yan uwanta Shi kam Yusuf komawa yayi gefen yana kallonta Cikin jin hau shin kukan Yace ki tashi mu tafi ko kuwa na koro miki karnuka Da sauri ta tashi Cikin tsoro ta shiga mota suka tafi Kafin su isa gida kuwa tayi bacci Sai ajiyar zuciya take sauqewa Bayan yayi parking ne ya juyo ya zuba mata ido... Gaisheku manyan matan Fasaha Writers Halima Auwal gaisuwata mai tarin yawa a gareki😍😘 ?🍇 NAYI NADAMA 👇🏻👇🏻👇🏻 MI WASMITI page 8⃣6⃣to8⃣8⃣Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Ina alfahari daku iyayena Allah ya biyaku da mafificiyar sakayya😍😘 Ido ya tsura mata Cikin fidda numfashi a hankali hankali Ko qefta idon ya kasa Kai ya dan Kuma juyawa Cikin sauqe qwayar idansa kan Qirjinta rigace da wondo a jikinta sun matuqar amsarta Sai Dan hula da ta tattara gashin ta ta tura ciki Sai yadin laffaya mai matuqar kyau ta yane jikinta a cikinsa Baccin da takeyi yasa ta Dan zame daga jingu nuwan da tayi ta Dan konto ta kanshi hular kanta ta zame ta fada kan cinyarsa Hannuta daya ta daura kan cinyarsa Daya Kuma ta daura kan kafadarshi Ta Dan motsa gamida Dan qara konciya a kanshi Motsin da tadanyin ne ya taimaka wa laffayar wurin worworewa ta bar jikinta Shi kam Yusuf Gaba daya ya jishi Cikin wani irin yanayi So yake ya dauke idanshi daga kan ta Amman ya kasa a hankali lips dinshi Na sama ya Dan rebe da Na qasan Harshe yasa ya Dan lashi lips dinshi Na qasan Da qarfi yayi wani irin ajiyar hrt A lkcin da ta qara kontowa kan cinyarsa Gaba daya yaji tsikar jikin shi ya mimmiqe qwayar idanunshi suka fara budewa da kyau A karo Na for a rayuwarsa da ya tsurawa qirjin mace ido Yadda kanta ya danyi kan cinyarsa Sai ya bawa qirjinta damar daqowa sama A take yaji jikin shi ya fara kerma Kai ya mayar jikin sit din yana fesa numfashi A ranshi yake cewa Toh me hakan me abin gani a jikin wannan rikitecci yar shi yanxu matsala larsa 1 yana tada ita ya tabbata da kuka zata tashi duk ta hanashi bacci Tsaki ya Dan ja gamida daqo kanshi Cikin samo mafita A hankali ya daqo hannuta Na kan qafadarshi ya hada da daya hannu da ya tafi Neman tsokana kusa da hajia🍌 Ya Dan dago kanta ya hada ya Dan jingina ta da jikin sit din da take zaune Fita yayi Ya za gaya gunta Kanshi ya zura Cikin motar gami da ruggumota Cikin jikin shi Kamar yarinya Da bayan shi ya koma ya rufe murfin motar A haka ya isa qofar shiga part dinsu Qara ruqqumota yayi Da hannu daya daya hannu Kuma ya bude qofar ya shiga da ita Kan 3str ya nufa da ita Cikin sanda Ya kontar da ita gamida Dan tattato gashin ta ya mayar matashi baya Duk yanayin abin ne Cikin gudun kar ta tashi Dagowa yayi Cikin ajiyar hrt da Cilla mata harara yana Aikin banza Jifa gaba daya yadda aka hadani da matsala Yarinya Sai kukan tsiya Tsaki ya kuma ja gamida tabe baki ya juya ya Nufi Part dinshi Kai tsaye Toilet ya shige ruwa ya watsa a jikin shi Yana fita ya sanya kayan baccin shi Rigace da wondo wondon har qasa Sai rigar iya qugunsa Daga samanta Kuma zip ne kalan fari da Dan ratsin Yellow A jikin shi Turare ya feshe jikin shi dashi Jikin window ya qarisa Cikin shaqar iskar da ta fara kadawa mai sanyi labulayen ya sassake gamida kashe wutan dakin Kan gado ya nufa Cikin ajiyar hrt ya konta ya jawo blanket ya rufe kanshi A hankali ya rumtse idanshi a take photon fuskarta ta fadomai Da sauri ya bude idanshi Dan Jin ihun da ta saki daga parlon Tsaki yaja gamida cewa sheke nan kuma mayya ta tashi ba zatayi baccin ba bazata barni nayiba Komawa yayi ya kontar da kanshi da nufin shareta Sai kuma yaji Sai qara surutai Take qara ta saki da qarfi Tana wayyo Allah Na kare wayyo ya Ahmad ka taimakeni Sosai take surutan da qarfi Kiran Ahmad da take ya tuni mai da amanarsa Shiyasa da sauri Ya miqe Cikin Yanayin shike nan ai Na kade A parlon konce take kan kujerar Sai faman riqe hannu kujerar take tana kuka tana qoqarin faduwa Da sauri ya kamota Cikin fada fada yace Wlh ke sokuwace ke kullum baza kiyi addu,a ba in zaki Konta kizo kiyi ta yiwa mutane ihu a gari Ita kam batama San yanayi ba sai faman shigemai jiki takeyi Tana qaqumoshi Yana tureta tana qara maqaleshi Cikin tsoron mafarkin da takeyi Dan har yanxu ganin Karen yana binta takeyi A fusace yasa hannushi ya rufe bakin nata Jin haka ita Kuma tasa hannu bibbiyu ta tura Cikin rigarsa Yarrr yaji tsikar jikin shi gaba daya ta miqe Idanshi ya rumtse da qarfi gamida Tallabota ya hadata da qirjinshi Dakinshi ya nufa da ita kai tsaye kan gado ya kontar da ita Ya daqo da niyar janye jiki shi daga NATA tai wani irin ruqqumoshi Da bude bakinta da qarfi ta sakemai qara Cikin kunneshi Sosai yaji qaran ya ratsashi ta Kuma bude baki zata Kuma cillara wani qaran Da sauri Cikin rashin sanin halin da yake ciki ya manna bakinshi kan nata Harshenta da ta daqo zatayi kukan ya cabke a kidime Hannushi ya Sa Cikin rawan jiki ya qara manna qirjinta da nashi Gaba daya yaji jijiyoyin jikin shi sun tsaya cak jinin shi ya tsinke bugun zuciyarshi ta tsananta harbawa a take zuciyarshi ta rinqa harbawa tana watsa saqonni a jikin shi zuwa qoqal warshi Lkci daya jikinshi ya fara Bari kamar mai rawan sanyi Lips dinshi suka fara qoqarin aikin su da suka saba Sai Wani irin sauti yake sauqewa hannushi bibbiyu yasa ya tallabo kanta ya qara mannawa da bakinsa Cikin wani irin salo da fitan hankali Ya rinqa tsotsar harshen ta Gaba daya ya manta waye shi ya manta a wacce duniyar yake ya manta da waye yake rayuwa ya rasa tunanin shi baki daya Sosai yake sarrafa bakinshi Cikin nata Ita kuwa Tunda ya kame harsheta Ta fara dawowa Cikin hayyacinta Hannuta tasa ta rinqa tutttureshi Amman ina Yusuf baima San tanayiba gaba daya ta tsorita dashi ba abinda yafi bata tsoronma irin yadda taji gaba daya jijinshi rawa yakeyi da garfi ta samu ta zaRo harsheta daga tsotsar da yake mata Da saurinshi yasa hannushi yana kamata yana qara matseta Cikin Kuka da tsoro ta rinqa tureshi Tana Dan bugunshi Tare da cewa Bana so wlh bana so ka barni mugu kawai wayyo Ummi Na Shi kam Yusuf kai ya rinqa juyawa yana ta danna ajiyar zuciya gamida matsota jikin shi da sauri ya samu ya Laso Pink slip dinta masu matuqar taushi tsotsar su yake yana ta susucewa Ita kuwa Aysha dukunshi takeyi sosai Tana mugu kawai azzalumi Jin haka ne ya Sa ya zare bakinshi daga Nata gami da matsota ya daura cinyarsa daya kan mazaunanta hannushi Kuma ya qara rufe bakinta dashi Ba tare da yayi mgn ba tayi tayi ta motso ta kasa Sai zare ido takeyi Tana sauqe numfashi Shi kuwa da qarfi qarfi yake sauqe ajiyar hrt A haka bacci mai nauyi ya kwasheta Shi kam Yusuf rayuwa yayi a iya wannan lkcin Cikin azaba ba abin da yake buqatar irin ya samu mai debemar kewa ko zai samu ya kauda ruwan fitinar dake cinsa A wani gefen xuciyar Sa Kuma haushin kanshi da kanshi yakeji a wani banqaren Kuma kunya mai tsananin ya rufeshi Cikin Jan tsaki ya zare jikinshi daga Nata Gaba daya haushin kanshi yakeji Toilet ya fada ya sakewa kanshi ruwan sanyi Wai ko zai samu hajia ta koma ta kama kanta Da qer ya samu ya fara nitsuwa Dole yayi wonkan sarki Yana fita ya kimtsa 3:25 Am ya fito Masallacin ya tafi Cikin Jin takaice da kanshi yakewa kanshi fada toh me kayi hakan Yusuf Ya za,ayi ka kasa konturol din Sha,awarka Me ajikin yarinyar nan mitsss yaja dogon tsaki Dai 2 lkcin da ya shiga Cikin masallacin Nafila yayi raka 2 ya dauki qur,ani ya fara karatu Koda yana Cikin karatun Sai abin yake tunowa Cikin takaici Ya rinqa addu,ar Allah ka bani ikon kauda kaina kan wannan yarinyar rabbi ka hanani jin kunya Allah ka sauqaqamin yawan buqatar da nake ciki A haka yaita addu a har akazo akayi sallan asuba Qur ani ya kuma dauka yaci gaba da karatu Har zuwa 12:20 pm Har dai akazo akayi azahar Yana son komawa gida bai San da wanne yanayi zai shigaba Haka ya zauna har akayi LA asar sannan Ya kama hanyan gidan Cikin murtuqe fuska wai shi karma taga qofa ta rai nashi Lol 😝 Ita kuwa Tunda baccin ya dauke ta bata farka ba sai 6 dai dai Da sauri ta miqe gamida fira daga kan gadon Cikin mmk ta Kuma wore idanta ta zubawa dakin ido A fili tace me ya kawo ni nan kuma Nan take Kuma ta tuno su Nenne sun tafi Ahankali ta sunkuyar ta kalli jikinta Riga dai da wondo sunanan Sai dai ba laffayan ba hula A hankali ta fara tuno mafarkin da tayi Na karnuka Na binta Kai takuma dagawa Cikin kallon dakin a fili tace toh kenan zuwana dakin nan Kuma ya akayishi ko dai abin da Na gani a mafarkin da gsk ne Kai a a ta bawa kanta amsa Hamma Yusuf dinne zai wani abin a a dama dai ya Ahmad ne A haka dai ta bar abin a matsayin mafarkin Tana idar da sallan asuban ta Dan Sa yar qaramar Riga Wanda iya ka cinta guiwa kalar read da hulanta sabida Dan yanayin zafin garin gashinta ta mayar ta baya Tana gamawa Yunwa Kuma tace assalamu alaikum Sosai takejin yuwar harda jiri jiri takeji Cikin ta kaici ta kira Sadiya amman Kuma layin bai shiga Parlo ta dawo ta zauna bayan ta Duba Cikin kitchen din ba wani Abu deffefe Zama tayi kan kujera tana riqe da jikinta hawayen Na bin fuskarta A hankali take fadin wayyo Allah Na yunwa nakeji wayyo Ummi Na Haka fa ta zauna har zuwa yanzun duk ta jeme A haka ya shigo ya sameta tana ta kuka Fuska ya qara hadewa😡gamida Watsa mata harara Ya ja tsaki ya wuce parlon shi Ganin haka yasa takaici ya kuma cikata Tashi tayi ta bishi tana kuka Da sauri ya juyo ya kalleta Cikin tsawa Yace me hakan zaki wani rinqa bina a baya kinata kuka Me akayi miki Qara matsoshi tayi Cikin Yanayin ta Na shigo bar da ta sabayiwa Ahmad dasu Adam Tace yunwa nakeji Ido ya Dan bude Cikin mmk yace toh yau kuma sabon salon iskanci ne Me kike nufi kenan Ni xan miki girkinne? Ita dai Sai kuka takeyi tana qara matsoshi sabida jiri takeyi Cikin kuka tace wlh yunwa nakeji Hamma Yusuf yau kwana 3 banci abinci ba Tsaki yaja gamida shigewa Cikin dakin yana fadin Sai kuma akace kizo kiyi tamin kuka Binshi tayi a baya duk inda yaje Sai ta matso gefenshi tana kuka Tana dire dire Sosai ya hatsalo da qarfi ya juyo Cikin zafin nama Ya matso dab da ita ido ya tsura mata gami da qara matsota........🙈 ?🍇🍇🍇 NAYI NADAMA 👇🏻👇🏻👇🏻Mi WASMITI .page 8⃣9⃣to9⃣0⃣Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Kuka ta Kuma saki gamida kamo hannushi ta matse a tsakiyar qirjinta Dan jin wani irin suka da yake mata Ga jiri da takeji gaba daya bata gani sosai Mmk yakeyi sosai Dan gaba daya ya lura ta daina tsoronsa kamar da Hannu yasa zai hanka data Sai kuma jin kanta yayi ta daura kan damtsen hannushi Cikin muryar kuka Take fadin Wayyo Allah Na wayyo cikin qirjina kaina yunwa zata kasheni Ido ya tsura mata cikin hade fuska Yace Ke da Allah can gafara Ni ban son koke kokenki Na banzan nan Hannu yasa yana daga kanta Amman INA ta maqaleshi So yake ya zuba mata mari amman Kuma zuciyarsa ta tunamar anar Ahmad ce Hannushi ya Dan zame cikin Dan Fada fada yace Toh ai saiki sakeni Inyaso nasan yadda zanyi Qara kamo hannun tayi Da Dan qarfi ya janye hannushi Dan jin ta fara sauya mai yanayin gudun jininsa Toilet ya shige Gamida rufe qofar Ita kuwa a bakin qofar ta tsaya tanata kukan Wonka yayi gamida maida kayan shi ya fito Dan yana jinta Yana fita tabi bayan shi Gaban madubi ya zauna Yana goge sumar kanshi Ita kuwa tsayuwa tayi a bayanshi tana zubda qollah😭 Shi dai bai kulata ba a hankali ta qara matsoshi tana Cikina Yunwa nakeji Tsaki ya ja cikin jin haushin ta ya miqe ya koma parlo A falonma zuwa tai gefenshi kan 3 str ta zauna gamida kamo hannushi ta kontar da kanta a damtsen hannushi A hankali ya sunkuyar da kai Ya zuba mata ido Dan jin gaba daya jikinta Sai rawa yakeyi Sai wani numfashi tafe sauqewa Hannushi ya zame gamida miqewa Ya kalleta afakaice yace toh ki sakeni mana zan fita Na seyo miki abincin. Ni dai mu tafi tare. tace dashi cikin kuka Da kaji mgnar ta kasan tana tare da yunwa Janye hannun yayi gamida ficeea Da sauri yana yarinya Sai koken koken tsiya Yana fita masallacin ya wuce Sai da yayi insha ya biya rstr Ya saye mata abinci Gida ya nufa da qafa yake tafe da yake ba nida tsana ninsu A bakin qofar shiga ya sameta jingine da qofar Sai kuka take yi Ganin ya wuce ne ta bishi da Dan sauri Gamida kamo hannushi Juyowa yayi yace Dan Allah ki daina takuramin kije kitchen ki dauko pilet. Cikin rawar murya tace Ni bazan iyaba Jiri nakeji Kai ya jinjina gamida miqewa ya dauko ya zuba mata ya tura mata gaban ta Da sauri ta ture pilet din. Tana Ni bazanci wannan kayan tafarnu wannaba Ni dai ka dafamin ko tea ne Zuwa yanxu kam ya gama hatsalowa Shiyasa ya miqe cikin fushi yana kar kici Dan Allah karma kici cikina ko naki In kinga dama ki tabbata a haka kaji iskanci Ni nema zan miki girki Daki ya nufa yanata mita Itama tashi tayi ta bishi a baya Tsayuwa tayi a gefebshi ta rinqa rusa kuka A fili yace wlh bappa Yaya kun cuceni Miqewa yayi kitchen ya shige inda yake jinta a dakin tana ta rusa kukan Da sauri sauri ya hada mata komai Ya kai mata Karba tayi da sauri cikin jin yunwar ta kurba Sai kuma tai maza ta kamo hannushi gamida Sa qara Cikin kufula yace Allah shi qara ai kina sane yanxu Na tafasashi Anan kuwa ta tasashi fafur dole shi ya fifita ya bata tasha Tana gama shanyewa ta daura mai cup din kan cinyarsa Ta Sa kanta jikin hannushi A take Kuma Sai zufe keta tsatsafo mata tako INA Lkci daya Kuma ta fara rawan sanyi Sai karkarwa takeyi.cup din ya dauka ya daura kan beed side Ya zame ya ja baya daita gamida tura mata pillows gabanta da bayanta Shiko yaje ya rurrufe ko INA gamida kashe filun A hankali ba tare da tuna komai ba yazo ya konta a gefenta Phone dinshi Ya zaro Adam ya kira cikin Sanyin murya ya daga gamida cewa wlh kai banza ne Yusuf ko yaushe Sai kadaidaci inajin dadin rayuwarta da mata ta Sai kawani matsamin Tsaki yaja cikin kufula yace banza kawai Na mamajo Kashe woyar in bai maba. dry ya danyi cikin tsokana yace gsky ka Bari da safe muyi mgn Dan yanxu kam inajin dumin matata. Mitsssss ya ja tsaki gamida katse kiran Lumshe idanshi yayi gamida shaqar sanyin da A,C ke fesa musu Ga wani irin qamshi da dakin keyi Lkci daya tunanin shi ya fara juyawa Blanket ya jawo ya rufe jijinshi Sosai yayi nisa cikin tunani Can ya rinqa jin Yadda take rawan sanyi Sai qara matsoshi takeyi A hankali ya Dan ja baya Ita kuwa jib dumin blanket yasa Sai qara matsoshi takeyi A hankali ta mirgina ta isa cikin jijinshi Qara matsoshi tayi Dan jin dumin jikishi Na ratsa ta Kam ta kamo shi Cikin a zabebben zazzabi da takeji Kanta ta tura cikin wuyanshi Tana sauke numfashinta Wayyo Allah shi kam Yusuf ya koma tamkar zaucecce Sai numfashi yake tafixga da ajiyar hrt da qarfi qarfi Sosai yaji sanyin jikinta Na ratsashi Duk da jallabiyar dake jikinshi Dan bai samu yashirin baccin ba Hannushi ya Dan Sa da niyar tureta Amman Sam baida qarfin hakan Dan duk jinin jikinshi ya tsaya Konyarsa kuwa tamkar an cunna mata wutane CiKin rashin sanin halin da yafada ya jawota jikinshi da qarfi ya matseta lkci daya Kuma ya Riga ajiyar hrt Lips dinsa suka fara motsawa a hankali jikinshi ya fara jarkin Ita kuwa jin dumin shi yasa ta qara maqaleshi gamida qara juyowa kanshi gaba Daya Hannuta ta Dan dago cikin yanayin mai fama da zazzabi Ta sauqe hannun kan mararshi A take yaji wani irin Abu ya ziyarceshi wata iriyar guguwar Sha,awa ta yunquro mai Shiyasa bai San lkcin daya saki Dan wani irin sautiba wayyooooi Shihhhhshi gami da matsota jikinshi ya rinqa shafa ma zaunen ta Burinsa yaji fatarta Na gogar tasa Amman ya rasa ta yadda hakan zai kasance So yake yajishi a sabuwar duniya Amman ya rasa ta Yaya A zuciyarshi kuwa cewa yake me kake sonyi haka Yusuf Tsaki yake ja Amman a cikin ranshi a fili kam Sai lips din Shi da suke ta motsawa Cikin kidima ya manna qirjinshi Duk da a ranshi wai ai so yake ya Kore mata sanyi da takejin. zaiyi Gaba daya ta fidda shi cikin hayyacinsa Dole tasa ya rinqa cakudata cikin jikinshi Da azabar da taurin kai ya samu baccin azabar ya debesu Asuban faru ya zame jikinshi cikin jin haushin kanshi da kanshi Qarin takai cinsa ma Sai yayi wonka A haka dai ya shirya ya tafi massalaci Ita kuwa tana tashi ta samu baya nan ta koma dakinta tai wonka da sallah gamida dawowa parlon Zazzabi kuwa har yanxu yana Dan damunta Shi kuwa Yusuf daga masallacin Makarantasu ya nufa Bai dawoba Sai bayan sallan insha Yau ma kamar jiya haka ta tasashi agaba da kuka tana yunwa takeji Dan tun jiya bata Kuma cin komai ba Shi kuwa fada ya rinqa yi Dan takaici kuma ba yadda ya iya a dole ya fita ya seyo mata Sannan Kuma tace ita abinci su d tafarnuwa bazata Ciba Dole yauma ya shiga kitchen Ya Dan mata abinci mai Dan sauki 🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 A hankali yanayin zamansuya fara can zawa wani irin Zama ya fara zama musu sabo Zuwa yanxu Yusuf qarfi da yaji ya zama shike kula da Aysha sosai Sun kuwa Dan saba dukda kullum Sai yayi ta mata masifa Wasu lktan Kuma da dama tana haddasa mai tashi muguwar Sha,awarsa ta yadda yake kwana da axaba Yau jumma,a Tunda Yusuf ya fita da safe bai dawo ba sai yanxu da Yake tafiya a hankali cikin yanayin shi Na nitsuwa Yake takawa Iskar damuna mai dadi da qamshi ke ta kadawa sosai yaji nishadi ya fara dibarsa Iskace mai sanyid a qanshin furannin A hankali walqiya ta rinqa haskawa Rugugi ya fara a hankali A haka ya iso tsakiyar parlon Ita kuwa Aysha gaba daya ta gama firgita da razana Wani irin walqiya akayi da sautin qaran aradu mai matuqar tsawa da rikitarwa dai dai Lkcin ........ Ina Alfahari daku members Na Gaishe ki Aysha s bayero Fatan kina lfy ?🍇🍇🍇 NAYI NADAMA 👇🏻👇🏻👇🏻 Mi,WASMITI page 9⃣1⃣to9⃣2⃣Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Ina godiya da kulawarku rdrs da addu,oinku garen Ya rinqa jin sautin kuka a cikin parlon Daga can gefen 3 str phone dinshi ya zaro gamida kunna torch din ta Hasken ya Dan gauraye parlon duk da ba wani haskene sosaiba Dan yanayi Na dare ga Kuma duhun damuna Sai in andanyi walqiya ne Sai a Dan ga hasken Can Ya haggota kan 3 str ta lafe ta jikin hannun kujerar Gaba daya ta qaqqame jikinta Sai faman karkarwa takeyi Ta rumtse idan ta Kuma gam Dan tana bala,in jin tsoron walqiya Kuka kawai take A hankali ya qarisa gun nata Ido ya Dan zuba mata cikin tabe fuska yace mutum Sai shegen tsoron tsiya Ita kam Sam bata jishiba Dan duk ta firgice Kai ya Dan kawar Dan ganin surar jikinta Na bashi tsoro Kukanta ya kuma jin ya qaru. Dan wani rugugin da akayi kusan 3 a Jere irin mai kamar nishin nan Tsugu nawa yayi a hankali Cikin sanyin murya yace Ke bude idanki me hakan Jin muryarshi yasa ta dan Bude idan da sauri Gami da zuba mai idon cikin hawaye Tace tsoro nakeji injin tsoron ruwan sama Toh ruwan cinyeki Zaiyi? Murya na rawa tace Hamma Yusuf ni ko a gida in ana ruwa Ummi bata barina ni kadai Kuma ko ya Ahmad ma ya Sani wlh inajin tsoron tsawa Sai hawaye shar 😭a idanta Gaba data Sai yaji jikinsa yayi sanyi tabbas yana iya tunawa Muddin ana ruwan sama duk abin da sukayi Ahmad yakan zame jikinshi ya koma kusa da ita ya ruggumeta ya rinqa shafa kanta Da taji tsawan Kuma Sai tai ta qaqqameshi Kuma ya lura tabbas tsoron tsawa take har cikin ranta Cikin sanyin jiki ya dago hannushi ya daura kan wuyanta gamida Dan tallabo bayan kunneta babbar yatsarsa Kuma ya daura kan kuncinta a hankali ya rinqa murza yatsar tasa kan habarta yana goge mata qollah😭 Ido ya qura mata cikin wani irin yanayi yau a fili yake gano kamar da ake cewa sunayi da ita a zahiri Kuma yaga kamar da ake cewa sunayi da Ahmad Qwayar idanta irin Na Ahmad ne sak Qara zuba mata ido yayi cikin Dan kada mata kai alamar ta bar kukan. Gaba daya yaji Ahmad ya dawo mar lkci daya yanayin shi ya sauya Ita kuwa cikin tsoron ta kamo hannushi ta riqe Tana mai zubda qollah😭 Wani irin walqiya akayi mai hasken gsk A lkci gida Kuma aka saki tsawa mai firgitar wa Da qarfi cikin razani ta abka jikinshi har saida ya koma ya fadi qasa kan carpen dirsham Da qarfi Kuma ta rinqa qwaqumoshi tana tura kanta cikin qirjinshi Shi kam Yusuf ya gama macewa a zaune bai iya tabuka komai ba Sai sanyi da ya farajin yana ratsashi Gaba daya qarfin jikinshi ya bace A take Kuma ruwan ya kece kamar da bakin qorya Sai iska mai sanyi da take busawa Da gyer cikin qarfin hali ya tattaro sauran jarumtarsa Ya yunquro Ya Dan koma jikin kujera ya jingina Ita kuwa kanshi ta qara mirginowa Gamida Sa hannu bibbiyu ta sanqalo wuyan shi A hankali ya rinqa furta mata Addu,oi cikin kunneta hannushi yasa ya qara matsota jikinshi Ita Kuma Sai faman qaqqanda rewa takeyi Hannushi yasa gami da tallabo fuskarta Gaba daya ta birkice Cikin qarfin hali ya miqe ruggume da ita kai tsaye bedroom dinshi ya wuce da ita Yana ruqqune da itan ya juya ya rufe qofofin gidan Gami da ajiye hasken phone dinshi kan beed side Zama yayi gamida jawo pillows ya jera A bayanshi ya Dan jingina dashi Ita kuwa jawota yayi ya daura ta kan qirjinshi Yasa hannu ya tattaro gashin kanta ya mayar matashi bayan ta Hannushi daya Kuma hannuta ya koma ya saka cikin nashi gamida harde yatsunsu Ita ma ta sanqalo daya hannuta a bayanshi Daya hannushi Kuma kan fuskarta ya daura ya rinqa shafawa har zuwa kan gadon bayan ta Yayinda daya Hannu kuwa da yake cikin hannuta ya rinqa Dan murza yatsunshi a hankali cikin tafin hannun nata Ajiyar zuciya ya rinqa sauqewa Dan jin wani irin taushi da laushin hannun nata Lkci daya Kuma ya fara daburcewa Lips dinshi suka fara Bari ga sanyin gari ga sanyin A,C Ga wani irin buqatuwa da yakeji Sosai ya qara matsota jikinshi ya rinqa shaqar qamshin kanta Sai faman tsotsar lips dinshi yake tayi makar zai tsinkesu ya hadiyesu ko yaji sanyi Ita kuwa zuwa yanxu ta samu bacci ya debeta Yayinda shi kuwa Yake ta faman azab tuwa Lkci guda yaji mararsa ta fara wani irin harbawa Qara matsota yayi wai ko zaiji sanyi Amman ina a haka ya kwana cikin azabar Bugata Kafin qari ya waye ko gaba daya ciwon Mara ya isheshi gashi yasha tabs din Na shima a banza Ko sallan asuba a gida yayi Dan bai iya mike tsawonsa Bayan ya idarne Ya Dan matso bakin gadon Cikin cije lips dinshi yace Ke Ke tashi kiyi sallah. A hankali ta bude idanta Cikin muryar bacci tai addu a ta yawo ta dawo bakin gado qafaqunta Na qasa Kai ya sunkuyar ya qurawa qafar tata ido yatsunta kab irin nashi ne Hatta farcensu iri daya ne har zuwa sharabarta Sai dai shi Jikinshi a kawai gashi Zara Zara masu laushi da baqin Mu samman ma qirjinshi da hannushi Sauqa tayi cikin Dan bacci 2 ta juya ta tsaya ta bashi baya Ta yi miqa ta yadda rigar jikinta ta qara yin sama Qirjinta ya taso Ido ya sauqe kan ququnta A hankali take tafiya Amman ququnta Sai wani juyawa yakeyi mazau nenta ya tsurawa ido Har ji yake kamar idanshi zasu manne a jikinta cinyarta ya kuma qara tsurawa idan A dai2 lkcin ita Kuma tayi woje Kai ya mayar jikin godon gamida lumshe ido A ranshi yake tunani ya zama dole NAYI Aure matuqar INA son Na kare mutum cina da lfy ta bazan iya jumre wannan uquba ba Hannu yasa ya damqi mararsa gamida miqewa ya koma kan gadon ya konta Ita kam Aysha Sai da tai wonka sannan tai sallah Ta zauna gaban mirro Mai ta Dan murza gamida Dan shafa turaruka masu sanyin qamshi Atamfa ta dauko Riga da siket ne kalan atamfar ya amshi jikinta yayi ras a jikinta Siket din ya Dan matseta Dan kwalin ta Dan tubke kanta dashi Miqewa tayi Ta nufi dakinshi Kan gadon taje ta zauna ta kamo hannushi cikin tura Dan bakinta tace Hamma Yusuf ka tashi mana yunwa fa nakeji ka ganifa rana tayi Cikin wahala ya bude idansa da suka rine sukayi jazur Tsura mata idan yayi cikin kamo gefen lips dinshi Na qasa. ya fara tsotsa Jikinshi dake rawa ya rinqa Dan kamewa A karo Na 2 tace ni ka tashi yunwa nakeji A hankali yace bazan iyaba Kije kitchen kiyi duk abin da kikedo kici jogolgolenki Qara matsoshi tayi ta kamo hannushi tana jawo shi Ji dumin tafin hannuta ya qara ingizo halin da yake ciki Gaba daya ya cika da takaici Dan ya rasa mafita Shiyasa ya miqe cikin fada yace zo xoki ficemin a daki yarinya sai naci kamar mayya Ko so kike ki kasheni tun kwana bai qareba Ki barni naji da abinda ke damuna mana Tasowa tayi cikin sanyi da Dan tsoro tace Hamma Yusuf baka da lfy ne ? meke damunka? Bansani ba yace da ita Toh meyasa baka iya miqewa? Me ruwan ki da miqewata. Cikin sanyi tace wlh baka da lfy gafa yadda idanka sukayi gashi baka iya miqewa Ka ganifa gaba daya Jikinka rawa yakeyi Gashi Sai faman cije lips dinka kakeyi.. Harara ya watsa mata gamida yin parlo kan 1 str ya zauna Sai zufa keta keto mai Ita Kuma phone dinta ta dauko Ta zauna a parlon ta Cikin sanin murya ya jiyita Tana cewa Hello Ya Adam ka gani ko Hamma Yusuf bai da lfy. Sai kuma ya jiya tayi shiru alamun ana mgn daga daya gefen sai Kuma yaji tana fadin Ya Adam wlh ko tsayuwa bata iyawa Sai cikinshi yaketa riqewa Gashi Sai rawan sanyi yakeyi Jin haka da sauri ya shigo parlon phone din ya fixge Cikin fada yace Ke ni nace miki banda lfy da zaki wani zaqe ki rinqa yadani gun wannan yayan naki mai bakin tsiya Yanxu ya isheni da surutun banza Da sauri ya daqo phone dinshi Dan jin ana kira yana dubawa ko yaga Adam ne Mitsssssss yaja godon tsaki gamida matsota cikin murtuqe fuska😡 yace Ni lfy ta lau Sai dai in kece baki da lfy Asalima ni lfyarce ta jawomin haka Amman tunda gani kike banda lfy toh zan tabbatar miki ni lafiyeyye ne kuma zaki gane kurenki Banza kawai sokuwa Ya qarshe mgnar cikin daga woyar tashi yana Dagawa Adam ya kece da dry Cikin dry yace wlh ka kusa ka kashe kanka Dab kake da ka resa ranka matuqar baka bar wannan baqin halin da mishkilanci ba kasanka sarai Allah yayika fitinenne Sai bakin jaraba sannan ka wanisa taurin Kai Banza jarabebbe Ustazu kawai Ka bada kai bori ya fada. A kufule yace Kai da Allah tafi daga nan ancema kowa irin kune jarabbabun tsiya Sai matse qanana yara kuke tayi Dan rashin abin yi Dry Adam ya kumayi tare da cewa toh Allah ya sauwaqa in Kuma mganinka ne ya qare ai Sai ka kuma saya. wai kaima Yusuf har zaka cewa wasu jarabbabu Ai gwara kowa da kai kam Katse kiran yayi Tare da juyowa kanta cikin Takaicin............ ?🍇🍇🍇 NAYI NADAMA 👇🏻👇🏻👇🏻 Mi,WASMITI page 9⃣3⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Gaisuwa ta mai tarin yawa gareku Yan uwana matan group din MUSAN JUNA MARUBUTA Allah ya barmu tareya😍😘😍😘 Ina jidake Ummee Garkuwa Jennifer👍🏻😍😘 Ido ya tsura mata cikin takaici Dan shi sosai yakejin takaicin yawan koke-koken da takeyi Gashi Sai tai ta bibiyarsa tana shigemai Cikin takaici Ya isa gabanta Kai ta dago ta kalleshi cikin zubda qollah😭 Tana Hamma Yusuf yunwa nakeji. Cikin fada yace Toh gani cinyeni Nace tashi ki cinyeni Tunda dai ke kin maida kuka abincin ki Ni wlh kin fara ban tsoro dan Haka kikayi tayin wannan kukan a lkutan baya baki bar yiba saida kika ciyemin Dan uwa mayya kawai fiti nenniya Kin cinyeshi kin huta saura nima kin cinyeni Dan da kullum kukun kike kina kiran sunansa yanxu kuwa kin dawo kaina ko? Kai ta rinqa girgizawa tare da sakin kukan takaici wai ita Hamma Yusuf ke kira da mayya harda cewa itace ta cinye mai Dan uwan shi. A kufuli yace ba zaki bar kukan bako? Cikin rawar murya tace Nifa yunwa nakeji Juyawa yayi ya nufi kitchen Cikin Takaici Fruits ya debo a pilet gami da Dan lalla besu Ya fito da nufin kai mata Dan ta barshi yaji da abinda ke damunsa A kan steps din haurowa kitchen din ya sameta a zaune Sai zubda qollah😭 takeyi A hankali ya zauna gefen ta Cikin sanyin murya yace gashi kici wannan Anjima in na danji sauqi Zan miki abin da zakici Hannu tasa a hankali ta sanqalo nashi hannun kanta ta kontar kan damtsen hannushi Tare da sauqe ajiyar zuciya Inabi ya dauko ya miqa mata Karba tayi da hannuta daya daya Kuma tana riqe da nashi A haka ta danci Yana zaune yana kallonta Cikin mmk Ita a kullum bata da wani abinci Sai fruits Kuma Sai Dan tea Sannan shima bazata Ciba dole Sai ta takurashi Kai ya Dan sunkuyar gamida leqo qwayar idanta Kai ya jinjina gamida take baki da sauqe ajiyar hrt A hakan tayi bacci a jikinshi ta Dan konto kanshi kanta Na kan damsten Hannushi Ta lumshe idanta gashin ta yayi lub a baya Sosai ya tsurawa fuskarta ido Ta yadda a hakan Kuma in kana Kansu bazaka ga qwayar idanshi ba Dan dama duk da Dan girman idan Yusuf Amman ganin idanshi yana wuya sabida koda yaushe kanshi a kasa yake Kuma a lumshe suke. A hankali yaji wani Abu na shigemar Cikin zuciya Lkci daya Kuma yaji jinin jikinshi ya tsinke yana wani irin harbawa, Da gudana, A fili ya rinqa sauqe ajiyar hrt Lkci daya Kuma yaji tausayi ta Na ratsashi A hankali ya Dan qara talla bota Gamida lumshe idanshi Jikinshi ya Dan rinqa sanyi Sai kuma bacci mai dadi ya debeshi. Basu tashi ba sai 9:35 pm A hankali Aysha ta bude idanta Da sauri ta matsa ganin yadda shima ya qwaqwumota hannushi daya kan qirjinta duk da ba wai bres dinda ya taba ba. Amman Sai taji haushin abin Dan yawanci duk abinda Yusuf keyiwa Aysha bata Sani Dan Sai in tana Cikin tsoro ko firgici ko bacci ne yake Dan shi shige mata duk da shima yakan ji Takaicin kansa Idanshi ya bude Dan jin motsin ta Kallonta yayi a fakaice Gamida Dan daqo hannushi da ta maida pillow A hankali ya danyi qara Dan zafin da yaji Dan hannu ya Tara jini Hannushi daya yasa yana Jan dayan Cikin qoqarin tashi dakinshi ya nufa Har yaje baqin qofa Sai kuma ya Dan juyo Itama shi take kallo Ganin ya juyo yana kallonta ne yasa tai sauri tayi dakinta. Bayan ya gama kimtsawa ya hada mata tea ya bata tasha shi Kuma Ya wuce school. 🌹🌹🌹 Kwanaki sun ja mokonni sun ja Har ya koma watanni sun ja Bayan watanni 7 Yau tun Da safe Yusuf bai fi taba Yakuma yaqi ko tafasa ruwan tea din ma yau yace bazai Yiba In taga dama ta shiga tayi Ita Kuma Sai nadewa tayi Kan 3 str Tace wlh Ita bazata iyaba Shi kuwa zaune yake can gefen Kan dining table Ya Sa laptop a gaban shi yanata Aikin karance- karance sa Can ta daqo tace Hamma Yusuf Wlh yunwa nakeji har qirjina ya fara ciwo. Bai kalleta ba bai Kuma yi mgn ba Hakan ya cikata a Dan qasa qasa tace mugu kawai azzalumi Sai kuma ta miqe ta nufi inda yake Jawo kujera tayi ta zauna kusa dashi Cikin tura baki tace Hamma Yusu! Bata qarisa mgnar ba ta tsura mai ido Dan ganin yadda ya wani tsura mata ido Cikin yanayin zanfa saba miki Juyawa yayi yaci gaba da aikin shi. Ita kuwa kuka ta fara a hankali da ta lura bai kulata ba yasa ta saki kukan da qarfi Don ta cika shi da takaici Kallonta yayi Cikin harara ya mige tare da tattara phone dinshi da laptop dinshi ya ja kujerar Ya fita yana juyawa Phone dinshi ya dauki suwa alamar ana buqatar mgn dashi Dagawa yayi Cikin nitsuwa da biyeyya yake gaida baba bello Cikin farin ciki Baba bellon ke sheida mai. maryam ta aihu ta sami da namiji Farin ciki ne sosai ya ziyarci rayuwar Yusuf Ba abin da yake fadi Sai Alhamdulillah (en yetti tak domen) Mun godewa ma haliccinmi. Ita dai sai ido take binshi dasu A can Kuma baba bellon ne yace INA Aysha? Gata nan baba ya bashi amsa Toh bata woyar Toh yace Cikin miqa mata Phone din karba tayi ta kara akunne Bayan sun gaisane Yake cemata Aysha Maryam ta aihu. Daga jin Maryam ta aihu kawai Cikin Salle ta !qaradi da tsantsar farin ciki ta cilla woyar gefe Ta tsaki qara mai qarfi gamida tsalle kamar yarinya Ta rinqa juyi a tsakiyar parlon Tana rawa Sai faman juya ququnta takeyi Tana Alhamdulillah (Amman hade do mi seyi) Amman yau dinnan nayi farin ciki (Mi yetti Allah mi hotai leddi am dayirdi am) Na godewa Allah zan koma qasa ta ta aihuwa Juyi takeyi sosai Gaba daya jikinta Sai rausayawa takeyi Duk ta gama kashe Yusuf kam a tsaye Bai taba zaton yarinyar nan ta cika hakaba Sam bai taba tsura mata ido irin na yau ba gaba daya ya wore idanshi kan mazauneta da suketa juyawa tana ta faman happy Ko idanshi ya kasa qiftawa A hankali ya zaro harshensa ya Dan lashi lips dinshi da suka fara motsawa Ita kam juyawa takeyi sosai har jiri ya fara diban ta So take ta tsaya Amman ta kasa Da qarfi ta rinqa yin baya-baya Zata fadi Cikin zafin nama da tsinkewar zuciya Yusuf ya tallabo ta fada qirjinshi A tsorace ta rinqa fadin Hamma Yusuf zan fadi rami a gabana Wayyo ka tai make ni wlh zan fada Cikin rami Sosai take surutai Hannu yasa ya dago kanta Cikin tsurawa pick lips dinta ido Yace ke bude adanki Ba dai bakya jiba Ke haka kikaga ya dace ki nuna farin Cikin ki Ba godewa Allah zakiyi ba sai rawa da ihu Ita kam Sam idanta a rufe yake ganin hakane yasa ya qara kontar da kanta kan kafadarshi ya rinqa shafa kanta zuwa bayan ta Har zuwa tsawon wani lkci Sannan ta samu abin ya saketa Tureshi tayi da Dan qarfin tayi cikin bedroom dinta Shi kam Yusuf ya gama macewa a tsaye dagyer ya samu ya koma kan 3 str ya zauna yana maida numfashi da qarfi-qarfi Jim kadan ta fito Cikin doguwar Riga baqa wacce tasha aiki da pick din zare Kanta ta yane da siririn mayafi shima pick Tayi tarha dashi fuskarta ta fito rasa a ciki Ga wani Dan ma daidaicin jaka rataye a kafadarta hannuta Daya Kuma janye da trolley mai Dan girma Cikin fara,arta da nishadi tace Hamma Yusuf ni kam fa na gama shirin, sannan kai Kuma kana zaune. Ido ya zuba mata cikin mmk Trolley ya kalla Cikin Jan tsaki yace lallai baki da kai bakima San abinda kikayi Ba Yana kai nan ya tafi part Inshi, Aiko da sauri ta bishi a baya gamida riqo hannushi Cikin karya suya da Neman alfarma tace Dan Allah Hamma Yusuf kar kamin mugunta ka hanani zuwa wlh Na gaji da garin nan ni nafi son in koma can qasa ta Baki ya Dan tabe gamida daga kafada da Dan ware hannu alamar bai shafeni ba, Aiko ta rinqa nacemai duk inda yayi tana biye dashi a baya Ita dai su tafi Can dai ya juyo ya kalleta Cikin murmushin mugunta yace In kinaso zakije mana. Ehh in a so ta bashi amsa da sauri. Ko ? Ehh takuma cewa. Kai ya kada gami da cewa Toh Amman fa da shara din zakibi dokana shike nan in kin qi kuwa bake ba zuwa Ehh na yarda tace dashi Cikin zumudi tace toh gayamin menene shara din naka? Kai ya jinjina yace daga yau ke zakina..... ?🍇🍇🍇 NAYI NADAMA 👇🏻👇🏻👇🏻 Mi,WASMITI. Page9⃣4⃣,Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Fuska a murtu qe yace Daga yau ki raba kanki da koke-koken Da kikeyin nan sannan Ki daina takuramin kin iya, girki bawai baki iyaba ki shiga kitchen kiyi girkin ki Ni ban damuba bance kiyi daniba Dan ni ba zanci kwabenki ba Sannan karki matsamin da batun tafiyar in kinqi kuwa, Kina gani zan tafi Na nabar ki. Cikin zumudi tace Na yarda zanyi Girkin Kuma nama bar kukan Ta fada tana mai goge fuskarta Tabe baki yayi Cikin cewa da kin kyau tawa kanki... Tun daga ran Kuma Aysha ta bar koke-koken Dan dama tanayi ne da gaya Dan ta cikashi Kuma tai tamai dry a fakaice in taga ya zage yana ta fifita mata tea Ta rinqa cewa mugu tunda dai kabar cin zalina da sauqi. Tun ran da ya gaya mata sharudansa Kullum da safe zata tashi tayi wonka da sauri sauri Dan ta shiga kitchen tayi musu breakfast Amman Sai tasamu ta makara shi har ya shirya ya fita Sai dai taci sauran abin da ya bari ta Kuma nadewa kan 3str tai ta woya da mutanen Gida pictures din baby Maryam Kuma tamkar dansu aka buga woyar ta Duk wani shirin ta ta gama Sai jiran Comandan nata take kullum tanason ta tabba yeshi Kuma tana jin tsoro kar allaura ta to no mata garma. Shiyasa dole takeyin shiru. Yau Alhamis wanda yayi dai dai Da kwana 5 da aihuwan Maryam Da yamma Liris Yusuf ya shigo Parlon Aysha Kai tsaye kan carpet ya zauna a tsakiyar parlon laptop yasa a gaba yana ta aikin latse-latse Ido ta zuba mai Cikin yanayin son mgn Kuma tana jin tsoro shiyasa Sai ta kalleshi Sai ta Kuma kauda kai can dai ta gaji Ta sauqo daga kan kujeran ta matso kusa dashi Cikin hikima Ta fara mgn A hankali Tace Hamma Yusuf. Bai amsa bai Kuma dagoba Hakan tasa ta qara matsoshi Cikin Qarfin hali tace Hamma Yusuf Kaga pic din boy dina Ko ? kalleshi ka gani kekkewa dashi mai Kama da ya Ahmad Kai ya daqo Cikin tsura mata ido Yace boy dinki Kuma Yaushe kikayi cikinsa? Har kika aifeshi? duk ban saniba? Baki ta tura Cikin jin takaici tace d'anane mana ai in munjema Zan roqi Maryam ta ban shi. Hmmm yace gamida harararta yace waya CE miki zakije? Da sauri ta daqo kai tace Dan Allah Hamma Yusuf kayi Haquri Wlh in banjeba zan mutu Kai ya jinjina yace toh ai naga ko sau daya baki aikata shara dinaba sannan Dan abinda Na ajiye in Na dawo zanci Sai ki tattareshi ki cinye. Haka mukayi Dake? Da sauri ta gyeda kai tana a,a Dan Allah kayi haquri wlh gobe kam zanyi na tuba Ta fada tana qoqarin zubda qollah😭 Da sauri ya daga mata hannu cikin murtuqe fuska yace ki hadiye hawayen ki Allah kika yarda kika zubda qollah😭 bazaki jeba. A zahiri har Cikin zuciyarshi Yusuf bai san meyasa ba Sam baison ganin fuskarta Nata tsiya yar da hawayen da zaran ya ganta tana kuka jikinshi ke macewa burunshi ya ruggumota a ranshi zai ke ji kamar ya lashi hawayen Dan tausayi ta da yakeji. a nashi ganin fa wai tausayi ne shiyasa ya dakatar da ita Ita kuma sai ta fara rau rau da ido Dan maida qollar Miqewa yayi. Ya fice daga gidan bai dawoba Sai dare.kafin ya dawoma tuni tayi bacci A parlon ta ganin haka yasa shima ya konta a parlon shi gamida bude qofar da daga labulen ta yadda zai ke hanqo ta. A haka ya kwana badan yaji dadiba Dan gaba daya yanxu ya saba da kwana da ita a girjinshi baccin dai yayi badan dadi ba. Kashe gari Jumma,a kam tun 5:00 Am Ta tashi tai wonka tana fita tayi sallah ta dauko wasu Riga da wondo black color Sai Dan rats in fari kadan Wondo. Dan gajere iya karsa guy warta rigar Kuma ta Dan rufe mata cibi yar ta kadan Amman daga baya bayan ta ya Dan bayyana ta kasan mazau nanta Sai gashin ta da ta kitse ta saki jelar ta gefen kafadarta Kai tsaye kitchen ta nufa Tana zuwa ta fara kici niyar fere doya Tana gamawa ta kunna gas ta daura shi daya gefen Kuma ta daura ruwan tea Lkci daya sukayi dai-dai yadda take buqatar Ta sauqe tea din ta daura a filas Sannan ta daura kaskon tuyan Ta fasa qoi da samai kayan qamshi sannan ta matso da niyar fara tuyan. ta debo zata zuba Cikin kaskon kenan Sai taji kamar motsin mutum Gaba daya jikinta ya bata ana kallonta Shi kuwa Yusuf tun sanda ta fara firan Ya zo bakin kitchen din Dan so yake ya fita da wuri yaje masallacin gashi yau zasu wuce 9j Yana isa qofar kitchen din yayi baqin gani injishi da fada Dan gaba daya ta watsa mai tunanin shi Lkci daya ya zamo tamkar an dasashi ba abinda yakeyi Sai Bin qugunta da Ifo ko qefta idan ya kasa sosai yake mmk yaushe yarinyar nan ta cika haka gaba daya jikinta Sai kadawa Yakeyi Zuciyarshi ke raya mai ya qarisa gunta ya shafi bye bye dintan ko zaiji sauqi Aiko yabi umurni hrt dinshi a hankali ya fara takawa har yazo dab da ita Gashi dama gaba daya jiya ya kwana da kewar ta Ya daqo hannushi kenan ita Kuma ta juyo Ganin yadda yanayin shi ya sauya Lips dinshi Sai bari sukayi ya bude idanan ras Sai faman kadasu yakeyi. hakan ya bata tsoro ta juyo da sauri Dan matsawa baya. aiko Hannuta Sai Cikin kaskon mayin Cikin jin azaba da radadi Ta saki qara gamida xillowa tayi bayanshi Salle takeyi kamar yarinya qarama lkci daya kuma yatsarta ma nuniya da tashiga cikin mayin tayi jazazur Gaba daya hannun nata sai karkarwa yakeyi Ihunta shi ya dawo dashi cikin hayya cinsa Da sauri yayi kanta ita kuma sai zillewa takiyi tana jawo qasan rigarta tana goge yatsar Da qarfi ya samu ya komo hannun gaba daya shima ya rikice Ita kuma sai yarfa hannu take tabs wayyo Allah wayyo Hamma Yusuf hannuna ya nuna Ganin taqiyin shirun ne yasashi Kamo yatsar cikin wani irin salo yasa yatsar cikin bikinshi A hankali yasa harshen shi ya rinqa zagaye yatsar gamida Dan tsotsar ta Da fare taji zafin dubin bakinshi sai kuma a hankali taji sanyin harshen nashi Na ratsa yatsar tata Shiyasa a hankali ta rinqa sauqe ajiyar hrt cikin tsura mai ido Shi kuma Gaba daya hankalin shi ya koma kan qirjinta Dan dukiyar fulaninta ya zubawa ido ganin yada suke tsaye cur kamar zasu tsone mai ido Da qarfu yayi ajiyar zuciya sanadin tuno yadda ta rinqa tsalle a gabanshi qirjinta Na kadawa ma zaunen ta Na juyawa Sosai ta zuba mai ido gami da sunkuyar da kanta Dan taga me yake gani Ido cikin ido sukayi A take taji jinkita ya fara rawa ganin yadda idanshi suka qara yin ja ya wani kamo lips dinshi sai tsotsa yakeyi A hankali ta fara zaro yatsarta daga kan harcensa Shi kuwa sai qara cabke yatsar yayi Cikin rawan murya tace Ha Ham Hamma Yusuf Zafi nakeji Jin yadda take mgn ne ya sashi komo hannuta ya zaro yatsar daga bakinshi Ido ya tsura mata cikin lasar lips dinshi da yin piki piki da idanshi Jan hannuta yayi ya wuce da ita har bedroom dinshi a baking gado ya ajiye ta Robar zam-zam ya dauko mai sanyi Gabanta yazo ya durkusa gamida kamo hannun. ya balle bakin robar Ya rinqa zuba mata ruwan zam-zam din yana shafawa A take taji wani irin sanyi Na ratsa hannu nata gaba daya. lkci 1 ta nemi zafin qunan ta rasa Sai sauqe ajiyar zuciya takeyi Tashi ya kuma yi ya jawo mata pillows Cikin wani irin murya yace Konta bari naje Na qarisa aikin Kai kawai tageda mai gamida lumshe idanta A ranta take tunani menene a kan harshen Hamma Yusuf Ko ya yake iya sarrafa harshen sa Da tunanin tayi Bacci Shi kuma zuwa yayi ya kashe gas din Ya koma parlon ta ya konta kan 3 str yayi ruf da cikin Ya rinqa matse kanshi wai ko zai samu nitsuwa Amman ina Sai wahala kawai da yake Sha Shi baison ta gane halin da yake ciki Da qer dai ya samu hajia ta Dan konta🙈 Sannan yaje ya hada sauran aikin Sai da ya hada mata tea sannan yazo ya tasheta Tayi breakfast Shikuwa toilet ya shige yaje yayi wonka Kafin ya fito ta koma parlo. bayan ta tattara wurin 10:27 Pm Ya fito cikin shiga ta alfarma Manyan kaya ya saka farare tas sai hularsa CE da takalmin shi ne baqaqe Sai aqoqon hannushi Na Axurfa da yaketa shegi Ya kifa hular nan tayi Ras a kanshi ta gefe gefe kuma da qeyarsa gashine kwonce lub Sai wani irin qamshi yake fita daga jikinshi Ido ta zuba mai Dan ganin yau kamarsa da ya Ahmad tafi ko yau she fitowa Gabanta yaxo ya Dan tsaya Cikin Kauda kai Dan gani yake kamar zata gane halin da yake ciki Dan dolece ta sashi Sa jomfa Dan baiso ta gani a sana yake😜 Cikin kauda kan yace ki shirya ana sauqowa sallan jumma,a zamu tafi Eprt Dan qarfe 2:20 pm jirgin mu ✈zai tashi Wayyo dadi gun Aysha ba,a mgn Qara tayi cikin tsantsar farin cikin da Rakadi ta buqa tsalle ta fada hikinshi hannu bibbiyu tasa ta sanqalo wuyanshi Cikin murna ta manna mai lafiyeyyen kiss a kumatun sa Na dama sai kuma ta arce a guje tayi Dakinta tana Alhamdulillah (habde kam mi hota tai) Yau kam zan koma. Shi kam Yusuf dole ya fada kan kujerar Dan ya samu ya saita kanshi tukun A ranshi kuma zafi yakeji meyasa take farin cikin komawa? Toh fa Yusuf anya Kansan menene a zuciyar ? Ni dai Garkuwa wannan tabayar nayiwa Yusuf kuma banda amsarta Amman kumuje zuwa 2:30 pm jirginsu✈ Yusuf ya dage xuwa qasarmu ta aihuwa Nigeria Qarfe bakwai dai-dai... 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 NAYI NADAMA 👇🏻👇🏻👇🏻 MI,WASMITI, page 9⃣5⃣Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Suka shigo Babban parlon gidan Adam da Yusuf suna jere riqe da hannun juna farin cikin fal zuqatan su Aysha ko tana shiga Amira tayi kanta da sauri cikin fara,a da tura katon cikin ta Cikin mmk Aysha ta ruqumuto Gamida shafa cikin Da alamu tabbaya Ta kalleta cikin zumudi tace Amira cikin kema har kin qunsa shine ko ki gayamin Na tayaki addu,a Allah ya raba lfy Amira kan sai murmushi da sune kai Dan kunya sosai Aysha ta bata ga Hamma Yusuf da take jin tsoro yanzu zaice sun ishesu da surutu Da sauri ta kuma sakin Amira jikin Maryam ta fada cikin kewar juna suka ruqqumi juna Sun kasa mgn sai dai su kalli juna su sake fadawa jikin juna. Ummi ce tai dry cikin qaunar Aysha tace Yau naga ikon Allah Aysha ase kinfi kewar yan uwanki damu Da sauri kuma ta saki Maryam ta konta jikin umminta cikin qaunarta tarinqa sinsinar ta tana I miss you so much my lovely Ummi Na Gaba daya suka kwashe da dry daga gun Ummi ta koma gun Nenne A haka dai duk ta bisu da gaisuwa. Shi kam Yusuf suna shiga ya zauna kan kujera 2 str bayan ya gaidasu daya bayan daya. Kaka dake ruqqume da jaririn tazo ta miqamai Hannu bibbiyu yasa gamida karbar yaron Cikin tsantsar son yaron ya zuba mai ido Lkci daya tunanin Dan uwanshi ya fadomai Qaunar yaronne ya rinqa ratsa zuciyarshi A hankali ya daqo yaron ya mannashi a qirjinshi Cikin sanyin murya da alamun quna a zuciya Ya kalli Maryam yace maryam Allah ya raya manashi da imani, Amin ya rabbi ta fada cikin muryar kuka Tare da qoqe qollah Aysha dake jikin Nenne ta miqe da sauri tayi gun Yusuf Cikin zaquwa tace Hamma Yusuf banishi Bai kalleta ba bai kuma Ciro 'Dan ajikin shiba Cikin jin haushi tace kabani yarona Mana Kaka dake qefensu tace toh in banda abinki A hakan zaki karbi Dan Ki xauna mana. Naqi in zaunan Ke wlh ai kuma mutum ya boni da shishiginki Da sa ido Ehh nayi Sa idan shegen baki Na kin samu kin miqe Harda wasu duwaiwuka da kika ajiye kin kasa daukan cikin sai she gen kadifiri Gaba daya kuma sai mgnar kaka ta Dan sasu murmushi Amman banda Yusuf Da sai yanzu kaka ta darso mai wani Abu a ransa Wani Aysha ta kasa daukan cikin Tofa Yusuf😜 Nenne CE tace Aysha zauna ko ki karbi danku Toh tace Gamida zama kusa da Yusuf din har hips dinta Na gogan cinyarsa Hannu tasa a hankali ta tura ta qasan jaririn daya hannu kuma ta sama Cikin qoqarin dago yaron ne ta yi kuskuren tura hannu har ya shafo oga Yusuf Da sauri ya matse cinyarsa gami da sauqe wani irin nannauyan ajiyar zuciya Itako batama San tayiba Daqa yaro tayi ta zuba mai ido cikin Sanyin murya tace photo copy ya Ahmad Kai ta sunkuyar ta rinqa subbatarsa Cikin rawar murya take fadin Maryam ina son yaron nan maryam zaki banishi Sai hawaye shar a idanta Shima jajari kamar ya sani sai ya rinqa kuka Hannu Yusuf yasa ya karbeshi ya sashi kan kafadarshi Cikin murya qasa qasa yace Kayi haquri dan Uwana banson jin kukan ka Randa Baban ka zai rasu ya gayamin kaine madadin shi a guna a hankali yaro kam ya fara shiru Ita kuwa Aysha cikin kuka Ta Dan roqqofo Jikin Yusuf har qirjinta Na gogar kafadarshi Tana tayar mai da tsikar jikinshi Da son samune duk ya hadasu ya ruqqume da jaririn Dan ya tabbata da Ahmad yana Raye da haka zaiyi, Hawayen Ta ne suka rinqa diga kan habarsa Cikin kuka tace Hamma Yusuf kawoshi ko yunwa yakeji Ido ya tsura mata cikin miqa mata shi ya hada da hannuta Ya riqe ta kasan blanket din yaro Ya rinqa murza yatsunta cikin salon lallashi Kai ya kuma dagawa cikin alamun kibar kukan A haka suka riqe yaron Yana kan cinyar Aysha Yusuf kuma idanshi Na kan yaron Baba bello ne yayi gyaran murya cikin girma yace Yusuf dama kai muke jira kayiwa yaro huduba da bakinka Dan wannan shine fatan Ahmad Kai ya jinjina cikin sanyin jikin ya daqo kanshi yace baba wanne suna za,a samai? Sunanka zaka samai! A hankali yace baba nikuwa da sunan biyaye Na zan mayar mai, A a Shi Ahmad dama yace matuqar Dai Allah ya bashi d'a namiji toh sunanka zai sanya mai Kai ya sunkuyar gamida karbar yaron ya mai huduba Da sunan Sa Aysha kuma sai sharar qollah take A hankali ya zaron hankicif dinshi mai laushi da taushi sai qamshi mai dadin shaqa yake fitarwa ya miqa mata Karba tayi ta share qollar ******* A haka sukai ta hiran yaushe gamo Har zuwa 11 Na dare Yusuf yasa su Usman da Rabi,u suka dauko akwatunan da ya ciko da kayan jaririn ba wani abin da bai yiwa wannan yaro ba yaro kam yasha gata Sai 12 sannan suka waste Adam ya dauke matarsa suka tafi Shi kuwa Yusuf Dama an gyara mai part dinsu Can ya tare Su Usman kuma suka koma dakin Adam Aysha kuwa ta dage ita dai tare zasu kwana Da yaron ta da yar uwarta Qanne babansu ma Dr umar sunzo daga Yola ***** Kashe gari Ran Sartudey Akasha biking sunan Yusuf qarami Ba wani shagali da akayi sosai sai walina da aka gudanar Yaro da mahaifi yarshi sunsha gata a gun yan uwa da abo kan arxuqi Anty Sadiya ma ta taka rawar gani Hatta su Rabi,u sun yiwa yaro kaya sosai Bare aje ga lodin kayan da tokwaranshi ya mishi wasuma sai ya kai shekara 9 Yana sawa Anyi suna lfy an waste lfy "-"-"-"-"-"-"- Yusuf ne kwance kan gado gaba daya yarasa abinda ke mai dadi a rayuwarsa Da ya rumtse idanshi ba abin da yake gani sai fuskar Aysha Sam ya rasa meke damunshi Ya rasa bacci mai dadi ya rasa sukuni Ba abin da yakeso gani daji kamar ita Yayi kewar tattausar fatanta So yake ya kori tunanin Amman ya kasa A fili yake cewa yaufa kwana 8 kenan da zuwanmu tsaki ya Dan ja cikin takaici Yace toh wai me hadina da ita Zuciyarshi ke cemai salon ta raina ka kake nema Gaba daya kuma ya kasa samun nitsuba yasha magungu nansa har ya gaji Amman Sam ya kasa nitsuba Tsaki yaja gamida miqewa Jallabi ya zura a jikinshi Cikin hada fuska ya nufi. Cikin gida Kai tsaye parlon Nenne ya wuce tun daga baqin qofa yaji hayani yarsu sunata dry Yana shiga ya samu hardasu Adam da Amira sun zo ga Anuty Sadiya ma tazo Sai dai tana shirin komawa Dan dare ya farayi Hannu Adam ya miqa mai cikin fara,a yace kai INA ka shigane haka Ga sakaliyarka ta buwa yemu da fitina wai ita yunwa takeji kuma bazata ci ko mai ba sai inabi da tufa ko dabino da kwakwa A deren nan fisabilililahi a Ina za,a samo matashi Abu sai kace mai ciki kodai da cikinne? bamu saniba! Shi kan Yusuf baki ya tabe gamida bata fuska Ita kuwa tana ganinshi Ta gyara goyon da tayiwa Yusuf qarami Ta matso kusa dashi cikin tura baki tace Hamma Yusuf Yunwa nakeji Bai kulata ba bai kuma kalleta ba Sai Adam da ya kwashe da dry yana tab lallai Aysha abin naki azimun ne Sadiya ce tai dry tace wlh ko a can haka take takura Yusuf gsky Aysha lamarinki da gyara Ita dai qara matsoshi tayi tare da kamo hannu shi Ta matse a qirjinta Ta manna kanta kan damtsen hannushi Cikin muryar maijin yunwar dan da gske yunwar takeji Tace Hamma Yusuf Wlh yunwa nakeji. Kai ya Dan sunkuyar cikin tsura mata ido Yace toh ya kikeso nai miki? Ko zaman ma bazaki barni nayi bane? Ita dai cewa take ni yunwa nakeji Juyawa yayi ya nufi kan dinning table ita kuma ta maqale dashi Kulolin ya bubbude Cikin Dan daga murya yace ba ga abinciba ki zauna kici Mana A a nidai ba tuwo Zan ciba !Adam kam dasu Nenne dasu Usman Mmk ne ya cikasu sosai Yusuf ne ke ta faman sunqullah da Aysha fada da masifar nan duk ya qare Adam kan sosai ya rinqa binsu da ido Cikin mmk Shi kuwa Yusuf parlorn Ya dawo itama tana biye dashi goye da Yusuf qarami da yake ta baccin sa Maryam kan sai sake baki tayi tana kallon su Amira CE ta Dan matso kusa da Adam a hankali tace ya Adam mu tafi gida bacci nakeji Cikin kula ya shafa fuskarta yace toh My mirah mu tafi ko Hannu ya miqawa Yusuf cikin dry yace to babban Yaya mukam xamu wuce inda mukafi wayo. Shi kuwa sai tabe baki yayi ya cilla mai harara cikin qasa qasa da murya yace wlh ka dai ji jikin ko kunya babu ka wani maqale a jikin mace yar qarama Shi kam Adam dry sosai yayi cikin jinjina kai yace Toh wlh ba wahalelle kamar ka kuma Allah ina gayama Kaine kake dab dajin kunyar Dan wlh ko yanzu kai abin tausayi ne ji yadda qanwata ke juya ka kamar masa a cikin kasko Wlh tausayi kake bani Ya rigada ka gama macewa a kan qanwata Saura qiris girman kannan naka yaje qasa warwas Sake hannushi yayi cikin kufala yace wlh kai banzane Wlh ni ba wata mace da zata kai a gareni bare Na wahala a kanta Kaima ka sani sarai Ina bata kulawa ne Dan ita amanar Ahmad ce kuma wlh ni tausayi ma take ban Dry Adam ya kumayi tare da daga mai gira daya Yace ai da Zara kaji wani Abu wai shi tausayi To ka gama narkewa cikin wutan so yaro baka game bane Duk mgnar da sukeyi ba Wanda yaji ko ita Aysha da take gefensu bata jiba. Dan sai faman diri take cikin son yin kuka a ankali Ta kuma cewa yunwa fa nakeji. Da qarfi cikin fushi da tsawa Yusuf ya juyo gunta Kamar mai kwada mata Mari sai Kuma ya bige da cewa Kai naa shiga uku yanzu Dan Allah munxo gidan ma bazaki barni nasha iskaba Dan Allah kar ki cinyeni Aikin banxa sai shegen fitinar tsiya Ki biyoni part dinmu kizo ki karbi Inabin akwai guntun da Na ajiye Dan dama Na sanki kin iya naci mayya kawai Yana kaiwa nan ya fita Adam ne ya bishi a baya cikin tsokana yace ai wlh ka hadu da raini kenan tunda ka kasa Nuna mata cewar kaifa namiji ne Yoh ba dole ta rainaka ba Tunda zata ke zaton kai mata mazane Tunda bazaka iya mata wani Abu ba ai ka ciyar da ita Don dole A haka sukayi sllm suka tafi Sadiya ma ta fito ta tafi tare da mijinta Yusuf kan yana shiga toilet ya fada wonka yaje yayi cikin jin zafin maganganun Adam a ranshi yake cewa mayya zatasa yara su rainani a banza A hankali ya tabbayi kanshi wai shinma da gaske ne zata iya rainani Wai tamin kallon mata maza kai INA A haka ya fito bai Sa komai ba ajikinshi Sai wondo 3qtr sai turare da ya feshe jikinshi dashi A haka ya fito parlon ya fito keban ita kuma ta shigo Cikin Dan murguda mai baki tace gani ka bani Ni kam Zan tafi Kallonta yayi a fakaice cikin jinjina kai lallei kuwa Yarinya kin rinqa Bai kulata ba ya wuce ta gefenta bakin qofar yaje ya tura qofar garam ya murda key din ya zaroshi Cikin mmk da tsiwa tace nifa ka bani in zaka bani ka wani rufe qofa Danni bacci zanje inyi ehe😏 Kai ya jinjina cikin cije lips dinshi a ranshi yace zaki shiga taitayinki. ?🍇🍇 NAYI NADAMA 👇🏻👇🏻👇🏻 MI,WASMITI. page 9⃣6⃣ Na Ayasha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 A hankali ya tako yazo gabanta Ya tsaya cikin murtuqe Fuska Itama kai ta dago Sai kuma tayi saurin rumtse idanunta gam Lkci daya jikin ta Ya fara rawa Tsoro ya kamata Dan tunda suke da Hamma Yusuf bata taba ganin shi ba rigaba Qirjinshi da hannushi sun bata wani irin tsoro Qirjin cike Yake da gashi baqiqqirin Mai taushi da laushi yana konce lib a ajikinshi sai shewi yakeyi hannushi Da sharaban qafafunshi A ranta take cewa Na shiga uku Anya kuma Hamma Yusuf ne wannan Ido ta bude da sauri jin Ya qara matsota Ido ya tsura mata cikin Yin piki piki da idan nashi Hannushi yasa kan qirjinta Ya kwance abin goyon Da ta goya Yusuf qarami Da sauri Ta buge hannun nashi Dan jin yana tabo albarkatunta Cikin tsiwa tace Me haka ya za,ayi ka kwance mai zanin Goyonmu in ya fadifa Me zaka cewa uwarsa Dan kai baka San wahalar yaro ba Ni ka bani in zaka Zaka bani ehe😏 Duk mgnar da takeyi kanta a gefe Dan tsoron ganinshi take Shi kuma shiru yayi ya tsura mata ido yadda take zuba mai tsiwa harda Murguda mai baki A ranshi yake cewa lallai yarinya kin gayamin mgn Bansan wahalar daba! Da kyau Cikin ajiyar zuciya ya qara Sa hannushi Ya kunce abin goyon ya juya bayanta Ya ciro yaron a bayanta Cikin bedroom ya nufa Ita kuwa da sauri ta sake Qaton lufayan jikin ta! Ta bishi a baya Tana ni kabani yarona wlh ni banson haka Bai kulataba har sai da ya kontar dashi can gefen gaqon Ya juyo Cikin qatsaita Gabanta Ya tsaya Ita kam taki.kallonshi sai wani kauda kai takeyi tana ja da baya Shi kuwa yana binta a baya Har ta isa jikin gini Hannushi yasa daga qasa ya jawo hijabin ya cire mata ya wurgar dashi can gefe Ido ta zazzaro😳🙈🙊 da sauri ta kaleshi gamida Sa hannu bibbiyu ta tare qirjinta Dan dama zanin goyonne ya rufe mata qirjin Da garfi tace Me hakan Cikin tsura mata ida Ya daga mata qirarsa daya😉 Murya a daqile yace Fitsara Ba kin iya yarashin kunyaba Baki ta kuma murgudawa Gami da kaucewa zata Wuce ta gefenshi Tare da cewa 😏ni baba son iskanci Aikin banza kawai! Da qarfi yasa hannushi ya kamo damtsen hanbayenta duk 2 ya budesu daga kan qirjin nata Ya turata zuwa jikin gini Ya ware hannayen nata ya dannesu a jikin ginin Qirjinta ya fito ras a gabanshi Albarkatunta suka wani Taso kamar zasu stone mai ido A take bugun zuciyarsa ta tsananta Numfashinsa ya fara carkewa Ita kuwa Sai kuka ta saki Cikin mutsu mutsu kuma ta kasa qwatar kanta Kai ya Dan sunkuyar Cikin rawar murya Yace Ehh Na yarda ni Dan iskane Kuma yanzu iskancin Zan nuna miki Ba daikince ke fitsa rerriya bace Zanyi mgnin wanban bakin da kike murgudamin Gobe ko kudi aka baki kimin tsiwa bazakiyi ba. Cikin kuka tace Wlh bana so mugu kawai azzalumi Da sauri yace qarya kikeyi kina so kam In byake so me ya kawoki dakina ? In bakya so meyasa zaki zomin ba ko Riga? Ba dai so kike A miki ba shine kiketa maqalemin toh zaki samu Baki ta kuma murgu dawa Tace wlh Allah ya isa mugu azza lumi ba kai kace nazo zaka ban inabi 🍇 Ba Sai kuma tai shiru cikin zaro ido Da firgici da bugawar zuciya Jin yadda Hamma Yusuf ya Hade bakinshi da NATA Cikin wani irin salo Ya cabko harsheta Tamkar mayunwacin zaki Tsoronta ya qara tsananta gaba daya jikin ta sai rawa yakeyi Ihu take sonyi Amman INA ya riqe harshen ta sai wani irin sarrafashi yakeyi yana tsotsa tamkar maye Sai numshi yaketa fixga Jikinshi kuwa tuni ya fara rawan sanyin Hannuta ya saki Dan ya tabbata yanzu kam ya gama mata illa Dan tsoro da firgici sun tafi da qarfinta Kan qirjinta ya daura hannushi har rawa suke tamkar mazari Bakinshi Na cikin nata Ya kuma rinqa Murza dukiyar fulaninta tamkar ba qobe Ina gaba dayan su tsayuwa ta gagaresu Dole suka zame kan carpet Cikin azam ya qara matsota jikinshi Gaba daya jikinshi sai rawa yakeyi Ita kam Aysha Hamma Yusuf yau ya zame mata dodo Sai zazzare ido takiyi tana tsurawa fuskarsa ido Shiki baima San tanayi ba Da qarfi ta samu ta sabulo harshen ta daga kan nashi Wayyo Yusuf qara matseta tayi tare da sakin wani marayan qara tamkar Dan da uwarsa ta qwace mai nono Da sauri ya kuma cabko Pink lips dinta Allah sarki yau kam Yusuf ya samu ya hade da abin da yake ta bege🙈😝 Hannun ta tasa tana tureshi Jin laushin tafin hannnta yasa jinin jikinshi tsinkewa A take ya ji wani irin kuzari Cikin azama ya cicci bota yayi kan gado da ita Ita kam sai wutsul wutsuk takeyi A hankali ya sake lips din NATA ya rinqa bin duk jikin ta da kissing har ya iso Kan qirjinta Gaba daya ya fita hayyacinsa sai juyata yakeyi ta yadda yaga dama Hannu 2 yasa ya runqumota gamida manna bakinshi kan mamanta Ya rinqa tsotsa Sai gurnani yakeyi Ita kuma ta samu an sake mata baki Sai kuka takeyi tana qoqarin cire mamanta daga cikin bakinshi Kuka take sosai Tana wayyo Allah na wayyo ummina Na shiga uku Hamma Yusuf zai kasheni Mugu kawai azzalumi I Hert U Wlh Na tsaneka Bana sonka ni kai ba Dan uwana bane Mugu. dama kai ka mutuma ya Ahmad dina ya rayu! A hankali kala manta suka rinqa ratsashi Lkci daya Jikinshi ya rinqa macewa Yanayinshi ya sauwaya Bakinshi ya zaro Gamida komawa jikin pillows ya koma ya konta cikin fidda wani irin nishi Ita kuwa da sauri ta yunqura zata miqe Sai kuma taji Yana riqe da hannuta Gam Cikin sanyin Murya yace Koma ki konta _Amrita_ ba abinda zan miki, Toh fa yau kuma Aysha ta koma *Amrita* kenan😝😀 Hannuta ta rinqa qoqarin qwacewa Amman ta kasa Shi kuwa da yaga haka da qarfi Ya fizqota ta fada Kan qirjinshi da yake bata tsoron Matseta yayi da hannu bibbiyu Cikin rawan murya Yace *Amrita* Anan zaki kwana kiga time fa yanzu 2 Na dare zaki samu sun rufe qofar shiga Ban son kije ki haduda wani abin cutarwa a gareki ke da Yusuf qarami nawa Amrita kinsan Cewa Ku 2 biyayena ya barmin amanarku Ke kin kasance amanar tawace Shisa kika zama amrita fatan kin game ma,anan *Amrita* Dan kar kiyi tunanin Wani Abu akan sunan _Zadai ka gane_😝 Ita kam kuka takeyi cikin fushi da tsoro tace Ka sakeni in tafi Gwara Na hadu da komai ma ai Kaine babban abin cutawa ta Bai kulata ba sai Jawota kawai da yayi Ya daura qafarsa daya kan mazaunenta Hannushi kuma ya daura kan qirjinta Kanta ya daura kan kafadarshi Cikin tsawa yace maza kiyi bacci Kar ki tayarmin da yarona da rikicinki. ta bude baki zata kuma mgn ya cabko Harshen ta Zai fara tsotsa ta ture kanshi tace nabar kukan Murmushin Mugunta yayi yace aiko da kin kyautawa kanki A haka cikin qirjinshi Baccin tsoro da wahala da firgici ya kwasheta Shi kam Yusuf yadda yaga rana haka yaga dare Daren wannan rana ya mishi duhu da tsawo Yasha maganinshi har ya gaji Amman bai samu nitsuwar da yeke buqataba Tana baccinta Amman shi kwana yayi yana zirga zirga Ya kuma yiwa kanshi alqawari bazai mata abinda bata soba sai da yardarta Yaje parlo ya dawo kan gadon ya tsura mata ido In ya gaji yasa hannu ya Dan shafi mamanta sai ya kuma rinqa sauqe ajiyar zuciya A haka dai har aka kira sallah Da gyer ya samu yaje masallaci Dan ma a cikin gidan yake Dan gaba daya ciwon Mara ya addabi rayuwarsa Yana shigiwa ya samu har yanzu bata farka ba shima Yusuf qarami Dan albarka ya bar Abbanshi ya Dan Shana Sai yanzu yake qoqarin tashi A hankali ya qarisa bakin Gadon Cikin sanyin murya da tsotsa lips dinshi Ya rinqa kiran ta A hankali Amman bata motsaba Sai da ya Dan sunkuya cikin sanyin hannushi ya Shafo qirjinta Gami da cewa *Amrita* ki tashi ki maida yaron nan gun mamsnshi a bashi nono Cikin razana da firgita ta miqe Sai kuma tayi saurin rufe qirjinta da hannu Shima kai ya sunkuyar cikin murtuqe fuska waishi kar a rai nashi _su Yusuf manya wai a dole kar a rainashi_ Ita kam sai hawaye a fuska share Dan tsabar takaici Shi kuma juyawa yayi Hijabinta ya dauko Ya wurga mata ya koma gefe ya dauko qur,aninshi ya fara karatu Sa hijabin tayi gamida ruggumar Yusuf qarami Ta fita tana sharar qollah da Jan Allah ya isa Binta da ido yayi Cikin ransa ya ji murmushi ya Dan kufce mai Sosai yake tunata yadda ta tsorita a Daren jiya A fili yace dama matsiwaci ya kan kasa CE matsoroci ai Ita kam Aysha tana shiga taci karo da Nenne Da sauri ta sunkuyar da kanta ido cike da qollah Gani take kamar kowa yasan abinda Hamma Yusuf ya mata Dakin Maryam ta nufa Tana shiga ta samu ita kuma ta fito daga wonka Kenan Da sauri ta qarisa gunta Cikin zubda qolka ta daura Yusuf qarami kan cinyar Maryam tace Maryam bashi nono ya Sha Itako Maryam sai leqa idanta takeyi Dry tayi cikin sanyin Tace Daga zuwa karbo Inabi sai kuma aka tsaya karban pakala ko? Ai ni wlh dama nasan wayone kawai Hamma Yusuf yake yi Wai kibiyoni kixo ki karba shi dai yasan abinda yake so Taci gaba da cewa Su kuma haka Allah ya yisu Haka ya Ahmad yake da Kuma kinga ya Adam ma ba sauqi Ita kam Aysha kuka ta saki gamida Kontar da kanta kan Gado Maryam tace toh lallai abin naki nayine Cikin kuka tace Maryam wlh ni bansan abinda Hamma Yusuf yake nufi da niba Wlh so yake ya kashe ni Yanzu gaba daya sai kinji yadda nakeji Qirjina Duk ya lallatsemin Mamana sunyi jazawur Mutum kamar maye Cikin sanyin Maryam tace to Aysha ai Hamma Yusuf yama yi haquri yaufa kusan kwananku 18 Amman bai nemi haqinshiba Aysha kam ta gano Maryam bata San wanne irin zama sukeyi da Hamman nasuba Shisa cikin kuka Ta shige toilet tayi Alwala ta fito tayi Sallah Da Nenne ta shiga sai tai maza ta rufe ido Wai ita maiyin bacci Ita kuwa Nenne dadi takeji ganin yanzu komai ya daidaita tsakanin yaran nasu Ita kam Aysha tun daga ranan take wasan buya da Yusuf Shi kuwa Yusuf Allura ta tono mai garma Ya gomce bai tsakalo jarabarsa ta tsiyar nan ba zuwa yanzu Koyasha mgni basa mai aiki Randa Adam yazo ya sameshi yana ta daura magunguna Yasha tsiya kam Har ya hatsala Yanzu Sam bai iya bacci Da ya rufe idanshi Qirjinta zaike gani Kullum sai yayi mafarkinta Sosai yakejin nishadin in ya tuni yadda tsoron shi ya kamata ta rumtse ido sai Zuba kuka takeyi Mmki yake yadda lkci daya tsiwar tata ta gudu sai tsoro Yau kwana 5 kenan da faruwar abin Bayan sallan isha Yusuf ya nufi dakin umminshi Dan yunwa yakeji ga bege da buqatuwa Yana shiga Ya samu Aysha ita kadai A dakin tana kan sallaya daga dukkan alamu Ta Idar da sallah ne Amman gani Hamma Yusuf ne yasa ta tashi Cikin hikima ta rinqa jero nafilfili Kai ya jinjina cikin ajiyar zuciya Dan ya ganota sarai A hankali ya koma bayanta kan sallayar dai dai lkcin da tayi zaman tahiya...... ?🍇 NAYI NADAMA 👇🏻👇🏻👇🏻 MI,WASMITI 9⃣7⃣,Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇 ?🍇🍇🍇 ```Ina qaunarki da alfahari dake Khaleesat Hydar```😍 Qara motsota ya kumayi Tare da manna faffadan qirjinshi kan bayanta Hannushi ya zaqoyo ta gabanta Ita kam Aysha Tun da taji Motsinshi kusa da ita taji gaba daya tsoro ya rufeta tsikar jikinta ne yatashi yarr A lkcin da taji Yasa bakinshi ya kamo zip Din rigarta ya zugeshi Da sauri ta juyo cikin tsiwa tsiwa Tace Me hakan me nayin halin akuyanci Ni gsky banson takura katsakeni Ni ban iya rashin kunyaba. Bai kula taba Sabida zuwa yanzu Ya fara daburcewa a hankali ya cusa hannushi cikin rigar tata Cikin sabon salo Ya daura hannushi kan bres dinta Cabkesu yayi kamar a kidime ya fara shafasu da luguiguitasu Gaba daya ya birkice sai wani irin numfashi yake ta Fizga Ita kuwa Abin ya wuce saninta Zuwa yanzu kokonto ya fara kamata Anya kuwa Hamma Yusuf ne yake mata Wadan nan sabbabin darusan kodai Aljanine Cikin kidiman d qoqarin kwace kanta daga gareshi ta juyo Dan taga shi din ne kam Shi kuwa samun haka ya sashi samun damar daura kanshi kan cinyarta Harshen shi ya zura cikin hudar cibiyarta Da Dan qarfi ta saki Qara gamida ci gaba da janye jijinta Kuka ta saki Tare da cewa Na shiga uku Kai mayene Cinyeni zakayi Wayyo Allah Na. A hakali Cikin shan yaji Gamida tsura mata ido Murya a daburce Yace waye Dan akuya Sannan waye mayen Duk maganar da yakeyi hannushi Na kan abinda yafi komai fidda mai hankali a jikinshi Ya dage sai cakudasu yakeyi Hannuta ta Sa Tana jawo nashi Ganin bazata iyaba Yasa tasa kan yatsunta ta rinqa Jan Gashin hannushi Tana ka sakeni ni sallah zanyi Ido ya kuma tsura mata cikin murtuqe fuska yace Garya ne Ba sallan da zakiyi Ai kin idar Ganina ne yasa Kika wani ci gaba da sallah Toh wannan sallah da kikeyi INA da damar katseshi Qara matsota yayi ya cire Hijabin jijinta Rigar ya ya tartare ya maidata kan wuyanta Kanshi ya nufa kan bres din nata da sauri tace me hakan Cikin isa yace Akuyancin Zan goda miki Tini ya manne bakinshi Ya fara sarra fata Cikin qorewa da karantar abin Bakinta kuwa tuni Ya mutu sai hawayen dake Zuba shi kuwa Murzata yake iya son ransa Wai ko zai samu sauqin Abin dake cinsa Suna cikin haka Kamar daqa Sama yaji Slmar Usman Da sauri cikin murtuqe fuska ya jawota ya kifata kan cinyarsa Zip din rigar ya zuge ya hadamata shi miqewa yayi cikin taqqal tanqqal Kamar bugegge ya koma kan kujera ya zauna gamida da Zaro phone dinshi Ya rinqa latsawa Sannan ya amsa slmar Ita kam tuni ta miqe cikin gyara daurin zaninta Tare da ninke sallayar Usman Na shi Yace Hamma Yusuf barka da Hutawa Kanshi a qasa ya Dan geda mai kai alamar youwa Ganin su biyu ne a dakin yasa Usman kuwa juyawa Da sauri tabi bayanshi Har taje bakin Qofa Taji shi Cikin narkekkeyir Voice Yace *Amrita* Tsayuwa tayi bata fita kuma bata juyoba Takowa yayi Cikin qarfin hali Ya Dan sunkuyo Kanta gashin ya tattara ya tubke mata A hankali yace *Amrita* Yunwa nakeji Hannuta ya komo Ya tura cikin rigarsa Qasan cibiyarshi Ya daura hannun nata cikin ajiyar zuciya yace Kijifa cikina ba komai Sai yunwa Ita kuwa ido ta zazzaro Jin inda yake qoqarin tura hannuta Da sauri ta fizge hannun Cikin azama tayi Babban parlonsu inda nan suke taruwa suyita hira Tana shiga ta samu su baba bello dasu Nenne da Ummi da ya Adam suna zaune Daga dukkan alamu Mgna CE mai girma da ma himmanci sukeyi Shi yasa sai kuma ta juya a hankali Ta nufi Cikin Kitchen Tana zuwa sukaci karo Da Lami mai aiki Riqe da cup Din tea Hannu tasa ta karba cikin cewa youwa tawa nagode Da sauri Lami tace Ke Aysha Na Yusufa ne fa Karki Sha. Cikin tsiwa tace To sai me in nashi ne wlh shanyewa zanyi muga ta iko da mulki Wai ke mama in dai Hamma Yusuf ya saki aiki Toh sai ki wani ajiye aikin kowa sai nashi Shi kuma sai wani mulki yake shinfidawa Fada take tana tafe Kanta a kasa Tana yau sai dai ya kwan da yunwar Da sauri ta daqo Kanta jin taci Karo Da mutum Cikin zaro Ido ta miqa mai Cup din tare da cewa Ni kam ga tea dinka ba ruwana. Dry ta bashi sosai Da ta zage tana mai iyayi Amman daga ganinshi ta daburce Sosai dryar taso kubce mai Amman sai ya kuma murtuqe Fuska yace Wa zaisha sauranki Duk kin zuba yawunki A ciki qazama kawai Ni zaki bawa jogolgolonki Allah ya kiyaye Ya tabe baki gamida yamutsa fuska ya kalli Lami yace a karo min wani kar a samun a wannan cup Din toh tace cikin mutun tawa Shi kuwa juyawa Yayi ya fita yana ai sai ki shanye yawunki *lol su Yusuf to wanne yawun kuma ya rege da bakashaba kai jin kai dai zai wahal da kai ka gama tsotse bakin year mutane sannan ka fito kace wai baka sha yawunta ba😂😝* A parlor kuma Cikin hikima da qirma baba bello da Abba ke yiwa su Ummi da Adam nasiha Cikin sanyin Abba yace Na tabbata kun sheida Allah shike rayawa kuma shi ke kashewa nakwo San kun yarda macecce bai dawowa sai dai idan dama suna yayi Ko? Nenne da zuciyarta ke ta bugawa tace Wannan haka ne mun yadda da haka Dan Allah a gaya maba meke faruwa Cikin ajiyar zuciya Abba yace Shekara 1 da ta gabanta Munyi kuka munyi jimami mun shiga tashin hankali Na rashin Ahmad Cikin rashin sanin Ahmad suna yayi ba mutuwa ba. 😳😳 cikin rashin fahimta Ummi da Nenne da Adam suka firfiti da ido woje cikin kidima d firgicin zancen da suke jin. Kai Abba ya Jinjina musu Cikin gsky da gsky Ya fara basu lbrin yadda abin ya kasance Randa Ahmad ya rasu Mun dauko gawar da niyar zamuje muyi mata wonka da sutura Ni da hydar da Dr Umar ardo A wurin wonkanne Hydar ya kalli yatsar Ahmad Na harbawa cikin tsoro da firgici Ya ke sheida mana da fari mun dauko gizone kawai Dan firgicin rashinshi ya samu hakan Amman daga baya sai mukaga Jijiyar kanshi da ta dunduniyar qafanshi suna harbawa A take Dr Umar ya goggo dashi anan take muka gano doguwar suma yayi kuma tabbas zai iya rasa ran nashi ko yaushi Toh ganin haka yasa a Daren Dr Umar ya fita yaje ya shirya mana komawa India Amman sai ta Yola Ganin bamu da tabbas din rayuwar Ahmad yasa mukaqi sheidawa kowa hydar ma muka hanashi fada tun cikin Daren muka fita da Ahmad zuwa kamanni hospital Sannan muka dauko wota qawar da aka rasa yan uwanta mukazo ni da Hydar muka mata wonka muka mata sutura Koda gari ya wayyi ita aka sallah ta Kuma ita aka binne In Baku mantaba a ranan Ni da hydar muka tafi India Tare da cemuku Nine ban da lfy hawan jinjina ya yau Shi kuwa Dr Umar zaku Iya tunawa sai dare ya dawo gun gaisuwar makokin Bayan yaga mu jirginmu ya tashi zuwa Abuja canma muna zuwa muka kuma miqewa India India Qoqarrun likitocin zuciya Suka dugufa sosai Wurin cetoh Rayuwar Ahmad Babban matsalan a samu ya farfado sannan ai matsa aikin tiyatar zuciya Mun zauna tsawon wata 7 Ahmad bai San inda yakeba sai numshin da yake fitarwa da taimakon Na ura A haka wata tana ya farfado Farin ciki a gunmu ba a mgn A take Na kira Dr Umar Na sheida mai toh ase lkcin Dana kira suna tare da yaya bello Toh shima anan Dr Umar din ya mai bayanin komai Dama kuma yana zuwa duvani a tunaninshi ni dinner ba lfyan da gske A cikin week din akayiwa Ahmad aiki Daga nan kuma ya sake komawa rayuwar bacci har tsawon wata 4 Sukuwa doctors sun bamu tabbacin insha Allah zai tashi cikin lfy Toh yau kimanin wata daya kenan da farfadowar Ahmad kuma ya miqe garau sai dai an dorashi kan magunguna Sannan Mun mishi bayanin komai Tun daga ranar da Hydar ya dawo Duk motsin da akayi a gida sai ya tura mai ko hira akeyi sai ya kira ya ajiye phone shima yayi ta jinku Ahmad ya shiga rudani sosai Shi ko yaushe Nenne Na biyaye Na Adam a wanne halin suke ya maryama take kullum sai ya sani a gaba da kuka kamar yaro shi dai Biyayen shi Ya matsa min sosai. Cikin zumudi da tsantsar farin ciki su Nenne suka rinqa sharar qollah Adam miqewa yayi cikin kaduwa yana Yusuf INA kake Da sauri Abba ya riqo hannushi Cikin hada fuska yace ai matsalar Ku kenan Ku 3 nan muddin kaji Abu sai Yusuf da Ahmad sunji suma kuma haka suke shima kanshi Ahmad Walahi sai da yamin alqawarin bazai kirakuma Amman za ake hadaku yanajin muryarku Kai ya kada cikin sanyin jikin yace Abba wazai tayani farin cikin rayuwar Ahmad in ban gayawa Yusuf ba? Mu zamu tayaka Ya bashi amsa gamida jawo shi ya zaunar Cikin sanyin Abba yace Mu har yanzu bamu gamsu da zaman Yusuf da Aysha bazamu bar Ahmad ya dawo ba har sai mun tabbatar duk sun ruggumi juna da tausayawa juna da kula da juna kuma ba abin da zai sasu hakan sai rashin Ahmad a kusa Bazan bar Ahmad ya dawo ba har sai randa muka gamsu da zamansu Har sai naga Yusuf ya yarda da ita amatsayin matar aurensa tukun Dan shi kam Ahmad tuni ya dauki Maryam a matarsa sannan ya cire batun Aysha a ransa Cikin sanyi Baba bello yace wannan shine yanzu abin da ya rege mu ga yanayin zaman Aysha da Yusuf Din Cikin zumidi Nenne tace wlh yanzu Yusuf da Aysha sun daidaita Kansu Kawai Ku barni naje Na Duba Ahmad A hankali baba bello yace Ba komai dama Ahmad mun dawo dashi yana cikin Abuja Kuma dama nima a kawai wata sheriyar da zamuyi A satinnan kuma a abujan ne za muyi dukda dai mutanen nan Taraba ne Jukunawa ne sai Ku tayani da addu,a Dan zasu iya yin komai a kaina In zanje xamu tafi tare Toh Allah ya kaimu suka amsa baki dayansu rabbi kuma ya kareka daga sherrinsu Amin ya amsa tare da rufe musu yaron da addu,a Wata ranar Jumma,a Da yamma liqis Yusuf ne tafe cikin qorewa yake dravin Cikin nitsuba yayi parking a harabar gidan kaka Cikin takun miskilanci ya nufi cikin gidan A parlor ya sameta riqe da mayafinta Tana ganinshi tace yauwa Aysha kiyi sauri ki fito mu tafi ga Dudabe yazo zai regemana hannya mu huta tafiya da qafa Ko Dudabe ? ta fada tana kallon idanshi Fuska ya kara murtuqewa ya kalleta a yatsine yace da yake ni bawanku ne ko ? Da banxo bafa Kawai daga ganina sai ki wani CE ni zan kaiku Ehh din sai ka kaimu Kam sarkin baqin hali kawai. Toh zan gani ai! Yace cikin yatsine. Daki ta shiga da sauri sai gata kuma ta fito Tana mita Mutum ya shiga wonka kamar mai canza fata Dan jaraba har yanzu fa ko wonkan bata fitiba Bai kulata taba Kuma baiyi mgn ba Tsaki ya Dan ja cikin. Ranshi kuwa wani sanyin yaji dama fitowan Na dolene Dan ya rasa yadda zaiyi ne Da abinda ke damunsa Cikin sauqe ajiyar zuciya ya miqe cikin dakin ya nufa Da sauri kaka tace kai Dudabe INA zakaje? Ban sani ba ya bata amsa a kufule Toh me zakayi a dakin? ta kuma tabbayarsa? Gun mata ta zanje! ko zaki hanani ne? Ya bata amsa Cikin mmk tace toh su mata ta manya juyawa yayi lkcin da yake dab da shiga dakin ya harareta yace ko ban kaibane In shiga gun Amanata Kai ta jijjiga cikin sake baki tace a a banceba Allah ya kiyaye hanya a fito lfy nima nayi gaba. Yauwa dako kinyiwa kanki adalci ya fadi tare da shigewa ciki *Lol su Yusuf kace matarka kamu dawo kace amanarka toh wanne daya zamu dauka*😝😂 Ita dai kaka fita tayi cikin mmkin yusufa a yau din Shikuwa Yana shiga kai tsaye.ya nufuni..... 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👇🏻👇🏻👇🏻 *MI,WASMITI* page 9⃣8⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Sisters ngd da kulawarku gareni Allah ya bar zumunci da qauna* A hankali ya zauna a a bakin gado Cikin ajiyar zuciya Ya Dan ture kayan da Ta fitar. Da nufin sawa in ta fito Pillows y jwo Ya konta cikinsu A rigingine Ido ya lumshe Cikin wani irin sabon Yanayi. Ita kuma cikin sauri Sauri ta kammala ta fito Daure da towel A ququnta Dan idan ta kaishi kan qirjinta bazai rufe ququn nataba Bakin gado ta matso Gamida Dan jawo gefen towel Din tana Dan goge damtsen hannuta Tana Dan yarfa hannu A hankali yaji feshin ruwa Na sauqa a fuskarsa Ido ya Dan bude cikin Bugaqar zuciya Da sauri ya rumtse idan Dan ganin ta a haka zai dauke mai numfashi Ita kuwa Duk abin da take Batama San dashi a gunba Shiyasa take Ta rausaya wa ko a jijinta Mai ta Dan laqakato Ta murza a hannuta Ta rinqa shafe qirjinta dashi Shi kuwa idanshi sunki Yarda da hukuncisa Na rumtsesu ya hanasu Ganin abincinsu A hankali ya bude ido Dai dai lkcin Da ta sunkuyo Ta kanshi da nufin Lalubo Kayanta Qirjinshi ne ya rinqa bugawa da qarfi Garfi a take hankalinshi Ya fara barin jikinsa Lkci guda yaji wani irin sanyi Na ratsashi Tuni ya wore idanshi ras Lips dinshi kuma tuni sun fara bari Da sau cikin azama ya kamo gefen lips enshi Na qasa ya fara tsotsa kamar zai tsinkesu Lkci guda ya daburce Numfashi Sa ya fara carkewa. Da qarfi cikin kidima yayi wani irin ajiyar hrt a dai dai lkcin Da yaji Qirjinta Na gogar fuskarshi Ido ya qara budewa Ita kuwa pillows din ta dauke ta cillashi gefe Ta qara sunku yowa Kanshi Bres dinta suka dire kan bakinshi da gemunshi Cikin rashin sanin halin da yake ciki da kidima Kawai ya manna bakinshi kan bres din nata ya Sa hannushi daya ya sanqalo Bayanta Ta konto Kanshi luf Ita kuwa Tsoro da firgici Sukasa ta saki qara da qarfi Cikin kuka Da kidima take kiran Kaka Wayyo kaka Kaka INA kike kixo Na shiga uku Duk ta kidime sai kaimai bugu take Qara matseta yayi Cikin qarfin hali ya zare harshensa daga kan bres Dinta murya Na rawa Yace Ke ki dawo hankalinki Me kike ta ihu nine fa Hamma Yusuf dinkine Ita dai sai bugeshi take yaxu ta gane shi amman bata bar bugunba Da qarfi ya hade hannayenta duk biyu ya riqe Da hannushi daya Daya hannun kuma Bakin bres Dinta yasa yatsu biyu Ya Dan matse da qarfi Cikin tsura mata Ido Qara ta kuma saki cikin fiffixgewa Qara matsewa yayi Da qarfi Tace Hamma Yusuf Kasheni Zakayine? Kai ya jinjina cikin sanyi murya yace Ke dai kike son kasheni Cikin tsiwa tace Ni banson mugunta Da iskanci Wlh ka fita hanyata Ko in kira kaka ingaya mata Mugu kawai azzalumi Sake hannun nata yayi ya fizgota da qarfi ta fada qirjinshi Matseta yayi da gsky Ya rinqa goga qirjinta a nashi qirjin Hannu yasa ya kunce towel din Da qarfi Ya birki tota Ta bude baki zatayi kuka Ya cabke harshen ta Ya rinqa tsotsa yana Wasa da bres Dinta tuni ya fita hayya cinshi Sai gurnani yakeyi Da fidda numfashi da gyer Qara matsota yayi Cikin jikin yasa hannushi biyu Kan bres dinta yana sarrafasu cikin qorewa Da tsantsar buqatuwa Gaba daya ya fita hayya cinsa Ita kuma kuka takeyi Sosai Tana wayyo Allah wayyo Hamma Yusuf Kayi haquri Dan Allah kabari Kuka takeyi sosai shi kuma zafin kukan nata yakeji So yake yayi mgn Amman ya kasa Ya bude bakinsa da nufin Yin mgn sai yaji numfashinsa Na fita Da qarfi ya qara manne bakinshi kan lips dinta ya rinqa Tsotsa yana Ruggume da ita hannushi daya Na buga bayanta daya kuma Na kan bres Dinta ture hannushi take tana Qirjina ciwo Da qarfi a kidime ya tashi ya tallabota So yake yayi mgn Amman INA sai Wani irin kuka da ya kece mai Shi dinma A zuciyarshi yake jin Wani irin Abu mai naiyi ya danneshi So yake ya lallasheta ya gayamata abinda zai mata dadi Amman ina sai gurnani yakeyi Jin haka yasa itama ta qara rudewa Cikin kuka ta riqe hannushi da suke rawa kar kar cikin rawar murya tace Hamma Yusuf kayi haquri Dan Allah ka barni Hamma Yusuf zaka tsinkamin bres Fa ko kasheni Kake sonyi ne? Kai yarinqa kadawa cikin juya kai Alamar a a Da gyer cikin fixgar numfashi Yace *Amrita* Ni ne zan mutu wlh zan iya rasa raina ya zanyi Na Gaza haquri Ki taimaki Dan uwanki Cikin share qollah tace Ni wlh banso Wlh ni banson ka Ka barni ni wlh tsoro kake bani jowata yayi cikin rawan jikin ya daura ta kan qirjinshi Ya rinqa Dan buga bayanta Yana shafa Kanta Har zuwa Dan wani lkci Sannan ya dawo hayya cinsa Ita kam sai Kuka Can dai Yaji an fara kiraye kirayen sallan Manqariba Cikin qarfin hali Y daqota daga jikinsa A hankali ya sauqi Yazo gaban mirror ya dauko towel Dinta din Hannu yasa ya Kamo nata Ka fada ta maqale Ido ya tsura mata Cikin rawar murya yace So kike Na sake ko Jarabebbiya kawai😡 Mmk ne ya kamata sosai wai ita Hamma Yusuf ke cewa jarabebbiya Muryarshi ta qara katseta Ki tashi ko Na hawo ne Na miki abinda kike son? Da sauri ta miqe Tazo bakin gadon Ta tsaya daga kan gadon shi kuma yana tsaye a qasan A hankali Ya wore towel din Ya daura mata shi a qugunta A hankali Ya manna kanshi a tsakiyar qirjinta Gami da sauqe ajiyar hrt Can kuma ya do go Cikin murtuqe Fuska Ya daura hannushi Biyu kan bres Dinta yana cewa Suma basu da kunya kamar ke Sai suyi ta tsokale idan mutum Shiyasa dole Na hukuntasu Ita dai sai hawaye Qara shafarsu Yayi ya Dan kamo Bakin daya bres din Nata yasa a bakinshi Ya fara tsotsa kuma Lkci daya ya fara yin qasa qasa alamar zai durqushe Ganin haka yasa ta share qollarta Tasa hannu Ta kamo Bres Cikin sanyi da tsura mai ido Ta zaro shi Daga bakinshi Cikin lumshe ido Yace Hmmm hashii Hannu ya kuma kaiwa Ya shafesu A hankali cikin rashin sanin sanda zancen ya fito Ya furta *I love you my Amrita* Yana fadin haka ya juya ya nufi Parlon Har yaje bakin qofa yace Ki shirya ki fito mu tafi Ko Na dawo Bayanshi tabi Da ido A fili ta kuma sakin kuka Tare da cewa Wanna wacce iriyar rayuwace Anyya kuwa Hamma Yusuf yana da imani Siket dinta ta dauko ta zura cikin share qollah Tace Allah ya isanmin mugu kawai Duk ya cakudeni Bayan ta fito Ta sameshi a parlo Ya zauna yana damqe da Mara Yana ganin ta ya miqe Hannu yasa y kamo nata Cikin sanyi Yace Amrita marana ciwo Hannushi Na cikin NATA suka isa gun motar bayan ya rufe gidan Suna shiga Yaja tana gefenshi ta kauda kai Ganin haka Yasa ya Jawota kadan Ta Dan matsoshi Ba kunya ya zura hannushi cikin Rigarta Ya cabke bres Dinta ya rinqa shafewa Har saida itama da kanta taji yana sauyata A hankali ta juyo ta kalleshi Bayan sun isa gida yayi parking Amman kuma hannushi Na jikinta Shima ita ya tsurawa ido Kai ta karyar cikin muryar kuka tace Hamma Yusuf zan shiga cikin gida Numfashi ya sauqe cikin sanyin Yace toh Na hanakine Kalloshi tai cikin takaici Ya maqale bres dinta sannan ya rufe qofa kuma wai ai Na hanakine Shikuma ya kuma matseta cikin sanyi yace Ki tafi mana Ido ta kura mai Shima tsura mata idon yayi A ranta tace Amman lallai Hamma Yusuf Dan duniya ne bai da kunya Kan hannushi da yaketa mutsu mutsu a cikin rigarta ta kuma kalla Cikin sanyin tace ka sakeni ka kuma bude min mota Na riqeki ne ? Ya tabbata yeta cikin isa A hatsale tace ni Na gaji Zaka sani ciwon nono Kai ko a jikinka. Cikin yamutsa fuska yace Waya gaya miki ai so nake kema kiji irin azabar da kike jiyar dani inje inyi jinyar marata ke kuma keje kiyi Na bres Dinki masu shegen Neman tsokananan Da gyer dai ta samu ta zulle ta gudu cikin gida. Aiko a Daren ranar daga shi har ita ba Wanda yayi bacci Shi ba abinda yake mai yawo a idanshi sai surarta Sha,warta sosai take cinsa Ya kuma rasa dalili Jinshi yake in bai malla ketaba zai iya resa ransa Kwana yayi a zaune Ita kam ta konta kam Amman da ta Dan motsa bres Dinta ke tuna mata Hamma Yusuf Dan sunyi tsami Mmk fal zuciyart ase dama maza basu da kunya Ase haka Hamma Yusuf yake kamar maye Lallai kuwa Zai gane itama tana da NATA salon muguntan A haka dai suka kwana Kaka kuwa ase gidan Adam taje Dan Amira Na naquda Aiko washe gari da azahar ta haifi danta namiji Bayan sun dawo gidane Suka sheidawa su Nenne Maryam da Aysha kam sunaji Suka shirya Suka tafi tare da ya Rabi,u Basu Dade da isaba Hydar ma ya iso daga Yola Murna kam ba,a mgn Adam ya hada yan qanneshi Ga Hydar ga Aysha ga Maryam ga matarsa kuma yar uwarsa ga kuma danshi Cike suke a parlon sai hira da nisha di suke Sha A haka har akayi maggariba bayan sun dawo ne Aysha da Hydar suna Zaune suna cin abinci a pilet daya Haqiqa dama can shi Hydar yana jin Aysha fiye da ranshi a jikinshi Ase qaunar ta dolece uwa daya uba daya Suna cikin hakane Yusuf kuma ya iso Tunda ya shiga ya ganta Yaji wani irin baqin ciki ya tokare mai maqoshi Sosai Yaji zafi ya za,ayi Ta rinqa fita anquwa ba tare da ta nemi ixininshiba Bayan ya karbi Dan ya mishi addu,oiCikin hikima ya tsura mata ido yako ci sa,a sukayi ido 2 cikin murtuqe fuska ya watsa mata harara Ita kuwa baki ta murguda mai cikin tsiwa Lips dinshi ya cije Cikin isa yace Ke Amrita taso mu tafi A tsiwace tace tare muka zone ni a gidan Dan uwana zan kwana ehe Ganin zata jamai raini yasa ya fita A cikin Mota yana son ya kira Kuma bai da phone number finta A karo Na forko a rayuwarsa da yaji baqin cikin rashin number wata a woyarshi Can dai ya tuna ya kira Hydar Cikin fada fada yace Hydar wai bakuji nace ta fito mu tafi bane Kun wani ajiyeni cikin mota sai kace yaron gidan Ku Cikin girmamawa Hydar yace Hamma Yusuf wlh taqi tun dazu muke gama da ita harda kaka sai kuka tasa Rai a bace ya fito Ya dawo cikin gidan cikin fada yace Ke ki fito mu tafi Cikin tsiwa tace bazan koma bazan tafi da kaiba tafiyarka da ban tawa da ban Kaka ce tace Dan Allah Dudabe am ka barta ta kwana cikin yan uwanta Cikin fushi yace ban amince ba bada yawuna ba Adam ne ya kalleshi cikin mmk yace toh Biyaye kaje zan dawo da ita anjima A kufuli yace ke wato ban isa da ke bako yayi Kyu Cikin Fushun ya juya ya fita Sosai yakejin zafin fitan da take ba tare da izinishi ba Kai tsaye gida ya koma A babban parlon ya samesu a tare suna ta hira Cikin halin miskilancin ya wuce kitchen Goran FARO ya dauko mai sanyi wai ko zaiji sanyin a ransa A can kuma yana fita ganin yadda ya fita a hatsala Yasa Adam ya ingiza keyarsu A bakin gate ya sauqe su ya juya ya koma su kuma suka nufi jikin gate din Suna isa bakin gate din..... ⒽⒶⓊⓈⒶ ⓃⓄⓋⒺⓁⓈ ⓈⓄⓀⓄⓉⓄ ⓌⒽⒶⓉⓈⒶⓅⓅ ⓃⓄ: 07068808039 ⓌⒺⒷⓈⒾⓉⒺ : ⒶⒷⒹⓊⓁⓂⓀⒾⒷⒶⒷ.ⒽⒺⓍⒶⓉ.ⒸⓄⓂ 👇🏻 _MI WASMITI_page9⃣9⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 ```Amadadin sauran ma rubuta nake miqa saqon Gaisuwarmu ga yar uwarmu Anuty Ruky ma rubuciyar d'alibina da mariya Muna miqa saqon taziyarmu gareki Na rashin yar Uwarki Rashida Allah ya jiqanta da Rahama ya kai haske makoncinta``` 🍇Suna zuwa bakin gate Mati mai gadi ya kafa ya tsare ya hanasu shiga Cikin mmk Maryam ta ke tabbaya yarshi akan wani dalili zakace ance kar mu shiga Waya yasa ka hanamu shiga gidan? Cikin bin doka da umurni yace Babana ne yace kar Na kuskura Na bar Aysha ta shigo Gidan Cikin takaici da hatsala Aysha tace Hamma Yusuf ne yace kar kabarni Na shiga Gidan ? Ehh shine ya bata Amsa Cikin takaici tace aiko Baimin hakaba nasan nan ba gidan ubana bane Basai ya tozartani Ba basai yamin koran Kareba dadin Abin muma muna da gidan uba Hannun Maryam ta kamo cikin zubda qollah tace Maryam zomu koma gidan ya Adam ni gobe da sassafe zanyi sammako na koma Yola gidan ubana A hankali Maryam ta bude baki cikin jin zafin abinda Hamma Yusuf ya musu Tace Aysha ai shima Hamma Yusuf nan ba gidan shi bane Kai kuma mati Wlh ka bude mana qofa ko kuwa Na kira ya Abubakar Na gaya mai kuma ka sanshi sarai wlh horon sojoji zaimaka Cikin sanyin yace Toh ni ya zanyi Umurni Babana ya bani kar Na barta tashiga inko Na barta a bakin aikina Jin haka ya hatsala su Cikin fushi suka tura shi suka shige Suna shiga harabar gidan Aysha ta fara kiran Hamma Yusuf Da qarfi Yana sama gun Abba ya jiyo kiran nata Tate suka sauqo da su Usman Su Ummi da Nenne da suke parlon duk suka zubawa qofar shigan ido Anuty Sadiya da ta iso ba jimawa itako sai kallon Yusuf take cikin Tuhuma Shiko cikin Isa da Qasaita da murtuqe Fuska ya rinqa tako Sitep din yana sauqowa Suna shiga Hawaye shar A fuska ta isa Gabanshi Cikin muryar kuka Ido ta zuba mai Murya Na rawa Tace Na gaji wlh nagaji Hamma Yusuf nagaji da tozartani Da takeyi Dan wulaqanci dacin Fuska shine zaka saka mai gadi ya hanani Shigowa gidan Ai ko bakamin Hakaba ni nasan nan ba gidan ubana bane Ai dama Na sani a tsawon shekarunnan Dan bakasan cewa ni ba yar gidan nan bace da kasani Na tabbata da ka Dade da korata Amman Alhamdulillah Muma muna da gidan Uba Yanzu ka dates Igiyoyin aurenka a kaina ka gani Ko awa daya bazan, garab! Tunda ta fara Mgn da kukan Ya tsura mata ido Cikin murtuqe fuska Sai yanzu Ya daga mata hannu Cikin tsawa yace Ya isa Haka Ehh ni nace ya hanaki Shiga ko kina da abin yi akayi Ki rufe min baki Banson Rashin tarbiya Da kika fitan Wa kika tabbaya? Da izinin Wa kika fita? Waya baki daman fita? Ko zaman kanki kikeyi? Cikin Fushun ya qara matsota Yadda baki tabbaya yeniba dole Haka sai ki koma inda kika Fito Haka jiyama kika tafi gidan kaka ba tare da Neman izinina ba Ko gani kike kinfi qarfi nane Kamo hannuta yayi Cikin Fushun sosai yace bacemin da gani Ya tureta! Jikin Ummi Ta fada cikin Kuka mai tsuma rai Cikin tafasan zuciya da baqin ciki Ummi ta Dan tureta Ta nufi gaban Yusuf Tana zuwa Ta zuba mai mari Mai bala,in Zafi cikin Fushi da zubda qollah Tace Subahanallahi Yusuf Kasheni kake sonyi So kake ka fasamin zuciya Shi kam cikin mmk Da rudu ya tallabe kuncisa Yau Ummi harda mari Idanunsa suka kada sukayi jazazur Gaba daya jijiyoyin kanshi suka tashi Lips enshi sai rawa suke Kai ya kawar cikin tsurawa qofar fita woje ido Yana jin zantukan mahaifiyarshi Na ratsashi Sautin Kukanta Na soya mai zuciya Cikin ifirgicin jin kala manta ya zame Ya zauna kan sitep Din Kuka take tana Kaitona da kai Yusuf Na haifeka nasha wahalarka Amman a karo Na forko Ka kasa yimana biyeyyah ka kasa son abin da muke so Cikin zubda qollah Tace Allah sarki duniya Allah bai barin wani Dan wani yaji Dadi Da ya bar rayuwar Ahmad kusa damu yaro mai biyeyya da sanin darajan Iyaye Amman sai Allah ya nesantashi damu ya kusantoka damu Wlh da kai muka rasa yafi da rashin Ahmad Cikin sauri Nenne tazo ta rufe bakin Ummi Tana girgiza kai tace Haba Ummi Ya za,ayi bacin rai yasa kike furtawa danki Irin kalamannan Ita dai Ummi Sai qollah A hankali Ta matso Kusa da Aysha Ta ruqqumota Cikin NADAMA tace Aysha kiyi Haquri Duk abinda Yusuf Ya miki Nina Jamiki. ki gafatceni Insha Allah tunda bakya sonsa dole ya sakeni Kuma saidai shi ya bar gidannan Cikin quna ta juyo ta kalleshi Tace wlh kaji kunya ka kasa son yar matar da tasoka fiye dani Dana haifeka Tasoka kamar ta mutu kai kuma kaqi jininta yarta da ta yi alqawarin baka tun kan ta haifeta Maryam kam da Aysha sai kuka Shiko Yusuf ya rasa a duniyar da yake Yau an tono mai rashin Dan uwanshi Ya tabbata da duk za,a taru a qishi toh Ahmad zai zame mai *Garkuwa* Cikin fushi yaji Ummi nacemai tashi ka ficemin daga nan bana buqatar sake ganin ka Har sai.ka rubuto min takaddar sakinta ido ya bita dashi Dan ya kasa tashi Sai da ta kuma watsamai tsawa sannan ya miqe ya fita da gyer Dakin Ahmad ya bude ya shiga Zama yake sonyi Amman zaman ya gagareshi So yake yayi kuka kukan yaqi zuwa Sai zirga zirga yake tayi Sai yaje gabanta photo su su 3 ya rinqa mgn Shi kadai A wahalce yake cewa Ahmad meyasa ka tafi ka barni bayan kasan ba mai sona sai kai kadai Ba mai fahimtata sai kai Ba maimin uxuri sai kai Sai ya kuma dawowa bakin gado Ya rinqa tura kanshi cikin pillows Lkci daya ciwon kai mai tsanani ya rabkeshi Ga zazzabi mai zafi Sanyi ya rinqa ratsashi Dumi yake buqata Dumin jikin Aysha ya tabbata in yajita cikin jikinshi zaiji Dan dama dama A haka ya kwana cikin azaba da tunani da tsoron Fushun iyayenshi Gashi baba bello bayanan bare yaje gunsa ya samu sauqi Ita kam Aysha ta gommace bata furta kalamanda da ta furtaba Dan Ummi kwana tayi kuka Sai tai taneman gafararta tana Aysha ban karbeki Dan nacutar dakeba Aysha Yusuf Na Haifa Amman ke nakeji fiye dashi Sai da tarinqa kuka tana Ummi ni kam bakimin komaiba sannan tace toh karki sake cewa nan ba gidan Ku bane Meyayi Yusuf me yayi ki Karfa ki manta mahaifiyarki da mahaifin Yusuf uwa daya uba dayene Cikin kuka tace bazan qaraba Ummi. A haka ita kam Aysha ta Dan samu sakat da matsalan Yusuf Ta sake sai shanawarta take yau tana nan gobe tana can Sam ta mance dashi sai dai wani lkci yakan fado mata a rai sai taji tsanarsa ta diranmata a rai Yau kusan kwana biyar da faruwan abin Ba Wanda ya kuma ganin Yusuf In banda sallah ba abinda yake fita yayi Sai Adam da yake zuwa ya Dan je cikin gidan yazo mai da abinci dukda baicin ko mai sai Dan ruwan tea da yake Dan sha Maryam tamai bayanin komai Amman shi Yusuf shiru yayi bai gaya maiba Sai yanxu da suke zaune Sunata mgnar batun yadda suna zai kaya Sannan Adam ya Dan gyara zama yace Biyaye Na,am ya amsa kanshi a qasa Cikin sanyin yace Yusuf meyasa kake barni so yake qoqarin yi maka illah a zuciyarka Yusuf har sai yaushe zaka cire girman kai da miskilanci ka ruqqumi abin da kakeso Kana son matarka meyasa ba zaka iya furtawa ba Cikin yamutsa fuska da tabe baki yace Ai sai kuma kai tayi banza kawai ka dauka kowa maye ne irinka Cikin tsura mai ido Yace ai wlh kai taka maitar tamafi ta kowa Yusuf Zafa ka kashe kanka Qwayoyin da kake Sha zasu maka illah Tsaki yaja cikin tashi zaune Yace kai biyaye ni banda matsala komai Da sauri yace qaryane duk Wanda ya ganka yaga mai matsala sai dai zurfin cikin ka kawai Son Aysha ke dawayni da kai da begenta Sai tunanin Fushun da Ummi keyi da kai, Wadin? yace cikin tabe baki yace Wlh bata kai nasota ba bare sonta yayi dawayni da ni ba me zanso a jikinta kawai dai ni INA tausayinta ne kuma kasan ita Amrita amana tace kuma a gabanka Ahmad ya ban amanarta Miqewa yayi cikin dry yace ehh lallai da da saura baka gasuba Yusuf Amman dai shawarata kaje kaba Ummi haquri zaifi Sauran kuma basai Na baka shawaraba da kanka zaka nemi mafita Yau suna yaro yaci sunan Ahmad Anyi biki sosai yaro yasha gata Yusuf kuwa zuwa yanzu ya gama gala baita Shiyasa yau ana idar da sallan insha dakin ummin shi ya nufa Zaune ya sameta a bakin gafo Cikin sanyin ya qarisa gunta cikin sanyin sanyi ya zauna gefenta a hankali ya daura kanshi kan jinyarta Cikin rawan murya yace Dan Allah ummina ki gafarceni ki daina fushi dani Na tuba kimin afuwa Cikin fushi ta ture kansa ta miqe gamida cewa fitanmi a daki banson ganin ka! Cikin mmk ya tsura mata ido Ita kuwa a fusace ta buga mai tsawa ficemin a daki bana qaunar ganin ka Miqewa yayi cikin qoqarin riqi hannuta Yana mai Karya wuya yace Ummi Fushunki masifa nefa a kaina ki gafar ceni Da sauri tace fita nace ko Haka ya fita jikin a sanyaye Yazo dai dai qofar fita part din Ummi sukaci Kari da Aysha da take gudu da zare ido Dan ganin hadarin da ya taso sai iska da walqiya da ake zubawa Cikin tsoro ta fada jikinshi Da sauri ta kuma janye jikinta zata wuce ciki ya damqi hannuta Yana ja tana tirjewa ya nufi part dinsu da ita.... ?🍇🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👆🏻👇🏻👇🏻 *MI WASMITI* page 1⃣0⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 ᴀʙᴅᴜʟᴍᴋɪʙᴀʙ.ʜᴇxᴀᴛ.ᴄᴏᴍ Janta yake tana tirjewa har suka isa Dan farfajiyar part din Nasu ganin yana qoqarin Janta ciki Yasa ta sunkuyo da kanta ta kama damsen hannushi ta ciza Zafin ya ratsashi Cikin takaici Ya yarfar da hannuta Yace tafi Nace ki tafi Lkci daya kuma ruwa ya keto kamar da bakin qorya Ga isaka mai sanyi dake busawa Sai walqiya sake ratsa garin taraba baki Daya Tallabe hannushi yayi cikin Kunan rai ya duqa a gun Ya rumtse idanshi ruwa Na sauqa kansu hasken fitulun wurin suka ratsasu A hankali yace *A,ish* Ki tafi ki koma inda kike son zuwa ki barni Ki tafi ki barni Allah zai zama ga tana Kuma shi yasan taimakon da zaimin Inma mutuwa tace hutu a gareni toh Allah ya dauki raina da gaggawa nabi Biyayena Na huta da quncin rayuwa tunda Ahmad ya rasu ban sake farin cikiba Na kasa samun madadinsa *A,isha* ke baki da burin da ya wuce ki gasamin zuciya Tafi ki barni ko nace Ki tafi A dai dai lkcin kuma aka saki tsawa mai firgitarwa Cikin tsoro da razani ta fada Jikinshi Cikin rawar murya Tace Hamma Yusuf tashi Tashi ka rakani Ni tsoro Nakeji Da qarfi ya miqe cikin Fizgar numfashi Ya angizata Ya juya ya hau kan baranda jikin windo yaje ya tsaya jikin fada yace Duk inda kike zuwa yawon naki Nike rakaki ne? Ko kina Neman izini nane Gani walqiya yasa ta qara matsoshi Cikin sanyin murya yace *A,ish* Kiji tsoron Allah fa kina sane da duk matar da ta fita ba tare da izin mijintaba har taje ta dawo Mala,iku Na tsine mata Ido ya tsura mata cikin takaici yace Kalli irin shigar da kike fita da ita Ko wanne jakin da doki ya qaremiki kallo Gaba daya ya fita hayya cinsa Cikin sanyin yace Kinmin laifi Sannan Dan nayi mgn kika hadani da Ummi Sannan kika qaura cemin A hankali ya matsota Murya Na rawa Yace *A,ish* Ke bakiyi kewar mijin ki bane? Bakya jin kewata da rashina a kusa dake? Cikin tabe baki da jin qarfi quiwar ganin tsawan ya Dan lafa Tace waye mijin nawa? Wayeshi da zanji kewarsa? Ni ban da miji sai Wanda zan aura kwananan Yanxu ma sakina nake jira gashi kuma Daba banda iddar mutum a kaina Kalamanta sun kasance Tamkar wuta a zuciyarshi a take bugun zuciyarshi ta tsananta Numfashi Sa ya fara daukewa Da qarfi cikin dimuwa zai juya kenan hannushi ya bugi gilas din window Aiko lkci daya taimar mugun yanka A tafin hannushi Sai jini Yake tsiyaya gashi dama rai ya baci jinin ya tsinke Jinin ne yake zuba tsosai Sai kuma ya maida hannu ya matse gilas Din jikinsa kab sai rawa Yakeyi ya kasa mgn sai tsura mata idon da yayi Cikin tsoro ta matsoshi Ganin jinin Na zuba har Qasa hannun ta kamo Cikin rawar murya tace Hamma Yusuf (Laru iyayam no rufata ha judema fa) Kaga yadda jini yake zuba a jikinka fa Ka sake glass din Kaji sai qara matsewa yayi Cikin maida numfashi Yace ki bacemin daga nan ki barni mana Badai ni ba mijinki Babe INA saki kikazo nema Ki fita harkata Qara matsoshi tayi ganin gaba daya baya cikin hayyacinsa Yana fadin tunda ba mai sona da tausaya mi ai gwara Na mutu Ku huta da ganina Dama haka kuke fata har kuna cewa da ni Na mutu Allah ya barmuku Ahmad Toh zan bashi Ku huta Dama nafi kowa buqatarshi sai Na bishi Bakya sona Da sauri tace Hamma Yusuf ka sake Muna sonka mana Da sauri yace qara kikeyi Aysha Ba sona a qwayar idanki Qara kamo hannushi tayi Cikin kuka tace Hamma Yusuf Ya za,ayi kace ban sonka Kaifa Dan uwanane Na jini Jikin yarfe hannu Yace Waya CE miki irin wannan son nake so kiyi min A a bashi nake keso ba Aysha nifa mijinki ne ki dena ganina a matsayin Hammanki Na wuce wannan matsayin Cikin tsura mai ido tace Ni kai ba mijina bane! Kai ya kada gamida qara matse glass din Yana fadin toh ni mijinki ne ki yadda da cewa ni mijinki ne Gaba daya ya rude ya rudata lkci guda kuma ruwa ya qara kecewa Gashi duk sun jiqe Cikin tsoro tace Toh ka sake hannu ka Na yarda! Jin haka yasa shi janye hannushi da sauri Ya tallabo Fuskarta bakinshi Ya hade da NATA cikin rawan jiki Ya lalubo harshen ta Ya rinqa tsotsa gaba daya fuskarta kuma ya shafeta da jininshi Duk jikinsa sai rawa yakeyi Da gyer ta zame bakinta daga nashi Zata juya ya kamata Bai tsaya ko INA da itaba sai dakin Ahmad Suna shiga Ya matsota jikinshi Cikin rawan jiki ya rinqa balle boturan Gaban rigar tata bayan ya zaremata After dress Dinta Duk ya rude ita kam sai ido take binshi dasu Haka kawai itama takejin wani Abu Na mata yawo shiyasa batayi yunqurin hanashiba Yana cire rigar Ya balle bel din ququnta Cikin sanyin murya yace Cire Wondon nan ya jiqe Yana fadin haka yana Zare riqar jikinsa da wondon Da sauri ta rumtse idanta Gudun yin mummunan gani Jinshi ya sunkuyo yana Jan Jens din jikinta yasa ta bude ido Daga shi sai towel a ququ girjinnan duk a woje Tsoro ne ya rufe ta sosai lkcin da taji yana zare pant Dinta Da qarfi tace Hamma Yusuf Me haka Bai kulata ba saida ya zare Ya ciccibota Ya haye kan gado da ita Cikin blanket Ya shige da ita Wore towel din jikinshi yayi gamida matsota jikinshi cikin Kidima ya dire hannushi kan bres Dinta gamida furta I miss you A,ish Yamutsata yake kamar ba gobe Ita kam Aysha in nace tsoroma Na rege Dan jin jikin Hamma ta a fili ya qona mata ruwan kai baki daya Shiko zuwa yancu ya manta menene kunya bare nauyi bare wani gudun kar ta rainashi Cikin wani irin kuka kamar yaro ya manna bakinshi kan bres Dinta ya rinqa sarrafa fatan kuma da hannu mai yankan Sam baijin zafin Shafata yake daga kan lips Dinta yabi da yatsu 2 Har zuwa kan bres Dinta a hankali yazo kan cibiyarta Ita kam Aysha sai miqa takeyi Duk gabban jikinta suna budewa suna karbar saqonnin Hamma Yusuf Dinta A hankali ta daqo hannuta ta daura ka qirjinsa Tana shafawa Da sauqe ajiyar zuciya dan ta Dade tana Sha,a rawar taji ya kallan laushin gashin qirjinshi nashi yake Sautin Ku kanshi ne ya dawo da ita hayya cinta Kissing Dinta yake daga fuska har qirjinta har kan cikita har zuwa cibiyarta har ya gangara inda bazai faduba Duk ya kidime ya rude ba abinda yake yi sai qurnani da nishi da wasu zantukan da baza,a gane ba Bata gama tsinkewa ba sai da taji shi yana qoqarin yi mata rumfa da qirjinshi Yana mai cewa *Ihshat* Kin amince dani ? kin yarda da baqoncina? kin amince Mu zama ma,aurata? Cikin tsoro da rawar murya tace Hamma Yusuf kayi haquri wlh inajin tsoro Bazan iyaba zakajimin ciwo Hamma Yusuf Kafi qarfina ! Cikin Gigita ya zame ya konta rubda ciki Ba abinda yake Sai nishi Yana Wayyo Allah Aysha marana zai balle Zan mutu Ki taima kamin Cikin tsoron ta taso ta zauna Cikin murya kuka Tace Hamma Yusuf karbar mgn kayi shiru zai bari A hankali ya mirgino Jikinta kanshi ya daura kan cinyarta Gamida Dan jawota ta sunkuya ta yadda Ya samu bakinshi ya iso bres Dinta Cabkewa yayi yayi luf a jikinta Yana sarrafa ta cikin sauqi da jin dadin yanayin garin da iskar dake busowa ji yake ba wani mahaluqin da ya kaishi jin dadi a yanxu itama shiru tayi Gamida qara sunku yowa Dan itama yana tsumata da salonshi Qirjinshi take shafa,wa Tana tura hannuta cikin sumar kanshi A haka har suka Dan samu gamsuwa da juna A hankali ya zare bres Dinta daga bakinshi Cikin Sanyin murya Yace *A,ish* Shiru bata amsaba Qara matsota yayi gamida kamo tafin hannuta yana wasa da yatsunta Yace *Habitti* Ajiyar hrt ta sauqe. Cikin shafo bres Dinta Yace *A,ish* Ummi Na fushi dani Bansan ya zanyiba Kowa haishina ke ji Bana son bacin ran umina INA tsoron Fushinta Rayuwata zatayi duhu In tana fushi dani Ki tayani Neman gafararta Cikin wani irin voice tace Hamma Yusuf Ba Wanda ya tsaneka A hankali ya lalubo Phone dinshi Ya haska fuskarta Cikin ajiyar hrt Yace Yarinya Kema a hannu kike Tsoron ki ne zai cutar damu Ji yadda idanki ya koma Cikin kunya da takaici Ta yunqura Da sauri ya kamata Ya matse a girjinshi Cikin sanyi tace Ummi cefa ta aikeni Gidan kaka kuma tasan Na fito Dan ta kirani da ta ga hadari Nasan yanxu tana can tana jirana Cikin isa yace Da safe sai kice a gun mijinki kika kwana Bataso a dole ya matseta ya hanata fita Da asuba yana tashi ya hada musu rawan wonka ita ko duk tana bacci A hankali yazo ya bude blanket din iya qirjinta Sai yanxu yaga gaba daya ya shafeta da jininshi A hankali ya tallabota bai direta ko inaba sai cikin ruwan dumin Da sauri ta bude ido Cikin sauri ta kuma rufewa ganinshi shima cikin ruwan Ya miqo mata hannu Jawota yayi ya rinqa shafesu da sabulu da ya dauko a dakinshi da kayan da zasu saka dan Na jiya a jiqe suke Bayan sun fito dukkansu daure da towel Ya matsota cikin kauda kai Ya zura mata wota yar rigarshi mara hannu sai hula Cikin mmk da zare ido tace INA kayana Sun jiqe kuma duk sun taba jini Ina tsoro kar umminki ta gani tace Na miki fyadeh ya fada cikin tausayawa kanshi Ko in je in dauko miki? Cikin takaici tace Yanzu ya zanyi Matsota yayi ya zura mata rigar Ya sunkuya ya xira mata Dan 3 qtr shi Inda yazo mata har qasan guywarta jawota yayi gabanta mirror Yace gashi kinsa kaya me ya rege Cikin tura baki tace sai inje a haka Ehh mana yace tare da fita ya nufi massalaci Itako har ya dawo bata tafiba Shima dama ya shi gone Dan ya kwashi kayan nasu Gabanta yaje cikin Sanyi da murtuqe fuska yace taho nan Hannu yasa ya kamo nata Ya jata suka fito Kai tsaye dakin Ummi ya nufa da ita Yana kiyi sauri muje yanzu nasan Ummi tana dakin Abba Kina cire kayan ki kawomi abina kar a gani a ranshi kuwa Allah Allah yake su hadu da Ummi Dan zata dauka ita Aysha ita ta bishi Suna shiga Dakin Ya matsota gamida Sa hannu ya zuge Zip din rigar Kenan Qofar toilet ta bude Da sauri yasa hannu Ya..... ?🍇🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👇🏻👆🏻👆🏻 *MI WASMITI* page1⃣0⃣1⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Cikin lumshe ido Ya shafa bres Dinta gamida Dan matsota Da sauri ta buge hannushi Ta matsa gefe Harara ya watsa mata gami da juyawa Da sauri ya sunkuyar da kai fuska a kunyace ganin Ummi da ta kafeshi da ido Cikin tuhuma A hankali ya bude Baki yace Ummi an tashi lfy Batayi mgn ba sai hanyar fita da ta nuna mai da hannu Cikin hada fuska A hankali yace Ummi kiyi haquri Fita dai nace Toh yace gamida Dan Sosa qeya ya fice Itako Aysha kunya ta hanata motsawa Sai da Ummi Tace Ki cire wannan kayan haukan Cikin jin kunya ta shige toilet ta Sa doguwar rigarta sannan ta fito Cikin tuhuma Ummi tace Ina aikena? Kai ta kuma sunkuyarwa cikin inda inda tace Hmm dama Damanfa Daman mefa? Kimin mgn Dama Hamma Yusuf ne ya Karba. Toh meya kaiki gunshi Rau rau tayi da ido Ganin haka yasa umin ta fice tana zanyi mgnin shi Badai rashin kunya yakeson koyaba Shi kam Yusuf a wunin yau ya wuni Cikin nishadi Mai da wani tunani sai nata So yake yaji muryar ta Amman ya rasa ta ina Zai ganta Gashi begenta ya mai mugun kamu Konce yake a parlosu shi kadai Yana ta tunani number ta yake son samu Cikin zaquwa ya miqe ya zauna Adam ya kira Yana dagawa Yace ya dai biyaye ? Tsaki Ya Dan ja cikin daqilewa yace Number Yarinyar nan nakeso ka ban. Sarai Adam ya gane Amman Dan ya cinnashi ya fada da bakinshi yace Ai yaran suna da yawa wacce daya kasan yan matan da suke sonka basu da adadi A hatsale Yace can da shirmenka Ni Na taba cema ka ban number watace bare ka tallatani Cikin dryar mugunta yace Toh number wa kakeso? Cikin yamutsa fuska yace Dan iska Number qanwarka zaka ban Dry yayi sosai sannan yace Shege ai Taurinkai Kashe maishi yakeyi Shiko katse kiran yayi Ba a jimaba yaga number Da sauri Ya daga Cikin zumudi Ya kirata Har kiran ya katse bata dagaba Kamar zai bari sai kuma yaji ya kasa Haquri Ita kuwa tana kitchen Tana ta aiki Dan baba bello Na hanya Bayan ta gamane ta koma daki da niyar yin wonka Har ta shiga toilet taji woyarta Na Neman agaji ᴀʙᴅᴜʟᴍᴋɪʙᴀʙ.ʜᴇxᴀᴛ.ᴄᴏᴍ A hankali ta fito Daure da towel Cikin sanyin murya Tai slm Ganin sabon number Ne Ajiyar hrt ya sauqe da qarfi jin voice dinta Cikin sanyi yace *A,ishhhhh* Shiru tayidan tuno wannan sabon sunan Wanda tasan Mutum dayane ya rada mata shi Kuma ya shiga ranta Muryarshi ta qara Katseta Cikin mutuwar jiki Yace *Habitti* Me kikeyi INA kike nai ta kiranki byake daqawa Shin bakisan zakisa zuciyar Yusuf ta fasheba Cikin jin katsala ta qara narkewa jikin pillows A hankali taji Yana huramata iska A kunne ta cikin woyar Ajiyar zuciya ta kuma sauqewa Cikin narkekkiyar murya Yace Aysha Bata Amsaba Cikin shauqi ya qara matso pillows cikin qirjinshi Yaci gaba da cewa Dan Allah kiyiwa mijinki mgn kina sani firgici A,ish ko byeke ji nane Habitti Cikin sanyin jikin tace Hmm ahh INA jinka Toh me kikeyi? Wonka zanyi! Cikin kasala yace ki zo nayi miki a nan Shiru batayi mgn ba Cikin karya murya yace *ishat* dina kizo hammanki ya miki Ko inxo nandinne? Cikin Shauqin da ta samu kanta a ciki da mmkin hali irin Na Hamma Yusuf Tace Sai kazo din ai A dakin Ummin? Cikin furza iska Yace cike inxo din mana ki gani Fuska ta tabe tace toh Kazo Angama yace Ita kuwa katse kiran tayi tana ai dai duk fitinarka ka nitsu Cikin sanyi ta shiga toilet din ... Shi kuwa yana miqewa cikin Miqar jaraba da begenta Ya juyo kenan ya ga Adam tsaye a bakin qofa ya harder hannu a qirji ya zuba mai ido Cikin tuhuma Ganin haka yasa ya gano cewa ya jima a gun Murtuqe fuska yayi cikin kauda kai Yace kai Kauce Cikin tsura mai ido yace anqi a kace din Ina zakaje Kollonshi yayi cikin isa yace Gun matata zanje ko kana da mgn? Dry Adam yayi yana lallai Yusuf wlh baka da kunya Ni kake gayawa haka ka manta zantu kanka Na bayako? Tureshi ya danyi Cikin cewa koma dai mene ai dai mata tace mallakina Ni wlh matsala ta da kai Adam ka fiye Sa ido Babban banza Kawai😡 Ya fadin haka yayi cikin gida Da sauri Adam ya bishi a baya Yana wlh kai kam Yusuf sai Allah ne kadai yasan sirrin ranka Mutum sai muna furci kanaso kana kaiwa kasuwa Shi dai tsaki yaja ya wuce part din Ummi A hanyar shiga bedroom Dinta sukaci Karo da ita Cikin kauda kai Yace Ummi yunwa nakeji Wucewa tayi cikin parlon Sai da taje har kan kujera tare da amsa SLM Adam da kaka da suke shigowa tare Lkci gufa kuma ta juya gun da yake Sai wayam baya gun Cikin mmk tace Toh INA yashiga kuma Hira sosai su kaka da Adam da Ummi keyi Amman ita hankalinta Na kan Yusuf din A can kuwa A hankali ya bude Qofar toilet din Cikin Sanyi ya maida qofar ya rufe Ita kuwa Ta cika baf din da ruwa ta murza sabulu a jikinta ta kada ruwan kumfa ya cikashi Tayi luf a ciki Idanta a lumshe Cikin ranta kuma gaba daya Tunanin Daren jiyane a ciki A hankali tasa hannuta ta shafa qirjinta Dan tuno yadda Hamma Yusuf ke shafa qirjinta A ranta tace Banji abin da nakeji ba in Hamma Yusuf ya shafa qirjina ba Baki ta Dan tura cikin Qara rumtse ido Tace hannun Hamma Yusuf da bane Dana kowa a duniya A fili tace Meyasa meyasa hakan ne Hamma Yusuf Cikin sabule kayan jikinsa Ya shiga cikin Ruwan Bakinshi ya kai kan kunneta Yace Mekuma NAYI ganifa nazo Da sauri cikin tsoro da mmk ta bude ido Sai kum taji kunya ta diran mata Shi kuwa Jawota Jikinshi Yayi cikin Sanyi Yace menene a nan din ya fada yana shafa qirjinta A hankali ta sauqe ajiyar zuciya Cikin Sa hannu ta sanqalo Wuyanshi Murmushi Yadanyi cikin rada Yace I miss you My dear Qara maqaleshi tayi Cikin kidima ya hade bakinsu Wuri daya A hankali qabbansa suka rinqa sakewa cikin mutuwar zaune Ya kamo harshen ta da ta rinqa lasar jajayen lips dinshi da suke bata dry in suna karkarwa Lasar lips din take cikin salon da itama batasan tanayiba Dan Hamma Yusuf cire mata hankali ta yake a jikinta Maida ita yake irinsa Kama harshen yayi yana tsotsa yana kuma murza bres Dinta ga sanstin ruwa ga Na sabulu gana fatarta Tuni ya kidime ya kidima ta Sai numfashi yakeyi sama sama Ita Kuwa a hankali Take Ki ranshi cikin mayen love Tana Hamma Yusufff A dakin Ummi fa Ummin kuwa yanxu ta shigo Dakin cikin Mmk take jin alamun mgn a toilet din batayi zaton yana cikiba Ta matsota bakin qofar da niyar cewa Aysha lfy take mgn a bayan gida Dai dai lkci Yusuf kuma ya tashi cikin kidima yana lalubo bres Dinta ya samu yasa a baki Ganin yadda yakeyi yasa ta gano me yake muradi shisa cikin kidima itama Ta tallabo kanshi kamar yaro ta Dan dago qirjinta Cikin rumtse ido Ta tura mai bres Dinta A bakinshi Cikin kidima da gigita ya cabke yana sarrafata Ita kuwa cikin wani irin Abu da ya ratsata Ta qara maqaleshi Cikin sakin Dan qara Tare da cewa Hamma _Yusuffffffffff_ Bai iya amsawa ba sai nishi Dan yakeyi Jin haka yasa Ummi kuwa Barin dakin da sauri Kunya CE taji ta rufeta ba iyaka ji take kamar ta nitse A fili tace Na shiga 3 yaushe Yusuf ya koma Mara kunya da dai nasanshi da kunya Parlon takoma gunsu kaka Shi kam Adam shima zaman jiran ganin ta INA Yusuf zai fito Ne yakeyi Su kuwa a toilet Aysha ta haukata Yusuf shima ya haukata Duk sun zama tabbabu Ba abinda Take cewa Sai qiranshi take cikin Rada tna Hamma ```Yusuffffffff``` Da gyer ya dago ya kalleta cikin tsura mata ido Da shafa Abinda yake tafiya da imaninshi wato bres Dinta Murya a daqile Yace Aysha Haka zamuci gaba da rayuwa Aysha bazaki tausaya manaba Kiga halin da muke cikifa A hankali ta matsoshi ta manna kanta kan faffadan qirjinshi Tasa hannu daya tana wasa da tattausan gashin qirjin nashi Ido ta lumshe A ranta tace Hamma Yusuf nima ka gama min illah bansan lkcin da ka karyamin zuciya ba A fili kuwa Lumshe ido tayi Cikin tura baki Tace Ni ka tafi kar Ummi tazo Tallabo fuskarta yayi cikin rada Yace Aysha shekarunki Nawa yanxu Cikin kasala tace 20 Qara matsota yayi ya manna qirjinshi a nata Yace In dai kina da lfy to wlh bazaki juri irin zamannan da mukeyuba Wlh ni kam bazan iyaba Ina cutuwa Aysha nifa ba waliyi bane Dole INA da buqarta matata a kusadani Ina buqatar kulawarki Wlh yau dinnan zan iya rada raina muddin Baki matso gareniba Haquri Na ya Gaza Kimin tallafi In ba so kike Na mutuba Duk ya qara rudata Da sabon salonsa Cikin shogoba tarinqa Dan bugun qirjinshi Tana Hamma Yusuf ka tashi ka fita Ido ya tsura mata qaunarta Na ratsashi Cikin sanyi ya kife guywarsa duk biyu Murya Na rawa Yace Kimin alqawarin zakizo gareni yau In dai kina son Na rayu In kuwa da gsky ke kuke son Na mutu toh ba yadda Na iya Itama ido ta tsura mai Cikin sanyi ta miqa mai hannu Tace bazan iya tashi ba Daqo ta yayi cikin Kada kai yace nima zan iya faduwa ko a hanya ne kema kinji Bakida qarfi bareni Yana dagota Ya miqa mata towel Zata daura a qirjinta yace a qasa zaki daura Cikin tura baki tace sabida me? Sabida ban tafiba tukun kuma ban gaji da kallon abina ba Cikin jin tsikar jikinta Na tashi ta matsoshi A hankali Ta manna qirjinta Kan nashi tana gogawa Shiko ido ya tsura mata cikin mmki A fili kuwa cewa yayi Wlh kin kusa ki qarisani Bata kalleshiba ta juya ta hada bayanta da qirjinshi Cikin hikima ta kamo hannayenshi duk biyu ta daura Kan bres Dinta Da qarfi ya saki ajiyar zuciya gamida Komawa jikin gini Ita kuma cikin murmushi mugunta Ta fita tana juya mai ququ Tana fita ta zura rigarta tayi Parlon Cikin nishadi Taje gun kaka Dake cin Fruits Zama tayi itama tanaci Tana ya Adam yanxu kam tunda Amira ta dawo gida kullum sai an ganka Cikin dry yace wato da bana zuwa kenan ? Dry sukayi Gaba dayansu Dai dai lkcin Yusuf ya fito Fuska a murtuqe Har zai wuce Kaka tace Kai wannan d'a da baqin hali kake yanxu wato bamu kaima ka kellemu ba Adam kuma miqewa yayi da sauri Yana zuwa hannushi Ya tura cikin gashin kan Yusuf Shi kuwa tabe baki yayi yace Ni banma gankiba Sarkin mita Ummi kuwa ita kunya kallon ida sukema takeyi Suna fita Adam yace Wlh Yusuf iskanci ka ya girmi shekaru na Kasan Allah ka fara ban tsoro Zaka cinyemin yar uwa ka toskeni Ni INA bin taka yar uwar a hankali Cikin Rawar murya kamar mai shirin kuka yace Adam zadai ta kasheni ita Wlh Ummi bata saniba zata rasa danta a banza abin yamin yawa Allah sarki Adam sai yaji tausayi yinshi Cikin Sanyi Yace Yusuf Aysha matar kace Insha Allah bazata kashe ka ba Yau zan samo ma mafita Tunda kaga dama nima yanxu a gida zanke kwana tunda Amira ta dawo gidan itama A haka ya Dan bashi qarfi guywa Tun da akayi sallan insha Adam ya jashi suka koma parlon Ummi Baba bello Kuwa da yaje Abuja A dole Ahmad ya biyoshi da yasan halin da Yusuf ke ciki Dan Adam Na gaya mai komai Gashi tafi yar moto Sukeyi dan Ahmad Yace yana son ganin gari Kuma zasu biya Yola So haka yasa zasuyi isan dare Wata qil su isa irin qarfe 1 zuwa 2 haka. Su kuwa su Yusuf Suna zaune Adam ya tasa Amira a gaba Yana ta tura kan Ahmad qarami wai yasha nono Ummi Na kallonsu cikin tsokana tace Adam wannan da nakafa kurane Cinye mana diya zaiyi Cikin tsokana Adam ya kalli Yusuf dake ta Bin Aysha da ido Yace Ummi ai wlh Yusuf ya gado Shi kuwa Yusuf bata fuska yayi ya miqe yabi bayan Aysha..... ?🍇🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👆🏻👇🏻👇🏻 *MI,WASMITI*,Page 1⃣0⃣2⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Da sauri ya Sha gabanta cikin Karya murya da lumshe ido yace A,ish Bata kulashiba ta kauce ta juya zata Fita da sauri ya kamo Hannuta Cikin rada tare da tsura mata ido yace Dan Allah ki saurareni Plxx ki daina wahal dani haka Wlh ina azabtuwa.qara matsota yayi cikin tausayawa kanshi yace wlh Ji nake kamar zan mutu Ki tausayawa Dan umanki Da sauri ta Dan tureshi Cikin murguda mai baki tace Sai me ni me nawa a ciki Ba abin da ya shafeni Inma mutuwa CE ai ba kanka aka faraba kuma ba kanka za,a qarebe Hanyace kaje Muma muna zuwa Ai in maye ya manta uwar da baici ta manta ba Banza Sokuwa kuma Me zata iya maka wanne taimako zan maka A hankali ya farajin ranshi Na tafasa Cikin murtuqe fuska ya kamota ya matse ta jikin gini ido a juye yace Na mutu ko baki da matsala da mutuwa ta ko Aysha ni kike gayawa haka Kin kyau ta A hankali ya kuma sakinta Cikin sanyin yace Ki sani Koda yau ko gobe ko next week ko next month ko next year Na rasa raina ko lfy ta Kece sila Ke kika kasheni Juyawa yayi cikin cize lips inshi ya fice Kamar zay hadiyi zuciya Yana fita Sama ya haura Kai tsaye parlon baba bello Yaje ya kwana kan 3 str dan Bai son damuwa Bayan azabar da yake Sha Adam ne ya miqe yabi bayanshi Cikin sanyi Ya shiga ya sameshi Konce ruf da ciki Ya tura hannushi Ta qasa ya damqi mararsa Cikin kula yace Biyaye meke faruwa? baiyi mgn ba Sai qara matse mararsa da yayi Sunkuyo wa kanshi Yayi cikin kula Yace Kasha mgnin ka kuwa? Kai ya gyada mai alamar ehh Sai zufa dake keto mai Duk jikinshi ya fara bari Zuciyarshi ta fara harbawa da sauri sauri Cikin mmk Adam yace Toh Amman Yusuf Wannan fa ba shine mafita Ba dama Na tabbata a kawai randa mgnin zai Gaza sama maka nutsuwa Ka tashi mu tafi Part namu Ni zan turo Aysha Da qarfi ya samu ya yunqura ya zauna cikin Rawan sanyi Yace Banson Ka barta Adam ka barta Meyasa? Zan barta ya tabba yeshi cikin kulawa Cikin tausa yawa kanshi Yace Aysha fa Tace bata sona Bata qaunar ganina Tace ko Na mutuma Ba ruwanta Ita bai shafeta Ba Ga ummina itama Bata qaunar ganina Ko gaisuwata bata amsawa lkci daya Ya rinqa karkarwa Sai riqe Mara yakeyi A tsorace Adam ya talla boshi Lkcin da Numfashinsa ya rinqa Fita ba tare da ya komaba Duk Sai damqe mararsa yake dafe da qirjinshi Jijiyojin hannushi da qoshinsa duk sun taso Sama Sosai Adam ya firgita da tausaya mai cikin hatsala da tsoro ya sauqo Dakin Ummi ya nufa A dakin ya sameta da Aysha Da Maryam Harda Amira Cikin fahimtarwa Ummi ta musu Bayanin dawowar Ahmad Lkcin take sheida Musu Ahmad Yana raye kuma yau zai dawo Cikin tsoro da mmk da kaduwa Duk suka daqo ido Suka xuba mata Baki Na rawa Maryam tace Ummi ya Ahmad kuma Ummi ko dai mafarki nakeyi Kamo hannu Ummi Aysha tayi Cikin Zubda qollah Tace Ummi Bakya mna irin wasannan Ummi wannan wanne irin zance ne Ummi macecce Na dawowa ne Maryam ne ta qara ruqqume Yusuf qarami Cikin Zubda qollah Tace Ummi kina Nufin Yusuf ba maraya bane mahaifinshi Na raye Dan Allah kimin bayani Sauqowa tayi cikin Gsky da gsky ta kamo Hannusu Su duka Tace Maryam Na taba miki Qarya ko Wasa? Kai ta qirqiza Alamar a a Cikin sanyi Ummi tai Musu bayani Mai gamsarwa Gaba daya ido Suka rinqa Bin juna dashi Kowacce da tunanin ta Maryam kam daqo Yusuf qarami tayi ta rinqa Kissing dinshi Da gudu ta ture Adam dake qoqarin shigowa ta nufi Part din Nenne A namma Nenne ta jadda mata hakan Itako Aysha da Amira Sai hamdala sukeyi Cikin fada Yace ke Aysha Kixo Da sauri ta Isa gunshi Cikin Murna ta sanqalo hannushi Baki Na rawa tace Ya Adam Ya Ahmad Na bai rasuba Ya Adam wanne irin Godiya zanyiwa Allah Na Ya Adam Me zanyi A yau NASA Ya Ahmad Na farin ciki Cikin Fada yace Farin cikin Ahmad ya kan kasancene Yayinda Yusuf ke cikin Farin Ciki Gashi ke kuwa baki da buri Sai son baqan tawa Yusuf Ko kin manta Ahmad kan sadaukar Da duk wani Farin cikinsa da jindadinsa ga Yusuf ne Ga Ahmad can ya kusa shigowa garin taraba Kuma wlh bai begen ko uwar da ta haifeshi kamar yadda yake begen Yusuf Gacan Yusuf Kuma zuciyarsa na qoqarin Fashewa Cikin sanyi Ta tsura mai ido Shiko zame hannushi Yayi ya nufi gun Ummi Jikin a sanyaye yace Ummi inajin tsoro Kar randa Ahmad zai dawo garemu Yusuf kuma ya barmu Wlh Ummi Yusuf bai da lfy Ummi fushinki Na cin ran Yusuf Ummi kinsan biyaye Nada matsala zuciya kam ko? Cikin Dan rashin damuwa Ummi ta tabe baki tace Adam ba yanxu ya bar nan ba Ni banga me akayi maiba Baqin halin shi ne kawai ya taso Kai ya jinjina cikin Jawo hannu Aysha Yana zo nan Da sauri Ummi tace Kai Adam sake min Y'a Ka fitanmin daga nan Ba inda zataje Cikin sanyi yace Dan Allah Ummi Dan Allah kiyi haquri Cikin fada tace Adam fitamin daga nan Zaiyi mgn tace Ya isa tafi kawai zamu rufe qofa Juyawa yayi cikin Rashin mafita Da sauri matarsa ta bishi a baya Cikin kula take cewa ya Adam Meke damun Hamma Yusuf din A INA yake Hannuta ya kamo Suka haura saman Yana zomuje kiga halin da Yusuf ke cikifa Suna shiga Adam ya saki hannuta da gudu ya nufi Kanshi ganin yadda yake juyi a tsakiyar carpet din parlon Yana damqe da Mara Sai yunqurin amai yakeyi Kuma ba abinda yake hararwa Itama Amira isowa tai da gudu Tana Hamma Yusuf Shiko Adam jijjigashi yake yana Yusuf Yusuf shi kuwa Sai bishi da yakeyi da fizgar numfashi Da gudu Amira ta sauqo Qasa cikin kuka Take kiran Ummi da qarfi tana Ummi Ummi kixo Wayyo Ummi kizo Hamma Yusuf Sai kuma ta nufi Sade din Abba tana Abba kazo Hamma Yusuf fa bai Da lfy Allah sarki Abba cikin rawan jikin ya fito Yana Amira INA Yusuf din meke damunshi Cikin kukan tace yana parlon baba Ganin ya fito ta kuma yi bakin dakin Ummi tana Ummi wlh Hamma Yusuf baida lfy Aysha dake Konce Gefen Ummi Cikin sauri ta miqe ta zauna Hannu Ummi ta riqo Tana zare ido Tace Ummi Ayyah Ummi kije ki Duba shi Mana Lkcin Amira kuma ta shigo Duk ta rude hannu Aysha ta kamo Tana ja tana kizofa kiga yadda yake Ganin yadda amiran ta rude yasa ta bita Ummi ma ta miqe ta bita a baya Suna fitowa Parlon Abba Na sauqowa da sauri yana Adam dauko shi mu tafi asibiti Dai dai lkcin Su Ahmad kuma sukayi SLM Da qarfi Aysha ta fizge hannuta cikin Na Amira Cikin tsalle da karadi Ta afka jikin Ahmad Ruggumishe tai kamar zata mai dashi cikin jikinta Ba abinda take furtawa Sai Ya Ahmad Na Ya dawo Jin ihunta ya fiddo Maryam a guji Jikin bugun zuciya Tana zuwa kuma Sai tayi tura ta zuba mai ido Sai kawai ta durgusa a gun Sai kuka ya kofce mata Nenne ma Sai Kuka Shiko Ahmad Sai murmushi yakeyi Cikin yanayinshi mai sanyi Yace Ummi INA biyayena Ya fada yana ture Aysha daga jikinshi Gabanta Nenne yaje ya tsaya Sai hawaye kawai a fuskarsa Durqusawa yayi a gabanta ita kuwa dafe kanshi tayi cikin Sauqe ajiyar zuciya tace Allah ya maka aibarka Amin ya amsa cikin Sunkuyar da kai ya isa Gaban Maryam daketa ta rusa kuka ruqqume da dansu Cikin murmushi Ya bude hannushi Murya a saqile yace Ina kikene maryama Na Duba gabas ban ganki ba Na Duba arewa ban gani Jin haka yasa ta taso ta fada qirjinshi Da qarfi ya sauqe ajiyar hrt Yana mai cewa Na godewa Allah daya manike Maryama taho masoiya Sake Maryam yayi ya juya gun Amira daketa sharar qollah Yace Amira ba mgn ne A hankali ta matsoshi cikin Kuka tace Hamma Hamma Yusuf fa Da sauri ya wore idanshi cikin Kaduwa yace Meyasa mu biyaye Na INA yake Cikin kuka tace Yana parlon Abba Allah sarki Ahmad Da gudu cikin Kaduwa ya haura sama Baba bello Na biye dashi a baya Suma su Ummi duk suka bisu a baya Suna shiga Ahmad Yayi Kansu Adam dake tallabe da Yusuf Sai yunquri yakeyi Ga rawan sanyi Hannushi kuwa duk biyu ya damqe mararsa Idanshi A rumtse Ganin Haka ya ruda Aysha Tsoro ya kamata da sauri Jikin tsoro da kuka ta isa gabanshi Da sauri ta kamo hannushi Tana Hamma Yusuf Ka tashi ka bude idonka Duk da wahalar da yake ciki ya gane Muryoyin nan biyu Na Ahmad da Aysha Cikin kaduwa da tsoro Ya bude idanshi a wahala Kan fuskar Aysha ya sauqe ganinshi Baiga Ahmad dake ta gefenshi riqe da hannushi Da iya qarfinshi ya fizge hannushi a NATA Cikin rawar murya Yace sakeni Karki qara tabani Ki barni Bakince Na mutuba bai dameki ba Kunce Dani Na mutu Ahmad ya rayu Bakwa sona Shi kuwa Ahmad yana Sona shine Kadai Mai bin bayana shine mai min uxuri Gashi yanzu Naji Ahmad a kusa dani Na tabbata Kurwar Ahmad tazo Bikon tawa Zanbi Dan Uwana Zan mutu Ku huta da ganina Cikin Sauri Ahmad ya ruqqumoshi Murya Na rawa yace Biyaye Na bude idanka Ba kurwatace ba nine Dan uwanka Ahmad INA Raye ban mutuba Itako Aysha sai Kuka duk ta rude A lkcin da taga Ya sauqe wata iriyar nishi Sai kuma yasake ko inanshi yayi Luf Da qarfi ta fada Kanshi Fuskarshi take jijjigawa Tana ki ranshi da qarfi Tana Hamma Yusuf Ka tashi Wlh bance ka mutuba Ka tashi Ina sonka Kife kanta tayi Jikinshi Cikin tsananin kuka Ta rinqa sabbatu Tana ya Ahmad ka gaya mishi Nibance ya mutuba Dan Allah Hamma Yusuf ka tashi Ummi kixo kice kin yafe mai Zai tashi bazai mutuba Gaba daya Suma tasasu kuka Nenne CE Taxo cikin sanyi ta kamo hannushi Ta Dan matsa Gun baba bello taje Wanda ya zama tamkar an dasashi Tace Suma yayi Jin haka yasa Adam dauko Goran ruwa mai sanyi ya Rina fesa mai a fuska A hankali Ya bude idanunshi A hankali ya tsurawa.Ahmad ido Sai kawai Ya fada jikinshi Ruggume juna sukayi Cikin Kuka tamkar yara Ahmad ba abinda yake dafi Sai Cewa yake Yusuf Insha Allah zamu rayu tare Bazamu qara yin nesa da juna ba Sai indai mutuwar gske ta riskeni Shiko Yusuf Sai hamdala yakeyi Lkci daya kuma Yunqurin aman ya sake Taso mai da sauri Aysha ta kuma fashewa da kuka ta fada jikinshi Tana Hamma Yusuf Ka gafarceni Wlh bansan hakan zai cutar da kaiba Jinta a jikinshi ya angiza Tunanin shi Cikin rawan hannu ya matseta a qirjinshi Murya Na rawa Yace A,ish Ina sonki Fiye da yadda nake son raina Na rayu da sonki a zuciya ta tun bansan kainaba Kefe farinciki Na Kece haske rayuwata kin kasance bugun cuciyata Dan Allah kar ki gujeni Qara matsota yayi ya manta da kowa a gurin Baijin kowa bai ganin kowa a wurin Sai ita Duk ya rude Gaba daya suka juya suka bar parlon ganin Yana mammatse yar matarsa tuni ciwon maran ya fara tsikararsa Suna fita Ya tallabo fuskarta Ya tsura mata ido Cikin rawan murya yace A,ish Kin yadda dani ki yadda da baqoncina cikin rayuwarki Ki taimaka min ki bani Haqqina Idanta ta rumtse cikin Bugawar girji da tsoro ta manna bakin ta kan lips dinshi da suke ta rawa Jin bakinta kan nashi yasa shi kidimewa da gigicewa cikin rawan hannu Ya tura hanna yenshi cikin rigar Baccin dake jikinta A hankali ya sauqe ajiyar zuciya itako tsoro ne ya rufeta jin yadda a cabke....... Ku biyoni page 103 kusha karatu Da ganin salon koyarwar Hamma Yusuf😝 🍇🍇🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👇🏻👆🏻👆🏻 *MI,WASMITI* page 1⃣0⃣3⃣Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 oh amrita shine abinda yusif yake fada yana juyata kamar waina a cikin tanda wani irin nishi yake futarwa kamar tsohon zakin daya shekara beci abinciba aysha kam ta tsorata da halin da hammanta yake ciki ga wani feelings da takeji na tsananin bukatarsa kawai saiji tayi ya sureta yai part dinsa da ita yana zuwa ya azata akan bed ya fara balle riggar jikinsa yai wulli da ita yai jifa da wandon aysha tana gani ta runtse ido kawai sai ji tayi anja rigarta ana shaffo nonuwanta abubuwan da sumafi daukan hankalinsa kenan yana cafkarsu ta saki wata kara data gara fidda hamma daga hankalinsa bakin nan ya kama rawa ba shiri ya cabki bakinta wani irin zazzafan rommans yake mata wanda betaba mata irinsaba tun tana jurewa harta fara maida martani kwata kwata hamma yusif ya fita daga duniyar ya tafi wata hakama aysha wani irin feelings take ji wanda sex kawai take bukata nonuwan nan kuwa sunsha tsotsa kamar za a guntule dan kan kawai asshhh isss washh dinsu kake ji a dakin bakajin komai can ya cabji nononta yana gurnani yana mutsikasu can kuma saitaji dib ya dauke wuta kamar wanda ya suma ya kankameta some munite letter san nan taji ya jata yana fadin amrita allah yai miki albarka kinshayar dani dadin da vantaba shaba a yau a zuciyarsa fada yake a hakama na kere dadina inahga na shiga wan nan korama uhmmm garin dadi na nesa kawai wani killer smile taga yanayi batason me yake tunaniba ita kanta yau ta bukatu da kasancewa da hammanta iya bukatuwa tana wan nan tunanin taji ya sunkuceta sunyi toilet a toilet dinma sunfi 1hour suna abu daya shine murza nono da shansu kamar sabon jariri lol😜 A cikin gida kuwa suna shiga kowa yai bangarensa ahmat tunda suka shiga yake kallon maryam kamar yamaidata ciki su ummi kam da nenne kowa dakinsa yayi sabida sun fahimci abinda yake damun yusif ga kuma ahmat da sukaga yanabin maryam da wani kallo ko ba a cemusuba a matsayinsu na manya sunsan ma anar kallon adam kam yau yasamu damar shakiyanci sai dariya yake kasa kasa yaiwa ahmat sallama wanda har yakai kusa da maryam ya dangi hannunta sunyi daki sai dagawa adam hannu yayi suna shiga ya rungumeta a tare suka saki wata ajiyar xuciya me karfi maryam ta saki kukan murna tana sauke yusif karami a bayanta yai wuf ya karbeshi yana hamdala da allah ya nunamasa kwansa a duniya san nan yaje ya kwantar dashi a gefan bed ya dawo gun maryam yanazuwa yaimata wata runguma yafara yamutsata abinka da gwaron shekara da watanni kisses dinta yake kamar ba gobe itama tana mayarmar ranar ahmat yayi kukan dadi ba a dadi assuba ta gari lovvers Gari na wayyeww gida ya fara cika da yan taya farin cikin dawowar ahmat rabi u usman haidar iyayen kuka kenan har sun fara kukan murna abdull da sadig sai murna ake barinsu kaka innayi da innah da baffa ba magana ancika sai yanzu su hamma yusif suka fitk shida aysha shifa tunda yaji ahmat be mutuba yake jin dum wata matsalarsa ta kyau kana ganinsa kaga sabon ango sai yar ramar da yayi ta azabar ciwon mara daya sha yanazuwa sukai rungume juna shida ahmat da adam suna murna aysha kuwa hannun ahmat taja tana ya ahmad dina wai wacce irin murna ya kamata nayi ne su baki abin magana akai wuff akace party za a hada mana kawai hamma yusif yana zaune yana latse latse a waya kamr hankalinsa baya kansu nan ko komai ake hankalinsa yana kan amrita kai innace muku xan rubuta iya murnar da familys din an sukai a ranar zan iya cika page din nan ban gamaba saidai na takaita ranar anyi walima da ciye ciye kowa yana farin ciki hala aka watse da alkawarin za a je a gyarawa su ahmat gidansu gobe saisu koma taro ya tashi kowa ya tafi yana murna Nima nayi murna da cikar familyn nan Kubiyoni kusha labari yanzu aka fara ?🍇🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👇🏻👆🏻👆🏻 *MI,WASMITI* page 1⃣0⃣4⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Su Abba da su baba bello Duk gidan suna cike Anata hira Har kaka Da Anuty sadiya Suna cikin cikar Farin ciki Ahmad ne Da Yusuf Suka shigo a tare riqe Da hannun Juna Adam Na biye dasu A baya Suka shigo Kan carpet suka zauna Nenne tai murmushi cikin jin dadi tace Yusuf sai yau naga Yelwarka ta dawo Kai ya sunkuyar Cikin furta Alhamdulillah. Baba bello ya Dan kallesu cikin Bada umurni Yace Ahmad Sai Ka shirya Gobe Kuje Yola Dan Goggonku tace Sai dai Tazo nace ta bari Zakuje Dan dama Maryam tunda ta aihu Batajeba Gashi Adam ma zai Kai takwaranka su ganshi Dan haka Ku shirya gobe kuyi sammako Kuyi Yola. Cikin Farin ciki Maryam ta miqe tana Yauwa Baba ni barima naje Na shirya Amira ma miqewa tai Gamida miqewa Aysha. Ahmad Qarami tana Aysha karbeshi Nima naje Na shirya mana Ture Dan pilet din gabanta tayi Wanda take cin Inabi da tupa A ciki Ta kalli Amira cikin Harara tace Toh ai nima zanje Nai shirin. Ki bawa Ummi shi Cikin, dry Amira tace Toh fa ai banji Ance dake za ajeba da kike wani cewa zakije kiyi shirin, Cikin harara tace toh ai Sai ki hanani Sai kuma ta juya Gun baba cikin Sanyi tace Baba INA nima zanje? Naje Na shirya ko? Ido ya Dan zuba mata Sai kuma ya juya ya kalli Yusuf da ya hade fuska Cikin Dan murmushi yace In mijinki ya barki zakije Mana Ki tabbaya in ya barki Sai ki shirya. Baki ta tura cikin Takaici Tace toh Baba ai in kace naje dai shi kenan Ko ?Hamma Yusuf, ta fada tana Kallon fuskar Yusuf Din, Rai a hade ya qara yamutsa fuska yace Bazaki jeba, Ido ta zaro cikin Hatsala Tace Ni da gidanmu kace bazanje ba ? Bai kulata ba Sai ta kuma hararanshi tace Wlh zanje Haka kawai Kowa zaije saini Kace ba zanje ba Ko kallonta bai kumayi ba. Sadiya CE ta jawo hannuta Tauzanar da ita cikin rada Tace ke Ki nitsufa a gabansu Abba kike Kinga zai daureki da jijiyoyinki Kimai rashin kunya a gabansu Waya CE miki haka ake tabbayar miji Abu bare uwa uba Namiji irin Yusuf Basa son izzah Ki kula Kiyi lup ki nema a tsanake cikin faran ta mai Sai ya barki Tura baki ta kumayi Cikin sanyi tace Ayyah Hamma Yusuf Dan Allah ka barni naje kaji ko ? Miqewa yayi cikin Isa Yace Bada yawuna ba. Hannu Ahmad yaja suka fita Adam ko karbar Ahmad qarami yayi ya nufi gun matarsa Itako Aysha Gun Ummi ta matsota cikin Shirin zubda qollah tace Ayyah Ummi Dan Allah Ku barni muje da yan uwana A hankali Ummi tace Aysha Bani da ja da abinda Babanku yace Ki nemi yardar Hamman naku. Miqewa tayi Cikin zubda qollah Tace Shi kenan kuma Sai ace Sai Hamma Yusuf ya yarda zanje wani wurin Bayan kuma ansan Dama kullum zagina yake Na fiye yawo Sadiya ce ta bita dakin Ummi Kan gado ta sameta tana kuka tsaka ninta da Allah Dan Aysha in taji Tafiya gaba daya jikinta rawa yake Bare wannan tafi yar da za ayita cikin farinciki Cikin sanyi Sadiya tace Aysha tashi Tashi kiji Kinji ko? A hankali ta tashi Hannuta ta riqe cikin sanyi Tace Tashi ki ji INA kina son Zuwa yolo? Ehh ta bata amsa da sauri Murmushi tayi cikin dabara tace Jekiyi wonka Kizo Insha Allah zakije. Cikin murna tace Dgske Anuty Ehh ke dai jekiyi wonka To tace cikin Jin qarfi quiwa ta fada toilet Wonka tayi mai rai da lfy Tai buros Tana fita Anuty Sadiya da kanta Ta rinqa Murjeta da mayuka da turaruka Cikin Hikima ta gyara ta tsaf Da kanta ta zabo Mata kayan Bacci Ita kuwa Sai dry take tana ke dai Anuty kina son gashin nan nawa kuma kema kina dashi Dry ta danyi lkcin Da ta miqa mata wasu riqan Bacci Farare masu ratsin ja ja Masu taushi da laushi Sai qamshi suke fiddawa mai dadin shaqa Rigar yar yelo yelo bata da kauri ko kadan Daga gefen Hanna yenta kuma ragane Hannu kuma mai Dan guntune Dan wondon kuma iya karsa cinyarta. Karba tayi ta saka cikin Lumshe ido Tace Kai suna da kyau banma taba sasuba Ya Hydar nane ya kawo minsu Ga yadda suka min kyau Anuty Dry tai cikin Kada kai tace Aysha ai dama ke kekkyawa ce Qara dauko Turaren lailatu sahra tai ta fesheta Dashi Cikin Fahimtarwa Ta Miqa mata Hijabin da ta jiqeshi da qamshi Tace sakashi Kije Gun Yusuf Ki qasqantar da kanki Karkiyi mgn cikin izza Ko fushi Kiyi mai mgn Cikin Neman Alfarma Ki tausasa laffuzanki Na tabbata zai barki kije Da sauri Ta koma kan gado ta konta Cikin tura baki Tace wannan mugunne zai yarda cikin sauqi Ni bazanjeba! Cikin sauqe ajiyar hrt taja Hannuta tace Kije Insha Allah zai barki In kuwa bai barkiba Na miki alqawarin Zan nace Sai ya barki Amman dai kije din. Miqewa tai cikin Cewa shi kenan tunda kince zaki tayani... Tana fita itama Sadiya ta fita ta nufi part din nennenta 🌹🌹🌹🌹 Tana fita Ta nufi part dinsu Cikin jin dadin iskar dake Busawa Da alamun hadari Ga walqiya dake haskawa daga qasa alamun gagarumin hadarin Sukuwa dama su Yusuf Suna fita Maryam ta biyosu Cikin Dan sauri sauri Tana ya Ahmad Yana jin muryan ta Ya tsaya cikin Jaye hannushi daga cikin Na Yusuf Din tana zuwa Ta matsoshi cikin Sanyi ta kamo hannushi Tace ya Ahmad Na shirya kaya da yawa ko in munje zan dade ai? Matsota yayi cikin Shafa fuskarta yace Bazan iyaba maryama INA buqatar ki Ni wlh tafiyarba da za,a barta Sai Next week A barni da iyalaina naji duminku kuji dumina. Shi kam Yusuf ganin Sai shirin shafe juna suke ya sashi Wucewa cikin Cewa Shi dai biyaye bazai canzaba Yana shiga part Dinsu Dakinshi ya wuce Tartare dakin yayi Ya gyareshi tsaf ya Kuna A,C Ya feshe dakin da Turarukan daki. Dakin yayi ras Komai Na dakin Farine da ratsin Ja ja Hatta bedsheet din da blanket Din da carpet din tsakiyar dakin da labulayen Ya bude widdunan da labulayen Iskar daminan Mai qamshi Na ratsa dakin Ga qamshin furannin Cikin garden dinsu Sai kukan tsuntsaye ke tashi, Lkci Daya yanayin Ya canxa tunanin shi Da gabban jikinsa Gaba daya ba abin da yake muradi Sai Ya jishi cikin jikin A,ish Dinshi Surar jikinta kawai ke rudasa Cikin tasowar Wata muguwar Sha,awa Ya rege kaya Jikinshi Ya fada toilet Wonka yakeyi Yana tunanin Ya zaiyi ya samu ganinta Da gyer ya fito Yana fita Daure da towel a qugunshi Ya rinqa Bin jikinshi Da turaruka Shi dama Yusuf ma abocin son qamshi ne Gashin kanshi ya rinqa gyarawa Yana zaune kan Dressing stool Ya Na shaqar qamshi Sai lumshe ido Yakeyi A hankali ta tura qofar cikin yin slm Idanshi a lumshe ya sauqe wata sassanyar ajiyar hrt Qarasowa tayi Cikin Dan daure Fuska Shiko Ta jikin madubi ya Xuba mata ido Farin cikene damqan cikin ransa Ji yake tamkar ya rinqa buga tsalle ya ruqqumota Amman bai son ta rainashi Gwara ya tsare gudun kar ta ganoshi Ya Dan harareta Cikin isa Ya miqe Ya koma bakin gado Ita kuma Matsoshi tayi gunshi Cikin jin haushin yadda ya wani Share ta Murya kamar zatayi Kuka Tace. Ayyah Hamma Yusuf Dan Allah kayi haquri ka barni inje Yolannan Baki ya tabe Cikin mugunta yace Ban aminceba. Sai dai in satar hanyan zakiyi yadda kika saba Sai kije keda mahaliccinmu Qara kontar da murya tai cikin Kauda kanta Dan Sam bata son ganin qirjinshi A hankali Tace Ayyah Dan Allah fa Hamma am Ido Ya tsurawa bakinta Da yake sheqi Cikin fara canxawa Yace Nace bazaki jeba ko. Ita kuwa Zuwa Yanxu ta gama qulewa Cikin sanyi ta miqe Baki a tuntsure Tace Kada ka barni din mana Dan kaga amsa nazo Na tabbata yeka shine kake min wulaqanci Ai ni dama Na sani bazaka barni ba Juyawa tayi cikin Takaici Tace Ni wlh in Dan tanine Baka isa Na nemi ixininka ba, Ta juya zata fita Ya miqe cikin zafin nama Bakin qofa yaje ya rufe qofar ya Juyo Gunta Rai a bace Dan har cikin ransa yaji zafin furucinta Fizgota Yayi cikin Zafi Ya turata jikin Gini Cikin fada Yace Ni kike cewa ban isaba? Ni dinne ban isanba? Jin yadda ya matsota Yasa ta rinqa Juya kai cikin Zare ido alamar a a Zare hijabin Jikinta Yayi Cikin Hada fuska Yace a yau dai zan isan zaki tabbata ni isheshene Yana cire Hijabin Ya tsura mata ido Cikin Daukewar Numfashi Ya jawota Cikin qirjinshi Ya rinqa shaqar qamshi jikinta Dana iskar damina Ita kuwa Tureshi takeyi Cikin Cemai Ni ka sakeni Baki a mace Yace A,ish Bata kulashiba Sake Hanna yenta yayi Cikin Rawan jiki Ya daura hannushi kan qirjinta Boturan rigar Ya fara ballewa Da sauri Cikin fushi Ta huge hannushi Tana me hakan Ni banson Jawota yayi Cikin rawan murya Yace Ni kam INA so Dan Allah Aysha Kar ki cutar dani a wannan Daren jumma an Ki barni Farin cikina ya cika Jawota yayi Bakin Gado Ita kuwa Tirjewa tayi Ganin Haka Yasa Cikin Garfi ya Fizge rigar Hannushi ya daura kan Qirjinta Bres Dinta Ya cabe Cikin wani irin yanayi Ya rinqa matsarsu Ita kuwa hannu tasa zata tureshi Ganin haka yasa cikin Sanyi ya kamo hannuta Cikin Fita hayyacinsa Ya konto towel din jikinsa Hannuta ya jawo zai daura Kan mararshi Jin haka yasa ta tureshi da sauri Taja da baya ta fada kan gadon Ido a juye ya Haye gadon Jawota jikinshi Yayi cikin rawan Murya yace Dan Allah kiyi haquri ki tausaya min Cikin halin takaici tace Ni ka barni Tashi yayi ya zauna Cikin sanyi ya komo hannayenta Ya zaunar da ita A hankali ya manna bakinshi kan NATA Cikin Wani salo Ya zura mata harshensa cikin Bakinta Bata kamata sannan bata janye jijinta ba Hannushi ya daura Kan qirjinta Ya cabke Bres Dinta A hankali ya rinqa Shafarsu Yana murza Kansu Lkci daya ya sauqe mata Wata irin muguwar kasala Da shauqi Gaba daya taji gabbanta Na buduwa suna karbar saqonin Hamma Yusuf Din nata A hankali ta daga hannayenta Cikin macewar jiki Tayi woni irin Miqa gaba daya Ta narke Cikin jikinshi Shi kuwa sai Sarrafa dukiyar Fulaninta yakeyi A hankali ya gangaro hannushi Kan mararta Cikin wani tsoro Jin hakan Yasa Aysha Ta saki wata maryaniyar ajiyar hrt Cikin Kidima ta Cabki harshen shi dake Cikin bakinta Ta fara tsotsa Cikin sanyi da lumshe ido Dan kuyarshi takeji Gashi wuta a kunne Gakuma suna saitin miro Gaba daya ta qara birkita Hamma Yusuf Dinta Sai karkarwa yakeyi da nishi A hankali taji Lips dinshi suna motsawa alamar sun fara kadawarsun Cikin sanyi ta zare harshensa ta laso lips din nashi Shi kam ya gama kadewa Qirjinta kawai yake kadawa Ya tsurawa fuskarta Ido Jin ta Dan sake shine Tare dasa hannu bibbiyu ta kare fuskarta Yasashi Kontowa Kanta Cikin kidima ya manne bakinshi Kan bres Dinta ya Rinqa Sha tamkar yaro Ya cabke dayan kuma da hannushi Ita kam Aysha A hankali Take Kiran shi Cikin rawar murya tana Shiiiihhh tana mimmiqewa Ta hura mai iska a kunne Cikin sanyi da sarqafewar murya Tace Ham Hamma Yusuffffffff ᴀʙᴅᴜʟᴍᴋɪʙᴀʙ.ʜᴇxᴀᴛ.ᴄᴏᴍ Sai ta kuma lumshe ido Ta Dan qara tura mai qirjinta Shi kuwa ya gama zaucewa Ba abinda yake buqatar Sai Kasantuwa tare da ita So yake yaji jikinshi Cikin nata Cikin qurnani da nishi Da shan yaji Ya rinqa Mutsutsukata Gaba daya ya gigice ya gigitata Tasowa yayi cikin Qarfin hali Ya kashe wutar Itako gaba daya take son tattaro qarfinta Amman ta kasa Sai jinshi Tayi Yayi mata rumfa da qirjinshi Jin ko INA nashi a fili Gashi itama duk ya rebata da suturanta Yasa tsoro ya diran mata Cikin firgici Ta kamo hannushi Tana karkarwa Tace Hamma Yusuf qirjina Ciwo Bayana ciwo Ka sauqa kamin nayi Cikin kidima Yasa hannushi ya lalubo bres Dinta ya rinqa shafawa Murya Na rawa Yace . Dan Allah A,ish Ki daure wlh Bazan wahal dakeba Plss matata ki agazamin Walahi zan iya rasa raina. Kuka ta saki cikin tsori ta Tace A a Hamma Yusuf wlh Bazan iyaba Ni ban tababa Cikin Fizagar Numfashi Yace Na sani A,ish nasan Baki taba ba. Wlh zan miki a hankali Bazan wahal dakeba Jawo hannuta Yayi ya daura Kan Mararsa Yana kinji Halin da nake ciki Janye hannuta tayi Cikin Tsoro Jin abinda yake Qoqarin aikata mata Gadan gadan Ya haye ruwan cikinta ya mata rumfa da qirjinshi Jin zai rabata da budurcinta Yasa ta dage ta tureshi Cikin kuka Tace Bana sonka ni bazan iyaba Kaima Bani kake soba Yarintata kakeso Da qarfi ya rufe mata Baki Cikin Rawan jikin da murya Yace Wlh Ke nake so Aysha Ba yarintarki nake Sha,awaba Ke zatinki nakeso Kuma sonne ya kawo Sha,rawar Ki yarda dani Kin sani da yarintarki nakeso wlh da Na Dade da cimma burina Cikin Kuka tace Wlh Hamma Yusuf yaudarata kakeyi Baka taba sonaba Koda a matsayin yar uwar ka bare a matsayin aurataiya A duniya ba wacce ka sana kamar ni Cikin Kuka kamar yaro Ya riqi hannuta Ya kafa guiwarsa A qasan gadon Ya daura kanshi Kan cinyar ta Ya fara mgn cikin kukan sosai Da rawan murya yace wlh Shaquwa zata sanya Yarda Idan nace miki ke kadaice a zuciyata Kuma ke Na zaba ki gaskatani ki bani dama Qara kontar da kanshi yayi Yaci gaba da cewa In na fada miki To Kiyarda mini Duk tsanani da wuya Zana sakarmi ki so😍 Kiyo riqo kar naga Kin gajiyar Indai kikai Haka so Ya habbaka Zamuga ken tfy Wlh A,ish Da shaquwa Aka samu yarda harso yasanyanmu kama da juna Tureshi tayi Cikin rawan jikin Tace Hamma Yusuf fada kaiwa kakeyi Cikin Qara matsota da rarrafe Yace Wlh Shi bugatan da nake ciki in Ya tsananta Zai iya taba qoqolwata Na qaqauta dakisan Nufuna Sirrikan cikina da zuciya ta Nake sheida miki Ki taimaka Ki ka war min Da buqatata Dan duk kan alamar Kin qullaceni Kina fushi dani Aysha Bazan ga ken yanayi ba Tunda byeka Ra ayi Dole Na qarfafa So nayo Miki Riqon da ba shayi In kauda kurenan Na baya dan Na faranta miki Ni nace miki Gwarai INA sonki Karki qi yarda Hannuta ya daura kan Qirjinshi Yaci gaba da cewa Me kike so Ya zamo alama Dan a kawai sabon Inko yarda kike buqata to ki sanya rebo Danke gudace Daba kamarki A zuciya ta da rayuwata A hankali kalamanshi suka rinqa Ratsata jikinta Yayi sanyi Jin tayi shiru Yasa Ya matsota Ya tura hannushi Kan bres Dinta Ya musu wani irin Cabka tare da sauqe ajiyar hrt Tureta yayi Ta koma kan gadon cikin Sheshsheqar kuka Ya haye Kan gadon Jawota... ⒽⒶⓊⓈⒶ ⓃⓄⓋⒺⓁⓈ ⓈⓄⓀⓄⓉⓄ ⓌⒽⒶⓉⓈⒶⓅⓅ ⓃⓄ: 07068808039 ⓌⒺⒷⓈⒾⓉⒺ : ⒶⒷⒹⓊⓁⓂⓀⒾⒷⒶⒷ.ⒽⒺⓍⒶⓉ.ⒸⓄm My sister nasan daga nam zaki fara karatun wannam labarin HUSSAINA BELLO FROM UNGUWAR ROGO 🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *NAYI NADAWA* 👆🏻👇🏻👇🏻 *MI,WASMITI* page 1⃣0⃣5⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Jawota jikinshi Yayi cikin Rawan murya Yake Bata haquri Da furta Mata kalamai Masu tsadar Samuwa Daga gareshi Hannushi kuwa Na kan Bres Dinta Itako Cikin tsoro Ta janye jikinta daga Gareshi Cikin duhun Ta lalubo Hijabinta Shi kuma Miqewa yayi Ya kunna wutan Gunta ya nufa Bayan ya daura Towel a jikinshi Matsota yake Tana kaucewa Har ya isa Gareta Hannushi Yasa ya tallabe fuskarta Cikin Sanyi Yace Dan Allah karki gujeni a wannan Daren Plss Ki kusan to gareni Wlh zan cutu Matuqar kika barni Cikin halinnan, Zamewa tayi gefe Da sauri Ta bude Qofar ta fice da sauri sauri cikin tsoro ta nufi cikin gidan Dakin Ummi ta shige Tana mai sauqe ajiyar hrt A hankali ta fada kan gado Ganin ba kowa a dakin yasa taji tsoro ya kamata Cikin tunanin. Tana zubda qollah Dan tabbas Hamma Yusuf Ya bata tausayi Hamma Yusuf ne Harda Kuka mutumin Da kukansa ke Da tsada Mutum mai Dauriya Da jarumta Gashi har Kuka yake Da hawaye tamkar Yaro, Shi kuma Binta yayi A baya Yana A,ish Ki dawo Dare yayifa A parlon ya tsaya ganin Gudunshi takeyi Durqu shewa yayi Kan carpet Ya rinqa Rawan sanyi Lips inshi Sai Bari suke Har haqoranshi Na bugar juna, Sai Hahhhhhh huuuum shiiihhh ahhyshihhh ykeyi Duk tsikar Jikinsa ta mimmiqe Kanshi Sai Sarawa yake Gau gau Lkci Daya zazzabi Mai zafi Ya rufeshi Mararsa ta rinqa tsikararsa Ba abinda yake Sai. Surutai Duk da iskar damina dake kadawa Ga walqiya Amman Sai zufa ke ketomai A fili Yake Cewa Aysha Meyasa, meyasa Kika gujeni A lkcin Da nake da buqatarki Ya zaki gujeni a lkcin Da kika, zama Jinin jika Cikin rawan murya yace Bazan iya Haquri ba, Cikin wahala Ya yunqura, Ya gyara Daurin. Towel din jikinshi Fita yayi Cikin sanyi yake Takawa har Ya isa Cikin parlon. Ummi shiru ba kowa Ga duhu Sai Dan haske, A can cikin bedroom Dinta A ranshi Yake tunanin Ummi kam dai bata kwana dakinta Sai dai Allah. Yasa Anuty Sadiya Bata dakin' Cikin zulimi Ya tura Qofar a hankali ya shigo Can ya hanqota kwance Cikin blanket Ta jawo pillows ta Tura kanta a ciki Wai duk" Kar taji tsawa kar taga walqiya. Jikin window Yaje ya bude. Window Ya tartare labulayen Iska ta rinqa Busowa Lkci daya. Kuma Ruwa ya Fara sauqa Cikin sanyi Ruwane mai qarfi Sai dai a hankali yake Sauqa. Ba abin da ake yi Sai walqiya, Da iska mai sanyi Sai sauqan ruwa.shuuuuu shuuuuu" a hankali. Ya qarisa. Kan gadon Zama yayi. Cikin rawan hannu Ya janye blanket din Ya ture Pillows din. Lkci. Daya kuma. Aka saki wata walqiya. Mai haske gske. Sai tsawa kuma ta biyo. Bayan walqiyar. Tsoron ya hadun mata Cikin, Firgita ta bude. Idan ganin.shine Yasa tai saurin.tashi tana jaa.da baya Hannuta, ya jawo Ya fizgota jikinshi " Matseta yayi da qarfi, Tare da sauqe ajiyar hrt. Cikin. Daqilewar Murya, Yace INA zakije' Meyasa kike gudana Mesa bakya tausaya min' Kinfi son Na cutune. Kai ta rinqa kadawa' Tana ni banson Ka sakeni, Qara matseta yayi Ya tallabo kanta Lips Dinta Ya laluba ya rinqa Tsotsa cikin nauyin zuciya' Hannushi kuma.yasa ya zare hijabin Tureta yayi Kan pillows ya kontar da ita Cikin rawan jiki' Ya haura kanta, Hannushi yasa ya ware Nata ya dannesu Kanshi ya, daura kan Qirjinta.bres Dinta ya cabke ya rinqa tsotsa kamar cikin Gigita" ita kam tuni ta nemi idanta, da bakinta kuka takeyi Sosai tana Wayyo Allah Na Wlh bana so ka barni mugu kawai " Bai Kulata ba Dan hankalinshi bai jikinshi Da qarfi ta yunquro jin ya taqwara qafafunta ya waresu ya shige tsakiyar cinyarta yana cishirin shigarta riqe hannushi tayi duka biyu' Cikin kidima da tsoro da zare ido Tace, Wayyo Allah Wayyo Hamma Yusuf Dan Allah da Manxonsa ka barni Kayi haquri plxxx, Na tuba Hamma Yusuf ka tausaya min Cikin kidima da rawan jiki da carkewar murya. Yakai bakinshi dai dai kunneta Cikin sarkeqar murya. Yace Bazan iyaba ki tausaya min Kiyi haquri ki nitsuba karkiyi naji miki ciwo Plxxx A,ish Ki nitsuba bazan wahal dakeba Kiyimin agaji Hannuta tasa tana ture qirjinshi Tana ,a,a. Dan Allah Hamma ka tausaya min Qara sake nauyin qirjinshi yayi kan nata. cikin Karkarwa ya ya matso da bakinshi kan kunneta a kideme yake Furta mata Addu,arga. (بسم الله الله‍م خنبنا الشيطاب وجنب الشيطان مارزقتنا) Cikin Kuka sosai take cewa a,a ,a,a Hamma Yusuf. Yusuf kam ya rikece ya fita haytacinsa baiji bai gani Shiyasa bai Jinta bare ya tausaya mata, Allah sarki Aysha azabar da take ratsata tasa ta Cillah qara mai qarfi Cikin damqe damtsen hannushi Cikin kuka sosai Tana Wayyohhhh Hamma Yusuffffffffff Zan mutu Hamma Yusuffffffffff ka kasheniiihhh Zafi zan mutu Shima Yusuf Kuka yakeyi tamkar yaro Kuka yake cikin Fitar hayyaci A haka ya rinqa Haqarta har saida Ya maidata cikekkiyar Mace, Qara ta saki Cikin qaqameshi Ta tura kanta cikin qirjinshi Hannayenshi ta qaqqame Shi kuwa Yusuf Cikin Shiga wota sabuwar Rayuwa da duniya Jinshi yake a sama Ya kasa gane wanne hali yake ciki Cikin kuka Ya zurma cikin duniyar ma,aurata Ya kamo tamkar zaucecce Ya rinqa zuba mata Kirari yana Aysha kece mace daya tamkar da dubu Kece Farin cikina kece rayuwata Kin kasance bugun zuciya ta In bakya tare dani cutuwa nakeyi kece kadai mai iya sani nishadi kin canzamin rayuwa kin jiyar dani dadin da ban taba jiba kece mai iya kawarmin da qishinahh" Ita kuma Aysha Tuni ta fara Dauke wuta Wasa wasa Yusuf Ya kasa control Din kanshi Ita kam kuka take har muryar ta ta dashi. Cikin lkci Daya Numfashi ta ya fara Carkewa Shiko bai bartaba har saida ya samu. Cikekkiyar gamsuwa Lkcin daya Ta sauqi wani nannauyan numfashi Shi kuwa Da garfi ya cakumota ya ruqqumota Cikin kuka sosai Ya zame Jikinshi Ya tallabota ya daura ta Kan qirjinshi Cikin Kukan Yake Fadin Aysha Ngd Aysha kin gama min Komai Aysha kinmi Kyautar abinda yafi komai tsada a gareki A,ish Me zan miki a duniya Na biyaki A,ish Kin gama da zuciya ta Yau kinsani cikin Farin ciki Kin gama min komai a rayuwa Hannushi daya ya daura kan bres Dinta yana shafawa yana sauqe ajiyar hrt gamida cewa Allah ya miki albarka Ita ko Aysha sai Wani irin kuka take mai tsuma zuciyar mai sauraro Gaba daya jikinta ya sake ko yatsarta bata iya motsawa Dan muryar ta ma kab ya bace Dan ta gama Wahala Lkci Daya zazzabi mai zafi Ya rufeta Sai rawan sanyi Takeyi Shima Yusuf tuni Zazzabin ya rufeshi Sai rawan sanyi yakeyi Cikin Rawan sanyin Ya yunquro ya Dan qyara mata konciya Tashi yayi cikin Rufewan ido Ya daura towel Din a jikinshi A hankali ya rinqa dafe Gini ya fta ya nufi part dinsu Dan jin Ana kiran sallah Gashi dagashi Sai towel Gashi duk jikinshi ya baci Kunya yakeji kar Ummi tazo ta sameshi a dakin shiyasa ya fice da shirin Yaje yayi wonka Ya Sa kaya ya dawo Ya gyara yar matarsa Amman INA yana zuwa dakin Jiri ya fara dibarsa Da gyer yayi wonka yana fita Ya kasa tsayuwa Gaba daya Sai rawan sanyi yakeyi, Dole ko sallah A dakin yayi yana idarwa Ya zame kan carpet din ya konta Zazzabi ko yace Bismillah Sai Jiri Yanaji yana gani Ya kasa tashi So yake ya ganshi gashi ga Habittin shi ya bata kulawa Ya ruqqumeta taji dumin jikinshi Amman ya kasa" Ita Kuwa Tana jin matsishi Yabar dakin Ta sake wani sabon Kuka So take ta tashi Amman ta kasa Shiyasa ta koma ta yi lub Tana mai kukan azaba da wahala. Ummi kuwa Tana tashi Ta sauqi qasa Dakinta ta shiga Cikin Sanyi ta matsota Kan Aysha. A hankali tace Aysha, Ke Aysha Tashi kiyi sallah Yau kuma kin makara ko,? Rufe idanta tayi Cikin azaba da kunya Taci gaba da Kuka Ummi bata jin kukan samida muryar ta ta dashe Har ta juya zata tafi Ta kuma dawowa tana Aysha ki tashi fa kar nasake zuwa baki tashiba Zata juya Aysha ta daqo hannuta cikin wahala ta riqo Hannuta Sai kuma kawai ta fashe da kuka Da sauri ta sunkuyo kanta Cikin mmk da tsoro Tace Aysha meke faruwa Meke miki ciwo Ita dai Sai kuka Jan hannu nata tayi cikin cewa tashi ki shirya mu tafi asbiti Da qarfi ta saki qara Tana wayyo Ummi bazan Iyaba Cakin mmk ta kalli inda ta Dan janye tan jinine gaba daya a wurin Lkci daya Ta gano halin da yartata ke ciki, Cikin Bacin rai Tace Yanxu Fisabilillahi Wannan wanne irin rashin Imanine da tausayi Komawa tai ta kamata ta jingibar da ita jikin gadon Towel ta dauko mata Cikin tausaya mata Allah sarki Ummi harda Qolloarta Dan ta tausaya mata sosai Miqa mata tayi ta shige toilet Ta hada mata ruwan zafi Ta fito Ta tallabeta suka shiga Ita ta taimaka mata Ta gasamata jikinta Sannan tai wonka Suna fita ta taimaka mata ta ziramata dogon riga. Tea ta hada mata Ta kawo mata bayan tayi sallah Kuma duk abinda take idanta a rufe yake Sai qollah dake bin gefen idon Sai tai Dan qara tace Ummi bazan iyaba komai ba Ummi qafafuna Cikin rarrashi Tace kisha tea Aysha Zamu tafi asbiti Kinji ko Da gyer tasha tea din kurba 3 Tace amai takeji Ummi kam duk ta ji tsoron yadda take rawan sanyin Usman ta qira yazo ya kaisu Asbiti Bayan sun ga shiryawa wa Sadiya takuma kira suzo su tafi tare Su biyu suka tallabeta suka fito da ita A parlon Sukaci karo Da Usman cikin Tsoro da tausayi ya matsota yana Sister me ya sameki Ummi mene ya sameta Cikin Dan badda abin Sadiya tace Ba komai jirine ke damunta Shiko Yusuf sai yanxu Jirin ya Dan sauqa Sai dai zazzabi kam nanan daram Ga ciwon kai Miqewa yayi da gyer ya shirya cikin Riga da wondo farare tas Turare kawai ya Dan pesa ya nufi part din umminshi cikin dauriya Dan kanshi kamar zai dare, A dai dai lkcin Da ya shiga a lkcin Aysha dake hannu Ummi Tai luuu da jiki ta sake a jikin ummin gaba daya suka nemi faduwa A tsorice Ummi ta riqota tana jijjiga Ganta tana Aysha Aysha bude idan ki Shiko da sauri Ya qarisa gunsu cikin Sunkuyar da kai gwayar ido a boye Ya tallabota jikinshi A hankali Ummi ta zame ta matsa gefe. Shiko, cikin sanyi yake Kiranta A,ish Amman INA Sai qara sakewa tayi a jikinshi lkci Daya tai luu da ido A tsorice Usman yace Hamma Yusuf ta sumafa sumatayi Ummi ma matsota tayi cikin tsoro tana Aysha Bude idanki Duk sun rude Shiko Yusuf Cikin far gaba ya qara tallabota Ya ronqofo ya zauna Gami da jingina da jikin Kujera Hannushi yasa tallabo kanta Cikin kula ya rinqa Dan juya kanta Yana Aish Ki bude idanki Ki tashi Karkiyi min haka Am so sorry my Habitti Sadiyace ta debo ruwa da sauri tazo tana gashi Yusuf ka yayyafa mata Ummi Kuwa hatsala tayi tana Ai Rashin imani ne wannan da qarfi hali Ka bamu yarinya mu tafi asbiti ka tsaya sakarci Sarai yasan Ummi haushinsa takeji Shiyasa cikin Boye idanshi ya sunkuyo Bakinshi ya manna Kan hancinta ya rinqa Bata numfashi Sa har zuwa Dan wani lkci A hankali Ta Dan yunquro cikin Dan tari da kuka Tana Wayyo Hamma Yusuf Dan Allah kayi haquri Na tuba Ita kam Ummi juyawa tayi ta fita Shiko Usman ganin kallon da Yusuf yamai Ya sashi fita yana Ni ba ruwana bare a harareni Cikin Sanyi Ya qara mannata jikinshi Gami da qara jingina da kujera Cikin sanyi Yace Anuty Sadiya A Dan hada min ruwan zafi Toh tace gamida Juyawa tayi Kitchen Itako. Aysha Kai ta dago Murya Na rawa tace Dan Allah Hamma Yusuf kayi haquri Hannushi yasa cikin taushi ya share mata qollah Cikin ajiyar hrt ya Manna bakinshi............. H̷A̷U̷S̷A̷ N̷O̷V̷E̷L̷S̷ S̷O̷K̷O̷T̷O̷: W̷H̷A̷T̷S̷A̷P̷P̷ N̷O̷: 07068808039 W̷E̷B̷S̷I̷T̷E̷: A̷b̷d̷u̷l̷m̷k̷i̷b̷a̷b̷.h̷e̷x̷a̷t̷.c̷o̷m̷ ᴀʙᴅᴜʟᴍᴋɪʙᴀʙ.ʜᴇxᴀᴛ.ᴄᴏᴍ ?🍇 *NAYI NADAMA* 👆🏻👇🏻👇🏻 *MI WASMITI* page 1⃣0⃣7⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 ```Kuyi haquri masu karatu Kunji ni shiru Na tsawon 4 days Wlh biki mukeyi Amman yanxu insha Allah zamu miqe har qarshe Dan Allah masu Nina ta prvt Kuyi haquri wlh abinne yamin yawa bazan iya binku daya daya ba in tura muku ta prvt dinba Ku rinqa binmu ta group Wlh baa wulaqanci bane``` Cikin riqarta ya rinqa shafa Cikinta Yana sauqe ajiyar hrt Tuqi yake Amman gaba daya hankali shi bai kan titin. Ido ya tsura mata cikin Raunin murya Yace ' Aysha Menayi miki haka mai tsanani Da kika kasa yafemin Hannuta ya kuma kamowa ya matse Cikin taushi ya jawota jikinshi Yaci gaba Da cewa ' Dan Allah Ki tausaya min Wlh bazan iya jumre rashinki a kusa daniba Plxxx ki kijiqaina. "Ita kuwa tureshi takeyi tana janye Jikinta daga gareshi Tana ' Ni ka sakarmin hannu kuma ka maidani Gida. Sake hannun nata yayi Yaci gaba da tuqi Ba tare da yace Mata komai ba Tafiya suke cikin Dajin Gembu Wanda duk Wanda yasan Gun yasan hanyace Mai cike da tsaunuka da tsirrei Da qoramai masu Gudana Qa sanyi dake ratsa illahirin Wurin sanyi ne sosai ta yedda daga nesa zaka hanqo tamkar Hayaqi ke tashi Sanyin ya hadu da sanyin A,C Ga qamshi dake ratsa su Na furrai Da turaren jikinsu Lkci Daya nishad'i Ya rinqa ratsa zuciyar Yusuf Tuqi yake Amman idanshi a lumshe Sai sauqe ajiyar hrt Yake Yana murza siteri Tuqin yake cikin qworewa da haddace hanyar Ita kuwa Aysha ido Ta tsura mai ganin yadda yake tuqi ido a rufe Sosai Hamma Yusuf yacika duk inda Namiji yake kaiwa Tabbas Hamma Yusuf da banne a cikin maza Haka take ta rayawa a ranta Tsajenshi ta kuma tsurawa ido Yayi luf gwanin Sha,awa Lkci Daya kuma ta saki Qara gamida Bubbuga cinyarsa ganin Motar tayi Cikin Tsaunuka Tana 'Hamma Yusuf Kana tuqi kana baci Dan Allah ka bude idanka So kake ka kasheni ne " bai kulata ba bai kuma bude idon ba Shiyasa ta qara qwagumo shi Tana 'Wayyo Hamma Yusuf Ni ka sauqe ni Dama ka d'auko ni ne Dan ka karni. A hankali ya bude idanshi Ya Sa hannu ya qara jawota jikinshi Yasa hannu daya kuma yana tuqi Kanta ya daura kan kafadarshi Hannuta kuwa Ya danna tsakiyar cinyarsa A tare suka sauqe ajiyar hrt Ita Na tsoro ne Dan har ga Allah Yanxu tsoron sa takeji Bare data ji Inda ya tura hannunta Shi kuwa Wani irin sanyi yaji Da Shauqi Shi yasa shi Ajiyar hrt Hannushi Ya tura cikin Qirjinta Yana son Lalubo Bres Dinta Amman yar rigarta ta hanashi sakewa Lumshe idansa yayi cikin Isa yace 'Ki cire rigar nan Ido ta zare cikin Tsoro tace Hamma Yusuf A cikin Motofa Tuqifa kakeyi. ' Ehh Na sani ya bata amsa cikin Rawar murya Yaci gaba da cewa ' So nake Na samu Nitsuwa Hankalina Bazai dawo jikina ba har Sai Na samu abinda ke damuna Ya zanyi Aysha Dole fa ki zama jaruma Ki cire tsoron nan Dan in ba hakaba Wlh zan iya fadawa wani hali "Janye jikinta take Sonyi Tana mai zubda qollah Tace ' Dan Allah Kayi haquri Hamma na Wlh Tsoro nakeji Gashi Mun fara shiga gari ma Yanxu kam. Ido ya Dan daqo Ya tsurawa garin. Cikin Sanyi Yace Har mun isa *Mai Samari* Ita kam samun ya Dan saketa yasa ta janye ta gyara zaman ta Ta tsurawa titin Ido. Ana kiraye kirayen Maqqariba Suka Isa cikin Birnin *Mambila* Kai tsaye ya wuce Family house dinsu Bappi mai gadi ya bude musu gate cikin Zumu d'in ganin Yusuf Dan Yusuf tamkar Hadari yake Daya iso Zasu samu Kyautar sanyi Yana parking Ya fito Cikin Bude hanna yenshi Yana mai shaqar iskar garin dayafi so fiye da ko ina A ransa Yanayin qarin Na tunzura Yanayin halittar da rabbi yayi mai Kye Ya miqawa bappi Cikin sanyi yace Bude but Ka shigar da kayayyakin Karba yayi cikin Dan Fara,a Yace ' can part dinki Zan kai ko? Ba tare daya kalleshi ba yace 'a a dakin Innayi zaka kai. An gama yace cikin Sauri ya fara kwasa " itako Aysha tin tuni Take on Fita yaqi bude mata Qofar Sai yanxu ya Dan zagayo Ya bude Qofar Cikin Yin piki piki da ido Ya Dan nuna mata hannu alamar ta fito Daya hannu kuma ya nuna mata qofar. Cikin Mmk Irin wasu lamura Na Hamma Yusuf din nata ta zuro qafarta Tana mai kallon shi Har ta miqe Shi ma idon Ya tsura mata Gami da qara matsota cikin Rada Yace 'Yadai Kike ta kallona? Na canxa ne? Ko dai Kema kewata ke damunku? Da sauri tai qasa Da Idon'ta Shiko Kamata yayi Ya manna ta a qirjinshi Cikin Shauqi Yace Kewarki ta kusa zautar dani Na kusa macewa Kin firgitani wlh Banson Kiyi nesa dani Shiyasa Na kawoki nan Dagani sake Masu gidan sunyi tfya. Janye jikinta tayi cikin Mmk da tsoro Ta nufi cikin Gidan. "Shiko Yusuf Phone dinshi ya zaro ya kira ta Baba bello ya sheida mai sunxo Amman su Bappa Yaya ba sannan Dan haka karsuce zasu zo Yana katse kiran ya kuma kira Ahmad Cikin Dan fara,a Yace ' B'iyaye Mun isa lfy Lau Dry shima Ahmad din yayi cikin Tsokana yace Ka sacemin Qanwata ka bar Ummi nata fada Sannan ka hana Usman zuwa Dan qarfin Hali Fuska ya Dan yamutsa yaci Gaba da cewa ' Ahmad Wlh Ummi bata San halin da nake cikiba Shi kuwa Usman Shi yawone kawai ke cinsa Yafi son yazo Ya tare cikin Labbun nan Yayi ta tsinke fruits Kamar wani biri. Adam ne dake gefe ya karbe woyar cikin Tsiya yace ' wlh andaiji Kunya Abu ya koma harda sace yar mutane Ni dai fatana kar ka cinyemin qanwata Yar marainiya. Tsaki yaja cikin Hada fuska Yace kai Ka cinyemin tawa qanwar Da Allah can da Sa idonka Ni banson masi Katse kiran yayi Ya nufi masallaci Bayan yayi Alwala Su kuwa Ahmad Dryar Yusuf Suka rinqa yi. " ita kuwa Aysha Tana shiga gidan ta rinqa mmk Ganin da gske Ba kowa a part din kakannin Nasu Sosai Take jin tsoron Hamma Yusuf din Parlon ta zubawa ido Komai nan tsaf gwanin Sha,awa Labulayen duk a sassake Ga komai a shirye hatta kan dinning table Komai tsaf Ba wani haske sosai Sai hasken Cikin show glass Sai sanyin A,C da Na yanayin garin daketa kadawa Parlon Sai qamshi yake Dan shi Bappa Yaya ko Qiftawa yayi ta wurin Sai ya Dade yana qamshi bare inda yake rayuwa A hankali ta zame gyelenta Ta ja Trolley ta. tashigar Cikin dakin innayi Toilet Ta shige Shawa ta sakarwa kanta Har Na tsawon wani lkci Sanyin garin Da sanyin ruwan suka sauqe mata da nishadi Cikin rausayawa ta rinqa murza sabulu mai qamshi A jikinta Bayan tayi brush Ta yi alwala Ta fito daure a Towel Zani ta zare ta daura Gamida Sa hijabin Ta tada kabbara Tayi magga riba Bayan ta idar ta dauko Qur,ani Tai ta karatu Har aka kira ishah Ta kuma miqewa tayi ishahn Tanaidarwa tai shafa,I Da witiri Sannan ta ninke abin sallar Gaban Mirror ta zauna Ta jawo Jakarta Ta rinqa murza mai a tattausar fararta Sannan Ta fidda humranta Ta bi jikinta dashi Ta kuma dauko Lovilia ta shafeshi a jikinta Miqewa tayi ta zabo Wasu tattausan Kayan bacci Rigace da Dan wondo Farare tas Sai Dan ratsin Yellow yellow a jikinsu Wondon guntu ne iya karsa guiwarta Sai yar rigar wacce iya karta Ququnta Daga samanta kadan Kadan kuma Ta danyi shara shara hannuta kuma ragace Gaban mirror ta koma dasu ta dauko Turaren Lailatu sahara Ta feshesu tsaf Sannan ta sakasu Ta dauko Hula Yellow ta murxa a kanta sannan Ta dauko phone Dinta Ta nufi Kitchen tana Zuwa Fridge Ta bude Tako yi Sa,a akwai Abinda take mararin Nono ta dauko mai sanyi Ta burgeshi Ta sanya sugar Sannan Ta Debi Fruits A pilet Parlon ta dawo Ta zauna kan 3 str TV ta kunna Ta koma ta zauna Cikin sanyi da Dan jin Tsoro Ganin yadda labulayen ke kadawa alamar hadari Na tasowa Can dai taji Iskar ta qaru sosai Tashi tay cikin Sauri Ta rufe Windows din Lkci Daya.kuma Walqiya ta fara haskawa Cikin Tsoro ta koma Jikin kujera ta da Zauna " Shi kuwa Yusuf Ganin hadarin Yasa shi Fitowa Gidan Baba Ahamdu Da sauri Ya shige mota Kai tsaye ```Jam baddu Restaurant``` Ya wuce Gudu gudu Ya seyomusi abinda zasu Dan ci da juices masu sanyi Bai zame ko inaba Sai Gida Hadarin kuwa kamar Jiransa yake Yana parking Ruwa ya kece kamar da bakin Qorya Fita yayi Cikin tattara ledodin Ya nufi Bakin qofar Cikin ruwan Tuni ya jiqe carkab Yana zuwa ya tura Qofar ya shige Cikin Sauri Yana 'Amrita Ina kike Ita kuwa Dan ganinshi da tayi Sai ta danji Sauqin tsoron Shi kuwa ganin ta share shi yasa shi Wucewa gefen ta ya ajiye Kayan hannushi A ranshi kuwa yana Oh kinji ba tsawa kenan Toh Allah ya Sa ai tsawan Tsayuwa yayi a gabanta Cikin Isa Yana 'Ke baki iya cewa mutum barka da dawowa ba ko? Bata kulashi ba Sai hararanshi da ta danyi qasa qasa "Shi kuwa rigar jikinsa da ta jiqe ya cire ya cillata gefe Ya kuma zame dogon wondon jikinsa Sannan ya cire yar bes Dinshi ya cillar gefe Ya rege daga shi Sai Bkss Cikin sanyi Yace ke " daqo idanta tayi Ta kalleshi Sai ta kuma Saurin kife Kanta jiki Kujera Jikinta har rawa yake Ganinshi haka ya bata tsoro sosai Shi kuwa Zama yayi a gefen ta Cikin Qara matsota........ ɦǟʊֆǟ ռօʋɛʟֆ ֆօӄօȶօ: աɦǟȶֆǟքք ռօ: 07068808039 աɛɮֆɨȶɛ: ǟɮɖʊʟʍӄɨɮǟɮ.ɦɛӼǟȶ.ƈօʍ 🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👆🏻👇🏻👇🏻 *MI,WASMITI* page 1⃣0⃣6⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Bakinshi Ya manna kan Kunneta cikin Sanyin murya yace A,ish kiyi shiru Kinji Na barki Bazan kuma abin da zai cutarda keba kinji Kiyi haquri kinji My dear sis. Shiru tayi cikin jin kun yarshi Ta manna. Kanta kan qirjinshi Hannu yasa ya ruqumota da kyau Ya jingina jikin kujera Ajiyar zuciya ya rinqa sauqewa Ido ya lumshe Cikin manna mata kiss A goshinta Can kuma Idon ya Dan bude cikin yamutsa fuska Jin Shigowar su Adam Da Ahmad Dan Sam baison abinda zai takura Mashi Amritanshi. Adam ne ya Dan kalleshi a fakaice Ya kuma juyawa ya kalli Ahmad da ido ya nunawa Ahmad Aysha dake lafe cikin qirjin Yusuf din Ya tabe baki Ya miqawa Ahmad hannu suka tapa Suka Dan kwashe da dry Adam yace Yusuf meke damunku? Cikin harara yace ciwon so ke mana dadi Ahmad ne yace Toh fa Wato ciwon so ke muku dadi Sai suka kuma.dry Kai ya juyo cikin kallon Ahmad a nitse Yana Biyaye harda kai Wato wannan Yaya Na zauren ya koyama Sa ido Dry Ahmad yayi cikin salonsa Na sanyin rayuwa da yanayi Yace a a biyaye bance komaiba Fatana asha ciwon so lfy Haka dai sukayi tayiwa juna tsiya Can. Maryam da Usman dasu Rabi,u Suka shigo a tare Gaba daya kallon mmk suka tsaya yiwa Yusuf Rabi,u ya kalleshi a fakaice gudun masifa Ya kuma yafito Usman ya daga mai gira Aiko suka kasa tsare mmkinsu Rabi,u Ne Dan Neman mgn Ya kalli inda suke cikin Daga murya Yace Ke Aysha tashi ki ban phone Dina Usman ko dry CE ta kofce mai Shiko oga Yusuf kai ya dago fuska a murtuqe ya watsa musu mugun kallo Tuni Usman kam ya fice Shiko Rabi,u matsawa ya danyi cikin hada fuska yace Ni phone na zata bani Zan tafi school Ne . Bazata bayarba ya bashi amsa a kufule Juyawa yayi ya fita cikin kunquni Haka ya maqaleta a parlon ko a jikinshi In Ummi tazo wucewa Sai ya kauda kanshi Har dai zuwa Dan wani lkci Bacci ya debeshi Ganin haka su Ahmad suka fice Suna dry. Suna baccin Nenne ta shigo ta samesu ruqqume da juna Klsu tayi cikin dry ta wuce kitchen gun Ummi. Cikin fara,a Tace Ummi yau kuma baccin a parlon ki za,ayishi kenan Tabe fuska tayi cikin takaici Tace yaro Sam Bayajin kunyar mutane yazo ya tare min a parlon Bayan ya yiwa yarinya mugunta sannan ya tsare kar a kaita Asbiti Dry Nenne tayi cikin sanyin tace ki bawa yaro matarsa sunyi komawarsu Can su gama magale juna baki gansuba bare kice rashin kunya ce Itama dry ta danyi sukaci gaba da aikin, Basu farkaba sai da sukayi baccin 2 hours Sannan Aysha ta Dan Juya cikin sauri shima ya bude ido Da sauri ya tallabeta Ya tallabo fuskarta ya tsura mata ido cikin ido Murya a narke yace I love you Amrita Kiyi haquri banson wahal dakeba Na kasa control din kai nane Baki ta Dan tura cikin kauda kai Qara manneta yayi ya daura bakinshi kan kunneta cikin shauqi Yace Kiyi haquri Ki yafewa Hamma Yusuf dinki. Kafada ta maqale alamar a,a Qara manna qirjinshi yayi kan nata Cikin rada Yace bafa laifina bane Laifinki ne Kai ta dago cikin alamun tabbata Ta kalleshi Gira ya daga mata Gamida cewa Ehh laifinki ne Dan ke kika gigitani Kika haukatani Ke kika jiyar dani abinda ban taba jiba Kedin ta dabance Ke dole en kasa sarrafa kaina Dan kedin ta dabance Qara goga qirjinta yayi a nashi cikin sanyin yace Aysha kina da dadin da bazan iya zama da qishinkiba plss karkiyi nesa dani Hannushi ya Dan kuma turawa cikin qirjinta Ya shafo bres Dinta cikin ajiyar hrt da lumshe ido Yace Wlh a duniya bayan qur,ani Ba abinda nake begen rigewa kamar wannan Ba abinda zan taba naji dadi da sanyi a raina da rayuwata da ruhina Aysha sai bres dinki Wlh hannuna qaiqayi yake min in ban shafesuba Bakina nauyi yake min, in ban tsotsesuba. Ya qarishe mgnar yana qoqarin Tura kanshi cikin qirjinta Da sauri.ta tallabo kanshi Ido cike da qollah Tace Plss Hamma Yusuf Na tuba Dan Allah kayi haquri Wlh bazan iyaba Ciwo jikina. Kai ya karya kamar marigayin zakara Cikin sakewar jiki yace Sai anjima Nazo ko? Kai ta sunkuyar cikin yuqqurin miqewa Sai kuma ta saki Dan Qara Da sauri ya miqe kamata yayi Cikin rawan jiki Yana Ohh sorry Amrita Hamma Yusuf dinnan bai kyau ta ba Sunkuceta yayi Sai dakin Ummi Kan gado Ya direta Kiss ya manna mata a goshi Cikin juya ido Yace wlh zanyi miss Dinki Dan Allah kixo Ki kwana da mijinki Kinji dumina inji duminki. Toh kawai tacema Dan ta rabu dashi Cikin salon Sha,awa yace Ki rinqa shiga ruwan zafi a kai akai Bari yanxu Na kawo miki mgnin Toh ta kuma cemai duk idanta a rufe Dan kunyar shi da tsoron shi takeji. Har ya juya zai fita ya kuma dawo Hannushi ya tura cikin Bres Dinta ya cabkosu Da Dan qarfi Yace Wayyohhhh Shehhhhhhhshh Ham Ya sauqe ajiyar zuciya ya fita Yana ki matso da moyarki kinji Noor hayat dina Kai kawai ta gyeda mai Dan gsky salon Hamma Yusuf salone mai tsadar gske Yana fita ya hado mata magunguna da tek awy Ga wasu kaji gasassu Sai qamshi suke Sai madara mai sanyi Da lodin inibi da su Apple mai sanyin gske. Sai wasu qattin boruna sukuwa ya cikasu tab da English wes da sleeping dress masu taushi da santsi da tsulbi Sai sweets lace da at ampopi masu kyawun gske Sai yan kunne da sarqa da abin hannu da zobe Na zinari Sai sheqi da gyelli sukeyi ga kye din dalleliyar motarta mai tsadar gske Turaruka kuwa ba,a mgn Duk ya hadesu. A parlon ya samu Anuty Sadiya Cikin Dan fara,a ta karbe kayayyakin ta shishigar Tana Yusuf wannan kaya haka Na mene? Fuska A sunkuye yace Anuty Na Aysha ne Tayi baccinne ? Ehh tace mai Tana mai zubawa kayyakin ido Shi kuwa dakin ya shige ya Dan shafo fuskarta cikin Sanyi ya tallabota Magunguna Ya Dan tura mata a baki ya balli Goran FARO Ya bata Duk abinda yakeyi tanaji Sai ta qara lumshe ido Yana gamawa ya gyara mata Blanket din Ya fice cikin kewarta A dakinshi. Wonka yayi ya zo ya kwanta Sai murmushi yake yana. Alhamdulillah Sam bacci ya kasa daukarsa ba abinda yake tunawa Sai Daren jiya Haka yayi ta juyi Sam ya kasa samun nitsuwa Dole yajawo phone dinshi Ya rinqa kira bata dagawa Gashi baison yaje kar aga zalamarsa Wurin text ya shiga A rayuwarsa shi bai taba dadara kanshi baifa bata lkci yayi wasu kalaman wai so ya turawa kowaba Amman gashi yau ya zauce Sai Zan tuka yake zubawa. Da gyer dai ya samu barawo bacci ya saceshi. Su kuwa a parlon Ummi Gaba daya sun cika da mmk Irin yadda. Hamma Yusuf dai Ya tsaya da kanshi ya tarkatowa Aysha irin wadannan abubuwan da yake fadin shi yafi qarfin ya solance a gun mace Rabi,u kuwa tsakaninshi da Allah yake fada yana Wlh nima dolene fa dolema kawai a Samar min moto Inba hakaba ayi bala,i haka kawai.ace Aysha ma najan motarta ni INA zare ido Ga Usman dai ya Ahmad ya bashi Abdul kuwa baba ya saya mai wato ni kam soko ko. Dry sosai suka rinqa yiwa Rabi,u Usman ko cewa yayi sunyi canjin moto Itako Aysha sai binsu da ido takeyi Saida Ummi tazo ta koresu tukun Ta Sam tayi baccinta Anuty Sadiya kuwa ta dage Sai hade mata kayan gyara takeyi. Kashe gari da sassafe Yusuf yxo A parlon ya samu Ummi Bayan ya gaidata ya miqe ya nufi cikin Dakin. Da sauri Cikin hada fuska Ummi ta dakatar dashi Cikin cewa Kai dawo nan Ina zakaje Wai shin kai bakada tausayi ne Nacema tana bacci tada ita zakayi kenan? Kai ya jinjina a Lamar a,a Fuska a hade tace Toh wlh ka kiyayeni Kar Na qara ganin qafarka a nan Kabarta taji dacutarta. Kana jiko? A Dan tsorice Yace humm Ummi dama mgnin Zan bata Kuma wai zan dubatane. Tabe baki tayi cikin yatsine tace gashi Ni ban iya bada mgnin ba ko? A a yace Cikin sanyi yace ayyah Ummi Dan Allah bari Na Duba jikin nata. Bazaka Duba ba wlh ka fice kawai Ta bashi amsa a fusashe Shiko gaba daya ya gama cika Haka ya juya a dole Ya fita Yana fita Ya kirata har Kusan sau 8 Bata daga ba A parlon su Ya zauna Cikin damuwa ya rubuta mata text Kamar haka. ``` Assalamu alaiki Ya sahibul qalbi Fatan kin tashi Lfy ya jikin Yayi sauqi ko ? Ko har yanxu yana ciwo? Dan Allah Amrita ki kulanmin da kanki Dan mu samu ki wore Dan wlh Na gaji da zaman Takura Amrita Daga yau zan fara mana shirin komawa Dan in muna qasarnan Za,a kasheni Yanxu nazo Ummi ta hanani Shiga Amrita ya za,ayi nida matata a hanani ganinta Dan Allah kixo gareni Wlh ke kadai nake son ji a kusa dani Plss ki tausayawa zuciyar Hamma Yusuf dinki Dan Allah kixo gareni Dan zuciya ta Na gasuwa da begenki Kijin Aysha Dan Allah ki taho.``` Dry sosai Anuty Sadiya takeyi da taga text din Cikin tsokana ta miqawa Ayshan Karba tayi tana Duba ajiye woyar tayi Cikin tabe baki Itako Sadiya Hadin Wani gari ta dama da madara Mai sanyi ta miqawa Aysha Tana gashi shanyeshi yanxu Kina shan wannan gaba Yusuf sai yayi kuka cur da hawaye, Ita bata daqo zanceba ta karba tana Sha tana lumshe ido Dan dadinshi Ummi da ta shigo yanzu cikin Fada Tace Sadiya Ban hanaki bawa Aysha irin wadannan abubuwan ba Ke kuma ba son zaqiba Sai dirka kikeyi Wlh zaki gane kurenki Gun wannan Fitinenne Wlh zai jinyatar dake shi ko a jikinsa Bakisha komai bama ya kika qare Kekuma Sadiya So kike ya kashe miki qanwa ko? Dry Sadiya tayi tace Insha Allah ba mutuwa Sai Ta zuciyarsa Ita Sam Aysha har yanxu bata ganeba Sai Sha take cikin nishadi. Haka Sadiya da Nenne suka rinqa Tsuma Aysha da Amira Itama Maryam har gida ake kaimata bayan Wanda aka mata kafin su koma Tafiya Yola kuwa dole aka dage Dan Ahmad yace bazai jeba Sai da Yusuf shiko yana jinya. Yau kusan 8 days kenan Ummi ta kasa ta tsare Fir ta hasasu Haduwa Ko woyarshi ta hanata dagawa Sai dai dubbban texis nashi Mgnaganu kuwa Yusuf Yayi magiya har ya gaji Yayi ta roqo ko muryarta a barshi yaji An hana. Ita kuwa Ummi Har yanxu gwada son da Yusuf kewa Ayshan take in bata gamsuba bazata bashi itaba bare su koma tare. Yau juna,a bayan an sauqo daga sallan Yusuf ya shigo gidan Ranshi a bace yau kwana 9 kenan hanashi matarsa Can gefen garden yaje ya zauna qarqashin Bishiyar maqqoro mai inuwa da sanyi Phone dinshi keta suwa Amman yaqi dagawa har sai da ta katse Kiran ya kuma shigowa a karo Na 3 Cikin hatsala ya zaro phone din Sunan Bappa Yaya y gani Tsaki ya Dan ja Tare da amsa kiran Bayan sun gaisa ne Bappa Yaya yake Cewa 'Dudabe Ka gayawa bello kace karku zo Gobe Dan munyi tfy Dasu innayi duka. Fuska ya tabe gamida cewa toh. Sainjima ya katse kira Yana toh ni menawa da tfyarku Yana wurin ya haqqo Usman Na Jan Trolley Ya bude matarsa ya saka Ya kuma komawa Ya qara fitowa da yar qaramar jaka Ido ya qurawa jakar sarai ya gano ta Aysha CE Shiyasa ya miqe cikin Dan sauri Ya isa gunshi Ido ya zuba mai cikin ayar tabbata Yace Kai INA zakaje Kuma kai dawaye Cikin Dan Tsoro Yace Gembu mambila zamu tafi Ni da Aysha kafin gobe INA kuma zakuxo ko hamma Yusuf? Hara ya watsa mai Cikin isa Yace Bazaka jeba. D sauri yace Bazan jeba ko bazata jeba? Fuska ya kuma hadewa Yace kai din bazaka jeba ko kanada mgn? Cikin maraicewa yace Ga kayanta Na cire ni ka barni nayi tfya ta Cikin Tsawa Yace Nace bazaka jeba Maza Kwashi kayan nata ka maidasu cikin motata Sannan kaje. cikin gida kace mata da motata ma zaku tafi Toh yace cikin Fushi ya kwashi kayan Ya mayar cikin motar Yusuf din Ya shiga cikin gidan. Shi kuwa Yusuf da sauri ya shirya kayan shi yazo ya shiga Cikin motar ya zauna Cikin Farin ciki Yana haggosu Suka isa Gefenshi Cikin sanyi Usman yace Zagaya can ki shiga Bari Na dauko igiyar Charge Na Toh tace cikin Murna, shi kuma Usman ya koma cikin gida rai a bace. Cikin Rausa yawa ta bude Gaba ta shige Hankalinta nata woje Dan haka bata ganshiba Shi kuma Jin qamshinta ya sashi sauqen ajiyar zuciya Tare Da lumshe ido ya Dan konto kanta kadan Hannushi yasa ya Jawo murfin motar ya garqame Ita kuwa Tsoro ya bata cikin Mmk tasa hannu zata bude Ya ficgota ta fada jikinshi Da sauri yayiwa Motar figan Nishadi Ya fice daga gidan. Hanyar Gembun ya miqa Ita kam sai Qoqarin janye jikinta take shi kuwa ya maqaleta Cikin rawa hannu ya tura hannushi cikin..... H̴A̴U̴S̴A̴ N̴O̴V̴E̴L̴S̴ S̴O̴K̴O̴T̴O̴: W̴H̴A̴T̴S̴A̴P̴P̴ N̴O̴: 07068808039 W̴E̴B̴S̴I̴T̴E̴: A̴b̴d̴u̴l̴m̴k̴i̴b̴a̴b̴.h̴e̴x̴a̴t̴.c̴o̴m̴ 🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👆🏻👇🏻👇🏻 *MI,WASMITI* page 1⃣0⃣8⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Qara shige mata yayi Cikin fuskantar juna Ya Dan jawota jikinshi Yasa hannu ya dauko ledar gasassun kajin Ya ajiye gefenshi Hannu yasa ya Dan yaga Ya miqa mata Cikin Dan rawan sanyi Yace 'bude baki kici. Kai ta dago ta tura baki Gami da cewa 'Na qoshi, Me kikaci? Ya tabba yeta cikin tura mata a baki Kai ta kuma kawar wa Ganin haka yasashi Matsota da kyau Ya Dan daga yar Rigarta ya tura hannushi A hankali ya rinqa shafa cikin nata ido ya tsura mata Gamida cewa 'Kici abinci Kar ki cutarmin Da kanki ki cutar dani Kinji ko Amrita. Janye jikinta ta yi cikin Ture hannushi tace ' toh ni ka barni, Miqa mata yayi a baki tare da cewa zan barki in kinci In kuwa baki Ciba Wlh bazan barki ba Ya qarishe mgnar yana tura hannushi Saman bres dinta. " jin haka yasa da sauri ta bude baki ya samata Ita kuma ta kamo hannushi zata fitar. Yai maza Yace Sai kin gamaci zan barki. Haka ta haquri a dole ya rinqa yagar naman yana tura mata Ya kuma dauko juice ya bata Har Sai da taji Kamar cikinta zai fashe Cikin qoshi tace ' Hamma Yusuf ka barni haka ji nake kamar zanyi amai A jiye cup din yayi gami da ' cewa ' D'aga rigar inga cikin Juya fuska tayi Tana Tura baki Shi kuwa fuska ya murtuqe cikin fada fada yace ' bude in gani Ko in matseki Kin sanni sarai, Jin haka yasa ta daga yar rigar Qara matsota yayi yace ki daga ko in iso Dagawa tayi har zuwa kan qirjinta Ido ya tsurawa fatar cikin A ranshi yake fatan Allah yasa a yau dinnan ya dasa qonsa a jikinta A fili kuma Shafa cikin yayi ya juya ya nufi Bedroom din innayi Yana shiga wonka yayi Ya fito ya shirya tsaf Ya fito parlon daure da towel. Can ya hanqota rakube jikin kujera A hankali Ya qarisa gunta cikin sanyi Yace Aeeeshar tashi kije ki kwanta Miqewa tayi da sauri ganin zai zauna gefen ta Fuska ya Dan tsare tare da cewa Me hakan cinyeki zanyi ne? " kai ta girgiza tare da cewa zanje in kwanta ne, Kai ya gyada alamar Jeki "Tana shiga Ta haye kan Gado mai rumfar Ta sassake labulayen Ta konta luf abinta Sanyi Na ratsata A hankali ta rinqa sauqe ajiyar hrt Ganin har zuwa Dan wani lkci Bai shigoba yasa tandan nitsu Har bacci ya fara dibarta. " Shiko Tana tfya yabi bayanta da kallo Ququnta ta tsurawa ido Sosai ta tafi da nitsuwarsa Gaba daya ya daburce lkci daya lips dinshi suka fara sana,arsu A hankali ya lashi lips din tare da kamo gefen lips ya fara tsotsa kamar yaro Jikinshi duk ya fara rawa Har zuwa wani lkci Ganin bazai yiwuba ya jumre waba Yasashi Miqewa Ya kashe su TV Sannan ya rufe ko ina ya shige dakin. "A hankali ya dage labulayen Cikin hikima ya kwanta gefen ta Tare da sauqe labulayen, Ajiyar hrt ya sauqe Lkci daya kuma ya mirgina ya isa Gareta Hannushi yasa Ya jawota jikinshi Hularta Ta sabule Sannan ya Sa hannu a hankali ya rinqa zare rigarta daga jikinta Har saida ya cireta ya cillah gefe Hannushi ya kuma turawa cikin mararta Ya sabule zip din Dan gajeren wondon Dai dai lkcin Ita kuma ta bude idanta Jin yana ta yamutsa ta da rebata da kayan jikinta, Hannushi ta riqe Cikin Dan tsoro tace 'Hamma Yusuffffffffff Bai amsaba Sai Hannushi daya ya qarisa sabuleta Ya wore towel din jikinshi Ya qara manneta jikinshi Lkci daya ta zazzare ido tare da sauqe wani nannauyan numshi. " shi kuwa a kidime ya Sa hannushi ya lalubo bres Dinta Ya rinqa shafawa yana sarra fasu Bakinshi ya manna kan bres din ya rinqa sarra fata Hannushi daya kuma mararta yake ta shafawa yana Dan murzawa, Itako Aysha tsoro yasa ta qamqame hannushi Tana Dan Allah Hamma Yusuf Ka bari Wlh tsoro nakeji Zafi, Nishi ya rinqa sauqewa yana Rawan jiki Ya tashi ya zauna ya jawota jikinshi Bakinshi ya kai saitin kunneta Cikin Voice xex yace ' uhmmmm Hisshhihh Plxxx Aysha kitai maka Wlh bazan iya jumrewa ba Ki taimaka min Wlh Na kasa haqura Ki tausaya min Kiga tsawon kwanaki da Na zauna da kewarki " Hannushi ta riqe Wanda yaketa Latsar qirjinta Wanda gaba daya itama ta kidima ta Cikin Rawar murya tace ' ni dai bana so. Yunqura yayi cikin rawan jiki Ya kwantar da ita Cikin sanyi Yayi mata rumfa da faffadan qirjinshi Yana rada mata Am so sorry My dear Zan kula dake Ki kula dani Zan biki cikin Sauqi Insha Allah yau Bazakiji Zafiba Kinji Matata, Ta bude baki Zatayi mgn kenan Tai sauri Ta rumtse idanta Gami da Damqe hanna yenshi Tare da cije lips Dinta jin Yana ratsata Jikinta duk ya dauko Rawa Zafin takeji yana ratsata Amman bai kai Yadda ta zata ba irin Na wannan ranar ba Cikin Rawar murya Tace ' Shiihhht Hamma Yusuf Zafi Dan Allah ka barni, Ina shi kam Yusuf baima San tanayi ba Yau ya jishi cikin wata sabuwar rayuwa Ji yake da zai tabbata a haka da bazai gajiya ba Gaba daya ya fita hayya cinsa Sai wasu zantuka yake masu wuyar Fada Gaba daya jikinta Binta yake da lasa da subbata Ita kam Aysha tun tana Dan Daurewa.kar tai kuka Dan yadda yake Sa mata albarka Yana ' ki jiqaina Aysha ki taimaka ki barni Na gamsu Da nimar da Allah ya miki Ki taimaka min Ki ruqqume ni A matsa yin mijinki Na har abada Aysha ki daure Ki jiyar dani Dadin da ban taba jiba Gaba daya haka ya zauce ya zautar da ita Juyata kawai yake yana haqarta ta inda yaga dama Har zuwa 3:30Am Ita kam Aysha Gaba daya ta sake Sai Qollah take tana Qamqameshi Tana Hamma Yusuf Na gaji Bazan iyaba Zan mutu Numfashi Na zai dauke Haka tai ta magiya Sai 4 dai dai Hamma Yusuf ya sarara mata Ya koma jikin Pillows ya kwanta Ya jawota jikinshi Ya ruqqume ta tamkar zai maidata cikinsa Ita kuwa duk ta saki ta narke kanshi Tana kukan Gajiya da rashin bacci Ta maqale jikinsa Tana shaqar qamshinsa Shiko bayanta Ya rinqa shafawa yana Ohh Amrita Allah ya miki albarka Rabbi ya saki farin ciki kamar yadda kika sani Kin Daukemin duk wata buqatata A,ish Me kikeso Na miki A duniyar nan? Cikin Qara maqaleshi Ta shafi sajenshi A hankali Tace Ka barni Ka dena takura min, Ka tausaya min Hamma Yusuf kafi Qarfina Bazan Iya daukar Yawan buqatar ka ba, Numfashi ya furzar gamida Kamo lips Dinta ya Dan tsotsa Sannan yace Ai zan mutu in Na barki Aysha waya CE miki bazaki iya daukar nauyin buqatuna ba Ai ke ta dabance Ko ganin ki nai nakanji gam suwa, " A haka dai ta dan lafe a jikinsa har, akayi assalatu Cikin Dan baccin da ta farayi ne taji ta cikin Ruwa Da sauri ta bude ido Sai kuma ta rumtse ganin Tare suke da Hamma Yusuf din nata Ya caxge kamar bashi ba Jawota jikinshi yayi Tare da shafa qirjinta Idan ta kuma budewa Ido ta tsura mai shima itan yake kallo Girarsa daya ya daga mata cikin Rada yace Sunefa suke tsoka nata Ya fada yana nuna bres Dinta Baki ta Dan tura tace Me sukayi Kanshi ya manna kan qirjintan yana Cewa sunce Na matsosu, Itama miqa ta danyi Dan ya fara sauqe mata wani salon Fitina Qirjinta ta Dan dago ta tura mai Da sauri ya cabke har jikinshi Na rawa kamar wani Yaro ya rinqa tsotsarsu Ita kuwa ido Ta lumshe tana shafa kanshi da qirjinshi "A haka dai da gyar sukayi wonka Suka fito Suna fita tea ya hada mata mai kuari ya bata tasha Sannan ya tafi masallaci Itama tayi sallahn "Yana dawowa Ya cire rigarsa Ya raba gefen ta ya kwanta Yana lalubota Cikin Baccin ta tashi A Dan gajiye tace Wlh Na gaji bazan iya ba plxx Hamma Yusuf bacci Kai ya gyada cikin Sanyi Yace kiyi Baccin Ni ki barni da qirjinki ya isheni Haka ya rinqa yamutsa ta Sai 11 suka tashi Gidan baba Hamisu sukaje bayan sun kimtsa Acan sukaci abinci Bayan axahar suka fita shida baba hamisu Ita kuma tai ta bacci Sai 9 Na dare sannan suka koma gida " yau kam Aysha kuka tai tayi taqi Amincewa Dan gajiyar jiyama bata barta ba Shiko Yusuf haka ya haquri ba Don ya soba Sai Don tausayinta yakeji Dan shi da kansa yasan Ya murzata da yawa " itako Aysha tun daga ran nan Ta samu damar Kaucemai bare da ta gane bai son Takurata Haka kullum yake kwana cikin buqatuwa itako tai ta baccinta " Yau ma kamar kullum Kwance suke Cikin Blanket A hankali ya matsota Murya Na rawa Yace Aysha Da ixinin Wa kika juyamin baya Bana gaya miki Banson hakan da kikeyi ba? Cikin tura baki tace ngji Bacci zanyi Cikin Dan rauni yace Aysha ki tausaya min mana Wlh bazan iyaba Yau kwana 4 muna tare Amman kin hanani haqqina Tashi tai ta zauna Cikin Dan yamutsa fuska tace Wlh kai Hamma Yusuf ka fiye jaraba Na lura so kake ka tsotsemin ruwan jiki Ido ya tsura mata cikin Kufula yace Bani NAYI kaina hakaba Allah ne yayini Haka Kuma kinsan haqqinane kam ko? Konciya tai ta juya mai baya Tace Ai jarabar tafi qarfina ne, Ka takurani ka hanani sakewa wlh Tai qasa qasa da murya tace jarabebbe kawai Shiko ya jita sarai ranshi ya baci matuqa Miqewa yayi ya sauqo qasa Kan carpet ya wurga pillow ya kwanta A ranshi Yake jin zafin Abinda tai mai watoh shi ya zamar mata kamar dole ko Ita kuwa tana jin ya sauqa ta gyara kwanciya tai luf Abinda Shiko ya kasa bacci Sai juyi yakeyi Yana cikin haka phone dinshi ya kama ruri a hankali ya daga Cikin sanyi yace Abubakar Na,am ya amsa cikin Sanyi yace Hamma Yusuf Bacci zanyi Sai kuma duk naji hankalina ya dawo gida Cikin gyara zama Yace Dan uwana Kazo mana muma munyi kewarka Abubakar katashi hsnkalin Ummi ma wlh duk ta damu da rashin zuwanka Ajiyar zuciya ya sauqe Tare da cewa Hamma Yusuf Zan zo Amman inaji Kamar zuwan qarshe zanyi Jikina Na bani mun kusa rabuwa, Da sauri Yusuf ya dakatar dashi cikin Tsoro yace Haba Abubakar Meyasa zaka gayamin haka Dan uwana Dan Allah kar ka gayawa mahaifiyarmu haka Dan uwana Dry Abubakar yayi cikin Raha yace toh ba komai Hamma Yusuf kayi baccin ka Sai da safe A haka suka katse kiran Kashe gari Yusuf Bai nunawa Aysha komai Ba da dere ko A kasa ya kwanta Abin takaici kuma bata kulashi ba A Daren ya samowa kanshi mafita Shi da kanshi ya rinqa murmushi Mugunta Kashe gari da yamma Ya shigo Parlon ya samu ta ajiye nono A kan stool Ta koma kitchen zata dauko spoon Wasu tabs Ya fitar daga aljihunsa Ya murza guda 2 cikin Nonon har ya juya Ya kuma Juyawa Ya qara murza 2 a cikin Nono Ya koma can gefe kan 1str ya zauna Yana kada Qafa Tana Fitowa ta dau cup din Ta jujjuya nonon Sannan ta rinqa Sha a hankali Tana Dan lallatsa phone Dinta har ta shanye, Shiko miqewa yayi Cikin tsare gida Yace Ki shirya In anyi sallah Mu tafi Restaurant Toh tace cikin Murna tace dama Inabina ya qare " bayan sun Kammalah cin abinci Yalodo mata fruits Qarfe 9 dai dai Suka shigo Mota Yaja suka Nufi Gida Itako Aysha tun a cikin Motan Takejin Wani irin Yanayi Na ratsata A hankali ta fara miqa Duk gabanta Suka rinqa budewa Ta kasa gane meke faruwa da ita " a haka dai ta daure Har suka isa gida Suna isa Wonka tayi Ta shirya cikin rigar baccinta Yar yeloluwa Mai budedden qirji Sai Dan igiya ta saman ta Dan daure Tana tufa ta shima ya shiga Ya watsa ruwan Towel ya daura a ququnshi Ya murza turare kawai a jikinshi ya koma parlon Ya kwanta kan 3str Ita kuwa Ido kawai Take binshi dashi Zuwa yanxu Ta gano Sha,rawar Hamma Yusuf dinne ke tsumarta Kwanciya tai Amman ta kasa nitsuwa Cikin Miqar ta miqe ta nufi Parlon ido ta tsura mai Cikin Piki piki da ido Sai wani miqa takeyi Shiko dago kai yayi ya kalleta ya yamutsa fuska, Yaci gaba da kallon shi A hankali ta isa Gefenshi ta...... 🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👇🏻👆🏻👆🏻 *MI,WASMITI* page1⃣0⃣9⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Wannan page din nakune matan "Gefenshi ta ratsa ta wuce Kan 1 str ta zauna Ta Dan jigina da jikin kujerar A hankali tayi wani irin dogon miqa. Ta Dan tura baki Ta juya ta kalli TV Wani Nigeria film yake gani Gaba daya ya maida hankali shi Kan tv su Kuwa arna Sai Zuba Roman's Suke, " tsaki ta Dan ja Tare da zamewa qasa Tana daddamqe jikinta " Shiko Yusuf sarai Ita yake kallo Mmk yake taurin kai irin Na Amrita A ranshi yace ko dama su mata haka suke sukan iya danne buqatarsa ba kamar mu maza ba Ko kunyace Murmushi Mugunta ya danyi Tare da tunanin Koma dai menene yau zaki gane kurenki Ita kuwa Aysha Qirjinshi ta tsurawa ido Ba abin da take so irin ta jita maqale a jikinshi Amman kuma ta rasa ta inda zata Fara Yau dama ace da hadari da zata fake da haka ta maqaleshi Tashi tayi ta zauna Cikin wani irin Voice Tace ' Hamma Yusuffffffffff Ya jita Amman bai kulata ba A karo Na 2 tace Shhhhhhhhhum Hamma Yusuf Gaba daya gashin jikinshi ya mimmiqe jin irin sautin da ta kirashi Dole ya juyo gareta Cikin sanyi yace 'Menene ? Kai ta kwantar cikin salon yin Kuka Ta kum cewa Hammaaa Ido ya tsura mata Cikin jin tausa yinta Dan a fili Yake hanqo Buqatarsa da take a jikinta da qwayar idanta Amman kuma gashi ta kasa Fada ko ta kawo kanta Kai ya jinjina Yace Amrita Baki da lfy ne? Kai ta gyada mai cikin Zubda qollah Cikin Son yin dry Yace Meke Damunki? Miqa ta kumayi Tare da danna qirjinta jikin guiwarta Murya Na rawa tace 'Nima ban saniba Bakisan meke damunku ba ? Ehh ta fada cikin Kuka daya kufce mata Shi kuwa kauda kai yayi cikin Murmushi mugunta Yace toh Jeki kwanta Miqewa tayi Taje jikin Tv ta kashe Shiko ido ya tsura mata cikin Hada fuska yace 'Meyasa zaki kashe bayan kinga Ina kallo, Juyawa tayi ta shige daki Tana Mutum baida lfy ma baza,a barshi Ya huta da hayanin Tv ba Tana fita ya Jawo Phone dinshi Yako yi Sa,a Ahmad da Adam suna Online suna ta hira Sai ga Abubakar ma dasu Hydar, "A dakin Ta kasa Zama Sai juyi take A fili Take cewa Na shiga Uku meke faruwa dani Can kuma ta koma Parlon Gabanshi Taje ta Durqusa Ji take kamar ta fada jikinshi Amman kunya takeji Shi kuwa yana ganinta Ya kauda kai Ya rigada ya gano Ta Kamu Ya kuma San Abinda yafi Burgeta a jikinshi Qirjinshi da damtsen hannushi Shiyasa yasa hannu Yana shafa Sajenshi Cikin sanyi Ta saki Dan Kuka tana ' Hamma Yusuf Sai ya amsa yace mene? Sai tai shiru Ganin haka Yace Tashi Muje ki Kwanta, Miqewa yayi Ya nufi dakin Tana biye dashi a baya "Suna shiga ya gyara mata blanket din yace xoki kwanta Ki bar kukan, " cikin tsura mai ido Ta hau ta kwanta Ya Dan ronqofo Ya gyara mata gashin Kanta Ya jawo blanket Din ya rufeta iya Qirjinta Ya juya Zai fice Sai Kuma ya juyo da sauri jin Ta riqe hannushi! A Dan mmk Ya kalleta ido cikin Ido Ita kuwa Sauri tai ta sada kanta qasa Jan hannushi zai ta kuma qara riqewa Juyawa yayi da kyau Ya tsura mata ido Cikin sanyi Yace ' Amrita Meke faruwa? Tsoro kike jine Kai ta girgiza alamar a,a Sai qara jowoshi Take Murya can qasa qasa Tace Hamma Yusufhhs Na,am ya amsa mata Sai kuma tai shiru Ganin haka Yasa ya janye hannushi Ya juya yana Tunda bazaki fadi meke damunki ba ya Na iya miki Cikin sanyi ta diro daga kan gadon Ta bayanshi Ta tsaya A hankali Ta ja igiyar Rigar baccinta Ta budata daga Saman Qirjinta ya fito Fili Qarisawa tayi Gunshi A hankali Ta manna qirjinta a gadon Bayanshi Cikin Wani irin salo Ta sauqe nannauyar ajiyar hrt Tasa hannuta ta zagayoshi Ta gaba Kan qirjinshi ta dire hannuta Cikin Rashin sanin ta iya salon Ta rinqa murza qirjinta a bayanshi Hannuta daya Na Murza nashi qirjin Daya kuma Tayi qasa dashi Ta kamo Towel din jikinshi Zata kunce, "Da sauri Ya juyo kanshi Yana kallon Ikon Allah Ita kuwa Luf ta rumtse idanta Dan kunya Cikin Dauriya Dan Aysha ta birkitashi Ta qona mai jinin jiki Murya Na rawa Yace Me hakan Kije kiyi bacci Ni kallo zanje inyi Qara Jan towel din take Da sauri ya riqe Hannuta Ya jata zuwa kan Gadon Cikin Daurewa Dan shima so yake ya rama Ajiyeta yayi Ya Dan ja baya Cikin Sigar ki kula Ya Dan sunkuyo Ya ja igiyar rigar ya hada Saitin qirjinta Mmk yake Yadda hatta qirjinta cikowa bres Dinta sukayi Kansu Yayi jawur Dan bakin Ya hade Da ka gani Kasan A hannu take Ita kuwa mmk Take Hamma Yusuf Dai Mutumin Da ko cikin Bacci Yaji qirjinta Sai Ya shafa wai Amman Yanxu shike rufe mata qirjin Shi ko zuwa yancu Makanta ta diran mai Bai ganin Komai Sai Ita Pillows yaja Ya wurga Tsakiyar daki Kan carpet Ya taka Yaje jikin Gini Ya kashe wuta Yana 'ki kwota kiyi Baccin ki Gani A dakin, "Juyowar da zai Yaji ta Ta fada Kan qirjinshi Ta narke Tasa hannu 2 ta sanqalo Wuyanshi Qirjinta ta rinqa Tura mai Cikin Goga mai ququnta Ta zame towel din jikinshi Tasa hannu daya ta Sabule rigar jikinta Cikin wani irin Rawan jiki Ta manna jikinta da nashi Hannushi ta jawo ta daura kan qirjinta " wayyo Hamma Yusuf shi kam Mutuwar tsaye yayi Ba abinda yakeji Da tunawa Sai Randa ya fara Ganin qirjin Amritanshi Randa shi Ya mammatseta tana kuka tana kaucewa, Da gyara ya samu Suka Isa kan carpet din " zama yayi cikin Sauqe numfashi Ya jingin jikin Gado Ya bubbude Hanna yenshi Tabbas a yau Aysha ta bashi mmk Ase dama cutar dashi takeyi Sarrafashi take da juya shi Kan cinyarsa Ta dare ta zauna Ta tallabo Fuskarsa Bakinta tasa cikin Nashi Ta lalumo Harshensa ta rinqa tsotsa Shi kam Sai Numfashi yake Sauqewa Can Kawai yaji Kuka ya kufce Mai Cikin Kukan Ya tureta gefe Ya matsa ya qamqame jikinsa Murya Na rawa Yace 'Amrita Ki barni Ki rebu dani In so kike ki kashe niba Meyasa Kike son Zalumtata? Matsoshi tayi ta narke jikinsa Tana Hamma Yusuf Kar kayi nesa Dani Cikin Wahala yace Nike nesa dake ko kece keyin nesa dani Sannan yanxu kinxo Kin birki tani Danace ki ban haqqina kuma Ki fara min kuka da mita Harda cemin Jarabebbe Toh kije ni Na haquri Zan daure koda zan Mutu Kije bazan Kusance kiba Matsoshi Ta kumayi Cikin Rawan jiki Tace Wlh bansan ya zanyiba Hamma Yusuf Tureta yayi yana kinsan Ya zakiyi Nine dai bansan Ya zanyiba Adan kun yace tace Hamma Yusuf Idan ban rabeka ba wazan raba Kaine Mijina Haqqina Yana kanka Ba gun Wanda zanje Sai gareka A hankali Yace Yau Kin nemi haqqinki A guna? Kin yarda bani kadai Bane jara bebben Harda ke? Matsoshi tayi Cikin Kunya ta fada jikinsa Cikin Salon salo Ta dago qirjinta sama Kadan Kanshi Ta tallabe Ta rufe mai baki Da bres Dinta Kanshi Na qirjinta ya yunqura Ya sunkuceta Sai kan Gadon Yana direta ya Dan juya zai dauko Pillows Ta jawo shi Jikinta da qarfi Maqaleshi Tayi Cikin Rada Yace Amrita ai zaki Karyani Ki huta Hannu tasa ta zagayoshi Cikin Kaiwa maqurar bu qatuwa Tace 'Bana son Duk wani Abu Da zai nesantani Da mijina Ba abinda nake shauqi Sai Hamma Yusuf Na Plxx Hamma Na Kar kayi nesa dani Cikin sauqe numfashi yace Ni nakine ke kadai Amrita Baki da kama a gareni Yusuf nakine Ke daya Dama danke rabbi ya bani Cikar haiba Aysha banji Komai a duniya Sai sautinki Ban ganin komai Sai fuskarki Aysha sonki A jinina yake Amrita ki ankilta min jikinki Dan shine nitsuwata Qara matseta ya kuma yi Cikin Isar da dubban saqonnishi zuwa gareta Ita kam Gaba daya ta maqale Hammanta Tamkar zata hadi yeshi Ba abinda take Sai Shi take Kira cikin Sautin Sarkewa Tana Hamma Yusuffffffffff Shiko ji yake Ba Wanda yake kiran sunan shi dai dai Sai ita Sai ta maqaleshi Tace Ohh Hamma Na i miss you so much Shi kuwa Yau Yusuf Larabci Yake ta bugawa Yana ya habbiti Noor hayatina Noor qalbina Ya A ish, Ahaka suka zauce Suka kidime Juya abarsa yake son ransa Yana murzata itama Gwayar da ya dirka mata bai sakiba Sai Maqaleshi take tana Hamma Yusuffffffffff Sune basu sararawa junaba har 4:20Am Sannan Ya sahirta cikin samun cikekkiyar gamsuwa Jinshi yake a saman gyajimare Cikin jarumta ya ciccibeta Sai Cikin baf ya direta Shima ya shige Luf sukayi Cikin Ruwan Bres dinta Ya shafa cikin Rada Yace Basu gaji bafa Idonta a rufe Tace Ai nakane Hamma Yusuffffffffff Tsura mata ido Yayi Cikin Shauqi ya maqaleta Yace Wlh da Na cuci kaina Dana kashe rayuwata da Na rebu dake Na tabbata bazan samu kamar ki ba Sai yanxu Na gano Tun da canma sonki Ke d'awayniya Dani Kanta ta kontar Kan kafadarsa Cikin Tura mai bres Dinta Tace ' Hamma Yusuf Ka manta dai Da ai baka da abin qi Sai ni Da sauri ya rufe bakinta Cikin Gskya da gskya Yace " ,ban taba tsanarki ba Sai dai tsoron ki Da nakeji Amrita Sabida a wancan Lkcin Ina miki Klon Qanwata uwa 1uba 1 Sai Kuma Ko yaushe Kece mai Tayarmin Da Sha,awata Dana ganki Nitsuwata ke tafiya Shiyasa banson Ganin ki Danaji Muryar ki Sai Na daburce Da zaran kin Dan tabani Wlh Aysha Sai nayi wonka Kin tuna randa Kika fada jikina a rafi Wai kije gun Ahmad Shiyasa ko yaushe nake mmk inaga su Ahmad Na maqaleku kuma basa jin komai Ase Dan ba Aure a tsakanin ku ne A lkcin kuma Badon INA kauce miki ba zaki Iya gane halin da nake ciki Shisa kike min kallon mugu Aysha Wlh Na cuci kaina da muka yi tsawon 2 year ban amshi a manataba Tsofinnan sun min gata Da suka aura min ke Sun kuwa yi miki Gata da basu bari Na sani ke matata bace Dan da Na Sani da Bazan iya haquri har ki girmaba Yawan fadan da nake miki ase kishine ban saniba Matseta yayi Itama lafewa tayi jikinshi Cikin Tsune kanta a qirjinshi A hankali yace Amrita I Love you so much Zan dauwama in mai begenki Qanwata a manata matata Da gyara sukayi wonkan suka fito Bayan sun gama komai Suka kwanta rama baccin deren da basuyiba 12 dai dai Aysha ta sauqo Kan gadon Cikin mmk ganin Hamma Yusuf Baya dakin Toilet ta shige cikin Tsoro da mmk jin qafafunta Na rawa karkar A daddafe ta shirya ta fito Parlon tsaye tayi a tsakiyar parlon Tana miqa Batayi auneba taji Yayi hogging Dinta ta baya Cikin Sanyi Yace Har yanxu Miqa kike Alamun baki Gamsu ba kenan Dan ba yunwa kike jiba ba bacci ba kawai Hammanki kike son raba kinji dumina Qara matseta yayi, Itako cikin Tsoro Tace 'a a Hamma Yusuf nagaji Qafata ciwo Sai rawa suke Dry ya danyi cikin Salon shauqi yace Qafafun basu gama karbar saqonnina bane Shiyasa Baki sababa So yanxu baqunta suke Sai Na gama koyar dasu Nima a farst night dinmu nayi fama da hakan Qafafuna suka rinqa rawa idan Na zauna da gyara zan tashi In an taba cinyata kamar nayi ihu sabida sunyi abinda basu taba yiba, *Inda mace zata iya gane namijin da bai taba kusantar mace ba kenan alamun suna da yawa wannan kadan ne daga ciki* Yaci gaba da cewa Gashi ke din ta dabance bana gajiya da ke A shogobance tace Ni wlh ban da qarfi Cocci beta yayi cikin Rada yace muje in baki Na qarin qarfi baby nah Kan gadon ya direta Tana 'ayyah Hamma Yusuf Shima karya wuya yayi cikin Koikoyarta Yace 'Ayyah Ki bar Hamma Yusuf dinki ya rege zafi......... 🍇🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👇🏻👆🏻👆🏻 *MI,WASMITI* page 1⃣1⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Ido ta lumshe cikin Kunya ta shafi sajenshi da ya kwanta lub. Shiko samun haka ya sashi Lafewa jikinta cikin Isar da saqonnishi Masu wuyar Man cewa, Cikin Rad'a yace 'Amrita ngd Allah ya miki albarka Rabbi ya cika miki Rayuwar ki da Farin ciki kamar yadda kika cika rayuwata da Farin ciki. "Lafewa ta qara yi a jikinshi Tana jin Bugun zuciyarshi Na harbawa kan nata A haka har zuwa Dan wani lkci Sannan Suka samu suka Yi wonka suka shirya Suka fito parlo Kan carpet suka Yi masauqi Yusuf tallabe Da amritarshi Yana ta riritata Itama Sam har yanxu ta kasa Jin ta gaji dashi Shiyasa bata tsiri halin Wahal da shiba.. "Suna cikin Hirarsu Tana lafe cikin Qirjinshi Sukaji! SLM su Bappa Yaya Da sauri ta yunqura zata tashi Shiko Sai qara matsota yayi. " Suna shiga Innayi da inna Suka bisu da klon Mmk Shiko Bappa Yaya Cikin Jin dadin ganin su Yayi Murmushi Dai dai lkcin Da ya zauna kan kujera da suke qasanshi. Cikin happy Yace 'D'ud'a'be Yaushe kuka zo? " Fuska ya Dan yamutsa cikin Daqile murya Yace ' ba nacema ban son sunan nan ba? ' ehh ka fada kuma bazan bariba, Kai dai wlh bakaji dadiba Mu muna sonka kamar mu mutu Kaiko kana kinmu kamar ka mutu! "Ajiyar zuciya ya sauqe cikin Dan raha ya shafa suman kanshi Yace ' ai gwara da Baku Mutuba Bappa Yaya da ka mutu da wa zai ban Farin cikina? " cikin mmki innayi tace ' menene Farin cikin naka? "Murmushi yayi da iya gskyarsa yace 'Aysha Mana. "Aiko su inna suka rinqa dry, Shi ko ko a jikinsa Bappa Yaya ne Ya Dan gyara zama ciki Girma Yace 'Yusufa Kaga ribar bin mgnar iyaye ko? Kaga illan bijire musu Kai da kanka kasan yanzu ka samu cikekkiyar rayuwa Sabanin baya da kake ganin Mun qwareka mu samman ma ni. Kai ya jinjina cikin Sanyi Yace ' Bappa Yaya *MI,WASMITI* ko mi wadi ha wakkati to do, *NAYI,NADAMAN* abinda Na aikata a wancan lkcin Bana son tunawa sauqina ma daya da rabbi Ya bar min Dan uwana Ahmad da biyaye Na ya mutu da bazan yafewa kai naba. Innayi tace ' komai ya wuce yanxu kam Fatan rabbi ya Baku zuriya d'aiyiba, Amin ya amsa cikin Zumudi da jin dadin addu,ar. "Haka sukayi ta Dan Hie ransu Biyar dai dai Yusuf ya Miqe cikin Kammala shirinsa Da Na Aysha Ya kalli su innayi Cikin Qaunar kakannin nasu Yace ' mukam zamu tafi Sai Next week In munzo, Bappa Yaya Yayi ta nacin ya bari Sai gobe yaqi fir Dan shi a ganinsa Zasu takuru A dole ya barshi Ya dauke yar matarsa Suka tafi. " cikin Mota Yusuf Tuqi yake Da hannu daya daya kuma ya jawo amritanshi Yana Dan Shafa bayanta Yana 'Amrita Bacci kike Jiko? Kai ta Dan gyada mai a Lamar eh Cikin Sanyin ya qara jawota jikinshi Yace Kwanta kiyi bacci Kan cinyar Mijinki Kinji ko Matata? Itako Ido ta tsura mai cikin Mmk hali irin Na Hamma Yusuf Wato Shi Hamma Yusuf ya yarda da love Ya Baiwa so Amanna Shi jin Kalmar so yake tamkar ruwan zinari Shi Yusuf irin mazannan ne da so ke mai dasu Bayi Ya maidasu tamkar basu San komaiba " A haka suka isa Gida Tana lafe a jikinshi Tana baccinta. Yana parking Rabi,u da Usman suka iso Cikin Qaunar yayan nasu duk da zafibirin Na Yusuf yan uwanshi Na matuqar qaunarsa Kye ya basu suka tattara kayansu Suka shigar cikin gida. Ummi Na ganin jakar Aysha Tace 'Usman sun dawo ko? Kai ya gyada Cikin Leqa hanyar shiga Yace ' wlh Ummi Sai.kinga yadda Autanki tayi kyau Sai kace wata balarabiya Sai dai ta Dan rame gsky. Ajiyar zuciya ummi ta sauqe cikin jin dadi Tace 'Toh ina take ne? Rabi,u ne ya Dan Sosa qeya yana Duba qofar shima yace ' kin Santa ai da shegen son jiki Bacci fa takeyi a cikin Motar ta wani Maqale jikin Hamma Yusuf Shiko Ya wani rashe wai baya son ta tashi Harda wani cewa Mu bamu da nitsuwa bamuga tana bacciba. Dry Ummi tayi Cikin Tsokana tace ' gashi a bayanku ai! Aiko a tare suka juyo Sai kuma sukayi dry. " a motar kuwa Cikin sanyi Ya sunkuyo Kanta hankali ya rinqa busa mata iska a kunneta Itako jin iskar ta qara sakewa tayi Luf ta juyo Qirjinta sama, Murmushi ya danyi Cikin Jin dadin Yadda take Murza shi Kiranta yakeyi Amman shiru Sai sauqe numfashi takeyi, Ganin haka yasa shi Cikin Qworewa Ya qara manna ta jikinshi A hankali ya tura hannushi Bayanta Zip Dinta ya zuge cikin Hikima ya maidata kan cinyarsa Hannushi Ya Dan tura cikin Rigarta Lkci daya ya dire hannushi kan bres Dinta A take kuma ya lumshe ido ya sauqe ajiyar hrt, A hankali yasa Dan yatsanshi ya rinqa zagaye bakin bres din Cikin Sauyawar voice Ya rinqa kiranta A,ishhhh A hankali ta bude ido Tare da Dan tsura mai idon Sai kuma ta Dan tura baki Cikin Muryar bacci tace ' Hammaaa Yusuffffffffff Ido ya tsura mata cikin D'aga mata Gira Hannushi ta Dan kama A hankali ta jawo hannu Shi kuwa Kai ya karya Yayi fuskarta tausayi Cikin Sanyi yace 'Aish In Neman alfarma ki zo gareni mu kwana tare Wlh bazan iya kwana banji duminki ba Plxx karki manta ni Baki ta Dan tura tana 'Hamma ni a gun Ummi Na zan kwana, Cikin Tausayawa kanshi Yace Mijinki kuma ya kwana Da waye Kamata yayi ya ruqqume cikin Tsokana yace Yarinya ki Adana mijinki Ummi ma ba dakinta zata kwana ba. "Tureshi ta danyi Ta bude qofa ta fito Shima fita yayi Ya zagayo yazo gabanta Cikin Gyara net dinshi Ya juyata Ya tura hannushi Ta gabanta ya lalubo Bres Dinta ya shafa cikin Rada yace Zanyi miss dinki Tabas itama taji Hamma a jikinta Shiyasa Sai ta lumshe ido Kawai. Tana bude idon Ta haqqo su ya Abubakar da Ahmad da Adam Da sauri ta janye jikinta Cikin Happy ta isa garesu Da Dan gudunta Tana zuwa kamar zata fada jikin ya Abubakar Sai kuma ta tsaya cikin Farin ciki Tana ' Oyoyo ya Abubakar Na nayi missing dinka sosai Shima Abubakar dry yake cikin Jin dadin ganinta da yanayinshi Na tsantsar qaunar yan uwanshi Yace Allah sarki Aysha wato yanxu kin girma Kin dena Son jiki, Dry tayi ta kamo hannushi tana Bazan girmanwa Dan uwana ba ai, Su Ahmad kam dry suka rinqa yi Har suka qarisa gun Yusuf Cikin Qaunar juna suka ruqqume juna Suna dry A hankali Yusuf ya qarisa gun Abubakar ya ruqqume shi Cikin Qaunar qanin nashi Yace *Babiker* dan Haka yake kiran Abubakar din yana don tsokanarsa tun suna yara bare kuma da ya zama dole akwai Dan reni a tsakaninsu Na irin shi Abubakar shi yake bin Yusuf a aihuwa. Dry Abubakar ya danyi Sai kuma ya matse Yusuf a jikinshi Cikin Sanyi da qaunar Dan uwana nashi yace Hamma Yucut Haka yake kiransa lkcin yarinta Shima Yusuf dry yayi Sai kuma yayi shiru Jin Abubakar bai sakeshi ba Kuma Sai Zuciyrsa da yaji tana bugawa da qarfi-qarfi. Cikin sanyi yaji Abubakar Na rada mai Hamma Yucut NAYI kewarku Ji nake kamar Na bar aikin Sojannan Na dawo Mu zauna nima in rayu cikin yan uwana kafin mutuwa ta rabamu, Da sauri Ahmad yace Haba Abubakar meyasa zaka Sa mana tsoro a zuqatanmu. Adam yace Gsky Abubakar banson irin zantu kan nan naka, Dry ya danyi Fuskarsa tai Ra's a zahiri Dama da yawa kance kab yaran gidan Abubakar ya fisu Kyau danshi Tamkar balarabe yake Ga qira ga cikar zati ga haiba sannan shi mai yawan fara,ane da son Al,ummah Dan shine qarami a Kansu Amman kab ya fusu tsawo da qiba, Cikin fara ar yace Toh ai rebuwa ya xama dole Brothers Na, Aysha kam Tuni Ta fara hawaye Dan ita tun kan ya Ahmad bata son jin irin zantu kan, Dry shi kam Abubakar yake tare da jansu suka tafi cikin gida. A babban parlon suka Zauna akayi ta hira Aysha ko da ta ga Ummi Sai tayi qasa d kai Itako data gane Sai ta shereta sannan ta saki jikinta.. "Bayan 2 week, Rayuwa ta musu dadi kamanni Family ya cika da Farin ciki Abubakar ma har yanxu yananan Gaba daya ya qara shigewa jikin yan uwanshi Tuni hutunsa ya qare Amman yaqi komawa yace yana son shima ya rayu da yan uwanshi Kuma yana son ya jejje xiyara gun yan uwansu Haka ya rinqa Jan su Yusuf da Ahmad suna kutsawa cikin yan uwa da abokan arziqi Har qauyuka saida sukaje. " shiko Yusuf yakan Dan lallaba ya dauke matarsa su arece hotel ya dirka mata qwoya suje sui ta macewa juna, Gaba daya yanxu Ya maidata Fulawarsa abin qawanyarsa. "Yau da dere Suna parlon suna cike suna hira Abubakar ya Dan gyara zama Cikin Kallon yan uwanna shi Yace 'Ya Adam Gobe nefa zamu je yolan Dan Inaga Na kusa komawa wurin aiki Gashi Hamma Yucut kuma saura 2 weeks Ku koma Saudia ko? Kai ya gyada mai cikin Tsurawa Dan uwana nashi ido Yace 'Ko Sai yaushe zamu kuma haduwa ne Babiker kam? "Cikin dry yace 'Wata qil har Abadan! !Gaba daya suka zuba mai ido Cikin Fada baba bello yace Kai Abubakar wannan wanne irin furucine Ummi kuma Kai ta rinqa juyawa Tana Allah ya rufamin asiri Nenne CE tace Amin Rabbi ya hanemu qara ganin wani gibin, " shiko dry yayi cikin cewa Yoh ai mutuwa ta zama dole dama rayuwa wata ran Farin ciki wata ran bakinci, A haka suka watse Sai Yusuf da duk jikinsa Ya mace Ya kalli Aysha da ke shirin Fita cikin Muryar tausayi Yace Amrita zoo, Kamar ta fita Sai kuma ta juyo Cikin Sanyi Tazo Gabanshi Hannushi ya miqa mata Cikin Mutuwar jiki Yace ' tai maka min in tashi Kamo hannu tayi ta ja Shiko ya yunquro da gyer Ya miqe, Sai kuma Ya fiz gota jikinsa Cikin Rada yace Muje ki taimaka kamin Ko kuzarina zai dawo Wala Allah d'umin jikin ki ya farfad'o dani Haka ya jata har zuwa Dakinshi.... ? *MI,WASMITI* page 1⃣1⃣1⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 ⸽⸽H⸽⸽u⸽⸽s⸽⸽s⸽⸽a⸽⸽i⸽⸽n⸽⸽a ⸽⸽m⸽⸽y ⸽⸽l⸽⸽o⸽⸽v⸽⸽e ⸽⸽m⸽⸽y ⸽⸽h⸽⸽e⸽⸽a⸽⸽r⸽⸽t ⸽⸽m⸽⸽y ⸽⸽s⸽⸽o⸽⸽u⸽⸽l ⸽⸽m⸽⸽y ⸽⸽b⸽⸽r⸽⸽e⸽⸽a⸽⸽t⸽⸽h ⸽⸽m⸽⸽y ⸽⸽e⸽⸽v⸽⸽e⸽⸽r⸽⸽y⸽⸽t⸽⸽h⸽⸽i⸽⸽n⸽⸽g ⸽⸽s⸽⸽u⸽⸽g⸽⸽a⸽⸽r ⸽⸽o⸽⸽f ⸽⸽m⸽⸽y ⸽⸽t⸽⸽e⸽⸽a ⸽⸽t⸽⸽h⸽⸽i⸽⸽s ⸽⸽p⸽⸽a⸽⸽g⸽⸽e ⸽⸽i⸽⸽s ⸽⸽f⸽⸽o⸽⸽r ⸽⸽y⸽⸽o⸽⸽u ⸽⸽f⸽⸽r⸽⸽o⸽⸽m ⸽⸽A⸽⸽d⸽⸽m⸽⸽i⸽⸽n ⸽⸽A⸽⸽b⸽⸽d⸽⸽u⸽⸽l Kan gado suka zauna Cikin sanyin jiki Ya zame ya kwanta kan cinyarta Yasa hannu ya zagayo bayanta ya tura kanshi tsakiyar qirjinta yayi luf kamar mai bacci Sai numfashi yake sauk'ewa a hankali Gaba daya jikinshi yayi nuk'ui Ita kuwa jikin gadon ta Dan jingina Dan har cikin ranta take jin tausayi Hamma Yusuf din nata Hannu tasa ta tallabe kanshi Kamar K'aramin yaro Ya k'ara Nanuk'arta A haka har zuwa wani d'an lkci sannan ya d'an d'ago cikin tsura mata ido yace "Amrita ki kwanta ko" Ido ta lumshe cikin Sanyi ta zame tayi luf Jikin pillows Shima k'ara matsota yayi A hankali ya manna ta jikinshi Jikin a sanyaye ya sabule Rigar jikinta Ya barta daga ita sai d'an gajeren wondo Shima hakan yake Jawota jikinshi yayi tare da da daura hannushi kan cikinta ya rink'a shafawa da d'an latsa cikin, cikin rada yace "A,ish Kina mana addu,a kuwa? A sanyaye tace "Addu,ar me fa?" K'ara matsota yayi cikin d'an Rawan jiki yace " addu,ar samun ciki mana Wlh inason baby inson inga jinina gashi har yanxu shiru" Baki ta d'an tab'e cikin yanayin ba damuna tace " ciki kuma aihuwa kuma yanzu gsky ni kam ban isaba" !Cikin mmk da jin tsoro da zafin mgnar ya tashi zaune ya tallabota Murya Na rawa Yace "Ayshaaa Sai yaushe kenan? Me kike nufi da baki isaba Plss ki taimaka kar ki datsemin hanyar Samun cikar burina da zuriya ta Yanxu ke ko Yusuf k'arami da Ahmad basa baki Sha,awa? Juyawa tayi cikin Yatsuna fuska tana " ni bacci nakeji" Abin ya bashi haushi shiyasa cikin Hatsala ya juyota gareshi A fad'ance yace "Sau nawa nake sheida miki ba,a juya min baya Meyasa bakya jin mgna ta Nace miki Muddin muna kwance tare ki dena juya min baya ba tare da izinina ba wlh Aysha kina cutar da zuciya ta da jikina duk sanda kika juya min baya Ki gaya min mana inma kin gajine Sai mu canza gefen kwanciya mu duka ba tare da kin juya min baya ba" Shiru tayi a ranta tana Na shiga 3 da hali irin rin Na Hamma Yusuf Yanxu ko kwanciya Sai ya tsara min, Shiko Juyata yayi shima ya juya A hankali ya dire hannushi kan bres d'inta murya na rawa Yace "A,ish dan Allah ki dena juya min baya Ki tausaya min wlh ni kadai nasan zafin da nakeji in kika bani baya. Shiru tayi Sai Jikinta da ya fara sakewa da mimmik'ewa sabida sak'onnin Hamma ta da take karba A hankali ta Narke cikin jikinsa murya a sanyaye Tace " Hamma Yusuf bacci nakeji Plxx kayi haquri Yau ka barni Na huta" Kai ya gyada mata Cikin K'ara ruggumota Tare da rada mata " ba abinda zan miki Kiyi baccin ki" a haka suka kwana cikin jikin juna Har zuwa safiya Bayan ya dawo masallaci Cikin gida ya wuce A parlon ya samu Abubakar da su Usman Duk suna riqe da carbi Abubakar ne ya kalli Yusuf cikin Murmushi yace "Hamma Yusuf Gwara aje a fara shiri.fa Dan su Usman kam har sun shirya" Fuska ya yamutsa tare da cewa " Sara kunan yawo ai su da sunji tfya jikinsu har bari yake, Dry Abubakar din yayi gami da cewa toh nima dai kaga tfyata bari inje in shirya, Yana fita shima Yusuf ya fita bayan ya gaida iyayenshi. Tsayuwa yayi yana k'arewa gadon kallo bata nan Har ya juya Sai kuma ya jita a toilet alamar wonka takeyi Zare jallabiyar jikinshi yayi gamida tura k'ofar ya shiga Itako jin motsin shigowarsa yasa ta bude ido Lkci daya kuma Sai taji kunya ta rufeta ganin yadda ya tsura mata ido Shiko matsota yayi ya tsuguna gefen ta Yasa hannushi cikin ruwan ya d'an d'ibo ya zuba mata kan kirjinta Yasa hannu ya dauko sabulu cikin sulbi Ya rinqa murza sabulu kan k'irjinta yana shafawa, A take yanayinshi ya canza ya fara piki piki da ido Lips dinshi suka fara rawa lkci daya sukayi jaa Tuni ya kamo gefen lips d'in ya fara tsotsa Duk ya cika ruwan da kumfa ita ko ido ta tsura mai a ranta tana jinjina halitta irin ta Hamma Yusuf Mutum kamar maye. Cikin sanyi taji yana mgn "Ohhh shmmmhhhht Amrita Sai kuma ta jishi Tsulum cikin ruwan Lkci gida kuma ya fara yamutsa ta Tuni ya birki tata itama Sai Lafewa take a jikinshi K'ok'arinshi ya samu kanta ya rege zafi Ita kuwa tak'i Sai nok'ewa take Suna cikin haka yaji ana buga musu k'ofa. aiko ta yamutsa ya cukuikuyeta son ranshi Itama ta taimaka mai Don ta samu ya barta Sai da ya d'anji gamsuwa sannan Ya fesa mata wonka Ragusa kanshi Ya mik'e ruggume da a barsa Sai hada fuska fa yayi Shi a dole an takura shi Ba a barshi ya shanaba. Ta gane sarai Shiyasa suna fita ta zura rigarta har taje bakin k'ofa ya kirata Cikin isa. Gabanshi ta Dan tsaya Shi kuwa mai ya mik'a mata Fuska a hade Yace " kina k'o'karin tafiya Wazai Shafa min mai? Karba tayi ciki tura baki a ranta kuwa Cewa take Wlh Hamma Yusuf ya fiye kalen fitina, Shiko zama yayi Ra's yana tsura mata ido Dole ta rink'a shafamai Har ta gama Y klta cikin Sigar k'auna da Sha,awa yace " jeki shirya Habitti yau zamuje Yola" Sosai taji dad'i Dan batayi zaton dasu za,a jeba Cikin happy Ta tallabo Kanshi Ta hade bakinsu Ta laso lips dinshi Sannan Ta sauk'o zuwa k'irjinshi Ta rink'a shafa sumar k'irjin Tana sakemai kiss tako ina Sai kuma ta juya da gudu tayi cikin Gida. Shiko murmushi ya rink'ayi yana shafa sajenshi da k'irjinshi Dan yasan guraren Na burge Ayshansa. Haka dai suka kammalah Shirin su. K'arfe 9 dai dai Sukayi SLM da iayensu Sannan suka yi musu addu,a Suka shiga Mota suka tafi Mota 2 ne 1 Abubakar ke tuk'i Ahmad Na gefenshi Aysha da Maryam Na baya Yusuf Na baya shima gefen Ayshan Sa Sai dayan kuma Adam ke tuk'i Amira Na gefenshi Sai Usman da Rabi,u dake Baya Tafiya suke cikin nishadi Motar su Na biye da juna. Sunyi tafiya mai d'an nisa har zuwa Wuraren *zim* Sun fara hank'o *Mayo balwa* Aysha da tun sanda sukayi nisa a tafiya jikinta Ya mace tayi nuk'ui jikin Mijinta Sai nuk'urkusarsa take Tana ita murd'a takeji Aman kuwa yak'i zuwa Sai yanzu. Ta samu ya tokarota Cikin Wahala. Ta kamo hannushi ta rik'e Jikinta har rawa yake Cikin Kuka tace "Hamma Yusuf Amai zanyi Amai" Shiko Yusuf da gaba daya Ya rude dukkan tausayinta ya cikashi Cikin Kula ya tallabota Ahmad dake gaba rik'e da Yusuf k'arami Ya zaro Blanket din yaron Ya mik'a mata yana "Hingo biyaye bata tayi aman a ciki" Karba yayi ya shinfida kan cinyarsa. aiko ta rink'a zuba amai Kafin kace kobo Duk tayi laushi Sai numfashi take sama sama Maryam kam sai sannu Take tayi mata Shiko Abubakar gudu ya k'ara yana "Sorry sis Bari nayi sauri mu isa Asbiti ma zamu wuce Cikin Aman tace A a ya Abubakar ni Ku kaini gida inma mutuwa zanyi Na mutu a gida. Da sauri Yusuf ya ruqqumota cikin Rawan murya yace " a a insha Allah ba abinda zai sameki. Haka dai suka isa Itako gaba daya ta gala baita. Dama tuni marya ta gayawa Baba Umar Tuni Shiko Dr Umar ardo Ya tanadi Norse Guda biyu Allah sarki Yusuf gaba daya ya rud'e Duk jikinshi Amai Suna isa Ya ciccibota A parlon ya direta kan 3str Ayyah. Hydar shima gaba daya ya rude Fifita yake mata rik'e da hannuta Yana sister Ki bude idanki Ga ya Hydar dinki Goggo Aysha ma duk Sai Jikinta ya mutu Tana Farin cikin ganinsu gashi wannan Abu ya kassarasu. Shi kam Yusuf Tallabeta yayihar zuwa sanda Baba Umar ya iso Gida Suna zuwa Suka fara yiwa Aysha gwoje-gwoje Lkci daya Suka gano Ciwon dake haddasa mata aman Cikin tsantsar Farin ciki Baba Umar Ya kalli Yusuf Da yayi kalan tausayi Yace "Congrats Yusuf Sai kuma yai Murmushi ya fice Yana An mata allurar bacci Yancu tayi wonka Tana tashi komai zai Normal. Abubakar ne Ya mik'e cikin Farin cikin ya ruggume Dan uwanshi Yana dry Yace " Alhamdulillah Hamma Yusuf Allah ya amsa addu,a ata Ase ba zanyi Kukan rashin aihuwa ba Hamma Yusuf wannan cikin Ko macece ko namiji ne Ni za,a bawashi Shima Yusuf murna da tsantsar farinciki Kawai Sai ya ruggume k'aninshi Yana mai zubda qollan Farin ciki Yana " Babiker Na bakashi Insha Allah kome aka samu.nakane Babiker ba zakayi Kukan rashin Aihuwa ba Dan uwana. Allah sarki Gaba daya Sai Suka cika da Farin ciki da tausayi Rashin aihuwar Abubakar Hydar ma Sai K'ollah yake sharewa Yana Allah ya raba su Lfy Shi mahaifi yarsu ya tuno. Shiko Yusuf so yake ya ganshi dagashi Sai Matarsa ya ruggume abarsa ya kula da ita Ya riritata Amman INA tuni Goggo Aysha ta jata sunyi Cikin D'aki Maryam da Amira ma suka bi bayan su Itako Aysha Sam batayi Farin ciki da cikinba Kuka ta rink'ayi Da k'er tayi Wonka suka dawo Parlon inda suke Cike Gaba daya Sai ya zama duk tattalinta suke Amman a hakan shi oga gani yake an takurasu ne Kukan da takeyi har cikin ransa yakejin Kukan Ita ko lkci daya bacci yayi gaba da ita bayan ta konta kan 3str Haka dai Sukuma sukayi ta hiransu da nishadi Da Farin ciki Tuni Goggo Aysha ta sheidawa su Nenne Ummi ko dad'i kamar bazata mutuba. Kai sunyi Farin ciki kam. Shiko Yusuf a takure yake Sam An hanashi Matarsa Yau kwanansu 2da zuwa Bayan sun gama cin Abinci Sun waste Yusuf ya koma bakin gate Ya zauna kamar wani maraya Tsaki yaja yafi a k'irga A fili Yace su wadannan basu da matsala. Yana zaune Sai ga Hydar da maryam Sun shigo Cikin Hade fuska Ya "cekai dady Dayake haka yake kiran Hydar tunda shi tokwaran Abbanshi ne. Da sauri ya iso gareshi Cikin girmamawa yace "Na,am Hamma Yusuf Shiko fuska ya murtuk'e Tare da cewa In ka shiga kace Aysha tazo Ga lamido Yazo dubata yana Part dinka. Toh ya amsa cikin Sauri ya juya Ya tafi. Shiko Ya tafi part din Hydar din, Cikin gida kuwa Aysha tayi wonkanta ta gama shirin Baccin Sai k'amshi Take Hydar ya shigo Cikin Xoleyarta yace 'Mai ciki Kije Ga Dan uwan Hamma Yusuf dinnan Lamido on top yazo dubaki suna can part dina. Aiko su Amira Sai dry Itako Jin haushin dry yasa ta xura k'aton Hijabi Tayi Part din ya Hydar din. SLM tayi ta shiga Sai kuma ta tsaya tana Kallon Komai Na parlon tsaf Kamar dakin mace A fili tace kai Ya Hydar ba dai tsaf taba, Shiko Yusuf jin motsinta ya fito dashi Itako tana shirin lek'a cikin Bedroom din Da sauri ta tsaya Gani Zasuci karo Shiko Cikin rawan jiki Da hannu da wata iriyar muguwar Sha,awa Ya fizgota jikinshi Ya ruggume tare da lalubo.... 🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👇🏻👆🏻👆🏻 *MI,WASMITI* page 1⃣1⃣2⃣Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Cikinta ya rink'a shafawa yana d'an murzawa lkci d'aya kuma ya tallabo konta ya zira harshensa cikin Bakinta ya llbo nata ya rink'a sarrafata da juyata cikin salon k'auna da begenta. Tuni itama ta mace da salonsa ta biye mai sai sauk'e numfashi yake yana binta da kissi tako ina har zuwa wuyanta ya ganggaro cikinta hannu yasa cikin rawan jiki ya d'aga y'ar rigar jikinta kanshi ya manna kan cikin yana shafawa gaba d'aya ya rud'e ya rudata Sai nishi yake, Sam ya kasa mgn, Ganin haka yasa ta kamo hannushi cikin hikima ta jashi zuwa kan gado ta zaunar dashi, Itama ta zauna gefenshi Sannan ta tallabo kanshi Cikin rad'a tace "Hamma Yusuf jikina ba k'arfi, duk kasala nakeji bansan ya zanyi ba gaba daya banjin dadin rayuwa ta".. Matsota jikinsa yayi cikin rawan jiki Ya ruggume ta jikinshi, ya rink'a shafa jikinta' Yana murza fatan cikinta Cikin rad'a yace " Ayyah Amrita Na sannu zai bari insha Allah Babynmu ke saki kasala Zan mishi fada ya daina wahal min da noor hayat dina". Baki ta d'an tura tace "Gsky ni bazan iyaba Wlh kasan yadda zakayi dani". Jawota jikinshi yayi ya sabule y'ar rigar jijintan gaba d'aya sannan ya janye nashi ya jawota suka kwanta, Murya Na rawa yace " Zo zonan kinji Ya habitti zan miki Allurar kuzari zaki daina jin kasala, Ta nan kuma zan isar da saqona zuwa ga d'iyarmu ta dena wahal da Amminta". yana mgnar ne yana shafe Ababenshi da yayi kewarsu tsawon 5 days. Itako hannushi ta riqe cikin shogoba tana "Hamma Yusuffffffffff Bazan iyaba plx ka barni Na huta jikina ba k'arfi". Cikin rawar murya da kid'ima ya matsota Jiki a hargitse yace " Dan Allah Na tuba plxx ki taimaka min wlh Na Gaza hak'ura jina nake kamar Na shekara ban rab'eki ba ke nake bege ke nake muradi". Zuwa yanxu itama da kanta tasan tayi kewar mijinta Na mijinki duniya dole ta yi cip Tuni ta shiga maida mai martani tana mai mak'al k'alemai Tana zuba mai shogoba shiko ya shiririce ya xauce kanta ya biye mata Ya zama tamkar sauna, Haka dai a birkice suka mak'alewa Juna Itama Aysha da kanta tasan tayi kewarsa Dan zuwa yanxu ta fara sabawa da nacin Hamma Yusuf Dolenta take jajircewa Dan dauke mai buk'atunsa gudunkar ya fada wata rayuwar, Haka suka rink'a farantawa juna har zuwa wani lkci sannan suka sahirtawa juna, Cikin gamsuwa ya mak'alota kan faffadan qirjinshi ya daura hannushi daya kan cikinta d'ayan kuma ya daura kan bres dinta yana shafarsu da latsarsu Cikin gamsuwa Jiki a sake da d'an rada yace "Amrita Kin San cewa cikinnan tun Fats night dinmu Kika cabesa Kika ajiye min Gsky Amrita Kin iya karbar sak'onnin Hamma Yusuf dinki",😍😎 Kanta ta tsune cikin k'irjinshi tana 'kai Hamma Yusuf ai kaine abin naka ba sauk'i Ba dole ciki ya shige ba Ka mammak'ale min Ka hanani sakat". Dry yayi ya shafa bres Dinta Cikin Nishadi Yace " ke dince Tamkar xuma kike ba,a miki lasa kadan a gaji Dole kike birki tani kike hanani sanin koniwaye kece kike dauke Control dina Muddin najiki cikin jikina Macewa nakeyi". Kanta ta kuma tsunewa tace "Gsky Hamma Yusuf jarumtarka tayi yawa" k'ara rufeta da k'irjinshi yayi Yana "yanxu ma k'ari nakeso wlh A,ish" Tallabe kanshi tayi Cikin rada tace " A,ish takace Keutar da rabbi ya maka ne Hamma Na ba wani hijabin a tsaka ninmu" Wayyo Yusuf gaba d'aya ya haukace ya kid'ime da kala manta da salon da take mai tuni suka macewa juna, Juyata yake iya son rensa. Itako Sai zautar dashi take da salonta. A haka suka kwana cikin nishadi, Kashe gari da asuban fari ta koma cikin gida a daki Ta samu su Amira Maryam Na ganinta ta danyi dry Cikin tsokana tace " ni kam Aysha yaushe kunyarku ta bace ke da Hamma Yusuf? Da gani ake duk kun fimu kunya haka shima Hamma Yusuf ake ganin yafi su ya Adam kunya Amman yanxu duk kun fitsre idonku" Kai ta Dan sunkuyar cikin Sanyi tace "wlh Tausayi ya bani Maryam saifa kinga yadda ya zama gaba daya tunda muka zo a takure yake Nima kaina INA tunashi Shifa Hamma Yusuf Ko bacci Bai yin mai dad'i in baya tare dani" Dry Amira tayi cikin shewa tace Yarinya kin zama yar hannu Hamma Na ya gama cika aiki" Hararanta tayi cikin Kwanciya da shirin Dan yin bacci Tana "Hmmm Hamma Yusuf Da banne Nima bansan San da ya maidani haka ba" Maryam CE tace "gskyanki Ki kula da mijinki Dan wlh ni da kaina jiya Na tausayawa Hamma Yusuf saifa kinga Yadda idanunshi suka koma kamar bugegge ase duk Jarabar tsiya ke cinsa" Mari ta Dan d'aka mata cikin Kunya tace "kin dai ji jiki Namma yayanki ne" haka dai sukayi ta dry. Kwanansu 4 a Yola duk sun zaga dengi sunje har gidansu Ummi, sun yawata cikin Yola son ransa Yusuf ko ba ruwanshi kiran matarsa zai su Shana a d'akin Haydar. Sannan yau suka koma Taraba Cikin kewar juna Hydar Kamar kar ya rabu dasu, Sun dawo cikin Farin ciki Gida akayi ta murna. Aysha ko tunda ta dawo Laulayi yace bas millah Komai taci Sai ta Harar Ga jiri Ga yawan bacci Gaba d'aya Kowa ya maida kulanshi gareta Ita kam ji take kamar tayi hauka Dan wahala duk Sai taji ta tsani cikin Da zaran ta keb'e da Hamma Yusuf Dinta tai ta kuka Shiko Sai dai yayi ta lallabata da bata hak'uri Dole tasa ya rink'a danne buk'atarsa, Ya Abubakar ma kula yake bata sosai. Yau saura kwana biyu Abubakar ya koma duk ya gama shirinsa Suma su Aysha saura 6 days su koma. Yau tun da safe Aysha keta fama da amai da jiri Komai taci Sai yayi woje cikin kuwa har ya fara d'an tasawa Dan yanxu ya kai 3 month. Zaune take Gaban Hamma Yusuf din a parlon Ummi ta d'aura kanta kan cinyarsa Ummi dasu Abubakar da Usman da Ahmad duk suna Zaune, Kuka take tana matse cikin Tana lumshe ido Cikin gala baita take cewa "Wayyo jikina cikina Ni kam naga ta kaina Wlh Na gaji da cikin nan Hamma Yusuf wlh kasan yadda zaka min". Kai ya sunkuyar cikin jin juya Wato tun dashi ya mata cikin Shi zaisan yadda zai mata gashi Duk shi a matse yake dan ya fara carkewa kwana ba adadi taren suke kwana Amman dole yake barinta Dan tausayinta da yakeji Itako Sai ta kwana nuk'urk'usansa Ummi har tsoro takeji Aysha tace a d'akin ta zata kwana Dan hanata bacci takeyi Shiyasa ita da kanta take cewa tashi kibi Mijinki Ni bazan iya sakalcin kunnan ba. K'ara matsoshi tayi cikin Jirin tace "Wlh Na gaji ni zan San yadda zanyi" Shiko ido ya tsura mata gami da Tashi yana cewa Ahmad "B'iyaye mu tafi", Mik'ewa Ahmad yayi cikin Dry yace "sannu ko Auta zai bari kinji In anyi Sa,a yana cika 4 month zai bari" Baki ta tura tana "Inadai ya Ahmad harda kai kuke min dry" Shiko Yusuf hannushi yaja suka fice d'akinsu sukaje suka Dan Sha hira sannan Ahmad ya tafi Shiko yayi shirin kwanciyarsa ya d'an kwanta a cewarsa kafin Sakaliyarsa ta zo. Itako tana shiga Ta zauna cikin gajiya da wahalan cikin, Tashi tayi ta d'auko Pose Dinta Cikin tsoro da k'arfin guiwa Ta balli mgnin da ta seya tun a Yola tsoro ya hanata Sha Ido ta rumtse Ta d'aga Harshenta tasa k'wayar a kasan harshen ta tana Haba wlh gwara Na huta Na gaji. Wonka ta shiga cikin K'arfin guiwar zata rebu da bone Ta fito ta kimts tsaf A fili tace "Yau bazanma je gun Hamma Yusuf ba". Ta kwanta cikin Sanyi lkci Daya taji sanyi ya fara rufeta a hankali ta lashi k'wayar taji Ya fara narkewa Ajiyar hrt ta sauk'e a take kuma taji Jikinta ya fara rawa Sai zufa ta fara ketowa a jikinta A take kuma taji Mararta ta carke Sai wani irin suka takeyi Tuni ai ta tashi ta zauna Wasa wasa Sai k'aruwa abin yakeyi Ban daki ta shiga Dan wani irin fitsari takeji tana tsuguna wa kuwa taji ta kasa yin fitsarin ta tashi ma ta kasa Sai dafe gini tayi ta samu ta mik'e, Shiko Yusuf gaba daya Kewarta dakewar babynshi sun hanashi Bacci So yake yaji d'umi cikin da nata d'umin ga begenta dake cinsa, Ya kirata yafi a k'irga bata d'agaba So Sai yake zaton ko ta samu tayi Baccin Kar ya tada ita A haka ya kwana cikin Takura A ranshi kuma yana ya gaji da hak'uri. Ita kuwa Aysha kafin zuwa k'arfe 4 ta gama fita hayya cinta duk ta birkice Kuka takeyi cur cur duk ta hargitse dole taimako take nema da tsoro ne ya hanata zuwa d'akin Hamma Yusuf Amman zuwa yanxu ta manta menene tsoron Dan azabar da takeji Cikin wahala ta fice ta nufi part dinsu. Shi kuwa 4 dai dai ya tafi masallaci d'an rege matsalarsa da nafilfili. Tana shiga tana ki ranshi "Hamma Yusuf cikina marata zan mutu" ganin baya nan yasa ta zame kan gado ta rink'a murk'ususu. Shi kuwa saida akayi sallah sannan ya wuce Cikin gida a parlon ya samu Ummi Suna gaisawa ya d'an Kalli Ummi a Dan kunyace cikin d'an fara,a yace "Ummi yau dai Auta tayi bacci kenan? Kallon shi tayi cikin fahimta tace "ba gunka take bane"? Kai ya gyada cikin Sanyi yace "a a bata jeba" kitchen ta shiga tana "a a kake dai ka Duba!" Toh yace gamida ficewa ya nufi d'akinshi kai tsaye Yana shiga ya hanqota kan gado a hargitse Sai murk'ususu take Duk ta hargitse Tana ganinshi ta mik'e cikin Wahala ta fada jikinshi Shiko a buk'ace ya ruggume ta yana " "ohh Amrita I missi u plx ki tai maka" Itako cikin Kuka ta k'amk'ameshi Ta manna hannushi kan mararta tana "Wayyo Hamma Yusuf Cikina marata zan mutu" Cikin tsoro da firgicin yedda yaji mararta tayi tauri ga wani irin zafi da marar tayi ya tallabo kanta cikin tsura mata ido yace "Amrita yaushe ya fara miki? Kin gayawa Ummi kuwa? ya akayi haka ? Duk ya rude dai dai lkcin taji wani irin axaba da suka daya sok'i mararta K'amk'ameshi Tayi gami da sakin wani irin k'ara ta kuma bude Baki zatayi k'arar. Shiko cikin kidima ya zura harshensa cikin Bakinta nata harshen ya lalubo har zai kamo harshen ta da nufin hanata kukan Sai kuma ya tura harshensa k'asan nata Dan jin wani irin d'and'ano da ya bashi tsoro Ido ya zaro cikin Firgici ya tallabo kanta Murya Na rawa yace " Aysha me kika Sha? Me a k'asan harshen ki"? waya baki mgninan? ido ta tsura mai ciki tsoron ganin yadda ya hargitse. Fixgota yayi cikin rawan jiki yace "Wanne Dan iskanne ya baki wannan mgnin"? Kai ta rink'a juyawa cikin tsoro lkci d'aya kuma ta sunkuyo ta kalli cinyarta jin damshi Na bin k'afarta. Shima ido ya Sada k'asa ganin jininne ya fidda hankalinshi Jikinsa wata iriyar tsawa ya buga mata cikin fizgo hannuta yana " Aysha Xubar min da cikina zakiyi Cikina kika zubarmin? Sai kuma ya jata da k'arfi ya nufi part din Ummi A part din Ummin kuwa su Abubakar da Usman har dasu Ahmad da Adam suna Cike a parlon Cikin firgita da kidima yana shiga da itaya angi....... H̶A̶U̶S̶A̶ N̶O̶V̶E̶L̶S̶ S̶O̶K̶O̶T̶O̶: W̶H̶A̶T̶S̶A̶P̶P̶ N̶O̶: 07068808039 W̶E̶B̶S̶I̶T̶E̶: A̶b̶d̶u̶l̶m̶k̶i̶b̶a̶b̶.h̶e̶x̶a̶t̶.c̶o̶m̶ ?🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👆🏻👇🏻👇🏻 *MI,WASMITI* page 1⃣1⃣3⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Gaban Ummi ya jata suka tsaya murya Na rawa cikin kidima yace "Ummi kalli, kalli abinda Aysha ta aikata min" Itako Aysha Sosai tsoron shi ya rufeta ganin yadda ya daburce Shiyasa sai k'ok'arin k'wace hannuta take tana ciccije lips dinta Dan azabar da mararta ke mata, Ita ko Ummi ido ta zuba mai cikin rashin fahimta Su Ahmad ma duk ido suka zuba musu cikin alamun tabbaya. Ummi ce Tayi Dan ajiyar hrt cikin dan mmk tace "mene ta aika kuma? kai da baka rebo da fitina". cikin takaici da zafin abin ya zame k'asa a hankali murya Na rawa da alaman kuka ya rik'o hannu Ummi Cikin Cikar bakin ciki Yace " Ummi Ki kalli jikin Aysha fa Ummi cikina ta zubarmin Ummi meyasa meyasa haka Me laifin yarinyar da bata zo duniya ba me tayi da za,a kasheta Ko ni laifin me nayiwa Aysha da bazata ita yace min ba Ummi inma laifi nane ai ba kan 'yata ya kamata Aysha ta rama ba" Lkci daya kuma Sai hawaye shur shur a fuskarsa Gaba d'aya Su Ummi suka cika da Al,ajabi Su Ahmad kuwa ganin hawaye a fuskar b'iyayenshi ya tabbatar abin ya girmama. ya Abubakar ne ya mik'e cikin Zullumi ya tsaya gaban Aysha fuska a tsorace yace "Auta dgske zubar da cikin kikayi gaya min gsky dan Allah meyasa kika zubar da cikin da muka dade muna tsumayi Auta da gske kin kauda Farin cikin mu"? Kai ta rink'a juyawa tana matse ciki ga zufa dake keto mata tako ina ga jinin da takeji yana bulbulowa cikin wahalan tace " a a ni ban zubar ba ba abinda nasha" Cikin kad'uwa Ummi tace "Dama ya za,ayi ta zubar da ciki Inama zata San salon zubda ciki yarinyar da ba abinda ta sani Shi dai fitina yakeji" Shiko Yusuf cikin Kuka kamar yaro yace "wlh Ummi zubarwa tayi ai naga abinda tasha kuma Na jishi Wlh zubarmin da jikina tayi Ummi wlh kashe min 'ya tayi" Ahmad ne ya dafeshi cikin tausarsa yace "B'iyaye ka nitsu Mu tabbaya yeta Dan ni inaga zaiyi wuya tasan yedda zata iya wannan abin" cikin kad'uwa da jin ta kaicin yau Ahmad ma ya kasa gsktashi ya kallesu Cikin Rawan murya "Yace Wlh xubarwa tayi Ummi Gata Ku abinci keta"! A hatsale Ummi tace "ni dai banga komaiba Sai dai in Kaine zaka bin cike ta sannan mu kuma mu abinci keka" Jin haka yasa shi mik'ewa jiki Na rawa ya fixgota jikinshi Ya tallabo kanta Cikin bakinta ya tura yatsarsa Dan dauko guntuwar k'wayar Sai kuma yaji ta narke Sai dank'onta A harzuk'e Ummi tace "kai tafibcan sake yarinya mu tafi asbiti ba abinda tasha zaka bita da mita bayan tana fama da azabarta" rai a cushe ya k'ara jawota ya matsota jikinshi da k'arfi bakinshi ya manna kan nata cikin Rawan jiki ya dannan harshensa dai dai inda ta manna k'wayar ya rink'a goga harshensa Sannan ya zaro harshen nasa cikin carkewar murya ya zare harshen ya nunawa Ummi tare da cewa "Ummi kinga ni ko kinga abin da ta manna a bakinta Biyaye ka duba, Jiki a sanyaye Ummi ta tsura mai ido ganin harshensa yayi wani yellow Abubakar kuma Juyawa yayi cikin Zubda qollah ya zauna kan 1 str murya Na rawa Yace " Auta meyasa ya za,ayi ki zubda ciki Kinsan illar hakan kuwa Auta kisan kaifa me cikin ya miki" Ahmad ko Cikin takaici yace "Aysha kinji kunya Kin cutar da mutane da suka yerda dake wlh kin dasa mana takaici a rayu kanmu Ke wacce iriyar zuciya gareki" Shiko Yusuf k'ara matsota yayi cikin Rawan Murya yace "Aysha kin cuceni kin cucu abinda zaki aifa Har Gaban ubangiji Sai munyi hisabi Kin kashe min y'a A,ish duk tsanar da kike min bai kyautu ya shafi jinina ba Nasan dai nine byake so shiyasa har kika zubar min da ciki Kin cutar da zuciya ta Allah Sai ya saka min Kin yaudari Ummi da ta dauko duk yerda ta baki" Matseta yayi da k'arfi saida tayi K'ara cikin zare ido Yace "Wanne d'an iskanne ya saida miki mgnin? a ina yake? ki gayamin ko shi waye ne wlh Sai Na d'aureshi" Ido ta zazzaro cikin gala baita tace Wayyo cikina zan mutu Ummu cikina " Kicin zafin nama Ummi tamik'e tazo gabansu Hannu ta d'aga cikin Kid'ima ta yarfawa Yusuf d'in Wani wawan mari ta tureshi gefe tana fada cikin Fushi Tana "Haba wannan wanne irin rashin imanine yarinya Na fama da wahalar zuban ciki sannan kun tsare ta da bak'ak'en mgn ganu sannan kai harda matseta Zubar cikifa yafi aihuwa wuya kashe min ita zakayi"? Shi kam Yusuf dafe kunci yayi cikin rawan jiki da tashin jijiyoyin jiki Yana mai zubda k'ollah, Adam da tun dam'azu ya shigo yana jin duk abinda suke fada Ganin marinnda aka kifawa Yusuf Yasa shi shigowa cikin hatsala yana shiga Kan Aysha yayi cikin harzuk'a ya jawota ya rink'a yarfa mata maruka. Ita kam yanzu tsoro da hawala sun dauke ta shiyasa ta fada jikin Ummi tana mai kuka Da cewa Wayyo.ya Adam Na tuba Wlh bazan k'ara ba Cikin Fushun Ya k'ara yin kanta. Shiko Yusuf cikin Muryar kuka yace " Adam barta Ba komai Allah Na sane dani. Allah sarki Gaba daya Sai jikinsu ya mutu cikin kasala Ahmad ya jasu suka tafi part dinsu Adam da Ahmad suka rink'a tausarsa da bashi baki Shi dai Yusuf sai k'ollah yake sharewa Ya rik'o hannu Adam yana "Adam ba laifinta bane 'Kiyeyya CE ta sata haka Aysha bata sona ta tsaneni shiyasa bata son aihuwa dani ni Na nawa kaina tun da Na kasa sawa Aysha ta soni a ranta gashi k'iyeyyar ta shafi y'ayana" Ahmad ne ya rink'a juya kai yana "a a Yusuf Na tabbata Aysha Na sonka ka dena fadar haka" Shiko kai ya jinjina tare da sauk'e ajiyar hrt. A haka dai sukata bashi baki Sannan suka samu ya Dan nitsu, Itako Aysha Abu wasa wasa Jinin ya balle ga ciwon mara kamar k'ara shi ake kafin zuwa 9 Na dere duk ta fita hayya cinta Dole Ummi ta kira Abubakar ya kaisu asbiti dama tun safen Ummi tace suje ita tak'i tana tsoro kar mgnar taje kunnen Abba Aiko suna zuwa asbiti akace Sai an mata wonkin ciki Sannan Sai mijinta yazo yasa hannu Kuma gashin sun gano zunda cikin akayi ba zubar kanshi bane, Abubakar yace Ayi komai Amman Ummi tace a,a a dai je a gayawa mijinta Dole Abubakar ya koma Gida yana zuwa ya sameshi a harabar gidan yana zaune shi d'aya idanshi a rumtse A hankali ya zauna gefenshi cikin sanyi Yace "Hamma Yusuf" A hankali ya bude idon ya zubawa Dan uwanshi Shiko Abubakar kai ya d'an gyada mai alamun kayi haquri Cikin sanyin yace "Hamma Yusuf dama Aysha ne muna asbiti so ance Sai kaje Dan Sai an mata wonkin ciki" Da sauri ya mik'e cikin zare ido yace "a a ban yerda ba wanne k'atonne zai mata aikin ba wani aikin da za,ayi mata" hannu ya mik'ewa Abubakar yace "Mu tafi" Suna zuwa asbiti da kanshi ya shiga d'akin da take Sai murk'usuwa take. yana zuwa Ya kamo hannuta cikin sanyi ya Dan matse Rigarta ya d'an d'aga cikin ya tsurawa ido Gamida shafa cikin Lkci d'aya kuma Idansa ya cika da k'ollah" ya zauna gefen ta Abubakar ya kira cikin Sauri yace yaje gidaya kamo mai Zam zam da Zuma da garin habba. Toh yace tare da juyawa ya fita Shiko cikin Ya rink'a Shafawa yana kauda kai Ita kuwa Duk da wahalar tana ganinshi Sai kife kanta take A haka har Abubakar ya dawo Shi da kanshi ya Hada cikin Sanyi yace Amrita Ido ta bude a hankali ta tsura mai ido LLkc d'aya taji tausayinsa Na ratsata Duk ya fige a wuni d'aya Kai ta sunkuyar ido Na zubda k'ollah Matsota ya kuma yi ya mik'a mata Karba tayi tasha. **** Lkci d'aya ta fara jin sanyin ciwon Shiko tana Sha ya fita a wojen yacewa Ummi Ku dawo gida kawai ba komai Dr yace ya rigada cikin ya fadi Haka kuwa suka dawo gida Ummi ta rink'a bata kula ta mu samman Shi ko Yusuf tun daga ranar ya dena shiga d'akin Ummi Adam fushi yayi da ita Ahmad ma bai ko amsa gaisuwarta Ummi ko tun tana jin kunyar ta har ta saki Dan ko a fuska bata taba nuna mata ba Amman tana jin kunyar abin kam. Yau kwananta 3 kuma jikinta ya d'an worwore da safe . Tana zaune A dakin Ummi Tana goge kayan Yusuf k'arami Taji slmar Hamma Yusuf din nata A hankali ta d'ago kai ta tsura mai ido ya d'an rame Amman kuwa yayi wani irin kyau Sai kuma yanayin shi Na da suka dawo Sam ba wolwola a fuskarsa ko fara,a mishkilanci tab fuskarsa kallon shi take ba ko kifta ido. Shiko a hankali ya zauna can gefe Gamida zaro phone dinshi ya kara a kunne A hankali yace Ummi gani nazo ina jiranki Sai kuma ya katse kiran ya zauna yana latsa phone dinshi din. cikin sanyi tace ("Jam bandu na Hamma Yusuf ") Ina kwana Hamma Yusuf. Bai kulata ba sai kallonta da yayi ta gefen ido Dai dai lkcin kuma Adam da Ahmad suka shigo Kai ta sunkuyar tana mai gaidasu Amman duk ba Wanda ya kulata Sai juyawa da Ahmad yayi yana Biyaye bari inje gun Abba kafin ya fita don tare zamu fita Mik'ewa tayi da sauri tabi bayanshi cikin Sanyi tace Ya Ahmad ga kayan Lamd'o a kaimai da yake bata kiranshi Yusuf sai Lamd'o take cemai shi ko Ahmad yamutsa fuska yayi cikin Gyatsine yace " ni Na kawo kyyane bare in meyar" Da sauri tace Ayyah ya Ahmad kayi haquri ka kai musu Tsawa yayi mata cikin fita yana In sun dame ki Ki jefar dasu Dan nasan ba son harkar yara kike ba. Jiki a mace ta juya kenan Sukaci karo kicibis Ta fada jikinshi Cikin sanyin ta tura kanta a faffadan qirjinshi tare da lumshe idan ta shima jiki a mace... ?🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👆🏻👇🏻👇🏻 *MI,WASMITI* page 1⃣1⃣3⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Gaban Ummi ya jata suka tsaya murya Na rawa cikin kidima yace "Ummi kalli, kalli abinda Aysha ta aikata min" Itako Aysha Sosai tsoron shi ya rufeta ganin yadda ya daburce Shiyasa sai k'ok'arin k'wace hannuta take tana ciccije lips dinta Dan azabar da mararta ke mata, Ita ko Ummi ido ta zuba mai cikin rashin fahimta Su Ahmad ma duk ido suka zuba musu cikin alamun tabbaya. Ummi ce Tayi Dan ajiyar hrt cikin dan mmk tace "mene ta aika kuma? kai da baka rebo da fitina". cikin takaici da zafin abin ya zame k'asa a hankali murya Na rawa da alaman kuka ya rik'o hannu Ummi Cikin Cikar bakin ciki Yace " Ummi Ki kalli jikin Aysha fa Ummi cikina ta zubarmin Ummi meyasa meyasa haka Me laifin yarinyar da bata zo duniya ba me tayi da za,a kasheta Ko ni laifin me nayiwa Aysha da bazata ita yace min ba Ummi inma laifi nane ai ba kan 'yata ya kamata Aysha ta rama ba" Lkci daya kuma Sai hawaye shur shur a fuskarsa Gaba d'aya Su Ummi suka cika da Al,ajabi Su Ahmad kuwa ganin hawaye a fuskar b'iyayenshi ya tabbatar abin ya girmama. ya Abubakar ne ya mik'e cikin Zullumi ya tsaya gaban Aysha fuska a tsorace yace "Auta dgske zubar da cikin kikayi gaya min gsky dan Allah meyasa kika zubar da cikin da muka dade muna tsumayi Auta da gske kin kauda Farin cikin mu"? Kai ta rink'a juyawa tana matse ciki ga zufa dake keto mata tako ina ga jinin da takeji yana bulbulowa cikin wahalan tace " a a ni ban zubar ba ba abinda nasha" Cikin kad'uwa Ummi tace "Dama ya za,ayi ta zubar da ciki Inama zata San salon zubda ciki yarinyar da ba abinda ta sani Shi dai fitina yakeji" Shiko Yusuf cikin Kuka kamar yaro yace "wlh Ummi zubarwa tayi ai naga abinda tasha kuma Na jishi Wlh zubarmin da jikina tayi Ummi wlh kashe min 'ya tayi" Ahmad ne ya dafeshi cikin tausarsa yace "B'iyaye ka nitsu Mu tabbaya yeta Dan ni inaga zaiyi wuya tasan yedda zata iya wannan abin" cikin kad'uwa da jin ta kaicin yau Ahmad ma ya kasa gsktashi ya kallesu Cikin Rawan murya "Yace Wlh zubarwa tayi Ummi, Gatanan a bincike ta" A hatsale Ummi tace "ni dai banga komaiba Sai dai in Kaine zaka bin cike ta sannan mu kuma mu abinci keka" Jin haka yasa shi mik'ewa jiki Na rawa ya fizgota jikinshi Ya tallabo kanta Cikin bakinta ya tura yatsarsa Dan dauko guntuwar k'wayar Sai kuma yaji ta narke Sai dank'onta A harzuk'e Ummi tace "kai tafibcan sake yarinya mu tafi asbiti ba abinda tasha zaka bita da mita bayan tana fama da azabarta" rai a cushe ya k'ara jawota ya matsota jikinshi da k'arfi bakinshi ya manna kan nata cikin rawan jiki ya dannan harshensa dai dai inda ta manna k'wayar ya rink'a goga harshensa Sannan ya zaro harshen nasa cikin carkewar murya ya zare harshen ya nunawa Ummi tare da cewa "Ummi kinga ni ko kinga abin da ta manna a bakinta Biyaye ka duba, Jiki a sanyaye Ummi ta tsura mai ido ganin harshensa yayi wani yellow Abubakar kuma Juyawa yayi cikin Zubda qollah ya zauna kan 1 str murya Na rawa Yace " Auta meyasa ya za,ayi ki zubda ciki Kinsan illar hakan kuwa Auta kisan kaifa me cikin ya miki" Ahmad ko Cikin takaici yace "Aysha kinji kunya Kin cutar da mutane da suka yerda dake wlh kin dasa mana takaici a rayu kanmu Ke wacce iriyar zuciya gareki" Shiko Yusuf k'ara matsota yayi cikin rawan Murya yace "Aysha kin cuceni kin cucu abinda zaki haifa Har Gaban ubangiji Sai munyi hisabi Kin kashe min y'a A,ish duk tsanar da kike min bai kyautu ya shafi jinina ba Nasan dai nine byake so shiyasa har kika zubar min da ciki Kin cutar da zuciya ta Allah Sai ya saka min Kin yaudari Ummi da ta dauko duk yarda ta baki" Matseta yayi da k'arfi saida tayi K'ara cikin zare ido Yace "Wanne d'an iskanne ya saida miki mgnin? a ina yake? ki gayamin ko shi waye ne wlh Sai Na d'aureshi" Ido ta zazzaro cikin gala baita tace Wayyo cikina zan mutu Ummu cikina " Kicin zafin nama Ummi tamik'e tazo gabansu Hannu ta d'aga cikin Kid'ima ta yarfawa Yusuf d'in Wani wawan mari ta tureshi gefe tana fada cikin Fushi Tana "Haba wannan wanne irin rashin imanine yarinya Na fama da wahalar zuban ciki sannan kun tsare ta da bak'ak'en mgn ganu sannan kai harda matseta Zubar cikifa yafi Haihuwa wuya kashe min ita zakayi"? Shi kam Yusuf dafe kunci yayi cikin rawan jiki da tashin jijiyoyin jiki Yana mai zubda k'ollah, Adam da tun dam'azu ya shigo yana jin duk abinda suke fada Ganin marinnda aka kifawa Yusuf Yasa shi shigowa cikin hatsala yana shiga Kan Aysha yayi cikin harzuk'a ya jawota ya rink'a yarfa mata maruka. Ita kam yanzu tsoro da hawala sun dauke ta shiyasa ta fada jikin Ummi tana mai kuka Da cewa Wayyo.ya Adam Na tuba Wlh bazan k'ara ba Cikin Fushun Ya k'ara yin kanta. Shiko Yusuf cikin Muryar kuka yace " Adam barta Ba komai Allah Na sane dani. Allah sarki Gaba daya Sai jikinsu ya mutu cikin kasala Ahmad ya jasu suka tafi part dinsu Adam da Ahmad suka rink'a tausarsa da bashi baki Shi dai Yusuf sai k'ollah yake sharewa Ya rik'o hannu Adam yana "Adam ba laifinta bane 'Kiyeyya CE ta sata haka Aysha bata sona ta tsaneni shiyasa bata son Haihuwa dani ni Na nawa kaina tun da Na kasa sawa Aysha ta soni a ranta gashi k'iyeyyar ta shafi y'ayana" Ahmad ne ya rink'a juya kai yana "a a Yusuf Na tabbata Aysha Na sonka ka dena fadar haka" Shiko kai ya jinjina tare da sauk'e ajiyar hrt. A haka dai sukata bashi baki Sannan suka samu ya Dan nitsu, Itako Aysha Abu wasa wasa Jinin ya balle ga ciwon mara kamar k'ara shi ake kafin zuwa 9 Na dere duk ta fita hayya cinta Dole Ummi ta kira Abubakar ya kaisu asbiti dama tun safen Ummi tace suje ita tak'i tana tsoro kar mgnar taje kunnen Abba Aiko suna zuwa asbiti akace Sai an mata wonkin ciki Sannan Sai mijinta yazo yasa hannu Kuma gashin sun gano zunda cikin akayi ba zubar kanshi bane, Abubakar yace Ayi komai Amman Ummi tace a,a a dai je a gayawa mijinta Dole Abubakar ya koma Gida yana zuwa ya sameshi a harabar gidan yana zaune shi d'aya idanshi a rumtse A hankali ya zauna gefenshi cikin sanyi Yace "Hamma Yusuf" A hankali ya bude idon ya zubawa Dan uwanshi Shiko Abubakar kai ya d'an gyada mai alamun kayi haquri Cikin sanyin yace "Hamma Yusuf dama Aysha ne muna asbiti so ance Sai kaje Dan Sai an mata wonkin ciki" Da sauri ya mik'e cikin zare ido yace "a a ban yerda ba wanne k'atonne zai mata aikin ba wani aikin da za,ayi mata" hannu ya mik'ewa Abubakar yace "Mu tafi" Suna zuwa asbiti da kanshi ya shiga d'akin da take Sai murk'usuwa take. yana zuwa Ya kamo hannuta cikin sanyi ya Dan matse Rigarta ya d'an d'aga cikin ya tsurawa ido Gamida shafa cikin Lkci d'aya kuma Idansa ya cika da k'ollah" ya zauna gefen ta Abubakar ya kira cikin Sauri yace yaje gidaya kamo mai Zam zam da Zuma da garin habba. Toh yace tare da juyawa ya fita Shiko cikin Ya rink'a Shafawa yana kauda kai Ita kuwa Duk da wahalar tana ganinshi Sai kife kanta take A haka har Abubakar ya dawo Shi da kanshi ya Hada cikin Sanyi yace Amrita Ido ta bude a hankali ta tsura mai ido LLkc d'aya taji tausayinsa Na ratsata Duk ya fige a wuni d'aya Kai ta sunkuyar ido Na zubda k'ollah Matsota ya kuma yi ya mik'a mata Karba tayi tasha. **** Lkci d'aya ta fara jin sanyin ciwon Shiko tana Sha ya fita a wojen yacewa Ummi Ku dawo gida kawai ba komai Dr yace ya rigada cikin ya fadi Haka kuwa suka dawo gida Ummi ta rink'a bata kula ta mu samman Shi ko Yusuf tun daga ranar ya dena shiga d'akin Ummi Adam fushi yayi da ita Ahmad ma bai ko amsa gaisuwarta Ummi ko tun tana jin kunyar ta har ta saki Dan ko a fuska bata taba nuna mata ba Amman tana jin kunyar abin kam. Yau kwananta 3 kuma jikinta ya d'an worwore da safe . Tana zaune A dakin Ummi Tana goge kayan Yusuf k'arami Taji slmar Hamma Yusuf din nata A hankali ta d'ago kai ta tsura mai ido ya d'an rame Amman kuwa yayi wani irin kyau Sai kuma yanayin shi Na da suka dawo Sam ba wolwola a fuskarsa ko fara,a mishkilanci tab fuskarsa kallon shi take ba ko kifta ido. Shiko a hankali ya zauna can gefe Gamida zaro phone dinshi ya kara a kunne A hankali yace Ummi gani nazo ina jiranki Sai kuma ya katse kiran ya zauna yana latsa phone dinshi din. cikin sanyi tace ("Jam bandu na Hamma Yusuf ") Ina kwana Hamma Yusuf. Bai kulata ba sai kallonta da yayi ta gefen ido Dai dai lkcin kuma Adam da Ahmad suka shigo Kai ta sunkuyar tana mai gaidasu Amman duk ba Wanda ya kulata Sai juyawa da Ahmad yayi yana Biyaye bari inje gun Abba kafin ya fita don tare zamu fita Mik'ewa tayi da sauri tabi bayanshi cikin Sanyi tace Ya Ahmad ga kayan Lamd'o a kaimai da yake bata kiranshi Yusuf sai Lamd'o take cemai shi ko Ahmad yamutsa fuska yayi cikin Gyatsine yace " ni Na kawo kyyane bare in meyar" Da sauri tace Ayyah ya Ahmad kayi haquri ka kai musu Tsawa yayi mata cikin fita yana In sun dame ki Ki jefar dasu Dan nasan ba son harkar yara kike ba. Jiki a mace ta juya kenan Sukaci karo kicibis Ta fada jikinshi Cikin sanyin ta tura kanta a faffadan qirjinshi tare da lumshe idan ta shima jiki a mace... ?🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👇🏻👆🏻👆🏻 *MI,WASMITI* page1⃣1⃣4⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇? I love my sister from unguwar rogo ⸽⸽H⸽⸽u⸽⸽s⸽⸽s⸽⸽a⸽⸽i⸽⸽n⸽⸽a ⸽⸽m⸽⸽y ⸽⸽l⸽⸽o⸽⸽v⸽⸽e ⸽⸽m⸽⸽y ⸽⸽h⸽⸽e⸽⸽a⸽⸽r⸽⸽t ⸽⸽m⸽⸽y ⸽⸽s⸽⸽o⸽⸽u⸽⸽l ⸽⸽m⸽⸽y ⸽⸽b⸽⸽r⸽⸽e⸽⸽a⸽⸽t⸽⸽h ⸽⸽m⸽⸽y ⸽⸽e⸽⸽v⸽⸽e⸽⸽r⸽⸽y⸽⸽t⸽⸽h⸽⸽i⸽⸽n⸽⸽g ⸽⸽s⸽⸽u⸽⸽g⸽⸽a⸽⸽r ⸽⸽o⸽⸽f ⸽⸽m⸽⸽y ⸽⸽t⸽⸽e⸽⸽a ⸽⸽t⸽⸽h⸽⸽i⸽⸽s ⸽⸽p⸽⸽a⸽⸽g⸽⸽e ⸽⸽i⸽⸽s ⸽⸽f⸽⸽o⸽⸽r ⸽⸽y⸽⸽o⸽⸽u ⸽⸽f⸽⸽r⸽⸽o⸽⸽m ⸽⸽A⸽⸽d⸽⸽m⸽⸽i⸽⸽n ⸽⸽A⸽⸽b⸽⸽d⸽⸽u⸽⸽l Yasa hannu ya d'an tureta cikin murtuqe fuska ya rab'a gefen ta ya wuce. Jikin gini ta jingina rik'e da kayan Yusuf k'arami gaba d'aya Salon rayuwar ta canza mata bata jin dad'in Rayuwar Sam. Adam dake gefen can kan kujera a zaune ya tsura mata ido cikin hada fuska yakirata Jiki ba kuzari tazo ta zauna gefenshi ta sad'a kai k'asa Shima shirun yayi Na d'an wani lkci sannan cikin ta kaici. yace "Aysha yanzu kinyiwa kanki adalci? Kinyiwa mijinki adalci? Kin yiwa Ummi adalci? Aysha butulcin ki ya sani jin kunya wlh Aysha kituna fa tsawon shekara 19 ni da kaina ban San cewa ba Ummi bace ta Haifeki bare Hydar bare ke bamu taba ganin maraicin rashin mahaifiyarmu a kanmuba bare a kanki Ummi ta rik'eki ta soki fiye da yadda taso 'yayanta Na cikinta A kullum ta kansa Yusuf cikin fushi sabida ke Yusuf da girmanshi bai wuce mari a gun Ummi ba saboda ke Haba Aysha yanxu kinyiwa Yusuf adalci kinyiwa Ummi kawaici"? Kai ta jinjina cikin zubda qollah tana girgiza kai a lamar a,a. cikin rawan murya yaci gaba da cewa " a zaton ki Ummi bata son D'an tane ? Shine fa d'anta Na fari a duniya a tunanki bata son taga jininshi ne Aysha yanxu duk kawaicin da bayin Allahnan suka miki da abinda zaki saka musu Ki tunafa irin son dasu Abba suke gwada miki kab family dinmu ba Wanda akewa son da ake miki Duk son da akewa mahaifiyar mu Sai da aka ninkashi a kanki Aysha ko sonne da gata yasa kike shirin tozarta mu Wato baki da mai miki fada ko"? kuka ta kama sosai tana "a,a ya Adam" Cikin cije lips d'inshi yace "Haka ne mana Aysha Kuma tunda hakane Ni Na kira Babanmu Na gaya mai abinda kikayi Na kuma fad'awa Hydar yanxu haka sun taso daga Yola So Sai ki tanadi abinda zaki gaya musu dan Na lura mu duk kin raina mu" Zuwa yanxu kukan take sosai a hankali ta matsoshi cikin kuka ta d'aura kanta kan guiwarsa Murya na rawa Tace "Ayyah ya Adam dan Allah kuyi haquri wlh bazan k'ara ba Ka kira baba kace mai wlh bazan sakeba kuyi haquri dan Allah" Ture kanta yayi cikin had'a fuska Ya mik'e tare da cewa "gafarar Allah da mijinki ya kamata ki nema ba ni ba Wlh ki gyara ala qarki da Yusuf in ba hakaba wlh ba ruwana da ke" Yana kaiwa nan ya fice abinsa. A parlon ya samesu Suna zaune Ummi ta kawo musu breakfast ya zauna gefen Abubakar Ummi dake ajiye musu pilet tana "a Adam dama kana cikine? "cikin girmamawa yace Ehh Ummi ai tare muke da Ahmad" Aiko naji dad'i yau yarana duk a guna zasuyi kari" Abubakar "Yace gsky kam Ummi yau kin hada yaranki" Dry tayi cikin nufan d'akin tana bari Aysha tazo Ta hada muku tea. Ita kuwa Aysha a d'akin tasha kukanta ita bama abin da yafi cinta kamar Fushun Hamma Yusuf d'in nata Gaba d'aya ta resa sukuni Kukan tayi mai isarta sannan ta kifa kanta kan kujerar A hakan Ummi ta sameta Cikin kula tace "Autan Ummi tashi kije ki hadawa yayunkin tea Ko bacci kikeyi"? cikin kauda kai ta goge fuska tace a,a Ummi bari inje Cikin boye fuska ta fita Dan kar Ummin taga halin da take ciki. A parlon Cikin sanyi ta zauna gefen Hamma Yusuf din ta jawo Cups d'in da pilets d'in Abubakar ta fara sawa ta Dan tura mai gabanshi cikin sanyi tace " ya Abubakar ina kwana" Fuska a d'an sake yace lfy ya jikin dai? "da sauk'i" tace cikin Sada kai k'asa Sannan ta hadawa Ahmad da Adam ta mik'a Musu ba tare da kallonta ba suka d'an fara cin abincin, A hankali taja d'aya cup d'in da pilet din ta hada mai tea d'in ta zuba mai cibs da d'an k'oi Ta d'an sunkuyo ta gefenshi cikin jin wani irin tsoro ne ko kunyace ko Nadama ce ta kasa ganewa A hankali tace "Hamma Yusuf Ur breakfast is ready" kanshi a k'asa tamkar bai jita ba Jiki a mace ta Dan juya gareshi cikin sanyi tace "Hamma Yusuf zaiyi sanyifa" Bai kulata ba sai phone dinshi da ya d'auka ya fara latsawa Ganin haka yasa ta d'an tura hannuta ta k'asan darning d'in ta d'aura hannuta kan cinyarsa cikin sanyi ta rink'a murza cinyar tashi tare da d'an kauda kanta tana "Hamma Yusuf ko wani Abu kakeso in defema" kai ya d'ago cikin Murtuqe fuska ya d'ago ya watsa mata harara Har saida taji ta kware da yawun bakinta da sauri ta janye hannuta daga jikinshi Shiko mik'ewa yayi cikin Jan tsaki da k'ara mata wani irin kallo Itako cikin sauri tayi k'asa da kanta. Kan kujera yaje ya zauna yana B'iyaye "Lkci Na tfy fa Abba Na jiranka" Adam ne ya mik'e cikin d'an sakin fuska yace "Yusuf Ko zamuje kaci girkin Miraa? baki ya d'an tabe cikin sanyi yace, "Azumi nakeyi fa" Ido Ahmad ya tsura mai Dan yasan abin da ya sashi cikin halinga Lkci d'aya ya k'ara jin haushin Aysha A haka shima ya mik'e tare da cewa B'iyaye bari in wuce gun abban. A haka sukayi part dinshi shi da Abubakar da Adam A haka suka d'anyi ta hira Har zuwa 2 dai suka fito Bayan sunyi sallah A farfajiyar gidan suka samu baba Umar da Hydar sun iso tare da Abba Suna ganin su sukaje suka tarbesu cikin jin dadin ganin juna Parlon baba bello suka wuce. Bayan sun gaggaisa Baba Umar ya kalli Yusuf dake gefenshi cikin Sanyi da ta kaici yace "Yusuf kayi haquri insha Allah ubangiji Na bayanka Kuma bazaka tabeba insha Allah zan d'auki mata ki kan Wannan mugun abin da Aysha ta aikata ma" Baba bello ne yayi gyaran murya cikin Kallon Dr Umar yace " mu bazamu iya gyarawa ba kenan Umar? Kana nufin mu Aysha tafi k'arfinmu ne? kai ya d'aga cikin sauri yace 'A a wlh ba haka bane Yaya bello Wlh rai nane ya b'aci matuk' gaya Amman ni ban tunanin kun kasa a kanta Amman a gsky gatar tayi yawa har ta fara sata kauce hanya Dan ganin ba mai tsananta mata" Ajiyar hrt baba bello ya sauqe cikin sanyi yace toh ko in haka ne ka barni da ita. zamu d'auki mataki kar kayi mata mgn Dan yanzu bata worwore sosaima tukun" Adam ne ya hada fuska tare da cewa Wlh baba ni da zaku barni da nasan yedda zanyi da ita" Hydar kuma cewa yayi ni wlh banyi zaton haka daga gareta ba Naji zafin abin a raina yarinya ai ba hakane a kantaba" Shi dai Yusuf Ido kawai yake binsu dashi A ranshi kuwa cewa yake Koma dai me akayi ai ta rigada ta cutar dani ta gama kuntata min cikin kuma ba dawowa zaiyi ba gwara a barta kar a k'ara min zafi 2. Baba bello kuma dole ya hana baba Umar mgn Koda aka kirata tazo su gaisa zasu juya Yola yau din. Gaba d'aya cikinta ya d'uri ruwa tana shiga ta zauna gefen ya Hydar din nata Tana "ya Hydar barka da zuwa" Ko kallonta baiyi ba Baba Umar d'inma da gyer yamsa gaisuwarta Ya bud'i baki zai fad'a kenan Baba bello yace "A a bamuyi haka da kaiba Ke Aysha tashi ki tafi aiko cikin murna ta fita Dan ta tsorita gashi duk kunyar kowa takeji. A haka suma suka juya suka tafi. Biyar dai dai Na yamma Yusuf ya shiga kitchen din Ummi yana Kiranta cikin yanayinshi Na rashin wolwola yana " Ummee Ummi dake tare da Aysha a kitchen d'in ta amsa mai tare da cewa mene Na kiran nan"? K'ara hada fuska yayi ganin Ayshan Na gun cikin juyawa yace "Ummi dama abin buda baki nake son ki had'a min Dan naga lkci kar ya k'ure' Toh tace tare da "cewa Aysha tashi ki fara hada mai Dan INA da aiki da yawa ki daura mai kunun nono nasan yana so gashi dama Hydar ya kawo mana sabon nono Maza mik'e" Cikin sanyi ta mik'e Shiko da sauri ya CE "Ban so a bari zanje gidan Anuty Sadiya ni wlh Ummi kin sani banson jogolgole da kwabe" Yana fadin haka ya juya Ita kuwa ido ta tsurawa k'eyarsa da gashin kanshi yayi luf a kwance Ummi ko cewa tayi Kiyi Aysha ki kaimai in yaga dama ya zubar, Ita a nata tsarin In ba haduwa sukeba bazamu dai dai taba ta kuma ga alama Yusuf fushi mai tsanani yake, Haka kuwa akayi ta hada mai komai Ana fara kiran sallah ta hada ta kaimai d'akin ba kowa shiru cikin kewar d'akin da mai d'akin ta har renta take jin kewar Hamma Yusuf d'in nata Tayi kewar komai nashi. ajiyewa tayi can gefe sannan ta tsurawa d'akin ido Komai nan tsaf Sai Kan mirror da ya hargitse da kolaben turaruka Ganin haka yasa ta tattara ta goge ta jerasu sannan ta canxa mai bedsheet da blanket ta shinfid'eshi ta share d'akin ta koma cikin gida ta dauko d'an kasko ta samai turaren wuta mai d'an Karen k'amshi da sanyi Ta sassake labulayen sannan ta kunna A.C Ta kashe wuta ta kunna Na jikin wani fulawa Wutan read Sai ya haska kalan komai Na d'akin Sannan ta juya ta tafi A cikin gida ta dama mai fura da nono mai sanyi ta Sa mai k'ank'ara a ciki. Sannan ta zauna ta d'an gyara gashinta Ummi dai Sai binta da ido takeyi Tana gamawa wonka ta shiga ta shirya cikin Rigar baccinta yar k'arama mai laushi da sulbi ta fesa turaruka sannan ta konta tare da cewa Ummi "saida safe" Itako Ummi dry tayi cikin gano logonta tace "Allah bamu Alkhairi" Ta fita Shiko Yusuf gidan Anuty Sadiya yaje Sukayi ta hira da Baban Yumin bayan sunyi buda bakin. 8 dai dai ya biya gidan kaka Dan dama ya kirata ta dama mai tura Yana karba a gora ya juya ya fita gidan ya nufa Da sauri d'an hadarin daya taso Sai iskar dake kad'awa Yana isa ya rink'a sauk'e numfashi da shak'ar k'amshin dakin sosai yaji Dan sanyi a ranshi Wonka yayi cikin jin iska Na ratsashi ya shirya ya kwanta duk bai lura da gyaran da akayi maiba bare yaga kulas din abincin Gajiyar azumi tasa lkci d'aya bacci ya d'ebeshi Gashi albarka cin azumin ya samu raunin abinda ke hanashi bacci. Itako Aysha Ummi Na fita ta nufi dakin nasu Cikin Sa,a ko ta samu bai rufe k'ofarba shiga tayi cikin hamdala sannan ta rufe k'ofar. Kai tsaye cikin d'akin ta shige hangoshi tayi kwance cikin blanket yayi luf yana baccinsa Samun haka yasa ta sauk'e ajiyar hrt gamida zare hijabin jikinta A hankali ta haura kan gadon cikin sanyi da kewar Hamma Yusuf d'in nata da kewar salon shi da tsarinshi da Begenshi ta raba jikinshi ta manna k'irjinta kan k'irjinshi ta tura hannuta cikin gashin kanshi Cikin hikima ta murza cinyarta cikin nasa cinyar tare da manna ...... ?🍇🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👆🏻👇🏻👇🏻 *MI,WASMITI* page 1⃣1⃣5⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Lips d'inshi ta rink'a d'an lasa da harshenta mai sanyi tare da goga mai bres d'inta a k'irjinshi gami da murza mai gashin kanshi. Shi kuwa cikin bacci ya rink'a jin wani bak'on yanayi Na ratsashi duk gabb'an jikinshi suka fara karb'ar sak'on nata lkci d'aya tsikar jikinshi ya fara tashi sanyi ya fara ka d'ashi tuni lips d'inshi suka fara Dan motsawa. Itako jin haka yasa ta cabke lips d'in cikin shauk'i da begen mijinta. Jin haka yasa shi bude idanshi a hankali tare da tsurawa fuskarta ido Lkci d'aya ya dan kuma kame jikinshi tare da d'an juyawa gami da Sa hannushi ya mirginata gefe shima ya matsa tare da juya mata baya. ba tare da yayi mgn ba. Ita ko ido ta tsura mai cikin tsoro da mmk Hamma Yusuf ne yau ya juya mata baya sannan Hamma Yusuf ne da k'aurace mata haka. kauda tunanin tayi ta kuma matsoshi ta manna k'irjinta a gadon bayanshi tasa hannunta ta zagayoshi ta rink'a wasa da gashin k'irjinshi. Hannu daya kuma kan mararshi ta d'aura cikin salon lallashi da ban hak'uri ta k'ara matsoshi cikin Muryar rad'a Tace "Hamma Yusuf" Bai kulata ba sai rumtse idanshi da yayi K'ara narkewa tayi a jikinshi cikin taushi da lallashi. Tace "Hamma Yusuf dan Allah ka gafarceni Plsss Kamin mgn Wlh reshin mgnar ka na damuna, kayi mgn Dan Allah Hamma Yusuf ka yanke min duk hukuncin da yayi dai dai da laifina" tureta ya kumayi ya mik'e tare da pillow a hannushi ya jefar kan carpet ya kwanta rufda ciki. Aysha kam zuwa yanxu kuka takeyi da hawaye cur cur kukan mara sauti Cikin kukan ta sauka gefenshi ta zauna ta kamo hannushi. Cikin rawan murya tace " Hamma Yusuf fushinka masifa ne a gareni ka gafar ceni Ka min mgn dan Allah ka tausaya min Na kasa samun nitsuwa nasan nayi ma laifi Amman kamin afuwa" Janye hannushi yayi cikin Jan tsaki ya kuma juya mata baya. Cikin kukan ta fada jikinshi ta rugumoshi tare da had'e bakinsu wuri d'aya ta jawo hannushi ta d'aura kan bres d'inta ta rink'a kissing nashi tako ina tana shafa fuskarsa gaba d'aya ta narke jikinsa. tana "Hamma Yusuf nifa matar kace meyasa kake juya min baya wlh bazan iyaba kamin duk hukuncin da za kamin Amman plss ka dena fushi dani" Sai kuma ta k'ara narke mai a jikinshi tare da k'ok'arin kunce igiyar rigar baccin Sa. Da sauri cikin fushi yasa hannu ya tureta daga jikinshi ya mik'e ya koma bakin gado, Murya Na rawa yace " Sai yanxu kika San ni mijinki ne sai da kika gama cutar dani wato gani jarabebbe zakimin duk abinda kike so kizo ki yaudareni me zakice min ai baki da bakin mgn a gareni Haba Aysha meyasa zakizo gareni ki fame min cutar da kika min"?. Kai ta rink'a juyawa tana matsoshi jikinsa ta fada tare da rugumoshi Murya Na rawa tace "Hamma Na kayi haquri ka gafarceni kar ka k'aura cemin Hamma Yusuffffffffff Kaine farin cikin Kaine cikar burina Wlh bansan da hakan ba saida ka k'aura cemin". Cikin d'an d'aga murya yace " k'aryane bakya sona k'iyayya tace tasa kika zubar min da cikina da kina sona dole kiso jinina dole kiso haihuwa dani Amman tunda hakane ni Na barki da mahaliccinmu Amman kuma ya zama dole *NAYI Aure* Dan Na samu mai haifamin yara dole Na nemi Cikar jin dadin Aure Dan bansan ribar auren da ba haihuwa ba" 😳kalaman Hamma Yusuf d'in nata jinsu tayi kamar ruwan wuta lkci d'aya ta kid'ime Fadawa jikinsa tayi da k'arfi ta mak'aleshi jikinta har rawa yake ta rink'a girgizashi da juya kai murya na rawan "Tace a a ,a a Hamma Yusuf wlh zan haihu wlh ina sonka Wlh Hamma Yusuf banson ka k'ara Aure wlh zuciyata zata buga" Kukafa ta saki tsaka ninta da Allah tana jijjigashi da shafeshi tare da sakemai kissi tako ina tana shinshinar duk wani sak'o Na jikinshi Hannu biyu tasa ta tallabe kanshi cikin tsura mai ido da zubda qollah tace "Hamma Yusuf" Bai kulataba shi tun randa ta zubar mai cikinsa bai kuma d'an jin sauk'iba Sai yanzu da ta mace a kansa take ta furta mai Kalmar so Kalmar da bai tab'aji daga gareta ba gashi duk ta kashe mai jiki da jikinta da take ta goga mai Har ranshi yaji dadin yadda ta rud'e da jin Kalmar zai k'ara Aure Dan shi dama gaba d'aya ya rud'e da tsoron ko sonshi ne batayi yana jin tsoro kar duk cikin da ta samu ta zubar mai. dry ke son kubce mai Amman Sai ya k'ara murtuk'e fuska Cikin fushi yace "K'arya kike gaya min da kina sona da baki zubbada min gudan jinina ba, dan ba yedda za,ayi nai wahala Na baki ciki ke kuma ki fidda min ajiyata, Don haka ba takura. zan Auri wacce zata iya rainon cikina ta Haifa min yara" K'ara tallabe fuskarsa tayi cikin Gsky da gsky ta tsura mai ido Murya a raunane tace. " Hamma Yusuf ina sonka ka yarda dani ina k'aunarka Hamma Yusuffffffffff Kaine cikon Farin cikina Hamma Yusuf da kai kad'ai zan iya rayuwar Aure kai kad'ai idona ke gani kai kasan salon zama dani wlh NAYI NADAMA zubar da cikin nan wlh nima ina son inga gudan ji ninmu wlh wahalan laulayine, ya sani haka kuma bansan haka kake son haihuwar ba Dan Allah ka gafarceni naji Na yarda zan mana rainon duk abinda Allah ya bamu" Tureta ya d'anyi gami da shafa bres Dinta cikin tabe fuska yace "Buk'atar ki dai ta ciyoki shine zaki zo ki yaudaren, Ni kuma yasu bazan iya aikin banza ba in miki ciki ki b'arar min da abina, Aure ne dai ya zama dole nayi shi Janye hannuta yayi ya mik'e ya shiga toilet jin an fara kiran sallah. Ita kuwa kai ta kife jikin gadon tai ta rusa kuka. yana jinta kukan na k'ona mai rai Amman kuma ya zama dole ya janyewa Aysha Dan ta k'ona mai zuciya. Yana fita ya zura jallabiya ya fesa turare ya nufi masallaci. Ita kam da gyar tayi sallah a d'akin nashi ta Dan lafe jikin kujera tana jiran dawo warshi. Shi ko ana fitowa massalacin ya nufi cikin gida A parlon ya tadda su Ummi harda su Ahmad da Adam duk sun zo yin SLM da Abubakar Dan zai koma yau d'in Suna ta d'an hira Shiko Abubakar Sai yai shiru ya rink'a binsu da ido in anyi abin dry ya d'an murmusa, Yusuf ne ya zauna gefenshi cikin kula yace " Babiker ban son tfyar ka yau d'inna ko zaka bari Sai gobe? " Kai ya d'an jinjina cikin sanyi Yace "Ai tfyar ta yau ta zama dole a gareni Sai dai kuyi hak'uri da reshina, nima zan tafi cikin kewarku da k'aunarku Y'an uwana rabuwa ta zame mana dole" da sauri Yusuf ya rufe mai baki cikin Jin tsoron kalaman d'an uwan nashi da mutuwar jiki da wani sanyi da yaji har cikin hanjinshi. Baki Na rawa yace "Ummi ki gayawa babiker Dan Allah ya dena gaya min irin zantu kannan bana so" ya k'arisa mgnar da k'arfi tare da fizgishi ya fada jikinshi suka ruggume juna, Sai kuma ya sakeshi ya juya ya fita Ahmad ne ya kalli Abubakar cikin sanyi yace "Abubakar meyasa Sa kake abinda ke bamu tsoro"? Shiko dry ya danyi tare da dafa Adam yace " kallesu fa ya Adam duk sun wani firgice yoh me a ciki Ku dama kunada masu muku Addu,a ko kun mace nifa ban dashi" Yusuf da yanzu ya fito d'akin Ummi yace "kaima kana dashi" Ahmad yace "sosaima Dan gasu Yusuf k'arami da k'anneshi masu zuwa daga baya duk nakane Sai ka zaba" Sosai yai dryar Farin ciki yace toh daga yau nine Abbinsu da sun fara mgn Ku koya musu sunana Abbi kuma su rink'a min Addu,a Allah ya kareni" Insha Allah sukaci gaba dayansu dan jin dad'in ya sake Shiko Yusuf A d'akin ya sameta zaune fuska a kumbure ido yayi jazir, tana ganinshi ta mik'e da sauri zata fad'a jikinsa ya dakatar da ita cikin hada fuska yace. "Dakata yanzu lkcin Rashida ne Dan zan kirata inji lfyarta" Kamar wasa aiko taji Yusuf ya dage Sai hira yake da wacce yake kira Rashida dan Sai wani lumshe ido yake. Lkci d'aya taji wani irin malolon bak'in ciki ya tokari zuciyar ta cikin rufewar ido ta fice kai tsaye d'akin Ummi ta wuce. Gaban Ummi da ya Abubakar ta zauna cikin zubda qollah cikin mmk ganin yadda fuskarta ta yi jazir Ummi tace. "Auta lfy? me ya same ki? Kukan da take dannewa ya kufce mata cikin rawan baki tace " Ummi wai Hamma Yusuf zai k'ara Aure Ummi har kiranta fa yakeyi a gaba na" Dry sosai ta kama Ummi da Abubakar Amman Sai suka danne cikin hada fuska Ummin tace "Ehh Auta" Cikin zare ido da dafe k'irji tace "Ummi ehh fa kikace toh sabo da me Aure fa Ummi yanzu kishiya Hamma Yusuf zai min" Saiko ta k'ara sakin kuka. Cikin Dan murmushi Abubakar yace "Sabi da haihuwa yake so ke kuma bakya son haihuwar" Cikin sauri ta juya gun ya Abubakar d'in nata jiki Na rawa Tace. "Wlh in so kuma zan Haifa mar ko 12 ne in zai ya bar batun Auren wlh zan haihu in Allah ya yarda" Gaba d'aya Ummi da Abubakar sun cika da Farin ciki Dan ganin K'aunar Yusuf d'in da kishinsa a k'wayar idanuta da jikinta. Shiyasa cikin sanyi Abubakar yace ke da mijinki ai ke zaki lallab'ashi Autan Ummi ni dai in an samu Na miji Amin mai suna" Baki ta d'an tura tace "wlh bazai yarda ba ya Abubakar ka tayani bashi hak'uri" Dry yayi sannan ya mik'e ya ja jakarsa Sannan yace "Toh ba matsala Muje parlon kinga lkci Na k'ure min" Toh tace gami da bin bayanshi Ummi ma bayanshi tabi suka fito. A parlon gaba d'aya zuriyar suna cike. Abubakar ya k'arisa Gaban baba bello Cikin duk'awa yace "Ba yau zan tafi Ku gafar ceni hak'ik'a zan tafi cikin kewarku" Kanshi ya dafa cikin sanya mai albarka Sannan ya wuce gun Nenne itama sanya mai albarka, Yana tashi yaje Gaban Umminsu da Abbansu Hannu su ya kamo duka ya d'aura a kanshi Cikin sanyi ya manna kanshi jikin Ummi tare da sauk'e ajiyar hrt Sannan ya maida kanshi jikin Abban. Murya na rawa yace "Ummi Abba Ku gafar ceni Ku yafe min duk wani laifi da na muku a rayuwata Ummi ki gafarceni wahal dake da nayi tun ina cikinki" Ummi kam tuni jikinta ya saki Ba abinda take Sai cewa take. "Baka min komai ba Allah ya ma albarka ya keutata rayuwarka Allah ya sanya sanyi a rayuwarka" Amin suka amsa gaba d'aya parlon. Cikin sanyi Abba yace "Abubakar ina alfahari da kai kuma ina mai ma fatan alkhairi a rayuwar ka Allah ya ma albarka" Amin ya amsa cikin sanyi ya saki Hanna yensu ya mik'e ya ruggume k'annesa su Usman sannan ya dawo gunsu Ahmad hada Ahmad da Adam yayi ya ruggume su cikin Sanyi yace "zan tafi da kewarku" Suma ruggume meshi sukayi suna muma zamuyi kewarku d'an uwa. yana sakin su ya kamo hannun Aysha yace "kinyi alk'awari ko? zaki min tokwara"? A hankali tace ehh, Dry ya danyi sannan yace "Da kyau" Hannun Yusuf ya damk'o ya jashi suka fito harabar gidan sauran ma suka biyosu a baya cikin tsokona a hankali yace "Hamma Yucut kaji ko Auta tamin alk'awarin mai suna, Kuma ni har ga Allah Na yarda naku gamsu da Nadamarta, Plss Hamma Yusuf a rink'a nunawa yaran pictures d'ina Dan su sanni" Kai ya gyada mai cikin sanyi yace "Insha Allah Babiker ai dama dole zasu sanka Abbinsu guda fa" Juyawa yayi cikin Happy ya ruggume d'an uwansan. Ciki sauk'e ajiyar hrt yace "Ina sonka Hamma Yusuf ina sonka ina sonka" har baki 3 Shi ko Yusuf ido ya tsura mai ya bude baki zai mgn kema. Yai sauri ya shige mota Fuska na zubda qollah yace Na sani kaima kana sona d'an uwana ya juya gun sauran Cikin share K'ollah yace "Kuma na San kuna sona nima ina sonku Amman Sai wota rana". Yana kaiwa nan yaja mota ya fice yana d'aga musu hannu. Gaba d'ayansu binshi da ido sukayi jiki a mace, har zuwa d'an wani lkci sannan suka koma cikin gida. Shiko Yusuf d'akin shi ya koma haka kawai yaji jikinshi Na rawa Sai dai ya zauna kusan awa 2 sannan ya mik'e cikin kasala yaje Gaban mirror ya cire agogon hannushi zai ajiye kenan idanshi ya k'ellah kan agogon Babiker d'inshi. Ki ranshi yayi a woya yana d'agawa yace "Ya akayi ne Hamma Yusuf"? cikin sanyi yace "ka manta agogon kafa" Cikin dry yace "Na baka" Da mmk yace "Na Daimon d'innanne fa da kake so sosai" "Ehh Na sani toh inada Wanda zan bawa ne da ya wuceka" Dry yayi yace "toh ngd k'anina" Cikin dry suka sallami juna, Shiko ya fada toilet yayi wonka zuwa lkcin An kira azabar ya wuce massalaci Bayan an idar ya ya bi bayan su Ahmad suka shiga cikin gida. Su Ahmad d'in sun isa tsakiyar parlon Shiko yana bakin k'ofan parlon yaji kira ya shiga woyarsa Sai da ya shiga cikin parlon sannan ya amsa kiran ganin Abubakar ne da mmk "yace har ka isa ko"? Yana mgnan yana hararan Aysha dake Tsaye a k'ofar kitchen. Gaba d'aya ido suka zuba mai jin ya saki woyarshi da k'arfi,ta tarwatse a kan tais d'in Ahmad ne yace lfy cikin mik'ewa ya nufi gunshi Ina kafin ya k'arisa gunshi Sai haggoshi sukayi yayi Luuu cikin sakin wani irin numfashi ya zube k'asa a............. ?🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👆🏻👇🏻👇🏻 *MI,WASMITI* page 1⃣1⃣6⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 ꃅꀎꌗꌗꍏꀤꈤꍏ ꎭꌩ ꒒ꂦᐯꍟ ꎭꌩ ꃅꍟꍏꋪ꓄ ꎭꌩ ꌗꂦꀎ꒒ ꎭꌩ ꌃꋪꍟꍏ꓄ꃅ ꎭꌩ ꍟᐯꍟꋪꌩ꓄ꃅꀤꈤꁅ ꌗꀎꁅꍏꋪ ꂦꎇ ꎭꌩ ꓄ꍟꍏ ꓄ꃅꀤꌗ ᖘꍏꁅꍟ ꀤꌗ ꎇꂦꋪ ꌩꂦꀎ ꎇꋪꂦꎭ ꍏꀸꎭꀤꈤ ꍏꌃꀸꀎ꒒ Cinkin firgici da rud'ani da bugawar zuciya Ahmad, ya tallabo shi ya d'aura shi kan cinyarsa, jikinshi na rawa ya tallabo fuskarsa cikin kasa mgn ya rink'a girgiza kai kawai, zufa Na keto mai tako ina bugun zuciyar sa💓💔 Na harbawa da k'arfi. Aysha ko cikin tsoro da zare ido da bugawar hrt da jin wani irin suka a k'akon zuciyarta 💘💔 ta iso garesu Murya Na rawa ta tallabo fuskarsa tana juyawa cikin d'imuwa ta rink'a ki ranshi da d'an k'arfi tana. "Hamma Yusuf, ka bud'e idonka menene ya sameka? me aka gaya ma"? K'ara shigewa jikinshi tayi cikin tsonanin tsorita, tace, "Wayyo Allah Na wayyo Hamma Yusuf na ka tashi ka gaya min meke faruwa? me ya sameka"? Juyawa tayi cikin kid'ina ta kamo hannun Ummu wace ta ke kamar an dasata ne Sai sanyi da ya rufe mata jikinta sanyin har cikin hanjinta a fili kuma Sai zufa ke keto mata. Jijjiga Ummin tayi cikin kuka tace. "Wayyo Ummi Hamma Yusuf dina Ummi in ya mutu nima nasan bazan rayuba, wayyo Allah na Ummi kiga baya numfashi baya motsi". Adam ne ya Dan juyo gareta cikin k'arfin hali yace, " Aysha ki nitsu kibar kukannan". Suna cikin haka phone d'in Ahmad ya d'au suwa kamar bazai duba ba sai kuma ya d'aga ganin Sunan Babiker ne a fuskar woyar Jiki Na rawa ya d'aga ya d'an kara a kunne. Lkci d'aya kuma ya saki woyar a k'asa cikin kid'ima ya rink'a juya kanshi Sai yanzu ya samu bajinshi ya bud'e kai ya rink'a juyawa yana. "Kai kai kai Sai kuma ya ruk'k'ume Yusuf a jikinshi da k'arfi ya saki wani irin kuka mai cin zuciyar mai sauraro. Kuka yake yana rawan sanyi yana k'ara k'amk'ame Yusuf d'in. Adam ne cikin tsoro da firgici Yace "Innalillahiwainnailaihi raji un yace haba Ahmad ka sanar damu meke faruwa"? Nenne da ta shigo yanxu jin kukan Ahmad yasa ta k'aroso da sauri Jiki na rawa tace. " meya faru me ya samemu a zuciyar nan? me ubangiji ya hukunta a kammu? Ahmad Ka gaya mana"? Ummi kam hannu tasa duka biyu ta tallabe cikinta da k'irjinta tare da cewa Wayyo Allah Na cikina sanyi kamar hanjina zasu tsinke" Da sauri Nenne ta k'arisa gunta cikin cewa "meke faruwa damu ne"? Aysha ce ta kamo hannun Ahmad cikin sakin wani irin kuka mai siririn sauri tace "ya Ahmad meya faru"? Cikin kukan da kifa kai jikin Yusuf a hankali Yace, "Aysha Babiker" Sai kuma kife kanshi. Ita ko Aysha cikin tsoro ta juya ta zubawa Ummi ido Sai ta kuma sakin kuka. Cikin rawan murya Ummi tace "Aysha me woyar ta kamo min? yau kuma gaya min ya zanyi da mu k'addari" cikin kuka da carkewar mgn tace "Ummi ya .. Ummi ya.. Ummi ya Abubakar" Allahu Akbar uwa da d'a Sai Allah Sai mutuwa, Ummi da fari murmushi tayi tana Kullum nafsin za,ikatil maut. Allah sarki Abubakar Na ase ban kwana kamin da gsk Ya Allah Na ka jik'an wanna bawa naka Abubakar". Ina Sai kuma zuciyar ta ta d'an yace Cikin sanyin sauti ta saki wani irin kuka tare da rik'e cikinta tana Wayyo cikina Allah Na Na godema da wannan jarrabawa rabbi ka fini son Abubakar Allah kasa can yafi mai nan Abubakar Na yafema duniya da lahira". Nenne kam itama kukan take sosai. tana Abubakar d'in ?" Adam ko Komawa yayi ya zauna dirsham ayyah Usman Dasu Abba da baba bello yanzu suka shigo gidan. Suna shiga cikin tsoro baba bello Yace "meya faru"? Ba Wanda ya samu da mar mgn Sai kuka Cikin firgici da hatsala yace, "Ku gaya min meya faru? kunyi shiru" Adam ne cikin kuka da wani irin voice Yace "Baba Abubakar Abubakar ne ya". Sai kuma ya kasa k'arisawa. Allahu Akbar cikin mutuwar jiki da tsoro Abba da Baba ballo suka zame kan kujera Usman ko da Rabi,u da Abdul, Hade kai sukayi wurin d'aya suna wani irin kuka mai sanyin sauti. Cikin k'arfin hali baba bello ya rink'a musu fad'a shi dinma kamar a gigice yake yana. " Haba Ahmad yanzu wannan shine matan da zakuyi wa d'an uwanku Adam har kai dinma kuka shine abinda zaku aikawa Abubakar Usman ase ba Addu,a zakiyi mai ba"? Ina shi ma Abba kanshi ya jingina jikin kujera yana ta nanata Addu,a Amman INA hawaye Sai zuba suke Ganin kukan Abba yasa Aysha sakin wani irin kuka sosai ta rink'a jin tausayi Abban. Cikin yin Hamdala Ummi tace "Ahmad accident ne Abubakar yayi"? Kai ya jinjina alamun a,a" Cikin mmk tace " toh me ya sameshi"? Murya Na rawa yace "Ummi kashe Abubakar akayi"! Gaba d'aya parlon suka juyo gareshi cikin rud'u da alamun tabbaya Abba ne yace waya kashe min Abubakar "?. Cikin sanyi yace "wani yaronsa ne Adamu " Baki Na rawa har suna had'a baki sukace Adamu, Adamu Dan y'iware nan"? Cikin gyada kai Yace shi ne. Adamu wani Yaron Abubakar ne shike wakiltan sojojin kan hanya Na yankin Taraba zuwa binuye state kuma yaron ya dad'e da farautan rayuwar Abubakar Dan yana hank'k'o kanshi a matsa yin Abubakar kuma yana jin takaicin yedda Abubakar ke ta kai mai birki kan halinshi Na zalumci. Toh da suka taso suna tfy har suka isa cek point na kan hanyar Y'iwaren ya samesu a lkcin azabar tayi sai ya tsaya sunyi sallah da driver shi cikin sanyi yace. "Sani muyi salla anan gunsu Adamu Sai mu wuce ko"? cikin tab'e fuska Sani Yace 'ni wlh oga ban son Adamunnan mugune" Dry ya danyi cikin sanyi yace "kake kyautatawa dan Adam zato kaji ko Sani? ba abin da zai faru face da sanin Allah" Shi dai Sani ba Don ya soba suka tsaya sauran sojojin suna ta murna da ganin ogansu Gashi da halin kyauta Sunyi sallansu Sani ya fito musu da Abinci da Ummi ta had'a musu sukaci tare da sud'in. Sun gama komai zasu tafi Wani daga cikin su yabi bayan Abubakar cikin sanyi yace "oga Dan Allah kake kula da kanka a Gaban oga Adamu" Dry yayi Yace ba komai Allah Na tare dani. Har ya shiga mota Adumun ya bishi rik'e da sanda irin ta kiwon shanu. Cikin dry Yace 'kai Oga tsaya ba kai kace Fullo bane Sanda bata cinka bari mu gani" Cikin dry ya d'an juyo yana "ai fulanin da nacema bana yenxub.. Kafin ya k'arisa Sai sand'ar yaji kauuu a k'eyarsa zai juyo ya kuma sake mai d'aya a gadon bayanshi ya yunk'ura zai taso ya k'ara mai d'aya a tsakiyar kanshi, Ganin abin ba Na wasa bane yasa sauran suka rarumoshi suka danne. Shiko Abubakar cikin azaba ya fad'a jikin Sani. yana numfashi da k'er yace "Adamu yanxu nizakayiwa haka Amman ka sani Sai Na rama" A take Sai ko ya fara aman jini. Ihu bayan hari ganin haka Sai Jikin Adamu ya d'au b'ari cikin tsoro da kuka Yace. "Na shiga uku Abbakar aman jinin kakeyi Dan Allah ka gafarceni" Cikin aman Yace "Sai Na rama fa" Cikin kukan Yace ka rama indai zaka yafe min Dan Allah Abubakar ka gafarceni". Sai ya kuma sakin kuka Shi kuma aman yak'i tsayawa cikin galabaita Yace Na yafema Dan Allah tunda Allah ma da kanshi yana son masu hak'uri da yafiya" Cikin nishi Yace "Sani kira min d'an uwana kira min Hamma Yusuf d'ina". Shine fa a lkcin ya kira Yusuf. Shiko yana jin muryar d'an uwanshi Cikin fizgar numfashi yace " SLM Hamma Yusuf Adamu yamin dukan kisa ni nasan zan mutu Amman Na yafe mai Hamma Yusuf ko Na mutu Ku barshi Na yafe maiii, Sai ya d'aura da Kalmar shahada... ganin haka yasa Sani zare woyar cikin firgita Yace.. "Hamma Yusuf Oga Abubakar ya rasu ya tafi ya barmu". Furucin kenan da ya buga zuciyar Yusuf ya sashi sumewa. Cikin Sauri Abba ya mik'e tare da cewa baba bello Yaya mu tafi mu d'auko gawarsa muyi mai su tura". har sun mik'e Cikin kuka Aysha tace Abba " kalli Hamma Yusuf shima a sune yake tun dazu bai numfashi " Su gaba d'aya Sai yanzu suka Ankara kan Yusuf dake ruk'ume jikin Ahmad. Kai Abba ya jinjina ya zo suka d'aga shi shi da Ahmad Sama suka haura dashi har kan gadon Abban suka direshi Abban ya duk'ufa kanshi cikin zubda qollah. A Ranshi yake cewa Rashin d'an uwa bai da misali". A hankali ya samu ya farfad'o sannan Abban ya mai Alluran bacci. Su kuma suka wuce.y'iwaren Kafin su iska sarkin garin yasa akayi mai sutura akayi mai sallah Aka kaishi gidan shi Na gsky da yake abokin bappa yaya ne su Abbanma Sai k'abarinshi aka kaisu suka gani washe gari da safen sukayi sammako suka dawo Adamu kuma da kanshi ya kai kanshi hukama dasu Abba sukazo aka kawoshi garesu Abba kam Na ganinshi Sai hawaye Shiko baba bello cikin kuka Yace "Adamu kaci amanar abota a duniya" Haka suka dawo gida aka zauna karb'ar gaisuwa Shi ko Yusuf tunda ya farfad'o akayi mai Allurar bacci bai tashiba Sai washe garin da safe bayan su Abba sun dawo. A hankali ya bud'e idanshi cikin wani irin tsinkewar zuciya da tuni abinda Sani Yace mai ya mik'e jiki Na rawa Toilet ya shiga Alwala yayi cikin firgici kar acemai gsky ne abin da yaji Sallolinshi ya rama sannan ya fara jera nafilfili. Yana cikin sallanne Ahmad ya shigo ganin yana sallah yasa ya juya. Parlon Ummi yaje cikin dashewar murya yacewa Aysha "Auta kije d'akin Abba B'iyaye ya tashi ki tafin mai da abinci" Aysha dake kwance jikin kakarsu innayi Fuska a kub'b'ure fuskar tayi jazir ga wani zazzabi mai zafin gske cikin jin jirin ta mik'e tana goge k'ollah. Kakace ta d'an rik'o hannuta cikin sanyi tace "Kar kije mai da kuka" Kai ta gyada cikin share k'ollah A hankali ta haura saman cikin sanyi ta bud'e k'ofar d'akin Abba ta shiga kanta a sunku ye Shiko jin motsin bud'e k'ofar ya juyo a firgice. ganin Aysha ya sashi tsura mata ido cikin son ganin fuskarta Itako jin jirin yasa ta zame gabanshi ta rik'o hannushi. Ido ya zaro cikin rawan lips d'inshi ganin hawaye a idon ta cikin tsoro Hamma Yusuf ya fad'a jikinta kanshi ya manna a tsakiyar k'irjinta ya Sa hannushi ya ruk'k'ume ta cikin tsoro ya rink'a juya kanshi yana murzawa a k'irjinta kamar yaro cikin alamar kar ta gaya mai baya sonji K'ara tura kanshi yake a k'irjinta Itama Sa hannu tayi cikin kuka ta manna shi da jikinta ta k'ara matsoshi shi kuma k'ara narkewa yayi a jikinta..... ```WANNAN NOVEL D'IN NA SADAUKAR DASHI GA Y'AN UWANA YAYUNA YA ABUBAKAR DA AHMAD ALLAH YA GAFAR TA MUKU Y'AN UWANA RABBI YA SANYAYA MUKU MAKON CINKU Yasa Aljannace makomarku".``` ?🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👇🏻👆🏻👆🏻 *MI,WASMITI* page 1⃣1⃣7⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Lkci d'aya jikinshi ya rink'a bari yana tsuma hatta jijiyoyin kanshi saida suka taso sama fuskarsa tai jazir sai k'am-k'ameta yake, ita kuwa kuka ta saki cikin dashewar murya ta sa hannuta ta tallabo fuskarsa ta rink'a juya mai kanta alamar yayi shiru, Shiko bai ma san halin da yake cikiba gaba d'aya ya resa me ke mai dad'i a duniya. A parlon kuwa Abba ne da Baba bello suka shigo Dan gaisawa da su innayi da suka iso bada jimawa ba har sun juya zasu fita, Baba bello ya kalli Ahmad dake zaune gefen kaka cikin sanyi yace. "Ahmad har yanzu Yusuf bai tashi bane "? Kai ya d'an jingina a hankali yace. " a a ya tashi". yana fad'a mai haka Sai suka fasa fitan suka juya suka haura gun Yusuf d'in. Cikin d'akin kuwa Yusuf duk ya rikice Aysha sai kuka take shima cikin azabar zuciya ya samu kukan ya kufce mai da samun kukan sai ya daina rawan jiki sai zamewa yayi kan cinyarta ya kife kanshi ya rink'a wani irin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro kukan da ka jishi kasan akwai k'una mai tsananin yawa a zuciyar mai yinshi. Itama Aysha kukan take tana k'ok'arin tallabo shi. Dai dai lkcin su Abba da Ummi da Baba bello da Ahmad suka shigo, Su Na shiga Kukan Yusuf da Aysha da yedda suka ruk'ume juna suna kukan. ya tona musu zuciya lkci d'aya Ummi ta zame gefen su Cikin kauda kai Baba bello ne yayi k'arfin halin mgn Bayan duk sun zauna sun sasu a gaba Cikin dauri yace. "Haba Yusuf wannan kuka ya isa haka meyasa bazamu d'au dangana ba shin ase ina yebonka ase kai d'in kafi kowa sakewar zuciya ji yedda kasa matarka a gaba kana kuka yanzu kasan tsawon wani lkci da Aysha ta d'auka tana kuka kalli fuskarta fa ka tausaya mata mana itafa abu 2 ne ya had'e mata kukan rashin d'an uwanta da kukan tausaya wa halin da kai mijinta zaka shiga na tabbata da ta ga ka daure da matsalarta zata regu kuyi haquri Yusuf am". Kai ya d'an d'ago Cikin kallon iyayen nashi lkci d'aya kuma ya fad'a jikin Abban su ya saki wani irin sautin kuka yana. " Abba shi ke nan Babiker Na ya tafi bazai dawoba ya tafi har abada" Allah sarki Abba shima kukan d'an nashi sai ya sashi kuka cikin kukan yace. "Yusuf Abubakar baiyi gaggawa ba kuma muma bamu makara ba hanyace wace dole ko wanne mai rai sai ya bita Yusuf ba Abubakar zamu yiwa kuka ba kanmu mukewa kuka, sabo mukewa kuka duk yedda muke sonshi Allahn da ya bamu shi ya fimu sonshi ka dena yiwa d'an uwana kuka, insha Allah muna zata masa Rahama ka tunafa kashesa akayi". Kuka ya k'ara saki Cikin k'uncin zuciya yace. " Wlh ba dan Babiker da bakinshi yace min ko ya mutu shi ya yafewa Adamu kuma yace min koya mutu kar muyiwa Adamu komai, badan hakaba wlh da Adamu Sai yaga k'ask'anci da sai ya d'an d'ani hukunci Amman Babiker yace kar amai komai". Jin haka yasa Ummi ma sakin kuka. Aysha ce cikin kuka tace. "Hamma Yusuf ka gani fa kasa Abba da Ummi kuka Hamma Yusuf kayi haquri ka bar kukannan". Ahmad ne ya matsoshi Cikin sanyi yace. "Biyaye Abubakar yafi buk'atar Addu,armu da kukannan dan Allah ka daure ko iyayenmu Sa samu sauk'in abin". kai ya rink'a jinji nawa Cikin sanyi Ahmad d'in ya rink'a goge mai k'ollan. A hakan suka samu ya d'an dawo hayya cinsa sannan suka jashi suka fita wurin amsar gaisuwa. Suna fita gefen kakansu suka zauna shi da k'anneshi dasu Adam Allah sarki bappa Yaya Sai hawaye ke wonke mai fuska ganin yau Allah ya zare mai d'aya daga cikin jikokin nashi. Cikin zubda k'ollah ya rink'a yi musu nasiha. Da deddere Abba da kanshi ya kira Yusuf Yace yazo d'akin shi su kwana tare su Adam kuwa baba bello Yace su d'auki matansu su koma gida jensu da safe Sa kuma zuwa kafin ai safakar uku. Shi ko Yusuf tun da suka shiga shi da Abba ba abinda yake Sai bawa Abba lbrin irin hirarrakin da Babiker d'in shi ya rink'a yima mai da yazo. da k'er Abba ya lallabashi jin kukan da yake har numfashin Sa Na fita, shiko Kasa baccin yayi Sai tashi yayi ya d'auro Alwala ya rink'a karatun k'ur,ani mai girma karatun yake da Farin Yana kuka daga baya kuma Sai kushi,i ya halarto mai Amman haka ya kwana ba bacci kam Sai rawan sanyi da yake. Itama Aysha a d'akin Ummi kukan da tasha ya k'ara ingiza zazzabi jikinta ga rashin cin abincin da takeyi lkci d'aya jiri ya sark'a feta ga amai da take Na wahala tayi kakari har ta banu amman ba abinda za harar kafin zuwa safiya duk ta galabaita. Kashe gari da sake ta kama ranarce za,ayi sadakan uku Dan da wuni akayi lissafin. Tun asuba su Abba da baba bello da su Ahmad da Yusuf dasu Hydar gaba d'aya dai zuciyar tasu suka hallara a masallaci gidan nasu da maqota da abokan arzik'i . Akayi Sada kan uku ana watsewa su Ahmad kuma da k'annesu suka suka d'auki k'ura,anai suka rink'a karatu da Addu,a da nemawa mamacin gafara.har zuwa Tara da rabi sannan suka koma Cikin gida, a safiyar Dr Umar ardo da Goggo Aysha ma suka koma Yola Cikin jimamin rashin da sukayi, Hydar kam Yace bazai komaba tukun, su Bappa Yaya ma sun koma Anuty Sadiya ma Abba ya sata tfya dole tana kuka. 11 da kadan Na safe su gaba d'aya suna zaune a parlon Ummi harda Nenne duk Dan su d'ebewa juna kewa. Ummi dake ta zirga zirga ta fito jiki a mace ta kalli kaka a hankali tace. "Kaka jikin Ayshan Na fa yak'i duk ta gala baita gashi ko ruwa tasha Sai ta harar ni Na tsorita da abin" . Hydar ne Cikin sauri yace. "Toh Ummi mu tafi asibiti mana" Kakan ma Asibitin tace suje, Shiko Yusuf ido ya zuba musu cikin rashin abin cewa, Sai Nenne ce tace "toh Ummi ta fito mu tsfin yafi ai ko"?. Kai ta jinjina cikin sanyi tace. " ko tsayuwa fa bata iyawa jiri da rawan sanyi, Amman dai bari Na tallabota". Ummi Na shiga ta sameta ta fito wonkan da ta tayata ta shiga da Dan matsa ruwan kuma Sai ta d'an ji k'arfi kadan duk da tana jin jirin, mai ta d'an shafa mata sannan ta taimaka mata ta zura doguwar riga sai d'an gyelenshi ta yafa, sannan ta Dan kamata suka fitoh parlon sunan isa, parlon sai jirin da wani irin duhu ya rufe nata ido, Cikin sanyi da rashin k'arfin tace "Wayyo Ummi zan fad'i duhu nake gani". Dai dai lkcin suka isa gun Yusuf aiko tai luu zata fad'i, cikin hamzari ya tallabo ta ta fad'a jikinshi lkci d'aya yaji d'umin jikinta Na ratsashi kara tallabota yay Cikin shafa fuskarta ita kuma Sai lafewa tayi jikinshi tana shak'ar k'amshin turaren shi sai ta lumshe ido ta kuma bud'ewa. Cikin sanyi ya d'an sunkuyo kamar Cikin rad'a yace. " Amrita meke damunku meke miki ciwo"? K'ara lumshe ido tayi kamar mai shirin suma. Ganin haka yasa Cikin sauri ya tallabota ya mik'e jiki na rawa Hydar ne ya mik'e da sauri rik'e da key din mota yayi gaba Yana mu tafi hospital sauri sauri gudu gudu ya shige motar da Hydar ya bud'e musu Nenne dake binsu a baya ta zauna gaba kusa da Hydar d'in sannan shi kuma yaja mota suka tafi. Suna zuwa Asbitin Doctor Suhana ta tarbesu su cikin kula da karamcin ta, lkci d'aya ta fara bin ciken lfyarta da abinda ke damunta da taimako abokiyar aikinta Anuty khady Cikin k'orewarsu da iya warsu suka gano Cikin dake jikinta da kuma rashin nasarar da maganin da tasha ya kasa yiwa Cikin. Cikin fara,a da happy Dr Suhana ta fito tana fita ta kalli Yusuf cikin fara,a tace. "Congrat Dr Yusuf Aliyu Muhammad matar ka Na dauke da ciki har Na tsawon wata 4". Ido suka zare Cikin mmk da kaduwa Hydar harda k'warewa, Shiko Yusuf fuska ya murtuk'e Cikin kauda kai Yace. "Dr Suhana mgnar gsky mukefa ba wasaba Abinda kika gaya min gske ne "? Cikin gsky da gsky "tace wlh da gske ne Cikin 4 mornt gareta wlh Dan mgnin da aka shawa Cikin baiyi tasiri ba sai dai kawai yaja mata koda ciki zatake yin period" Hamdalah Yusuf ya rink'ayi lkci d'aya kuma ya tuna mgnar Babiker d'inshi inda yake ce mai "Hamma Yusuf Dan Allah idan abin Farin ciki ya sameke kake bayyana Farin cikina kan fuskarka ban son jin ana cewa ba,a gane Farin Cikin ka da bakin cikinka, Koda bana raye idan kai Farin ciki har kai murmushi zanji dad'i". Tuno hakan ya sashi sujjada ga Allah Cikin farin ciki da fara,a ya rink'a hamdala, su Nenne da Hydar kuwa tuni su isa gunta suka rink'a fara,a suna hamdalah. Shiko Yusuf har zai wuce Dr Suhana tace Amman da d'an matsalah fa Cikin tsoro yake tabbata yarta. " matsala kuma? Matsala mece"? Dan murmushi tayi cikin sanyi tace, "Matsalar k'aramace wannan sanyin da take yawan ji har yake sata rawan sanyi gsky ba abinda zai cireshi sai d'umin jikinka". Kai ya sunkuyar Cikin wucewa yana, " wannan matsala ta k'are". Yana shiga kanta ya tsaya yasa hannu ya tallabota Cikin sanyi yayi murmushi Yace "burin Babiker Na zai cika da izinin rabbi Sai dai ban saniba ko zai kuma yunk'urin zubar min da cikina"? Kuka ta d'an saki Cikin sa hannu biyu ta zagaye k'ugunshi ta manna kanta kan jikinshi cikin sanyin murya tace. A a, a a Hamma Yusuf bazan sakeba wlh Na baya ma kuskurene nayima alk'awarin ko zan resa raina zan reni Cikin nan". Ajiyar hrt ya sauk'e tare da k'ara ruk'umeta suna shak'ar k'amshin juna da d'umin juna ganin haka su Nenne kam suka fice, Suna fita Dr Suhana ta shigo ta basu SLM da magungunansu sannan suka koma gida Cikin Farin ciki. A gida kuwa gaba d'aya tasowan wannan ciki ya ciki zuk'atan zuciyar da Farin ciki Ummi saida tayi kukan Farin ciki. Da Daren kuwa Yusuf ne zaune gefen Ayshan tana ta rawan sanyi Ummi dake gefe Cikin tausaya mata tace. " shin wai su basu bata mgnin sanyin nan ne".? Kai ya d'an sunkuyar Cikin Dan happy Yace "an bata mgnin Yana d'akina". Sai kuma ya d'an mik'e cikin sanyi ya kamo hannuta Yace. " zo Muje in baki mgnin". Itako jin d'umin jinshi yasa ta mik'e cikin kasala tabi bayanshi. Ita ko Ummi murmushi ta d'an yi da hamdala itama ta nufi d'akin mijinta. Suko suna shiga bedroom d'inshi ya jawota jikinshi cikin rawan jiki ya sabule rigar jikin..... ```Dubun k'aunata zuwa gareku matan group d'in Fasaha Writers INA yebawa gareku INA kuma alfahari daku ba abinda zance daku sai Allah ya barmu tare``` By garkuwan Fulani 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👆🏻👇🏻👇🏻 *MI,WASMITI* page 1⃣1⃣8⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Jikinsa ya zare ya jawota jikinshi cikin rawan jiki ya haura da ita kan gado tare da zare y'ar rigar jikinta ya cillah gafe, cikin fesa numfashi ya manna kanshi kan cikinta yasa hannushi daya yana shafa d'an cikinda sai yanzu ya lura da girmansa kad'an, itama mak'aleshi tai cikin kewar mijin nata da jin dumin jikinshi ta k'ara yin kasa ta had'a k'irjinshi da nata tasa hannu ta tallabo fuskarsa ta d'aura tsakiyar k'irjinta, tasa hannu tana wasa da gashin k'irjinshin. Cikin rawan jiki da buk'atuwa ya fara manta halin da yake cikin bai son jin komai sai matarsa ita yake gani ita yakeji. Shi da kan shi yasan yayi kewar bres d'innan dole cikin begensu ya sa hannu yana musu wani irin shafa da latsasu tamkar yau ya fara ganinsu da jinsu sai nishi yake sama sama, itama lunshe ido kawai take tana mimmik'ewa dan gaba daya gab'b'anta tuni sun amshi sak'on da Hamma Yusuf d'in nata ke aika masu , sosai ta fara maida mai martani duk ta susutashi ta birkita mai k'wanya ta tsinka mai jinin jikinsa, gaba d'aya jikinsa sai rawan sanyi yake tuni lips d'inshi sunka fara kad'awa sunyi jazir sun wani tsuke, Cikin sha,awarsu ta yunk'ura ta had'e bakinshi da nata lips d'in ta cab'e cikin salon k'orewa da shauk'i da bege ta fara kissing nashi, Shiko Yusuf mutuwar bori ya fara ba abinda yake sai lallatsata da shafeta cikin sanyi ya zare harshensa ya manna bakinshi kan bres d'inta ya musu wani irin kamu da tsotsa, Cikin yankewar numfashi Aysha kam ta saki wani gauron k'ara, gamida k'ara tura mai bres d'in ta tallabe kanshi kamar yaro, shiko tuk'uru yake sarrafata dan su da Kansu sun San sunyi kewar juna baranma shi Yusuf da yakeji kamar zai mutu in bata bashiba. Itako sai mik'a take. tana. "Ohhhh shiihhhhh Hamma Yusuffffffff". Shiko zuwa yanxu baida bakin mgna. Sai nuk'urk'usanta da ya keyi juyata yake tako ina yana sakar mata kiss yana shafe ababen marmarinshi. A hankali yai mata rumfa da k'irjinsa, cikin rawan murya kamar mai cutar bebanta yace. " Amrita Ina sonki ki soni koda rabin yadda nake sonki ki rik'e min cikina ki rainar min jinina, Kar ki, k'ini dan kokin k'ini ni bazan iya fushi dakeba bazan iya rayuwa ba keba ki jik'an mijinki wlh Aysha kece farin cikina kece jin dad'in rayuwata, kece nutsuwata kece ke iya gamsar da ni da sama min natsuwa". Hannu ta sa ta sank'alo k'ugunshi ta had'e su wuri. Da k'arfi ya saki numfashi dan jin jikinsu ya had'e sai kawai ya saki wani irin kukan jin dad'i da farin ciki, sai kuma ya kai bakinshi kan kunneta cikin kukan yace. "Amrita bazan cutar dake da baby Na ba ko? kar Na wahal daku dan kune farin cikina". Cikin rad'a ta k'ara shigewa jikinshi murya a daburce tace. " uhhhhhh hammmmm Shiihhhh Hamma Yusuf ba komai gaba d'aya ni da babynka d'umin jikinka muke son ji, bugun zuciyarka mukeson ta ratsa tamu baby ma yana kewar Abbanshi dan Abbanshi yayi fushi da Amminshi tsawon wata 1 baiji d'umin mahaifin shi ba". Allah saki dama dole masoya basa fushi da juna, Shiyasa Yusuf harda rakwafuwa yana. "Amrita kar kisake yin abin da zai had'amu har ta kai munyi nisa da juna". Itama kukanne ya kwafce mata dan Hamma Yusuf ya kusa kaita mak'ura saura ta sume dan duniyar da ya cillata a yau ta tabbata a cikin mata 1000 da wuya a samu 20 da suka taba isa wanna duniyar masoya da ma aurata bata taba jin yadda takeji yau dinba Hamma Yusuf d'in ya isarmata har abada Dole ta mak'aleshi tana kuka tana. " Hamma Yusuf bazan sakeba zamu rayu tare zamu rayu cikin farin ciki Kaine jigon rayuwata Kaine ka sanardani soyeyyar gsky kai da banne cikin maza mace bazata iya fushi da namiji kamar kaba". Haka suka mace cikin so da k'aunar juna sunyi kukan dadinsu sun more sun mak'alewa juna son ransu sun kashe kewar juna da ya cisu tsawon wata d'aya"........... ******************** Bayan wata Biyar Baba bello ya kammala gidaje 3 da ya Gina komai iri d'aya kattin gidaje ne naji da fad'a Komai ya tafi da tsarin zamani ya malla kawa Adam da Ahmad da Yusuf gidanjen a Jere suke Na Yusuf ne a tsakiya sai Na Ahmad a gaban nashi sai na Adam a bayan nashi. Yau jumma,a kuma yau ne suka tare a gida jen nasu duk da shi Yusuf yana Madina yaje karbo sakamakon kammala karatunshi inda ya zama cikken likitan musulunci,. ya tafi da k'yar dan ya nace shi sai dai ya tafi da marsa a cewarsa har sati 2 bai jitaba bata jishi ba, dole dai ya hak'ura ya tafin dan su Abba sunk'i ganin yadda cikin Ayshan ya girma,. Ran da suka tare sai aka had'a Aysha da Kaka dan kula da ita., Suna tare jumma,a ana zaton Hamma Yusuf sai next Friday sai akwai kashe gari asabar ya diro kamar saukar yeso. Yana isa gidan. Ummi tai tamai dry tana Auta ta komai haihuwa Yola dan babanta yace ta koma can sai ta gama 40 in ta haihunma. Abu kamar wasa sai ga Yusuf a zaune dirsham gaban Ummin shi Yana rikici kamar yaro yana. "Haba dai Ummi wlh ni bazan iyaba kawai adawo min da matata dan ni ban yadda ba da matata sai Na zama kamar banda mata dan Allah Ku tausaya min yanxu kwana 12 fa ban ganta ba den kice Wai ta komai Yola ni bazan iyaba Ummi kema kinsan ina buk'atar matata dan bazan iya rashinta a kusa daniba". Ummi kan kunyace ta rufeta jin zantu kan Yusuf shi ko a jikinshi ganin zai mata barin zance yasa tamai bayanin gsky, aiko ko minti 10 bai k'araba ya wuce gidansa dan dama yasan gidan dan tun kan ya tafi Baba bello ya basu takardun gidajen. Yana shiga kai tsaye parlon da ya hank'o da hasken wuta ya wuce yana shiga ya tsurawa Amritanshi ido ganinta tsaye kusa da TV tana wlh ke kaka sai kiyi ta cewa sai Arawa zaki kallah duk ki takurani. Juyo wan da zatayi ta ga Hamma Yusuf d'in nata cikin mmk !da zare ido ta juya da d'an gudunta, tayi gunshi, Shiko cillah jakarsa yayi ya ware mata Hannayenshi yana Came baby i miss you so much Noor hayatina, Itako Kaka dake gefenta mik'ewa tayi tana "lfy Aysha baki da wayoko yanxu da wannan k'aton cikin kike tik'a gudun nan"? Ita dai bata kulaba, da gudunta ta fada jikinshi Hamma Yusuf d'inta ya Sa hannu ya ruk'k'ume matarsa sai kuma ya had'e bakinsu yai ta tsotsa sannan ya zira mata harshensa yana mata alamar yayi missing ta kama kar yayi kula aiko ta cafe lkci daya suka fara sauya numfashi cikin sanyi ya zame da ita kan carpet ya tallabota da kyau ya samu ya d'an zare harshensa, Jin gyaran muryan da Kaka ta musu, Cikin borin kunya ya kauda kai yana " ohh Amrita ai zaki cinye min harshe, Ke kuma kaka me ya kawoki nan gidan? ni wlh kinsan banson sa ido ehe". Cikin mmk Kaka tace "oho ba matsala ai zan tafi da ka samu ma Na yima gadin mata ko "? Ta fada cikin fushi Shiko mik'ewa yayi cikin dry sosai yace kai Kaka wasafa nake ai ke tamuce bazama Ki komai gidanki ba tare zamu zauna. Dry itama tayi cikin jin dad'in sauyawar Yusuf ya komai mutun mai sauk'i da fara,a da raha da son yan uwa ya dena tsok'k'omar kowa a kanneshi ko don suma yanxu kan sun girma Hatta su Rabi,u da Usman sunyi Aure Hydar ma yayi da Abdul sai Sadip ne kadai ya rage bai yiba. Cikin fara,a tace "inji ba yau zaka dawoba sai sati mai zuwa "? Tab'e fuska yayi yace . " Na kasa wlh bazan iyaba kewar mata ta nakeji ai nama yi k'ok'ari ko Kaka? kwana 12 ba mata saura kad'anfa Na mutu Kaka". Kai ta jinjina tana. "ban saniba kai baka da kunya sam yanzuba kamar daba wlh". Kai ya d'an shafa ya kamo hannun Aysha ya shafa k'aton cikin ta yace. "Wlh Kaka son Y'ar yarinyar nanne ya canzani gaba d'aya" Duk sukayi dry haka sukayi ta hira Yusuf ko a jikinsa sai lallatsata yake yana. "Amrita nonon nan basu k'aru sosai ba anyako zasu isa babyn nan"? Ganin zasu zarce Kaka tace sai da safe ta shige dakinta sannan tace "Aysha kizo ki karbi mgninki fa" Tana fita ya mik'e da ita. " yana jeki karbo kizo Dan zan gyarawa baby Na hanyan fita". Tana shiga gun kakan ta k'ura mata ido cikin fad'a tace. "Wlh ki kula da wannan jarabebben mijin naji in kinyi garaje zai takalo miki nak'uda shi ko a jikinsa". Baki ta d'an tura cikin yatsune tace. " Toh Na barshi da wahala kenan kwana nawa baya nan duk da haka bazan,aga hak'urinsa ba ko so kike Na tauye mai hak'k'insa ni baccima nakeji". Tana kaiwa nan ta juya tana "ji tsohuwa da sa ido" A d'akin kuma dry Yusuf ya rink'a yi yana. "kai Kaka wato zan tsokalo miki nak'uda" Itama dryan tayi tana shafa sajenshi Lkci d'aya kuma suka mak'alewa juna cire rigarta yayi yana shafa bres d'inta yana. "Amrita zaki iya ko? in bazaki iyaba wlh zan hak'ura". Kai ta tura a k'irjinshi cikin sanyi tace. Toh in bazan iyaba wazai biyama buk'atarka? ko so kake Na barka cikin wahala? al halin kuma lfyta lau Ni cikina ba zai hanani kyautatawa mijina ba". aiko cikin Happy ya fara murzanta yana sauk'e gajiyarsa da kewar ta da buk'an tana, sai muntashi yake yana sabbatu da sanya mata albarka. gaba d'aya ya kasa control d'in kanshi itama yau jinshi take kamar wani dere da sukayi a Gembu ran da ya d'irka mata mgni. Dama kunsan ance mai ciki da ban take bare kuma dama Aysha matar ni,imace. Can dai Yusuf ya d'an sahirta mata jin gaba d'aya cikin ya takure gefe ya dunk'ule, yakomata yayi cikin maida numfashi ya rink'a shafa kanta da cikin. yana " ohhh Amrita Allah ya miki Albarka matar kirki y'ar aljannah". Itako shiru tayi tana shafa sajensa , dan wani iron fitsari takeji mai azabar zafi ga wani irin Sara da k'ugunta keyi sai zufa ke keto mata tako INA, cikin wahalan tace. "Hamma Na ka gamsuko"? Shafa bres d'inta yayi da cikin ta yace. "sosaima" Kai ta jinjina gamida yunk'uri ta mik'e ta nufi toilet. Cikin kula yace "Amrita Na wahal da keko"? "Ba komai Hamma Yusuf na" tace cikin k'arfin hali ta shige. Tana tsugu nawa sai fitsarin yak'i fita sai saran da bayanta keyi ya k'aru. Cikin Azaban ta fito tana zuwa ta kwana gefenshi ta d'aura kanta kan cinyarsa tana. "Hamma Yusuf bayana, bayana zai b'alle" Cikin firgici ya taso ya tallabo kanta gamida shafa cikin cikin tsoro yace. "Amrita karfa mgnar Kaka ta tabbata"? Jin sabon saran bayan ba sassauci ta mik'e da sauri ta shige toilet shima binta yayi da sauri tana shiga ta durk'usa a k'asa dan jin k'afafunta Na rawa duk sun mace Shima durk'usawa yayi gabanta Itako kusa jin wani irin azaba da nishi ta cakumo hannayeshi ta rik'e GAM ta rink'a wani irin nishi mai k'arfi, Shi kuma sauri yayi ya gyara mata durk'uson ya janye towel d'in jikinta saman k'irjinta yakuma jata ya mannata jikinshi. Cikin soro yace " kiyi nishi Amrita haihuwace ga kan baby ki rik'eni da kyau" Aiko ta rarumoshi ta matseshi da iya k'arfinta ta saki nishi cikin, abbaton sunan Allah. Shima k'ara rik'eta yayi Sai ta kuma sakin nishi mai k'arf aiko sai ga, Yaro k'ato fari tas ya fad'o cikin tafin hannun Hamma Yusuf d'in. Wayyo dad,I Hamma Yusuf Ruk'k'umesu yayi da baby da maman babyn yana hawayen farin ciki da hamdala ga Allah. shiko yaro sai kuka yake tsalawa alamar lafiya yake. Kai Yusuf ya sunkuyar Dan lek'a fuskar Amritanshi Cikin tsoro da firgita da kad'uwa ya zazzaro ido ganin halin da Ayshan ke ciki duk ta k'ak'and'are ta matseshi shi da yaron cikin azaba ta ...... By Garkuwan Fulani 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👇🏻👆🏻👆🏻 *MI,WASMITI* page 1⃣1⃣9⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Ta kuma yunk'uri da nishi mai k'arfi sai ga yarinya ta sumb'ulo, tana cillah kuka, Yusuf kam gaba d'aya ya cika da farin ciki sai hamdalah yake yana ruk'k'ume da family d'inshi, Ita kuwa Aysha komawa jikinshi tai ta lafe tana mai maida numfashi da sauk'e ajiyar hrt tana mai hamdala. Lkci d'aya Hamma Yusuf ya kimtsa yaranshi da matarshi shi da kanshi ya musu komai ita ya fara tallafawa tayi wonka tare da Dan gasa jikinta sannan ya fito da ita ya taima ka mata ta kimtsa tsap abinsu yara kuwa, goge su yayi tsap ya murjesu da mayuka sannan ya shiryasu tsap ya nad'esu cikin blanket nasu masu laushi da taushi farare tas. Har zuwa 5 ya kammala komai shima yai wonka ya fito ya nufi masallaci bayan sun idar da sallah ne Ahmad da Adam suka tsareshi a gaba suna mmk Wai yaushe ya dawo shine bai fad'a masu ba, Shi kuwa dariya kawai yake yana ruk'k'ume su, Cikin kewar juna da k'aunar juna, ya kallesu cikin farin ciki yace. "Na dawo jiya da dare dama nace sai kawai Ku gani da safe". Ahmad yace. "Aysha ta murd'a kabbunta ko"? Dariya yayi tare da cewa. "A a baby's sun kira Abbansu dai". Ido Adam da Ahmad d'in suka zuba mai cikin mmk da son gane zancensa. Kai ya jinjina musu alamar "ehh hakane" Adam yace. "Me kake nufi"? Gyara tsayuwa yayi tare da Dan sunku yawa yace. " ina nufin Aysha ta Haihu ta haihu jiya da dare bayan Na dawo ta haifa mana tagwaye". Lkci d'aya zuk'atan su suka cika da farin ciki Cikin zumud'in suka wuce gidan Yusuf d'in. A gidan kuwa Kaka na idar da sallah ta d'an fito parlon, ido ta tsurawa corridor d'in d'akin su shiru ba motsinsu cikin d'an tunani ta komai d'akinta tana shiga kuma taji muryar Ahmad na kiranta da sauri ta fito a parlon ta samesu ido ta tsura musu cikin tsoro sai kuma tayi ajiyar zuciya ganin fuskokin su cike da annuri. Adam ne ya kalleta da kyau yana. "Kaka sai kawai muka samu yan tagwaye kai Alhamdulillah". "Harara tasaki musu cikin tab'e fuska tace "ai koda bansan wahalar haihuwa ba haihuwar ba shan ruwa bane". Dariya Ahmad yayi cikin sanyinshi yace. " toh ni dai nasan biyaye na ba mak'aryaci bane kuma Na yard a da zancensa". Shiko Yusuf kawai d'akin ya wuce yana shiga ya samu Aysha na rik'e da woya daga duk kan alama da Ummi take mgn dariya take tana. "Wlh Ummi da gske Na Haihu kizo ki gani mana". Karb'e woyar yayi yana dariya yace. "Ummi ke dai kizo kigani" Cikin gsky da gsky tace. "Ni banson shirme fa" shima cikin gskyar yace. "Allah Ummi kizo ki gani" Toh kawai tace. A parlon kuwa tare suka fito shi yana rik'e da macen ita kuma tana rik'e da Na mijin. Kaka kam tana ganin Aysha ba ciki sai yara a hannu ta bushe a tsaye tana zare ido da tafa hannu, suko su Ahmad karb'ar yaran sukayi suna ta ruk'k'umarsu da sanya musu albarka, Ita kuma Aysha jikin kaka ta rab'a cikin tsokana tace. "Kinga Hamma Yusuf d'ina ko yazo ya takalo nak'uda ya kuma karb'i haihuwar bamu ma baki tsoroba". D'an tureta tayi tana. "Can tafi daga nan Ku dai wlh Allah ya shiryeku". Shiko Hamma Yusuf dariya yayi ya tallabo matarsa cikin so da k'auna yana. " kin biyani ban mancewa da ranaku biyar masu haske a rayuwata". Ahmad da Adam da kaka kam farin ciki kamar su had'iye hak'oransu. Kafin ace kobo gida ya cika da yan uwa yadda matansu Usman dasu Rabi,u Su Ummi harda kukan farin ciki Hydar ma yana ji ya kawo Goggo Aysha da matarsa Nafeesat Aysha kam tana shan gata da kula Yusuf ko duk nacin kaka da Goggo Aysha dole suke hak'ura da Yusuf da ya nace shifa tare zaike kwana da matarsa da yaransa dole suka yarda dan in sun hana ma a gunsu yake tarewa Ummi zatayi fad'a yace. ai yasan abinda yake shima kawai zai kula dasune. Ran suna yara sunga gata da so gun kakannisu da iyayensu Ahmad da Adam sun taka rawar gani inda suka hana Yusuf kashe ko sisi Yaron Yaci sunan Abubakar Abbanshi yace a kirashi da Abubakar d'inshi shi kuwa Babiker yake kiranshi ita kuwa mace sunan Ummi Aysha tace asa mata ana kiranta Mami, Anyi suna lfy an waste lfy Yara sun samun kula da gata tako wanna bank'aren. Yusuf kuwa duk lkcinsa Na matarsa ce da yaransa ba ruwanshi ko gaban kaka lallatsata yake yana shi fa wlh ya gaji ai jego kam ya k'are. Kaka ko tace jeki ya d'irka miki wani cikin tun yanzu shi ko a jikinsa.shi kuma sai yaita dry kawai. Yau asabar ta kama kuma yau satinsu 4 da haihuwa, Tara dai dai Na dare suka waste hiran da suke a parlon, Yusuf ya d'auki Mami dake bacci, Cikin murmushi ya manna mata kiss a goshi sannan ya kalli Kaka yana dan dry yace. "Kaka kalli yadda yarannan suke ta k'iba gashi basa rikici sai suita bacci abinsu shi babiker yamafi Mami Na girmi". Cikin tuna baya tace. Aishi Abubakar komai Na mai sunan shi ya d'auko in mutun ya ganshi zaice d'an shine Na cikinsa". Lkci d'aya fuskar Yusuf ta sauya, ya Sa hannu ya karbi yaron daga hannu Aysha ya had'a da Mamin ya ruk'k'ume su, A take kuma ya juya ya tsurawa TV ido cikin bugawar zuciya Tashan MBC Bollywood ne suka sako tallan film d'in *Kal ho laa Ho* wak'ar ya rink'a ratsashi yana tuna mai d'an uwanshi yana tuna yadda babiker ke son film d'in Lkci d'aya jikinshi ya fara tsuma cikin sanyi ya mik'e rik'e da yaran ya wuce d'akinshi, kan gado ya dire yaran yaje yai alwalah yazo yai ta nafilfili yana mai yiwa d'an uwanshi addu,a. Ita kuwa Aysha a parlon jikin Kaka ta rab'e cikin sanyi tace. "Kaka yau kuma Hamma Yusuf ba zaiyi bacci ba Kaka me zan mishi in sama mai nitsuwa Na tabbata yau kwana kuka zaiyi". Cikin share k'ollah Kaka tace. "Aysha nima bansan ya akayi nayi mgnar Abubakar ba da nayi shiru". Cikin sanyi tace. "Kaka ko bakiyi mgnan ba TV ya tuna mai ya Abubakar" A hankali tace. "Aysha tashi kije ki taushi zuciyarsa" Haka ta mik'e cikin sanyi taje gareshi tana shiga ta zauna gefen yaran ta zuba mai ido yana karatu k'ur,ani yana zubda k'ollah. Lkci d'aya shima yaro ya fara kuka, Itama Aysha sai ta tsurawa Hamma Yusuf d'in ido tana zunda hawaye. Jin kukan yaron yasa ya rufe karatun yazo ya d'auki yaron ya mik'a mata ganin tana kuka yasa ya had'a su da babiker din ya ruk'k'ume. Cikin sanyi yace. "Na bari kema kibar kukan Nasan ganin halin da nake ciki ya saki kuka toh Na bari Amrita bazan sake ba". Cikin kukan tace " kayi alk'awari"? A hankali yace. "Zanyi alk'awari bazan sake kukaba sai dai nai ta mai Addu,a, Amman kuma kema yau ki tausaya ki motso gareni Dan begenki ya kusan karni". Cikin sanyi tace. "Hamma Yusuf ban gama workewa bafa" Dariya ya d'an yi sannan ya d'age yaron daga cinyarta dan ya koma bacci ya kontar da yaron cikin sanyi yace. "Waya ce miki baki workeba aike bazaki San kin workeba sai ni zan gano mana hakan ke dai bani Na d'an d'ana wlh zan miki a hankali ". Ita dariya ma ya bata shisa cikin dryar ya lallaba ya hard'e abarsa, cikin sanyi da kewar juna suka haukacewa juna ya rink'a juyata da sarra fata. Cikin gamsuwa da Amritarshi ya kalleta cikin iya gskyarsa yace. "Amrita d'aya tawa tamkar da dubu bakya canzawa sai k'ara d'an d'ano da kike kullum jinki name kamar Daren forkonmu". Ita kam sai sumbatarsa take tana shafa sajensa. Haka rayuwa ta mik'e musu cikin jin dad'i. ********* *Bayan shekara 8* Wani yammaci mai dad'i iskar damina Na kadawa gari yayi shiru sai sanyi mai k'amshi dan ruwan da akayi aka d'auk'e sai duhu da duniyar tayi a hankali Hamma Yusuf ya shigo parlon Ayshan dayasha gyara sai k'amshin da yake fiddawa ta kashe wutan parlon ta kunna wutan cikin shoo glass sai ya bawa parlon wani kala mai kyau. Yaran dake zaune a parlon su 6 suna ta wasa suna ganibshi suka ruga gunshi Mai dan girman cikin Wanda suke kira Yusuf yace. 'Abba kaga Ahmad ko tun dazu yanata zagin Nana Wai tayi sallah bata yiwa Abbinmu Addu,a ba ita kuma tace tayi" kanwar Ahmad k'aramine Yar Adam shiko Yusuf baison ana tab'a k'anneshi matan ko kad'an. dariya Hamma Yusuf yayi cikin d'agawa Amritanshi gira yace. "Kuna jina ko duk Wanda Baiwa Abbi Addu,a zanyi fad'a dashi kuma bazan sake zuwa dashi saudiba". Cikin son Wanda sukewa Addu,an suka rink'a cewa. "Abba wlh kullum muna mushi, Abubakar k'ara mi yace "ni kullum sai namishi kuma incemai ina sonshi" Mamice tace Abbah Nina ina mishi". dariya yayi cikin jin dad'i yace. "Allah ya muku albarka" Cikin far in ciki suka amsa tare da ficewa suna Abba zamu tafi gidan Baba Adam yace gobe zai kaimu Yola " Cikin jin dad'i yace. "Allah kiyaye hanya" har zasu fita Aysha ta kalleshi da kyau dan tasan inda yadosa Sai tace. "Hamma Yusuf cikin sanyin nan,? maza ku dawo" Da sauri yace. "Kai maza Ku tafi Ku gaida su". Aiko suka fice suna murna shiko suna fita. Ya matsota cikin hararan love yace. ai kin San abinda ke tare dani shine zaki taramin yara su tafi can Adam yaji dasu kinga kaka nacan zata tare musu yaran suma su hole". Hannu tasa ta d'an tureshi tana. "Kai girman ma kamar k'arama abin yake mutun kamar inji". Cikin rawan lips yace. "Allah a hannu nake" yana fad'a yana binta a baya Ganin zata mai nisa ya cabkota ya wuce da ita bedroom d'inshi suna shiga suka fad'a kan gado cikin rawan sanyi da rawan lips ya jawota jikinshi yana shafa bres d'inta da suke cike tib kamar bata tana sharyawa ba sai shek'i suke itama tuni tafara juyashi tana latsar lips d'inshi da suke ta bari dan fitina cikin kid'ima suka mak'a lewa juna murya na rawa yace. *"Amrita jamana blanket kar Aysha Ali Garkuwa ta gammu ta samu abin rubutawa masu karatu".* ```Alhamdulillah ala kulli halin. Na godewa Allah daya bani ikon kammalah labarinan lfy ina godiya gareku my lovely fans Allah ya barmu tare Har kullum kuna raina Masoyana``` ```Afwan Afwan Afwan ina Neman yafiyarku Mace ko namiji baba ko yaro Wanda Na sani da Wanda ban saniba Wanda Na tab'a mgn dashi ko ita da Wanda ban tab'a mgn ba ni na yafewa kowa``` Jinjina gareku groups. By Garkuwan Fulani 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *NAYI NADAMA* 👆🏻👇🏻👇🏻 *MI,WASMITI* page 1⃣2⃣0⃣ Na Aysha Ali Garkuwa 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *🎷🎺🎤Yehhh Na jinjina muku yan social media ba mai rabani daku jama,ar social media kui haquri ga baitinku na biya*. ``` Mun jinjina muku Readers damu daku d'aya ne masu karatu kui haquri ga baitinku na biya``` *Tabba yarku ta isoni kamar haka?.* Garkuwa a baya kinyi wani kuskure novel din *Mi,WASMITI* da kikayi a duniya dad'inshi yayi ta kewaya groups ya shiga sak'ok'in Nigeria shin meyasa kika ware 'yan wasu groups d'in?. Su sukace ayi miki tabbaya nikum can zanmiki tabbayar sheidar suna k'aunarki gaba d'aya. ~Na jinjina muku y'an social media ba mai rabani daku Jama,ar social media kui haquri ga baitinku Na biya~ *Yehh dole naje duk inda rebo yake Na dena so babu gurin zuwa, ban raina ranar da novels tai mini ta sanadi an sanni garuruwa, Tinda nazo a cikin y'ay'an Adam duk ajizi ansanshi da mantuwa. Kui haquri ga baitinku zan biya. Garin masoyi nisa bai mini dana fad'a kuma yanxu ina tini, Allah ya k'addara in zamto zuma dana fito ai taimini sansani. Yau haquri zan baiwa zan baiwa fans na da sunfiso Na tsaya tamkar gini Rabbi nufeni silar novel da zanyi a gaba mutan k'asarmu su zauna lfy. ``` Y'an JANNART LAMID'O novel group duk Nisan da nayi musu amman dani sai alfahari suke novel na in sun gani ko a fushi suke farin ciki gurbi nasa zai shige da zanaje ni mu zauna so suke basu da niyar tsigen fiffige da gsky nunan k'auna suke Dan sun kirani sunai mini magiya, Kui haquri ga baitinku na biya. Na am b'ato mutanen ANEELURV ONLINE WRITERS group su y'an k'waraine basu da Tsok'k'oma idan kaje kafad'a musu zasu rikeka da kyau harda lallama. K'orai k'arai Na gane duniya mai sonka shikeyi maka iddima Masoya na MELODY NOVEL WRITERS gaisheku nai kuke reba gardama Kui haquri ga baitinku na biya. A FASAHA ONLINE GROUP Sunana ya shahara In an kirani jama,a basa gudu. Dan haka nai kiransu da azzama zasu rik'e ni muje mu haye tudu albarkacin k'aunar da suke mini Na dad'i suke Jan ragamar social media toh Ku sanyi bazan manta suba. WRITERS mu zamto tsintsiyaaa. Mutan MUSAN KANMU MARUBUTA group gurinsu Na yana basu shiri da mai mini hassada farin halinsu yasa suka kauda kai harma suke nema suyimin gata. Inda tarin masoya a ASY KHALEEL NOVEL WORLD group kunji yanxu Garkuwa ina fad'a Kui haquri ga baitinku na biya. Mutan DAN GYARANKANMU group sunai mini Addu,a fatansu ko yaushe Na wuce Sa,a k'auna suma ba,a barsu a bayaba basa zama da mutum mai min ba,a. NOVELS ARENA group Yadda suke mini cikin su suna akwai ni da jamma, a. UMMEE GARKUWA NOVEL GROUP zafi Kansu yayi musu da sunji nai jinjina a novel ban sasuba suna fad'a mini son da suke mini koda idanuna bai gansuba kuji dalilana Y'an Ummee Garkuwa novel group jinjina gida biyune kuma narraba muna kamar k'aunar da kuke mini idan Na raina nayi k'uriciya. Yehh y'an SMARTES ONLINE WRITERS Kullum tunan suke nai musu baiti laifin ya wuce. NOVEL GROUP kafin nai musu baitinsu sai kuma duniya ta d'auki Wai bazan k'arisa novel din mi,WASMITI ba. Kui haquri ga baitinku Na biya Kai kuji sabon al,ajab UMMYN YUSRAH NOVEL group suna nema forgive sun fadan Na Dave da Addu,a mai hassada shi zai zsmma sankace. Kui haquri ga baitinku na biya, Rufaida NOVEL group Sabon zance suke Wai ya akwai nace bazan sasuba toh ga baitinku Na biya. Can TABITAL FULAKU Suna tausa yamin sabida matsala ciwon idon da nake fama shi barin infad'a muku kar Ku damu rabbi yana tare dani zan rayu k'alau kan gsky . NOVEL MAKEUP & KITCHEN na yeba domin a fuska kunai mini farra,a Kui haquri ga baitinku na biya. Group d'in UWAR GIDA & Hauwa novels group dana zagaya Cikin su Aysha Ali Garkuwa kamar a group MAI,ADASHE,S FAMILY nake. MU GIRKA DA KANMU group da ZANGON LABARAI group Na Gaza rerrebe irin k'aunar da mukewa juna yadda kuke mini ga baitinku Na gino. GROUP d'in ZAUREN GUZURIN GOBE ALK'IYAMA da Group d'in RAYUWAR MATA A MUSULUNCI kamar da zan wuce akwai masoya Na ciki Na tuno (HUMM Addu,a bata fad'uwa k'asa Wata ran sai Na zamo tauraruwar duniyaaaa) Dubun jinjina da k'auna zuwa gareku masoyana wadanda ban abbaci sunan groups dinkuba ban banta dakuba fans Na aduk inda kuke INA k'aunarku😘😍😘😍😘😍 Ⴎᗯᗅ Ⴎℬᗅ ℍᗅႮՏᗅ ℕᝪᏉℰℒՏ ⅅᗅ ℳႮKᗅℽⅈ ᗯᗅℍᗅℒᗅℕ ⅅᝪℂႮℳℰℕᝨⅈℕG ℕᗅՏᗅ Fatan Alkhairi a garemu baki d'aya sai min had'a a novel Na gaba By Garkuwan Fulani A̲y̲s̲h̲a̲ A̲l̲i̲ G̲a̲r̲k̲u̲w̲a̲ ==================== ᴡᴀɴɴᴀᴍ ʟᴀʙᴀʀɪɴ ᴀɴᴀ ɪʏᴀ sᴀᴍᴜɴ ᴄᴏᴍᴘʟᴇᴛᴇ ɴᴀsᴀ ᴀ ɪɴᴛᴇʀɴᴇᴛ ᴡᴇʙsɪᴛᴇ : ᴀʙᴅᴜʟᴍᴋɪʙᴀʙ.ʜᴇxᴀᴛ.ᴄᴏᴍ ====================== Document made by: Ⓐⓓⓜⓘⓝ-Ⓐⓑⓓⓤⓛ ================== ℒᝪᏉℰ ℳℽ ՏⅈՏᝨℰℛ ℍႮՏᗅⅈℕᗅ ℬℰℒℒᝪ ႮℕℊႮᗯᗅℛ ℛᝪℊᝪ