SADAUKI ☆☆☆
N@ B ALEEYU
72...
Kansu tayo dasauri tana huci tana isowa Sadauki na jawo Aljal tafado ajikin sa yana lallashinta itakuma se Kuka take ganin hakan yasa nafee komawa baya, Sadauki yace "baby zan kai ta gurin mama ina ganin da matsala taki gaya min " nafee tace ayya kodai bakida lfy ne", Ajlal taki cewa komai se kukaj da take Wanda bashida dalili sadauki yaja hannun ta sukayi đakinta suna shiga yarufe ganbun đakin yajawo ta yace "ya akai kikayi haka " Ajlal tace inajin tawowar sune " sadauki yace thank you shona " after dress tasaka tareda karamun hijab, suka fito tamkar wasu sabon aure, Sadauki yacewa nafee Zan kaita gida myb in dade, Ajlal takara lafewa ajikin sa tace "Anty zakizo muje ne " murmushi nafee tayi mata tace no se kun dawo inada aiki ne sai kun dawo agaida mama" Ba Wanda ya Kula ta cikinsu
Wani shago yatsaya yayi siyayya Mai yawa Sannan suka dau hanya tinda suka shiga area corner din SADAUKI yafara wani iri, Ajlal na kule da yana yinsa musamman da suka iso dai-dai gate din seda yaja mugun birki yakoma baya, Ajlal tace lfy? um.. ahm... lfy Lau yabata amsa, slow-slow yake Jan motar har yayi parking, Ajlal tarike hannun shi tace "calm down namaka alkawari komai zai zo yanda kake so " "huuuuu yayi wani irin huci yafita motar
Fadar sarki suka fara zuwa bakaramun dadi yaji ba ganin su atare yasha albarka iri-iri Abunda yadade baisamu ba gun baban Shi, haka suka dunguma guri mama Ajlal ce rike dashi har parlon mama sun same ta tana cin tufa, kallo daya tamasa ta kauda kanta, tuni jikinsa yayi sanyi yazare hannun shi daga rikon da Ajlal ta masa yana neman fita waje, sake riko Shi tayi karo na biyu suka zauna kan carpet suna gaida mama,
Gaisuwar Ajlal dai ta karba tana tambayar ta ygd ya tsufa, sundade suna fira kamar batasan da zaman Ajlah a gurin ba, Ajlal ce ta soma cewa "mama Ajlah na jin yunwa " mama ta ballah mata harara tace "waye hakan shi bayada baki ne sai ke uwar son miji koh "
Ajlal ta karasa gun mama tarike mata hannu tace "haba mama Allah ma muna Mai laifi ya yafe mana bare Dan Adam tinda yagane kuskurensa yaka mata kiyafe masa kozai samu yagama da duniya lfy, kinsan fushinki akan shi babban bala'i ne tattare dashi komai nashi bazai yi albarka ba, na tabbata bazakizo ya lalace ba " takarashe zancen da muryar tausayi.
Sadauki yakaraso tareda haye kafar mama yana mata kuka, ganin haka yasa Ajlal shigewa bedroom,
Fada sosai mama tamasa daga karshe tamasa nasiha sosai takarashe zancen da kuka, bakaramun firgita yayi ba ganin kukan mama, aransa kuwa yadau al kawarin zai rike Ajlal tasakani da Allah zai soma raba musu kwana, gaban sane yabuga tunawa yayi da nafee ko ya zai fuskanceta da wannan zancen Oho gashi mama tamasa rantsuwa akan idan yakara cutawa Ajlal bata yafe masa ba dafe kan shi yayi dayake masa zafi, Ajlal kanta mama bata barta ba ta nuna mata hanyar dazatabi domin kwata mijin ta "koda ya manta dake kamar yanda fada bai zama hujja da zaki kyalesa ba dole ki jawo sa ajiki kina masa irin abubuwan da suka wuce a Hankali zai soma Tina ki, gashi har ya fara sauraren ki kinga kuwa ansamu cigaba acikin wannan damar zakibi ki Tina masa komai wani lokacin zaki iya fada da baki 'katina ranar munyi kaza Kayi me da me' wasu abubuwan kuwa basai kin fada ba zaki mai mata irin sune a Hankali zakiga yana tuna komai indai kinsa shi a hanya wasu ababen da kanshi zaiyi su", Ajlal tayi godiya sosai tana jin mama tamkar uwar cikinta,
Abunda sauran iyayen maza basa yi meyasa kike kishin matar danki, meyasa kike bakin cikin kiga danki yayiwa matarshi Alkhairi, bayan kina so ayiwa yarki, kisani matar danki 'yarki ce indai kin rikata da daraja tsakani da ALLAH duk Abunda tayi Wanda ba dai-dai ba kisata a hanya kijawo ta jiki kinuna mata yanda ake zama da miji domin kin fita sanin komai, kekuma kiga yanda zata rikeki uwa, wani lokacin uwayen miji su suke sakaci matan 'yayansu suna rainasu bakija girmanki ba yaza'ayi ta girmamaki, kekuma 'yar uwa Banda rashin kunya kina nuna miji nakine kisani uwar miji tanada daraja tinda ta Haifa miki miji ki girmamata tamkar uwarki duk Abunda kika samu kibata kirika nunawa mijinki muhimnancita idan yasiyo Dan nama ki gutsara a leda ki maita zaiji Dadi sosai Kuma zai yaba da hankalinki zaki Kara shiga ranshi sosai.
ALLAH yasa mudace
Muje zuwa☆☆
Tic-Tac-Toe | ||
+ | + | + |
+ | + | + |
+ | + | + |
New Game |