65...
Sai da yazauna Sannan yasoma warware Nadia
fuskarshi! Aikuwa gurin yadau ihun tsoro aka
fara gudu wasu na take wasu atake taron ya
lalace, kasan cewar anzo da sojoji tuni suka
gyara gurin ta Han yar tsorata su da bindiga,
Deene kuwa dasauran mabiyanshi tuni yafara
kwara amai tsabar tsoro da firgici wannan wani
irin mafarki ne " mai martaba sarki Abdul
Azeez yayi gyaran murya yace, " Alhamdulillah!
Alhamdulillah! Alhamdulillah! dukkan godiya da
yabo su tabbata ga Allah (s w t ) Wanda
yakaddara mini rayuwa agaba nida đana Aakil,
Anan mutanen garin suka kara rudewa dan
kuwa Aakil tin gama makarantar gaba da
primary ya bata,
Yafito rike da Afham yana nunawa yan gari
yaron Shi, murna ba'a magana gurin jama'a
mai martaba sarki Abdul Azeez yafara bayanin
inda yake da yanda aka cecesa hannun Makiya
da irin wahalhalun daya sha shida yarshi Ajlal
dakuma Aakil, jama'ar gari sukayi ta Kuka suna
tsinewa wannan azzaluman daga karshe yamika
ta'aziya wa iyalan waziri
Aakil yayi gyaran murya yace Kuna so kusan
Waye wannan fajirin, baikarasa ba sarki Abdul
Azeez yace kuttt Karka fađa duniya ka horon
wawa, Aakil yace bai saurari zancen uban nashi
ba yace Deeni da uwarshi,
Tuni jama'ar gari sukayi Kan Deeni tsawa Mai
firgitarwa sarki Abdul Azeez yayi yace nace
kukyalesa ni aka zalunta Kuma na yafe masa
Dan cikina ne sedai Nayi Allah wadai da auren
uwarka da samunka a Duniya , "bana bukatar
kowa yataba Shi kibarshi yaje zaya gani Duniya
Zata koya mishi hankali " na koreshi daga
garina tareda mahaifiyar Shi da duk wani
wanda yake tare dashi bana bukatar dake Ganin
fuskokin su a yau
Har kusan dare Ana Abu daya daga bisani aka
watse dasafe sarki Abdul Azeez yakomawa
kujerar Shi ta mulki sedai mutaya Shi da addua
Tsab aka gama shirin Kayan SADAUKI za'aje
dashi Pakistan domin duba brain din shi
Sekuma kafar Shi dake digishi,
Ajlal manne dashi tana kukan zai barta, fuskar
ta ya tallabo yasa halshe ya share hawayen "
kawata kidena Kuka mana kinsan Allah yace
yana son Mai hakuri " Ajlal takara kankameshi
tana kuka, kabir ne yayi tari yace Ina fah kusa
kuke wannan abun, dasauri Ajlal tasake Shi,
shikuwa yakara riketa yana neman lips dinta
sun dade a haka daga bisani ya wuce, kabir
cike da mamakin Abunda yagani bashida
Hankali Amma yasan yataba mace, hmmm
Sati uku sukayi a can bayan an masa aiki, cikin
sa'a yadawo normal sedai sunki Bari yadawo
seya cika wata daya sun kara tabbatar da
Abunda suka gani, Kwance take tagama bawa
faruq nono zuciyar tane take jin tana tashi bata
Ankara ba taji amai yazo mata anan gurin take
feso a man, jekadiya dake parlor tazo a guje
tana tambayar lfy meke damun ki kasa amsawa
tayi sema faduwa datayi agurin tuni, jekadiya
tabi fuskar ta da goshinta da kallo ta ware ido
tabdi jam wata sabuwa,
Kusan sati daya tana fama da zazzabi tarasa
gane meke damunta,
Shiryawa tayi Don ganin doctor Sega kabir yazo
gidan zai wuce office yace bari yazo yagaida
su, jekadiya tace "me Zai hana ya dubaki basai
kinje can ba, Ajlal tace olryt bari in masa
magana,
"Kabir yace Dama bakida lfy ne"? Aljal ta gyada
kai ta soma yimasa bayanin abunda kedamunta,
nan ya bukaci data yi fitsari takawo masa, strip
ya fidda a jakar Shi ya duba ta yana murmushi
yace your pregnant fah, Ajlal ta ware ido na
shiga uku aruwa Zan sha cikin ne kome, kabir
yadago ido yana murmushi yace wazaki Maida
karamun yaro yanda na ganku dinnan randa zai
bar Nigeria ai dagani komai kunayi, jekadiya
tace bar muna fuka dakinshi fa take kwana,
gaba dai suka sa dariya banda Aljal dake
jimamin wannan cikin.
Yaune Ajlah zai dawo se Soye soye ake Ana
murnar dawowan sadauki wanda yasamu lfy
Koda wacce Zai dawo yanzu Oho.....
Muje zuwa
UNDER MAINTENANCE