66...
Wayar Shi yake danna har motar tagama parking, yadau long time before ya fito daga motar, seda aka bude mishi Sannan yafito, wow na fada a raina real sadauki yadawo, sumar Shi nake kallo da aka yiwa gyara tamkar arjun kapoor, sanye yake cikin Riga da wando Wanda suka matukar fiddo da Shi, a gogon hannun shi Nake kallo Mai kyau, a hankali yasoma takawa zuwa cikin gidan.
Mama ce tazo dasauri tana murnar ganin sadauki tareda Anty maryam kusan duka families din gidan an hallara, murmushi kadai yake har yanzu banji voice dinshi ba, kabir ne yakai Shi dakin Shi domin yahuta, angyara dakin tsab, bedroom ya wuce yahaye gado yana Mai son kadaituwa shikadai,
Ring din wayar shi yatsayar dashi daga tunanin dayake, screen din wayar yake kallo daga bisani yadaga wayar baice komai ba se mutun dayake shimfide a fuskar shi, hello my cuddle boo, ya hanya hope ka isa lfy, yes yabata amsa tareda stinke wayar
Ajlal tagama shiri tsab tayi matukar kyau Zata Je dakin Ajlah mama ce takirata tana bata wani magani, sai gashi yashigo dasauri Ajlal tayi wulgi da robar magani taje tayi hugging din sadauki so tight, Sadauki kuwa se bata fuska yake, dakyar ya banbareta ajikinsa, yace thanks yajuya yana kallon faruq dayake mika masa hannu dasauri yadaga shi ma yana mishi wasa, duk suka bisa da kallo,
"Anty maryam yaushe kika sake haihuwa kin yi haihuwa Mai kyau boi din nan duk Ni yadauko ", "Anty maryam tace baka gane Shiba kenan Dan Ajlal ne, batareda yajuyo ba yace Waye Kuma Ajlal, Anty maryam tace gata nan a gaban ka"
Ok ban santaba Shi isa, "mama tace Ga iskanci matar taka zaka ce baka saniba", se alokacin ya yajuyo da mamaki a fuskar shi ya ajiye faruq kan kafar Shi yace "ban gane ba kamar ya matata yaushe Nayi aure wannan ce matata"? Daga mama har Anty maryam sunji wani iri barinma Ajlal da kwallah suka cika Mata ido, da gudu tashiga dakin mama tafada kan gado, Anty maryam ta rufa mata baya.
Mama ta kalli SADAUKI tace "yazaka rika wahalda yar mutane tin daka fara ciyon nan yarinyar nan take cikin kunci da bacin barai akan me zaka ce baka gane taba bayan ka gane kowa kokuwa ciyon naka na manta mace daya ne"
" Sadauki yace luk mama Nifa all I know is ban santaba banma taba ganin taba akan me zaki kakabamin ita wai harda babyn ta Dan kawai muna kama dashi, yana kai nan yasa kai yafita,
Wayar Shi yacire suka Soyy da nafee Sannan ya manta bacin ran daya Ke ciki,
Juyin Duniya anyi Sadauki yaki yardar dacewa Ajlal matar Shi Sam yaki aminta da hakan, sema zancen auren dayayi musu na nafee atake mama tayi rantsuwa bazai aure taba, Mai kyau ne ya katseta da cewa "insha Allah akan me zaki hana sa aure bayan sunna ne " mama tace wace sunnar ce tawuce wadda ya watsar wlh Allah indai Ina raye ban zaiyi auren nan ba,
Sadauki yagama kuluwa da mama "yace Toh shikenan indai har bazaku bari in auri zabina ba Toh wlh bazan taba yarda da waccan ba Kuma Zan bar muku garin inda bazaku kara ganina ba "
Mai martaba yace no soon zaka aureta Amma se in har zaka yarda da matarka , wani irin daci yakeji a zuciyar Shi a duk lokacin Da aka kira Aljal da matar Shi, dakyar yace zai yarda cos bazai iya losin nafee ba
" bawani shagali da akayi agidan mama taki sanar da kowa nata har yanzu kuma fushi take da Sadauki,
Karya sosai nafee tayi a wannan auren ba shagalin da ba'ayi ba biki kala-kala
Sadauki yakara gyara gidan tsab yacanza komai na parlor sedai Koda wasa baibi takan dakin da aka kira dana uwargida ba,
Alhamdulillah andaura auren Ajlah Muhammad da nafisa Ahmed, yar Babban minister a Abuja,
Ajlal Kuwa ta kode ta rame tayi bakikirin rabenta da abinci harta manta sedai asako Mata tabarshi a gurin mama da antiy maryam sunyi iyaa kokarin su taki hakura ga cikinta na bata wahala ga kuma faruq da mugun lakuwa, magani masu kyau kabir yake basa saboda haka baiyi komai ba sema kiba daya kara,
" kana jina Ajlah kasaka matarka agaba kaje da ita domin kuwa Babu uban dazai aje maka mace da Igiya uku a gida, Sadauki yace amma baba..... bai karasaba baba iro yace angama magana kuma wlh idan naji ance kana cuta mata nida Kai ne,
Bakin ciki kamar ya kashe sadauki yama za'ace randa amarya Zata zo yakoma da wata banzar, tsaki yaja yasa kiran Dan tanin bugu biyu yadaga, yace "Dan tanin kacewa yarinyar nan tafito Ina jiranta awaje" bai jira amsar Dan tanin ba ya stinke wayar.
UNDER MAINTENANCE
Pls cigaban sadauki
Tnks