SADAUKI ☆☆☆
N@ B ALEEYU
75....
Baby Waye wannan yarinyar kamar 'yar larabawa kyanta kadai Abun tsoro ne ace mijinki yagan ta fadan Waye Ita? Nafee tayi murmushi tace haba mama kanwar shi ce fah bakiga kama ba, dallah yimun shiru wawiya kanwar shi zai wani rudewa haka ke baki lura da reaction din shi kiduba irin kallon daya Ke mata man, wlh da sake, nafee tace mama Karki juya mun brain me kike son cewa ne, kallon 'yarta take cike da haushin rashin fahimta irin nata tace baby kisaka ido sosai akan Shi Amma tabbas Ina gaya miki wannan ba nono daya suka shaba hakama ba wando daya ya fidda su ba kisake tunani tana kai nan tawuce tabar nafee cikin zullumi da tashin hankali,
Bayan hajiyar nafee ta wuce ta nufi đakin Ajlal bata tsaya neman izini ba tabude ganbun đakin, cak ta tsaya ganin sadauki rungume da Ajlal yana bubbuga bayanta,
Ajlah miye haka Waye wannan ne Dan Allah firgice ya juyo yace yazaki shigo mana daki ba sallam kinzo da wasu silly question naki, lok Ajlah na gaji da Rena mun wayo da kake akan yarinyar nan kace Kanwar kace Amma Naga abubuwa suna faruwa wadanda suka wuce soyyayyar jini, Sadauki yace fine seki kure bincike kinji na kawo kanwata tanada matsala ga tsohon ciki Ke bakiyi hankalin tausaya mata ba bare kirika mata wasu abubuwan nikuma seki hana mun in kula da ita nan gaba atare zamu rika kwana Dan bazan Bari wani Abu yasa meta ba mama tayi kuka dani,
Sum-sum nafee tajuya tafita duk sun birkita mata kwakwalwa zancen wa Zata dauka,
Bayan kwana biyu Ajlal ta canza musu ta Dena musu breakfast kanta kawai take yiwa aiki ba ruwanta dasu,
Da shirin sa yashiga gurin ta yana mata sai yadawo bata tanka masa ba Har ya juya yafita,
Saukowa kasa tayi Zata dafa indomie nan ne ta hadu da nafee wadda tasha gaban Ajlal tace "ke wai mekike jine dame kike takama agidannan da har zaki rika share mutane"
Ajlal ta ajiye indomie dinta tace "duk Abunda kike ji shi nake ji Sannan duk matsayin da kike da Shi inada fiyeda naki gidanna"
Nafee tace "karya kike yarinya yaushe ma kikayi bakin magana keda kike Kanwar Mai gida wane matsayi gareki anan"
Ajlal tayi wata dariya tace "kekuma amarya koh idan Kuma ga uwar gida fah kinga dole matsayin ki karami ne" tana kai nan ta haura sama
Saurin rikota nafee tayi tace "mekike fada haka kedin ce matar Shi"
"Kwaraiiiii da gaske seki tambayesa"
Sosai jikin nafee ke rawa tajawo wayarta takira Sadauki ta sheda masa Aljal kuwa ta haura sama,
A fusace ya shigo gidan dai-dai lokacin Da Ajlal tafito đakin ta yariko wuyan rigarta fuskarshi ba annuri yace "mekika cewa matata" Ajlal ta tabe baki tace mekuwa nace mata na gaya mata gaskiyar da ka kasa furtawa ne "
Tasss kakeji yawanke ta da Mari Sannan yaturata kan kujera wani uban kara tasaki lokaci guda jini yafara mata zuba wani irin juyi take ganin duniyar na mata
Hannun nafee yaja wadda jikinta yagama sanyi sukayi đakin Shi da ita, Ajlal kuwa da rarrafe ta isa kofa bata ganin abunda take takawa Har ta isa waje tana dagawa Mai gadi hannu yazo aguje yana salati dakyar tace masa Ina driver,
Asibiti suka nufa aguje yake tuki ganin halin da take ciki, suna isa aka karbeta bata sha wahala sosai ba ta haifo yarta mace kyakkyawa duk sadauki ce yar ba inda ta baroshi bayan ta huta da awa daya aka nemi ganin Mai gidan ta Ajlal tace komenene zatayi, Dama Zata saka hannu ne akan wata paper ba musu tasaka kusan awa uku aka sallameta bayan tasha tea dasauran magunguna,
Tashar mota ta nufa direct ta shiga motar yola ta bar garin su Ajlah,
Kusan 6 na yamma suka isa ta shiga taxi zuwa gidan su, ba karamun murna Abban ta yayi ba musamman ganin ta da jariri sedai jikin shi yayi sanyi ganin ta ita kadai,
Nan Ajlal Ke bashi labarin wuyar data sha agidan da irin wulakancin da aka mata harta haihu, ranshi yayi matukar baci yace lallai koda shine autan maza bazaki koma gidan Shi ba aure tsakanin Ku yakare yazo nan yabaki takardarki Ina jiransa...
Toh fah wata sabuwa inji yan caca
Muje zuwa ☆☆☆
Tic-Tac-Toe | ||
+ | + | + |
+ | + | + |
+ | + | + |
New Game |