SADAUKI ☆☆☆
N@ B ALEEYU
76.....
Karo na farko da mama ta fara zuwa gidan Sadauki, saboda wata nurse data cewa kabir Ajlal tazo haihuwa ita kadai, ko sallama batayiba ta tura ganbun parlorn da karfi dai dai nan nafee tafito daga kitchen dauke da try a hannun ta, bin mama tayi da kallon mamaki koba a fadaba Tasan wannan maman Sadauki ce Toh Amma meyasa zata shigo musu gida haka kai tsaye ba sallama ba neman excuse, mama ta daka mata tsawa "lfy kika wani tsareni da idonki masu kama Dana mujiya"
nafee ta tabe " toh fah kekuma boyar Allah daga ina"
mama ta kara har zuka tace
" Ina mijinki "? Nafee tace "umm yana bacci waza'a ce masa "
Mama ta bita da mugun kallo aranta tace zamanki gidan Dana yakare a yau,
Jin hayaniya tayi yawa yafito sanye yake da jallabiyar bacci, cak yatsaya ganin mama gaban Shi yayi mugun bugawa lokaci guda kalaman ta suka dawo masa a kwanya, mama tace kaiii Ina 'yata? Jikinshi ne yasoma Bari am Im eh tana sama, murmushin takaici tayi tace jeka kirawo ta, kafafunsa ne Suka kasa daukar Shi yadade dakin Ajlal ba inda bai duba taba Amma Babu alamun ta har mama tagaji da tsayuwa ta samesa ciki,
Ina 'yata nace? Sadauki yace am wlh mama Dama Dama tassss kakeji ta wankeshi da mari "kana tunanin bamuda masaniyar abunda kayi ne? Toh wlh kaje kanemo yar mutane in bahaka ba wlh Zan daga maka nono, Sannan yanzu yanzu nake son kasaki waccan Mara kunyar matar taka "
"Haba mama bai kamata laifina yashafi ta ba" hannun shi tajawo tamkar karamun yaro har kasa nafee na cin Apple ko kallon mama batayi ba, mama tace oya saketa nace in bahaka ba wlh Zan tsine maka indai ita ke saka kana mun rashin kunya kana wulakanta yar mutane Toh wlh yau seta bar gidan nan Abu daya zaisa ta zauna in San cewa tana Juna biyu albarkacin jikana Zata zauna da kai shidinma yau seta bar gidan nan se randa aka ga Ajlal "
Wayarta taciro tasa kiran kabir minti shabiyar segashi yashigo ta nuna nafee tace "kabir waccan Mara kunyar zaka auna mun muga kotanada ciki "
Gabaki daya hankalin nafee baya jikinta tasoma kuka tana rokon mama karta rabata da Ajlah,
Mama tayi murmushi takaici tace "se yanzu kika San Allah se yanzu kika San darajar uwar miji, kabir kayi abunda nasaka mana, nafee tace no basai an gwada ba Ni banida ciki Amma Dan Allah Karki rabani da mijina,
Sallama sukaji Anyi da babbar murya dasauri nafee taje ta rungume uwar tata tana kuka, kallon wulakanci take yiwa mama tace " Ke "yimun shiru akan tace danta yasakeki shine kike Kuka miye garesa Wanda kika rasa iye, Toh wlh kinfi karfin nan idan harshi nonon halal yasha Toh yasakeki "
Sadauki ya runtse ido yana jin kalamanta har cikin ranshi, kabir yace " mekake jira kokuma ba nonon halal kasha ba "
Dafe kanshi yayi yana kallon mama dake binshi da murmushin takaici.
Maman nafee tayi guda "Ayyirrrrr yaro bazai iya rabuwa da baby ba, kinga ta nuna mama da yatsa tace danki..... bata karasa ba sadauki yace na saketa, se alokacin kwallar da mama Ke makalewa ta fado mata,
Maman nafee tace "saki nawa? Sadauki da zuciyarshi tagama kulawa yace Wanda ba'a dawowa, nafee ta buga kara tafada jikin mamanta.
Gudu yake sosai kamar zai tashi sama shikadai a motar fuskar shi ba walwala, karfe ukun dare ya isa yola yaje yakama hotel.
Tinda sassafe yayi wanka yafita batareda yayi breakfast ba yadauki hanyar gidansu Ajlal, kasancewar yayi zama agidan baiwani sha wahala ba yashiga fadar sarki, dukda gabanshi na faduwa baisan mezai tarar ba,
Dakata! Sarki Abdul Azeez ne yadaka mishi tsawa "dama nasan zaka zo a lokacin Da Dama ta kubce maka bana bukatar jin wasu kalaman yaudara abakinka kawai kabani takardar 'yata karshen zance,
Durkushewa yayi gurin idon shi sun kada sunyi jajir yace "nasan Nayi ba dai dai ba Amma Ni kaina bansan ya hakan take faruwa ba Nayi iya bakin kokarina na ganin na kyautatawa 'yarka Amma hakan ya faskara, duk acikin watannan ne nagane cewa Ajlal matata ce nagane kowa ye ita na boye mata ne Dan in mata surprise a duk lokacin data haihu " Bansan ya akayi wannan kaddarar ta afku ba Amma wlh.... Mai martaba ya katse Shi dacewa yimun shiru kafun kazo Duniya an rigaka so maza-maza kabace mun dagani bana bukatar sake Ganin ka acikin garin nan ma bare kayo tattaki har zuwa fada ta,
Sadauki ya dafe kan shi believe me wlh Ina son matata sharrin shaidhan ne kurum Dan Allah ka Kara bani wata Dama, Mai martaba yace ai Kaine shaidhan din sakaran yaro.......
Tic-Tac-Toe | ||
+ | + | + |
+ | + | + |
+ | + | + |
New Game |